https://www.facebook.com/profile.php?id=61567646455725 🌹RAYUWATA🌹 Story and writing *Bilkeesu Sa'eed Aliyu Ikara* 💞*Billy pinky*💞 ☀ NAZARI WRITER'S ASSOCIATION ☀ ▪GARGAD'I !!! 📢 Ban yarda wani ko wata su sauyamin labari na Dan wannan littafin Mallakar marubuciya Ne dan haka be careful. Wannan littafin nawa k'agyaggen labarine banyishi dan cin zarafin ki/ka inkinga yayi daidai da rayuwar ki/ka to alk'alamine🖊yazo da salonsa idan kuma kunci Karo da kuskure aciki kumin afuwa dan wannan shine littafina na farko dana fara wallafawa dan haka ba za'a rasa samun wasu kurakuren ba . ▪GUNDARIN LABARIN : ya kushin abubuwa da dama kamar : *Fadakarwa* 📢 *Nishadi* 💓 *Ilimantarwa*👌 *Tausayi* 😘 *Soyayya* 💘 Ku kasance tare dani a cikin tafiyar Billy pinky💞 duk a wannan k'ayataccen littafin me taken *RAYUWATA* Yah Allah inarokon ka da sunayen ka kyawawa masu tsarki, kabani ikon rubata abinda zai amfaneni nida al'umma. Ka tsareni rubuta abinda zai cutar dani da al'ummar MANZO ALLAH (s.a.w) .Yanda muka fara lafiya Allah yasa mu kammala cikin farin ciki 🌹 SADAUKARWA ga 🌹 _Oum Maryam _Aunty safiyya. _Hajara _Habibah BOOK 1 EPISODE 🌷 { 1 } 🌷 Sanye take cikin hijabi, light blue fuskarta sanye da nik'ab, idanunta dara_dara ga gashin idanunta zara_zara, ta cikin nik'ab dinta na hango dogon hancinta hannun ta rungume da alQur'ani kafarta sanye da safa da alama daga islamiya tadawo cikin natsuwa take tafiya bata wani yi tafiya me nisa ba ta karaso kofar gidan mai black gate ta tura kanta ciki tare dayin sallama cikin zazzakar muryarta. Tsakar gidan bakowa tsitt yake haka takara sallama akaro nabiyu amah shiru parlour tashiga bakinta dauke da sallama amma bakowa a parlour bata damu ba kasancewar tasan yazun haka sunacan suna bacci suna jiranta tadawo ta daura girkin. Cikin natsuwarta ta karasa bedroom din nanma bakinta dauke da sallama amma matashiyar buduwar dake kwance tana danna waya bata dago ta kalle taba balle ta amsa mata sallamar . Saida ta karasa tsakiyar bedroom din sannan tacire nik'ab dinta tare dazame Hijabin nata ta ninke tasaka a wardrobe Masha ALLAH shine abinda na furta gaskiya Allah yayi baiwa anan . Saidai ace Masha Allah Dan gaskiya kyakyawace ajin farko saidai kuma black bauty ce baza a kirata doguwaba bakuma za'a kirata gajera ba tsaka_tsaki ga pinkish lips dinta gaskiya idan nacemaku zan lissafomuku kyanta za aja lokaci dan haka nabaku dama kowa ya kiyastota dakansa. Cikin zakin muryarta tace '' anty Walida barka da hutawa '' . '' Barka '' abin datace kenan tacigaba da chat dinta itama batare datace komaiba tafita adakin madafa tashiga ilaikuwa ga wanke_wanke nan tun na safe amma ba aiba saboda suna jiran baiwarsu tadawo tayi ahaka cikin natsuwa tayi tagama tafara kokarin dora tukunya komai tatuna oho nagadai tafita daga ciki tanifi bedroom din Mom dattijuwar ce dabazata wuce shekara 47year zaune tana waya amma tana shigowa kuwq ta yanke wayar annurin dake fuskarta gabadaya yabace ko gaishe ta dayake bata amsaba tafara fadin '' lafiya kizo kitsayamin aka ? " tana mai kafeta da ido '' Dqma Mom zan tambayi me za'a dafane ? '' Saida ta kalleta sama da kasa kana tace '' wai sai yanzu kika dawo daga wannan kaddararriyar makarantar ? '' Tadaga kanta alamun amawa. '' Tindazu muna jin yunwa sai yanzu kikaga damar dawowa kenan? '' '' Ae yau Moma asabarne ba'atashi dawurine shiyasa ''. '' Karki damu zancire ki a makarantar ne dan bazamu iya zama da yunwaba sai Walida cema ta jika mana garin kwaki musha dan haka dolle ki hakura da ita '' . '' Dan Allah mom kiyi hakuri wallahi inason maranta ta ''. Mttsss taja tsaki kana tace da ita a cikin isah da gadara '' keni jeki jollop zaki girka mana dan yunwa nakeji bansan surutun tsiya ''. Haka ta juya ta tafi tana zuwa ta daura girkin ta kafin tagama ta gyara gurin yayi fes kamar ba wanda tashigo ta ganshi a haukace ba, wai daga jik'a garin kwaki shine akama guri haka Allah yashirya shine abinda kawai ta fada tana mai cigaba da aikinta .Bata dauki wani lokaci maiyawa takammala ta juye a kula sannan ta je tacema Mom takarasa tana wucewa daki bathroom tanshiga tayi wanka tare da daura alwala mafrib dan ta gabato .Koda ta fito bata ga Waleeda ba dan haka tasa rida doguwa mai dogon hannu mai taushi koda ta fito parlour Mom ce kawai ke cin abicin Walida kuwa ta cika tayi fam . Ta karaso domin itama ta zauna taci abincin dan yunwa takeji yau koh breakfast bataiba . '' ke '' naji an furta cikin isah da gadara. Ban zata koh Waye dani ake ba shi yasa ban dago ba. Amma a zayirin gaskiya ina sane cewar dani take shiyasa ban dago ba saida Mom tace '' wai safiyya ba dake ake magana bane? '' '' Na'am Mom '' na furta yayinda nake dago da kaina. '' Muna fuka kitashi k idafamin shinkafa dan na gaji da cin taliyarnan '', a cewar Walida ina niyar nayi magana Mom ta watsamin wani kallo ban ce komaiba natashi nafita nafara dafa mata ga yunwa na cina saida nagama dafa mata sannan naci tawa lokacin ma ta huce. Bayan nagama aka Kira mafrib na tashi domin na gabatar da sallah, koda na idar nayi azkhar. Walida Bata shigoba bale ince tayi sallah karatun alQur'ani nafara cikin natsuwa kowanne harafi ina bashi hakkinshi har akakira isha'i sannan natashi na gabatar da ita na dade ban tashi ba har Walidah ta dawo da alama waya take sanan nafita na yiwa Mom saida safe duk da bata kulaniba nadawona nayi kwaciya ta bayan da na karanto addu'o'in kwaciya barci........ My fans Dan Allah kuyi hakuri muhadu a page 2 karkumanta Kuna tare Dani Billy pinky💞 https://www.facebook.com/profile.php?id=61567646455725 💗 RAYUWATA 💗 ©️ Bilkeesu .S. Aliyu ☀NAZARI WRITERS ASSOCIATION☀ Kyawawan Nazari kafin rubutu na damfare da bin 'ka'idojin rubutu. Nazari kafin rubutu kan kayata duniyar Adabin hausa. 🖊️🖊️ Alkalami yafi takobi ⚔️⚔️ EPISODE : 🌷 { 2&3 } 🌷 ▪ Washe gari, 5:00 am Ta tashi tare da shiga bathroom, bata wani dau dogon lokaciba ta fito fuskar ta, ta jike da ruwa, da alama alwala tayi. Sallaya ta d'ako ta kabbara sallah ta dau dogon lokaci kafin ta fara rera karatun alQur'ani cikin zazzakar muryarta mai dadin sauraro tadau tsahon lokaci kafin ta aje alQur'ani tafara Azkhar kana tamike tare da ninke sallayar kana ta karasa bakin gado . '' Anty Waleeda kitashi ki sallah '', amma ko motsi batai ba . Takara Kai hannun ta da nifi Kara tashinta ta bige mata hannun tareda fad'in '' ke dan Allah tashi ki bani guri mutum na bacci kin ishi mututane in tashi in sallah to bazan ba '' . Mtss taja tsaki tare da jan bargo ta rife har kanta batare da tace komai ba ta tashi ta fita ta fara aikin gidan. Parlour ta fara gyarawa tareda share wa, sannan tayi mopping ta share tsakar gidan, wanki bayi tayi sanan ta dauraye kwanikan jiya kana ta daura breakfast kafin lokacin gari yayi haske bata dau lokaci ba ta gama breakfast ta shirya komai a parlour tana shirin shiga daki ta ji an kira sunan ta "Safiyya" Mom ce dake fitowa daga part d'in nata . "Na'am mom" ta amsa mata tana mai tsuguna wa ta gaishe ta. '' Lafiya kin gama aikin neh? '' "Eh mom na gama '' Ta fad'a cikeda natsuwa . '' Tom yau ba zaki barmu da yunwa ba mita jira har sai kin dawo dan haka ki soya mana miya idan yaso koni ce na dafa taliya tunda Waleeda ba girki ta iya ba '' a cewar Mom Kenan. '' Amma Mom lokaci zai cika kurewa kuma zayi lati ''. '' Iyye ina magana kina fadin lokaci zaicika kure wa, to wallahi in kiyi wasa makarantar ma sae kin barta inga ta tsiya '' . Mttsss ta ja wani uaban tsaki kana ta dora da fad'in '' dan Allah bace min da gani ''. Batace komai ba ta koma ta daura miya saida ta idar kana cikin sauri ta wanke kayan da tasan ta bata . Wucewa tayi bedroom shaf_shaf tashiga bathroom tai wanka ta fito daure da towel tana goge gashin kanta "Masha Allah" na furta ganin gashin ta har gadan bayan ta gaskiya tanada gashi mai cika da tsawo sae dai ace tabarakallah .Kaya ta saka ta shafa wani lotion mai kamshi amma na karamin kud'i ne, fauda ta saha iatama sama_sama sai kwalli da lips gloos kana ta fito parlour domin yin breakfas har a lokacin ba kowa a parlour. Tana kamallawa ta sake nufar bedroom , hijabin islamiyar ta ta dauko ta daura nik'ab a sama bayan da ta saka hijabe d'in tare da sa safa ta fiche daga gidan bayan da tayiwa Mom sallama . Batare da ko kallon arziki ta samu daga Mom balle tayi tsamanin zata amsa mata tayi tafiyan ta zuwa islamiya. Du da faruwar wannan abun, sam ban damu ba ina fitowa naci karo da baby '' anty Safiyya ina zaki ? ''. Da murmushi kwance a fuska ta nace '' zan tafi makaranta ne kinji my baby ? ''. '' Tom anty sae kin dawo '' yarinyar ta fad'a tana mai daga min hannu . Daga mata nayi ina mai karisa fita daga gidan . Kai tsaye makaranta na nufa dan sanda naje ma har anfara amsar hadda, zama nayi a kujera ta na tarar da Rumaisa kawata kusa da kujerar da nake zaune . Gaisawa mukayi tana mai cewar ''kai sopsy yau fa gaskiya kin makara da yawa ''. '' Uuhmm kedai bari kawai sis koh jiya dana fito da wuri koh breakfast banyiba ''. '' Tab kina kokari wallahi sis ''. Murmushi kawai nayi '' To yazan yi ?, ae sai haku na fad'a ina mai mekewa Naje nabada haddah muka cigaba da bita kasan cewar munyi sauka mai_maci ne mukeyi a yanzun . Koda aka tashi gida na nufa kaitsaye. Ba kamar jiyaba yau parlour da mutane, Mom ce sae 'ya'yanta suna fira cikin nishadi. Da sallama nashiga suka amsa ciki_ciki . Baby ce tazo da gudu ta rungume ni '' anty sannu da zuwa dama ina so zaki min home work anty Waleeda taki min ''. Nashafa kanta nace '' tom my baby bari naje ciki nayi wanka sai na fito koh ''. '' Yes antynah sai kin fito ''. Mumushi namata ina mai shigewa bedroom, wanka nayi nafito parlour dan in sami abin da zan sawa cikina .Kitchen nashiga amma ba komai da alama sun cinye taliyar da tace zatay daga dan haka taliyar yara na dafa shaf_shaf naci a kitchen din na wanke kwanikan dan wallahi yau ba wacce. zan ma girki ehe sae dai abin duk abinda zai faru ya faru ba ruwana . Ina fitowa baby tace '' anty gashi ''. Karba nayi na tayata yin home work d'in kana na wuce dakinmu. Wayyata na dauko na bude dan harna manta inada waya ma. Call ne ya shigo wayar Yaya Ansar sunan dake yawo a screen din wayar kenan . Cikin zumudi ta dauka murmushi kwance a fuskarta . '' Wa alaikas salm yayanah '' na amsa sallamar dayayimun. "Na'am my little sis yakike? ''. '' Lafiya lau yayanah yasu mom din? duk suna lafiya, Yaya yaushe zaka dawo'' ta fad'a a shagwabe . '' Kai little har kin kosa nadawo ne? ''. '' Yaya gaba daya na kosa ka dawo gidan duk ba dadi ''. '' Ummh yanzu kina inane? ''. '' Ina a daki ne ''. '' Har kin kamalla aikin ki ne halla ? Kici gaba da hakuri little kisan dai Mom tamkar uwa take agurin mu, dan haka kikara hakuri my little sis ''. ''.Tom yayah ae inayi ''. '' Nasani amma so nake ki kara akan wandda kikeyi komai a "RAYUWA" mai wucewa ne kinji ''. '' Tom yayanah insha Allah ''. '' Kinje islamiya ne a yau ? '' '' Naje Mom tace ma saita cireni a makarantar bayan kuma ba ita ta sakani a islamiyar ba ''. Ta karashe zancen ta kamar zatayi kuka. '' Kirabu da ita kawai tana fada ne insha Allah namayi kusan dawowa verry soon ''. '' Yaushe zaka dawo Yayana ? '' ta sake fada a wannan karon cikeda zumud'i dauke a fuskarta. '' Ban san ranar ba amma insha Allah nan kusa ne ina fatan hakan '' '' Tom Allah ya dawomin dakai lafiya yayanah ''. Da haka sukayi sallama tana ajiye wayar ta jiyo muruyar Mom na kwalla mata kira "Safiyya" . "Na'am Mom '' ta amsa tana mai fitowa dan ganin meke faruwa. '' Wai meye nufinki bazakiyi girkin bane koh me ? '' '' Anty Waleeda kaina ke ciwo yau bazan iya girkin ba ''. Ta lailayo wata ashariya '' ke har kin isah kice ba zaki girka mana abinci ba dan ubanki, to wallahi baki isah ba ''. Tana gama tijarar nata ta fice daga dakin. Ae kuwa tana fita nasa ma kofar key na saka karatu. Sama² na jiyo muriyar Mom tana sauke nata masifar dan har barci ya far daukana da alama yar lelen nata ce takai karana a gurinta '' Ina mara kunyar nan take bazaki bude kofar ba eyyye, lallai zaki sani karki fito ''. Tin inajin su har bracci ya kwasheni ban san yasu ka karkeba....... ____________ WACECE SAFIYYA ??? Sai mun hadu a page 4 Dan jin cikaken tarinhin Safiyya . 💗 RAYUWATA💗 Written and story by. Bilkeesu S aliyu. 🌸 Mallakar💋 💕Billy pinky💞 ✍️💖 AMANAR NAZARI WRITERS ASSOCIATION📚✍️ 📚🖊️ NAZARI WRITERS ASSOCIATION📚🖊️ _Kyawawan Nazari kafin rubutu na damfare da bin'ka'idojin rubutu. _Nazari kafin rubutu kan'kayata duniyar Adabin hausa. 🖊️🖊️ Alk'alami yafi takobi⚔️⚔️ Page••°°••4&5 "Safiyya A Ibrahim" shine asalin sunnanta . Malam Ibrahim dan kasuwa ne, annan cikin kaduna yake da zama, matar shi ta farko "Amina" wacce ake Kira da ummah. yar "Niger" ce, Tazo gurin yayarta N an cikin kaduna, su fara soyayya har yakaisu ga aure, "Amina" (ummah) , Iri buzayen "Niger" ce kyakyawace ajin farko kon dai san , Buzayen Niger da kyau . sun kai shekaraka uku basu sami haihuwa ba, Danginshi suce lallai sai ya 'kara aure, shikuma bashi da niyar aure, yace Allah shi zai basu haihuwa, Amah haka suyi ruwa suyi tsaki kafin ya amince zanyi, acikin Dangisu akwai wacce take son, shi wato "Zuwaira" Ita abashi akasha biki, Bayan biki baifi da wata biyu ba, Sai ga "Zuwaira" da ciki, wacce ake Kira da mom, sunyi farin ciki sosai, to daganan Zuwaira wato (mom) Wulakanci iri_iri takema ummah shi Wai juya, na yau da_ ban na gobe da_ban, duk wannan abin da ake malam Ibrahim wato(abba) Bai saniba, kasancewar ummah akwai hakuri, Ana cikin haka sai ga ummah da ciki, ranar missalta muku farin cikin, da "malam Ibrahim" ya shiga 'bata lokacine, da wasu daga cikin danginshi, Ummah matayi farin cikin sosai dan tahuta da gorin da ake mata na haihuwa haka antyn ta , Iyayen ummah duk sun rasu, daga ita sai umma halima yayarta kenan, umma halima tana da yara uku da _Yaya saif, _anty hajara, _buhaisa, Auta kenan itace sa'ar "Safiyya" Haka suyita rainon cikin su, har Allah ya sauke su lafiya, mom tariga haihuwa, ta haifi yarta mace, ranar suna yarinya taci suna Waleeda, Ansha suna lafiya, Ummah dai nada tsohon ciki, bayan suna da wata daya lokacin ma tayi arba'in, Ummah ta haifi d'a Namiji, ranar suna yaro yaci suna "Ansar" shima dai ansha suna lafiya, masu farin ciki nayi, masu ba'kin ciki nayi, Haka dai akai suna aka tashi, washe gari umma halima da yarta Anty hajara sukai suyar hakika, Suma dai suka tafi gida, Saidai fatan Allah yah kai kowa gida lafiya Ummah ta samu ciki, yafi so biyu amah mom tana zubar wa, kuma ba wanda yasan itake zubar wa, tunda Bokanta ne ke bata maganin, Wai ita haushi takeji ta haifi namiji ita kuma mace, (bayan duk kyautace daga Allah, amah mutane suna mance hakan, duk Wanda Allah ya bashi 'ya'ya mata, ya bashi hallitta mai tausayi, hallitta mai jinkai, hallitta mai cike da hakuri, Allah yasa mudace, ameen🙏) Haka taita ma ummah, sai daga baya sanda ta samu cikin Safiyya, ba wanda yasan tana dashi, sai abba da umma halima, har saida ciki yayi girma sanan, Mom ta gani, Aikuwa ta shiga tashin hankali, sosai Ta garzaya gurin malaminta, Yace mata ai yanzu ciki bazai zubeba yayi girma sosai, Saidai kafin yarinyar tazo duniya su kashe ta tun tana aciki, Yabata wani magani da zata na samata abinci. Ko abin sha to dayake Allah ba azalimin bawansa bane, ummah batacin girkin ta saidai in ita tayi, da Kanta , Har Allah ya sauke ta Lafiya, yarinya taci sunan maman abba wato,"Safiyya" Ummah nakiran tada Mami , Duk da haka mom Bata hakura, ba abba yana matukar son safiyya, yana kuma ji da ita, kasan cewar sunan goggon shi taci. Amah Saida mom ta shiga ta fita taraba su da mahaifinsu, Dan ko gidan yadawo suna zuwa gurin shi zai korasu, yaran mom kuwa yana jidasu sosai . Amah duk da haka matar nan, bata hakura ba sai da ta rabasu da farin cikin su, Dan kuwa tashi sukai aka nemi ummah sama da kasa bata, Gashi lokacin safiyya tana yarinya, dan bata Wuce shekara 6year ba, Ayi neman _anyi neman Amah shiru, har Niger anje amah bata, dama umma halima da mijin tane akan koma, Dan shi abba ma baidamu ba, Kamar ma ya manta da ita a matsayin matarshi, Haka akayi neman ummah akarasa, Bata ba labarin ta, ummah halima tashiga tashin hankali sosa,i yar uwar ta guda daya tilo da tarage mata, Itama tarasa ta, haka Yaya Ansar kamar hankalin shi zai gushe, Ayita mishi magani, sannan asami kanshi, Ko "safiyya" dake yarinya abin ya doketa , Amah mom ko ajikin ta da taga kamar za'a zargeta, Shine tasa baki harda Dan kukan ta, Ummah halima taso amsar "Safiyya" abba da yace yabata, amah mom tayi ruwa tai tsaki, saida abba ya amso ta, Wahala iya wahala yarannan sun shata tun "Safiyya" tana shekara bakwai 7 aikin gidan gaba daya, Ita keyin shi, tun tanayi tana kuka, harta saba, ya zame mata jiki, tun asuba take tashin ta da ruwan sanyi, In Yaya "Ansar" na tayata, shima takawo masa nasa,koka d'an Bata bari ya tayata aiki, makaranta ma, Mijjin ummah halima ne, Yasa su suda su buhaisa, da 'yar abba ya yadda, nan ma dan ance za'a had'ashi da hukuma ne shiyasa mom ta barshi, ya yadda, Harzu kuwa jami'a ,ba Abin da za suce, masa sai Allah yasaka masa da alkairi, Mahaifin da ya haifesu, ya kasa tallafar rayuwar su, 'ya'yan mom kuwa, sai makarantar dasu zaba, Komai nasu da namu ya ban_ban ta hatta gurin kwana, Tufafinsu, abincin su,abin shan su, komai nasu ya ban_banta Daga baya ne ma, dasu koma sabon gida, kanwar mom ta bata shawar ta hadasu daki daya da Waleeda, Kar mutane su zargi wani abun, shine yanzu suke daki daya, Amah badin Waleeda taso ba, Gidan ummah halima kuwa, saidai ta saci hanya, taje in ta dawo ta zane ta, Amah yanzu ta waye, duk wanda ya daga mata yatsa, a gidan saita karya shi, mom kawai take ragawa, wataran, Dan koba komai ta haifeta, sai abba tayi sati ma bata ganshi ba, Ita yanzu mom yaranta uku . _Anty waleedah, _Yaya safwan, _Sai baby, Ita kuma ummah yaranta biyu. _Yayah Ansar, _Safiyyah, Yanzu haka Yaya Ansar yana aiki ne a Abuja, ma aikacin banki ne, "Safiyya"kuma tagama makaranta, mass communication takaran ta, kuma tasa mu aiki yanzu haka, wani program suke gabatarwa, fannin islamiya kuwa tayi saukar hadda, Shikuma Yaya safwan, yana aiki anan cikin kaduna, itakuma anty Waleeda har yanzu aiki take nema, amah bata samu ba, Dan ita gaba daya halin mom ta dauko Wannan kenan✍️ Sai mun hadd'u a page 6 danjin yadda zata kaya😅 🌹RAYUWATA🌹 Story and written✍️ ©️ Bilkeesu .S. Aliyu 💞(Billy pinky)💞 07070260240 WhatsApp number or call 📚🖊️ NAZARI WRITERS ASSOCIATION📚🖊️ Book 1 EPISODE 🌷 {6&7} 🌷 Edited Cigaban labari.... Washegari. Karfe hudu na asubah, 4:00am ta tashi ta fara gyaran gidan, kasancewar yau Monday, zata gurin aiki, Kiran sallah farko tagama aikin ta, bedroom tanufa, Kasan cewar anty Waleeda yau ba adakin ta kwana ba, Saboda jiya ta rife kofar, Bathroom tashiga tafara wanka tare da dauro alwala, sanda ta fito ma anshiga sallah dan haka, agurguje ta saka riga, tafara sallah, koda ta idar azkhar tayi, karatun alQur'ani tafara, cikin zazzakar muryarta, cikin natsuwa, Kowanne harafi tana bashi hakkinshi, Bayan ta idar ta tashi ta soya musu miya, kamar dai jiya,kana tayi breakfast, har lokacin ba wanda yafito, bedroom Takoma p L a gurguje, body spray ta fesa da humra , Tsaf tashirya cikin abaya baka mai sulbi Wadda aka mata ado da jajayen dutsina masu sheki, Ta nannade tulin gashinta, tayi acuci da shi, simple Make up tayi, ta daura agogo na fata baki sai plate shoe mai jane da bakaken igiyoyi, sannan ta dauko gogaggen Hijabin ta milk colour, Tasaka tare da face mark, da eyeglasses, Masha Allah, "Safiyya" tako ina Allah ya mata zubi da tsari, Wanda yasanya take burge mutane ba maza kawai ba hatta ga 'yan uwanta mata ma, sai dai gonar miskilanci ce, sam magana bata da metaba, muryarta sanye take dawani irin sirri, wanda idan tai magana take dauke hankalin mai saurare, Cikin sand'a tafita a bedroom din tana leqa cikin parlour, bakowa dan haka cikin sand'a ta fice a gidan, nappep ta tare tare da fada mishi inda zai kaita, bayan yak kaita ta bashi kudin shi, ta wuce ciki , office dinsu ta nufa kai tsaye "Aisha" Tasamu a office din oyoyo "Aisha tafada tare da rungume ta, yaudai nariga ki zuwa Umm Wai duk saurin Nan danayi saida ki rigani zuwa? amah insha Allah gobe saina rigaki, mukullah Mr hijjab cewar "Aisha"tana miko ma "Safiyya" hannu sasanyan murmushin ta tayi itama tana mai miqa mata nata hannun, atare suka saki dariya, Ni kiga bani guri in zauna duk kin isheni da surutun ki, au sis haka zakicema , Murmushi kawai tayi tana zama agaban computer, Wai nikam "isha" ina aikimu na wacan satin ne? Kin manta ba yana gun "MD" ba oohh my God, wallahi na manta. Amah kinga bari inje in amso dan aikwai abin da ban gama, Tafada tana mikewa har takai kofa ta dawo Face mark dinta ta saka da eyeglasses dinta kana ta fice, Itadai "Isha" kai kawai ta gir_girza ta cigaba da abin da take. Cinkin takunta na nutsuwa da yanga da mutane da yawa suke fassarawa ta fito, Duk wanda ta gamu dashi takan daga masa hannu da fadin, Good morning wasu sukan tsokaneta, Iyakarta murmushi kawai dan in baka zauna da itaba ba zaka tabba tunanin tana da surutu ba Sam. Batacika yawan magana ako inaba saidai in ita taga damar hakan, shiyasa dayawan mutane kan daukarta shiru_shiru har wasu kan daganata da hakan a iya yardarsu. Basu saniba in aka tabota batada ragi Sam. Koda takarasa office din "MD" PA ce tace ta shiga! da sallama ta shiga office din, yana zaune, idon shi arufe amah yanajin sallamarta ya bude idonshi tare da yin murmushi, harkin karaso? Umm barka da safiya sir, tafada ba tare da ta amsa masa Question din shiba, Fatan kintashi lafiya? Lafiya lau! ta amsa mai tana mai kai zaune a kujera, Ina fatan dai lafiya? Nazo amsar aikin Dana kawo maka ne wacan satin! Okay, Dubawa yashiga yi, Daukowa yayi ya bata ta amsa tafice a office din, Da kallo yabita harta fice kana ya maida idanunshi yah lumshe, Itako tana fita ta ballama office din harara tare da jan tsaki, mutum sai kallon tsiya, Kai tsaye office ta nufa bata tadda "Isha" Aciki ba dan haka tafara aikin ta, Har "Isha" tadawo sunayi suna hira, Ahankali sauran members din office din suma suka shigo, Kasancewar su biyar ne acikin office din, Aka gaggaisa, Kowa yakama aikin gaban sa, Bayan takammala tanufi office din MD Knocking saida takai minti daya sanan ya bata izinin shiga ciki, Kallo daya tai masa tadauke kai, Kasancewar shidin me shegen san kalan mutane kamar zai cinyesu. Cikin san kawar da kallon dayake mata yace zauna . Zama tai adda _dadare tare da fadin good afternoon sir. Atakaice yace how are you? baijira amsarta ba yace kin gama? Yeas sir, nagama tafada tana mai mikashi takardun , Amsa yayi ita kuma ta Mike tafita, office takoma ta karasa abin da yarage musu sanan, Su wuce itada "Isha a motar ta, har kofar gida "Isha takaita sanan sukai sallama. Da sallama tashiga gidan cikin zazzakar muryarta, amah bakowa atsakar kidan, A parlour na iske dukka mutanen gidan amah ba yaya "Safwan da abba. Sai anty Waleeda da baby sai mom. Mom ce tawa tsomin wata muguwar harara, dayasa ni tacin face mask din na turo mata baki Mom good evening Koku good uwarki,dariya anty Waleeda tasa min itako baby tana ta home work dinta kamar ma batasan me akeyiba, Tsawa ta dakamin kan nazo a hankali na nufi gabanta ina kaiwa kasa, ban ma gama kaiwa qasaba ta shinfidamin wani lafiyayen mari daya gigitani dan har eyeglasses dina Saida ya fadi. Rumtse idanuna nayi hawayen daya cikasu nai kokarin mayarwa Dan bana so nabasu damar zubowa. "K Dan uban uwarki harni zan saki aiki kitafi sabgar gaban ki ki barminshi?" Karo na farko na dago na kalleta, ina Mai kokarin danne kukan dake kokarin zubo min, wallahi mom ban tafiba saida nagama komai. Miyar daki bari akan wuta uwarki ce tai fatalwa tazo ta karasmin. Rumtse idanuna nayi ina Mai jin wani takaici ba Abin dana tsana irin inji mom na zagin ummah bana iya daurewa sai na maiyar mata. dan haka yanzu ma cikin kaushi murya nace. Mom kunsha tabarraki kenan dan kisan komai yafito daga hannun ummah ta mai albarka ne. bare kuma kince fatalwa ai albarka ma saitafi. Bari inje in sallah inkara rokon Allah in zata dawo gobe har abinci ta kika mana ba iya miyaba ma. Ba mom kawai ba hatta anty Waleeda ma sakadde suyi suna kallo na. niko ko a kolar rigata na Mike tsam ina Mai nufa bedroom din mu Wannan kenan✍️ https://chat.whatsapp.com/CiFQHB3CNkRJ8gmX6banlC *🌹RAYUWATA*🌹 *Story and written*✍️ *©️Bilkeesu .S. Aliyu* _💞 (Billy pinky)_💞 *🤝🥰Amanar nazari writer's association*📚 [07070260240] *WhatsApp number or call*📱 *📚🖊️ NAZARI WRITERS ASSOCIATION*📚🖊️ Book 1📖 *EPISODE*🌷8️⃣▶️9️⃣🌷 Inashiga daki kukan Dan banyi agaban suba ya kufcemin. banyi zaman yi saba cire kayana nashiga bathroom, domin in wanka sai da na wanke bathroom din sanan nayi, alwala nayi nafito nasa ka doguwar rika mara nauyi pink coluor mai gajeren hannu, Sallaya na shinfida nafara sallah bayan na kamalah azkhar nayi tare da karatun alQur'ani da dazu banyi dayawa, Saida a Kira isha'i na gabatar da ita, kana na idda karatun alQur'ani danake, nadade ina addu'a kafin na mike nacire hijjab din na maida cikin wardrobe, Dan kwalin rigar na yafa na fito parlour, suna zaune sai kallo suke abin su ana shewa kamar ba 'ya da uwaba, da'alama ko sallah ba wacce ta tashi tayi, Dan nalura mom sai taga dama take sallah ,tom itama anty Waleeda haka take, Ba wanda na kula na wuce kitchen dan daukar abinci na, amah wayam da alama yauma ba abinci na, gashi dare yayi dan wajan karfe Tara tama wuce, fitowa nayi duk da irin yunwa da nake ji amah na hakura da abincin, da harara duk suka bini har na shiga bedroom din, gado na fada hawaye na zubomin, inda ace ummah na gidan nan bazata barni naje gurin aiki na dawo na kwanta banci abinci ba, yah Allah duk inda ummah take Allah katsaremin ita Allah yah sa tana cikin farin ciki da kwanciyar hankali ameen yah Allah. Duniyar tunani nafada na kara jin sautin yasa nasan Yaya Ansar ne, cikin zumudi na dauka barka da dare yayanah, Yauwa little sis yakike? lafiya lau yayanah! kaifa? lafiya! Maiyasa mekine naji muryarki wata kalane uhm? Yaya ba komai kawai dai natuna da ummah ne nafada hawaye na zubomin. Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi, kana yace kiyi hakuri. muciga ba da mata addu'a ahalin yanzu ita take so agaremu, kuma insha Allah tana cikin koshin lafiya kinji. Tom yayanah Allah yah sa. ameen yah Allah Little sis, Tom ya gurin aiki komai yana tafiya daidai ko? Wallahi Yaya komai lafiya ! ya naka kuma? Alhamdulilah.masha Allah haka akeso ai. Okay da kudi agurin ki yanzu? eh Yaya! akwai, Tom zasa miki wasu saboda gurin hawa nappep, ko cin abinci, Duk da nasan ko Babu bafa da min zakiba, Kai yaya Allah akwai, Amah nagode Allah yasaka da mafificin alkairi yayanah, Ameen little sis. Kije ki kwanta dan kisan gobe da wuri zaki tashi ko. Tom yayanah sai da safe, Allah yah tashemu lafiya, ameen yah Allah. Bathroom na shiga na dauro alwala, nai nafila raka'a biyu sanan nai addu'a na kwanta. _______~~ Washegari...... Kamar dai kullum yau ma hakance ta kasan ce karfe hudu 4:00am Na tashi nai duk wani aiki danake bayan nagama tsaftace gidan, na daura mana breakfast, kiran sallah farko na kamalla duk wani abin da zanyi, Dan har wanka nayi yau nai alqawarin wallahi ba zanyi musu miyar ba, saidai inna dawo su tsireni, ai saima mutum ya gaji da cin abicin miya, Dan haka alwala na dauro , ina niyar tada sallah natuna anty Waleeda adakin ta kwana, karasawa bakin gado na yi ina tashin ta amah ko motsi, koma tana jinane oho danaji ana niyar tada sallah nima nafara raka'atanul fajir, san nai sallah bayan na idar nai azkhar kana nasake tashin anty Waleeda amah ta'ki tashi daga baya ma sai cewa tai na ishe ta, kyaleta nayi, nafara karatun alQur'ani ban wani dau lokaci mai nisa ba natashi nafara shirin fita aiki. Cikin atamfa orange da ruwan ganye, dinkin riga da siket ne da fatan din atamfar ai kwalliyar rigar, sai shuwaris da akasa ka. Simple Make up nayi danko iyakar fauda, sai kwalli, da lips gloos, da maskara, da na taje eyelashes dina dashi, aifa ya fito gadar_gadar masha Allah, dan kwali ta daura saida yadan zame kasancewar gashin daya kwanta luf_luf a goshin ta. Parlour ta fita tai breakfast, har lokacin mutane gidan basu tashi ba, suna can suna baccin asara. Gogagen farin hijjab nasaka da face mask da eyeglasses sai plate shoe shima orange, ina shirin wayana na dauka ina Shirin fita sai ga kiran Yaya Ansar murmushi kwance a fuskata na dauka. ina kwan yayanah? Antashi lafiya? lafiya lau, har an shirya kenan? eh yanzu ma tafiya zanyi dan har nasaka hijjab. Okay natura miki kudin, saiki ciri ki aje saboda kudin transport Tom yayanah Allah yah saka da alqairi, Ameen, ki tafi karki makara, tom Yaya bye_ bye, Allah yah tsaremin ke, ameen yah Allah, Atm nadauka dan dama bawani kudi agurina sosai, nasaka a hand bag ta fita, su anty Waleeda suna ta shara bacci harna tafi, Nappep na hau muce. Inazuwa nabashi kudin shi na shige ciki.yau dai nariga "Isha" zuwa, Kasancewar yau inada gabatar da program banfi zaman minti talatin ba mu fita nida mukhtar, Munfita yatsaya shida mu'az kyalesu nayi nawuce sai dana gaishe da kowa kafin na tsaya nadan gyara fuskarta a agaban mirror san su shigo. Haka bakon mu nayau yashigo tuntuni Dan haka muka fara gabatar da program din. Yauma kamar kullum "isha ce takawo ni har gida, mun dade muna fira a mota kasancewar yau ba tazo da wuri, Sannan nashiga gida. bakowa a parlour dan haka kai tsaye bedroom na wuce, anty Waleeda ce kawai aciki tana kallo, Amah nai sallama Bata dago ta kalleniba bare insa ran amsawa, Kaya na cire nashiga bathroom, saida na tsaftace shi sannan nafara wanka na dauro alwala na fito, Kaya nake sawa saiga anty Waleeda agabana, sai masifa takemin wai natafi ban musu miya ba. Inda ace mom ce zan iya kyaleta amah anty Waleeda ko bata isaba, tunda bata kama girman taba, Umm banyiba ke meyasa bakiyi ba oohh ashefa baki iyaba ko nafada cike da rainin hankali, Ke harkin isa kizo kinamin aka_aka, saiku bari waccan ita tasani. Tazo tai magana amah wallahi badai keba ke asuwa, Ni_ni "Safiyya kike cema haka?" Anfada mikin ai baki ja girman ki bane shiyasa ttwws. naja tsaki ina barin guri naje na fara sallah inajinta ta fita tana kuka, Bansan me tace ma mom dinba ai sai gata a sukwane, ina kiki shegiya, yar gidan mayya, yauzan ga uban da yatsaya miki agarinan, inajin ta tagama zage_zagen ta, har na shafa addu'a. Sanan nace wallahi mom niba shegiya bace dan kin sani da ubana wallahi. Idan kuma ni shegiya ce to wannan ta kusa dake ma shegiyar ce. Nafada ina nuna Anty waleeda, Kuma wallahi uwa ta ba mayya bace saidai ko ke kinsan mayar data lashe kurwar abba, da ummah da haryanzu ba asan yadda takaita ba. Ina gama fada nashige bayi na rufe kofar, na basu baki sake suna kallo na. Ni kikace ma mayya har kike cewa nacinye kurwar ubanki ko to wallahi uban naki zai dawo, Za kisan uban wa kikawa sharri shegiya kawai, ga shegiya Nan agabanki nafada ina mai murguda baki daka cikin bayi. Kwafa tayi su fice itada yar tata...! ______________________________________ ______________ ABUJA.........✍️ _Sai mun hadd'u a page {10&11} danjin yadda zata kaya_🥰 https://chat.whatsapp.com/CiFQHB3CNkRJ8gmX6banlC *🌹 RAYUWATA* *Story and written✍️* *©️ Bilkeesu .S. Aliyu* _💞(Billy pinky)_💞 *🤝🥰 Amanar nazari writer's association*📚 [07070260240] *WhatsApp number or call*📱 *📚🖊️ NAZARI WRITERS ASSOCIATION*📚🖊️ _Kyakkyawan nazari kafin rubutu na ɗanfare da bin ƙa ido jin rubutu_ _Cikakkyan nazari kafin kan Ƙaya ta duniyar adabin hausa_ Book 1 📖 *EPISODE* 🌷🔟▶️1️⃣1️⃣ 🌷 *Nnamdi Azikiwe international airport Abuja* Jirgin daya taso daga Dubai yayi landing a Abuja. Cikin natsuwa duk wani passengers dake ciki sa suka fara fitowa. Vvip section Tsaye yake qam akan tsahonsa na tsayeyen namiji da babu ko rankofawa. Suite din jikinshi da basai an zauna bata lokacin lissafin kudin da suka lasheba. sun masifar zauna masa da tabbatar dashi a matsayin jarumin sa mai gara kan nera duk yadda yaso bisaga damar da Allah yabashi. Komai na jikinsa ba'kine sai d'an adon takalmishi da yake Pink da neck tie d'insa shima pink Mai azabar kyau. Agogon hannun sa kirar diamond, kamilalliyar fuskarsa Ma'abociyar kamewa da tsare gida a tsuke. Sai kwantaccen kashin kumatunsa siriri daya zagaye bakinsa zuwa hab'arsa kamar anzana da biro Wanda yaje har gaban goshinsa kwance luf_luf, fari ne tass. yanada manyan idanu wanda Kwayar idonsa ta kasance blue, sai taswirar hallitar kyawu hancinsa daya zauna daram kan kyakykyawar fuskarsa. Girarsa cike take da gashi dan sun hade girarsa guda daya kamar an tsagata. wanda bai saniba tuni ya sakashi ajerin larabawa, tuni kamshinsa ya baje wajen. Cikin nutsuwa, Kamala, haiba,nagarta yake saukowa daga matakalar jirgin. Body guys d'insa biye dashi *Abdulmajeed Abubakar saraki* Kenan. Gaba daya mutane dake gurin kallo ya koma kanshi, wasu suna sakashi jerin larabawa, tuni wasu su sakashi a jerin India wa, jerin motocin na alfarma da sukazo tarbashi gabaki dayansu bakakene sai ta tsakiyarsu wacce take fara dukkan su dauke da tambari, cikin sauri daya daga cikin yaran nashi ya bude masa ta tsakiyar tare da matsawa suna rissinar da kansu kasa, yana shiga su rufe kofar suma duk shiga tasu suyi sufara sharara gudu a titin kamar suka dai ne a titin, da anga tambarin motar asan waye mamalakinta, Kai tsaye *MAITAMA ESTATE* Suka nufa basuyi wata tafiya Mai nisaba, suka tsaya agaban wani irin gida gidan daya amasa sunan shi gida, haka kuma gidan da kyawunsa yadarama dukka gidajen, duk dacewa gidajen naka mancece niya da juna, amah duk yafisu tsaruwa, Idanu nasake warewa tabbatar da cewar, glass din danaga yana budewa get ne ko akasin haka, Batare da nagama tinanin ba, Motocin suka kutsa kansu ciki, Wanda hakan ya tabbatar min da cewa get ne. *WELL COME TO THE AA SARKI HOUSE* Shine ke rubuce asaman makeken gidan da manyan baki da mai kalar gold, Ajere motocin duk suka shiga makeken compound din da Sam bai da iyaka ga Mai kallo, kowace ta tsaya a muhalin da akeson ganinsa. Dolene kashigo wannan gida ka tsarkake sunan UBANGIJI mai rahama mai jinkai, danshike samarwa aduk sanda yaso akuma lokacin da yaso. Ginine daya ginu da karkashin makundan kudade da Sam zaka iya rantsewa da Allah ba'a Nigeria kakeba idan kana acikin sa. Dan iya compound kawai da abin dake zagaye da gidan, da kallon ginin a tsaye ya isa tabbatar maka nera tayi kuka, Wani irin dunkulalen ginine mai mutukar armashi da kayatarwa. Ga wasu irin ciyayi da furrani masu mutukar kamshi da sanyaya gida da 'kawatashi da sukaima ko ina ado. Da wasu jibga_jibgan motoci cikin wasu rumfuna kusan guda biyar ajere daga can nesa sosai. Wasuma rufe suke da tempol, sosai ma'aikatan ke Kai_kawo, Dan dole wanan gidan yanada masu kula dashi ta ko wanne fanni, Dukan su fitowa sukai cikin sauri su nufi wannan farar motar cikin sauri daya daga cikin yaran nashi ya bude masa motar tare dukkan su rissinawa sukai, saida ya dauki minti biyar kafin ya ziro kafarshi waje, Mai dauke da bakin takalmi, nanma ya dauki tsawon lokaci kafin ya fito gaba daya. Cikin nutsuwa, Kamala, haiba, nagarta, yake tafiya har yazo bakin wata hadaddiyar kofa mai wani irin zubin kyau da kowa ya kalla yasan ansiyeta da kudade masu yawa. Abude masa da sallama ciki_ciki yakara sa hadadden parlour dake matsayin main parlour komai nacikin sa atsaftace yake ga 'kamshi da sanyin ac amah ba kowa a parlour sai television dake ta aiki. Parlour na biyu yashiga, daya kasance kata faren gaske, haduwar parlour ba'a magana Dan ya 'kawatu 'kawatuwa ta mussaman. Komai sai kyalli da daukar ido yake tamkar ba'a talauci aduniya. Shima dai kamshi yake na mussaman, Sai kafar bene daya kasance mahadar sassan gidan uku. Gashi katan gaske bana wasa ba, dan duk da set din na kujeru biyar a cinkin sa, zama a iya kawo wasu group_group na kujerun guda goma batare da sun matsu juna ba. A hankali dattijuwar matar dake zaune a kujera 1sitter da laptop agaban ta da tun shigowar shi ta ture laptop din murmushi kwance a fuskarta da kin ganta kinsan tana cikin tsan_ tsar farin ciki. ADaganita kasan ba bahaushiya bace, dan farace sosai gashi sunyi matukar kama sosai, zan iyacewa ma komai nata ya dakko, Your welcome my son tafada tare da tashi ta nufeshi. A hankali ya lumshe idanun shi, yasaki murmushin gefen baki wanda inba kura mashi ido Kaiba bazaka gane yayiba, kamar wanda aima dole yakara sa ya rungume ta, "my son! atare su saki ajiyar zuciya, kana lafiya ya hanya? " ammiii! yafada cike da shagobba yana dagowa. "Na'am my son! Alhamdulilah. Nake kufa? Lafiya lau. Tafada tana kama mishi hannu. Wats kyakykyawar yarinya ce kimani shekara 21 kamar su daya dake saukowa daga upstairs, Tana zuwa karshe taja birki "yaya Majeed" tafada da karfi mamaki kwance a fuskarta, ai dagudu tak'araso ta rungume shi "Yaya majeed I miss you Soo much! Tafada tare da sake rungume shi, Humm trouble maker can't you see, just one month, ai ba dadewa nayiba. Uhmm "yaya aj aganinka ba kinjifa ammii tafada cike da shagobba, rabu dashi kinji auta, kinga tafiya yayi. Yauwa ammii nah baran nai wanka sai na fito, yafada cikin nuna alamun ya gaji da maganar, haurawa sama yayi Baiyi tafiya mai tsayiba, yakarasa wani katafaren part, Wanda gaba dayan shi glass ne, agaban kofar shiga ya tsaya itama 'kofar ta glass ce amah ba'a iya hango abin dake ciki, saidai na ciki yah hango na waje. Wani Abu ya matsa da hannun shi atake kofar tafara budewa, Yana shiga ta rufe. Wow shine abinda nafurta ganin tsaruwar part, gaskiya zama lissafomuku kyau dakuma haduwar shi za'aci lokaci dayawa amah nabaku damar kowa ya k'iyasto da kansa. Amah komai na ciki Pink and white ne sai Golden colour. Iya tsaruwa part din ya tsaru, gawani kamshi na mussaman dake tashi Mai sanyaya zuciya, Dasa nutsuwa. Kayan jikinshi yah rage sanan ya shiga bathroom ruwa yatara acikin bathtub, Kana yashiga ciki. Wanka yayi ya fito daure da towel, da wani kuma a hannun shi yana goge kwantaccen kashin kansa wanda ya sauka har zuwa gadan bayan sa, zuwa na kumatunsa, Close d'insa ya nufa daga can kusuwar bango ya danna wani ma balli atake adon wutsiyar wardrobe din, dake ta dai_daita ko ina ya shiga nade kansa. zallar gilashi garai_garai da hasken sa kesa a iya ganin komai dake cikin wajen ya bayyana. Kayane na alfarma matsu kyau da tsada. Bai dade sosai ba ya fito sanye cikin riga da wando farare tar nashan iska. Kan sofa dake kusa da gadonshi ya zauna tare da daukar waya, Dane_dane yadanyi sanan ya kai wayar kunnen shi ka kawomin laptop. Shine abin da kawai yafada ya yanke Kiran. Ba'adau sawon lokaciba aka Danna belt remote ya dauka ya danna kofar ta bude, yana shigowa kofar ta rufe cikin nutsuwa yace barka da hutawa. yafada yana aje masa laptop din. Hannu kawai ya daga masa, shikuma ya fita Laptop din yafara sarrafawa cike da kwarewa. Ya dade yana aiki da laptop din wayar sa tafara kara "Ammii" sunan daya fito a screen din wayar kenan. Murmushi yayi kana ya kai wayar kunnen shi, "my son mekake ne wai adaki har yanzu baka sakkoba kayi lunch. Sorry "ammii nah" natsaya wani aiki ne amah ina gamawa insha Allah zan fito. Aa kaida kafito kayi lunch in kagama saika karasa kaji "my son" okay "ammii" ganinan fitowa yafada yana rufe laptop din, waya kawai yadauka ya fito..........✍️ Sai mun hadd'u a page {12&13} danjin yadda zata kaya🥰 🌹 *RAYUWATA*🌹 *Story and written✍️* *©️ Bilkeesu .S. Aliyu* _💞(Billy pinky)_💞 *🤝🥰 Amanar nazari writer's association📚* [07070260240] _WhatsApp number or call_ *📚🖊️NAZARI WRITERS ASSOCIATION 📚🖊️* _Kyakkyawan nazari kafin rubutu na damfare da bin'ka'idojin rubutu_ _Nazari kafin rubutu kan kaya ta duniyar adabin hausa_ *Book 1* 📖 EPISODE🌷1️⃣2️⃣▶️1️⃣3️⃣🌷 Yana fitowa kaitsaye dining area ya nufa "Ammii da auta ne kawai akai, shima kujera yaja kusada Ammii. Abinci ne kala_kala da abinsha bayan sun gama ne, sudawo parlour suna fira shiko "majeed yana aiki a laptop kadan_kadan yake samu su baki, 'Yan matan gidan ne suka fara shigowa masa sannu da zuwa, Daga baya ma tashi yayi zai fita, My son inazuwa? Ammii zanje ne nagaida granny! okay adawo lafiya, Allah yasa "Ammii nah _________________ ___________ _____ *Kaduna....* Suna fita nafito daga bayin karatun da banyiba na dau alQur'ani zanyi, Saiga kiran "Buhaisa" Sis Na'am" 'yar gidan mom yakike? kedallah bansan iskanci! ta ina nazama 'yar gidan mom din? Sorry sisi nah kece ai dole a kiraki yar gidan mom din ai, Ummm ni rabuda ni da zancen wannan matar dan Allah! Yaushe zaki shigone kinsan dai mu wannan matar ta rabamu daku, Saidai ku kuzo badai muba. Humm zan shigo insha Allah sis karshen week dinan, akwai labari ne? Ai ba acewa komai saidai kin shigo din kwai sisi nah! Tom ki gaida min da ummah da anty hajja. Tom Insha Allah yaya saif din fa kokin manta dashine aa wllh, kawaidai nayi fushi dashine, amah saidai nazodin . Okay Allah yah kaimu please kizo da wuri. Insha Allah. Allah ubangiji ya yarda. Ameen" Ahaka muyi sallama karatun nafara ban dadeba a kira sallah isha'i na gabatar da ita, Na dade ina addu'oi kafin natashi, ina niyar hawa gado Dan nasan yau banida abinci a gidan. Jiyama da miyar ce kawai ban karasaba ban sami abincin ba balle yau da koyi banyiba, To Allah yah taimake ni abincin dare ba damuna yayiba. Shirin hawa gado nake aka bankado kofa, kina inane mara kunya? Abba ne ke wanan hargagin dagani an daurashi ne a keken bera shikuma ya hau ya zauna, Ni tsayawa manai ina kallon shi dan rabon Dana ganshi ma, Maybe nakusa one week, Barka da dare abba nafada in mai rissinar da kaina kasa, Barka da ubanki, wato kedai "safiyya bakida kunya koh? yanzu har Zuwaira zakicewa mayya, harda ta cinye Miki uwarki k haba alhaji zama zakai lissafamata abinda takai koko zaka dau matakine akanta ehhh Tafada tana mai katse abba. Jikinsa har rawa yake tsabar tsoran ta, ya nufoni da bu-la-la wai zai dakene, harda ka farfasa mata jiki tunda ita ta girma sai rashin kunyar tsiya, Sumar tsaye nayi ganin da gaskefa abba dukana zaiyi, Bawai yaune dukansa nafarko ba amah na yaudin yami ciwo. bansa sanda wasu zafafan hawaye su zubomin ba. Ba zato_ba-tsammani naji shigar bu_la-la ajikina, wata gigitacciyar kara nasaki ina mai guduwa, amah abba baiji tausayi na ba haka ya biyoni, danaga yana shirin illatani itakuma bata da niyar cewa yabari, na shide bayi ina mai rufo kofar . Abba da buga kofar yake kamar zai ballata, Amah inajinsu naki bude musu. Suka karaji fadan su da bugawa daga baya mom tajashi Suka fice. Kukane ya kufcemin inajin wani tikukin yana tasomin a zuciyata, haka nayi Mai isata natashi wanka nasake yi nagasa jikina, Kana na fito 10:30pm Nagani dana duba agogo, konciya nayi cike da kewar ummah nafada duniyar tunani, Kiran Yaya Ansar ne ya katsemin tunani na, Bandauka ba saboda basan yin magana kwata_kwata Har tagaji tayanke, Tunanin na ture nai addu'a na kwanta. Tunani yahana ni bacci dan haka nayo alwala nafara nafila nashiga kai kukana gurin Allah. Kana nafara karatun alQur'ani. nade sannan anty Waleeda ta shigo dawasu yan iskan kaya da kallo nabita dan da alama batama lura daniba, jakarta tacillar gefe tada gado kamar wacce tayo shaye_shaye nadade da lura anty Waleeda kamar ta kauce hanya amah bana son abinda nake zargi yazama gaskiya, Rufe alQur'ani nayi tareda nike hijjab na gyara mata kwanciya na kwanta tareda be kwanciya bacci. Washegari... Ban tashiba sai karfe bakwai dan yau nai alqawarin ba abinda zanyi agidan ko shara kuwa. Wanka nayi na dauro alwala, sallah nayi dan yau na makara sanan nashiga kitchen nasa ma cikin wani abu har time din gidan shiru ba wanda yatashi. ciki nakoma Tsaf nashiya cikin less pink da ayi kolliya da purple nasaka hijjab purple, sai facemask, da eyeglasses, kana na daura agogo sai plate shoe shima purple, jaka na dauka da waya, nafita ba wanda yatashi anacan ana baccin asara, Nappep na hau mu wuce, kudinshi nabashi nashiga ciki, sisi nah! Tsayawa nayi dan yau kwata_kwata banaji na dai_dai Lafiya kuwa kike sis naganki wani iri kamar wacce tayi kuka? Lafiya muje ciki kawai nafada mata ina murmushi, Koda mushiga bata sake tambaya taba saboda lura da banason magana. Fadaila ce tazo wai MD na nemana yinai kamar basan me take cewaba kamar mai bacci, Kice masa bata jin dadine ta kwanta! Okay! tana fita, Yaya Ansar ya kirani time dinma bacci ya daukeni dan wani azabeben ciwo kaina kemin ga zazzabi ya nashirin rufeni, Wayar "Isha ce ta dauka bayan sun gaisa tace masa banajin dadine na kwanta, Subhanallah! Tasha magani? Ciwon me take? Ya jerowa "Isha tambayoyi ajere, Yaya ciwon kai ne amah Tasha magani, Taimai karya dan tayi_tayi tasha ta'ki Dan "Safiyya" kwata_kwata batasan magani shima yasan hakan shiyasa ya Tambaya. Idan ta tashi kice takirani, Insha Allah yaya! Baijira amsarta ba ya yanke kiran. Karfe 2:00pm saiga MD har office din nasu, meyake damunta ne ya tambayi "Isha" good afternoon sir, Bai amsaba dan MD miskiline, shiya wasu ma har anfara kus_kus Sir ciwon kai ne! Tasha magani? Aa taki sha! Okay ki tasheta ki kaita gida, tadawo Monday. Okay sir! "Safiyya tafara k'okari tashin ta, A hankali na bude idanuna dasukai min nauyi, nasauke su akan MD wanda shima ni yake kallo, Cikin san kauda idonsa akaina yace ya jikin naki? Ai ciwon kai ne amah yayi sauki, Okay zata maidaki gida, monday inkinji sauki saiki zo. Magana nake shirinyi ya katseni ta hanyar dagamin hannu Program din Thursday koyi ranar Monday, Allah yakara sauki. Yafada yana ficewa daga office din Ameen na amsa akan labba. Sallama muyi da sauran muka fito, Mota mushiga naga tadau hanyar gida anguwar rimi zani fa kawai mu wuce. Okay Yaya Ansar yakiraki fa kina bacci yace kikirashi inkin tashi tana mai mikomi wayar. ________Abuja_____ *AA SARAKI HOUSE* Kaitsaye bangaran granny ya nufa cikin takunsa na 'kasaita, nutsuwa, gamida Kamala, shima dai part din saidai ace Masha Allah dan iya tsaruwa shima ya tsaru, Tsohuwa mai ran karfe tana zaune digir_gir tana dama fura yashiga da sallama ciki_ciki, furar ta dakata da damawa baki sake take binshi da kallo, Har gabanta yaje ya dukursa yana mai zare ludayin, aikuwa tadawo duniyar data lula waikaine "Abdulmajeedu" luuuu yayi da idanun sa yace uhm meye na firgita granny nine Mana. Yana mai tsauke ajiyar zuciya, Yaushe ka shigone Wai? Dazu! Yabata amsa yana mai kafeta da ido, sannu da zuwa kadawo lafiya? Tana mai shafa masa Kai, lafiya lau granny! Masha Allah "Larai Na'am hajiya" Zoki mikomin kofi, Tom...........✍️ *🌹 RAYUWATA 🌹* *Story and written✍️* *©️ Bilkeesu .S. Aliyu* _💞(Billy pinky)💞_ *🤝🥰 Amanar nazari writer's association📚* *[07070260240]* _WhatsApp number or call_ *📚🖊️ NAZARI WRITERS ASSOCIATION📚🖊️* _Kyakkyawan nazari kafin rubutu na damfare da bin'ka'idojin rubutu_ _Nazari kafin rubutu kan kaya ta duniyar adabin hausa_ *Book 1 📖* *EPISODE🌷1️⃣4️⃣▶️1️⃣5️⃣🌷* Daga wani korido ta fito alamun kitchen ne hannun ta dauke da flet da kofi, Har kasa ta tsuguna barka da dawowa babban mutum, Barka mama! An dawo lafiya? Lafiya! Daga haka bai sake cewa komaiba, Itama tashi tayi Takoma kitchen, furar tazuba mishi yanasha tana janshi da fira iyakaci yace uhm, koh a'ah itace amsar. Waini fatee yaushe zaka samo matar aure ne yaro yazama gon same-me, amah ace ba mata 'yan mata dayawa na sonka amah ka zauna ruwan ido, to wallahi karkabari raina ya 'baci dan dakaina zan nemoma mata akoye, Shima bukar din shida azma take ko azima sun zubama ido tunda karfin su kafi koh, Yaro sai shagobba tsiya kaje ka kanan nade mata ajiki kamar Kaine auta, umm kwafa tayi tana kallon shi a dole an'bata mata rai. Karo na farko da yasaki wani murmushi har hakoransa su fito masha Allah shine abin da furta, Har granny saida tasaki baki tana kallon shi, Tashi daya ya gintse fuska, yana wani kan_kance ido to granny ina ruwan kine uhm kinemo matar mana kiga inba'a aure taba, Ke tsohuwar nan saisa ido, yafada yana Kai kofin furar bakinshi, Baki tasake tana kallon shi wato nice tsohuwa mai sa ido, koh? kai badin 'yan matan gidan nan basu da ta ido ba ai acikin su zan zabama, amah na kauyen sunfi ta ido, Aciki zan nemoma zakuma kagani, Saida ta kai aya tashaki nufashi tana mai zuba mishi harara. Bai karacewa komai ba batun uhm. Yacigaba da shan furar shi hankali kwance, To ya dubai din komai lafiya? Lau! Sallama akayi daga kofa shigo mana Tafad'a tana gyara zamanta, wani dattijo ne kimanin shekara 50 ko sama da haka ne yashigo, Fuskarsa kwance da murmushi, Au audullahi kaine da ranan nan? saida yakai zaune yace nine hajja barka da rana! Yauwa barka! Majeed andawo kenan? Eh uncle dazu nadawo! Okay ya hanya andawo lafiya? Lafiya! Yafada yana tashi aa ina zuwa kuma granny tafada tana kallon shi, Lokacin sallah, yafada yana nuna agogon dake daure a tsin-tsiyar hannun sa. Ajima zaka dawo ne? A'ah! Madarar kafa? Akawomin part dina, Baijira amsarta ba ya fice daga part din, Ta wata kofa yabi saigashi a b'angare shi, Bathroom yashiga baifi minti talatin ba ya fito jikin shi da laima, Alamun alwala yayi close d'insa ya shiga ya fito sanye cikin riga da wando blue. Ko waya bai dauka ya fita kai tsaye, masallacin dake gidan ya nufa, Bayan ya fito daga masjid dine suka fara gaisawa da uncle's d'insa, Uncle abdallahi Uncle sulaiman Uncle kabeer Bayan sun gama gaisawa, kai tsaye part din granny su nufa shikuma ya nufi part din "Ammii" Na farko ba kowa aciki Dan har tv akashe yake, Dama kai tsaye main parlour ya nufa shiko duk 'yan matan gidan suna ciki, Kasancewar yafi ko ina tsaruwa da 'kawatuwa, yasa sunfi zama a cikin shi kowa na harkokin sa wasu na waya, kafin lokacin dinner yayi, Da sallama yashiga ciki_ciki ba wanda ya lura dashi a cikin su, Saida yazo tsakiyar parlour hankalin su ya dawo kanshi, gaba daya kowa ya shiga tai_tayinsa, har masu wayar denawa suyi, Barka da dare "yaya "Majeed su hada baki gurin fada, Saida ya gama binsu da kallo sannan yace ina "Ammii" Ya fada yana tsare auta da ido, yaya tana sama, okay! Kai tsaye sama ya nufa, ______________ _________ ___-_- Kaduna... Harzan kirashi na fasa dan nasan ina fada mishi zaice na koma, Shi zaizo nikuma bansan ya baro aikin shi ya tahonan, Wai dan Allah sis meye tsakaninki da MD ne? Umm sis kenan idan akwai ai kinsani maybe ma kin fini sani! Ni bawata alaqa tsakanin mu face na matsayin sa MD, da muke a karkashin sa, Umm haka dai kice sis amah wallahi MD sonki yake, da kan shifa yazo duba ki Dan ance bakida lafiya, Umm ni rabudani dazancen MD can mishi, Dariya "Isha tayi tace can muku dai ke dashi". Nima murmushi kawai nayi ban sake cewa komaiba har muka iso anguwar rimi, Abakin get ta tsaya au bazaki shiga bane ko gaisa da buhaisa? Eh gobe idan nadawo gurin aiki zanzo! Tom kigaida min momy, Nafada ina fita daga motar hannu na daga mata, ina kara sawa bakin get din shiga nayi bayan baba mai gadi ya budemin. Aa malama safiyya ce yau a gidan namu? Murmushi nayi tare da gaishe shi ina karasawa cikin parlour da sallama, anty hajara ce kawai aciki, Waya take batama lura daniba saida naje kusa da ita nazauna ina mai daura kaina acinyarta, Wayar ta aje cikin mamiki tace, "Safiyya meya faru? gurin aikin fa? Anty kaina ke ciwo! Umm wacce matar dai ko? bance komaiba, itama haka, sai kama hannuna tayi muka nufi sama, Muna shirin shiga bathroom ummah halima ta fito, Wanake gani kamar safiyya? itace wallahi ummah, ato gurin aikin fa? Ummah kinsan halin dai waccen shegiyar mata ai, Eh kuma hakane kuje dakina inazuwa, Kitchen tashiga ta hado tea mai zafi sanan tashigo dakin. Sakko kisha tea din saikisha magani, kadan nasha, maganin ko saida naga bacin ranta sannan nash, Dan a rayuwa natsani magani da allura, kwanciya nayi anty hajara tafita, Haka bacci ya daukeni. ________ ____ A b'angaren MD kuwa bayan yatashi daga office kaitsaye gida yanufa, Mommy ce kawai a parlour ganin yadda ya shigone yasata cewa suraj lafiya kuwa? Mom lafiya lau kawai dai ba najina dai_dai ne, Amah wani abu ya farune? Aa mommy bakomai! Tom shikenan kaje Kai wanka kafito muyi dinner, Da tom kawai ya amsa ya wuce dakinshi, Wai metasa bazaki Fahimta bane ina sonki, Wata zuciyar tace kawai kafada mata, Aa bazata amince ba Yarinyar akwai zafin Kai, To ya zanyi yafada a hankali alamun zancen zucine ya fito fili, "Yaya ya zakayi mene? mineet da mommy ta aiko takirashi, sunji shi shiru tafada tana karasawa kusa da Yaya nata, Bakomai! Haba yaya ya zakace bakomai batin naji kana tambayar zakai, Mineet nace bakomai aa yafada cikin tsawa Kai yaya Allah yabaka hakuri kazo mommy nakira, Tana fadar haka tafice, Zuciyarta na tunanin meya batawa yaya "Suraj raine, Shiko MD tana fita shima yatashi yayi wanka, sannan ya fita Parlour, Dad dinshi sai mommy da mineet ne kawai a dinning area din, suma da alama sun kusa kammalawa, Barka da dare dad, yauwa barka Suraj yau baka fito dinner da wuriba, Dad nadan kwanta ne shiyasa, Amah da magrib dinan zaka kwanta Suraj, Kinga kyaleshi maybe baya jin dadi ne kisan daga gurin aiki yake, Okay hakane, Yauwa mommy kawai kaina ke ciwo, Okay gama kasha magani kawanta tom, Mineet dai kalon su tayi dan tasan ba ciwom kai bane, Amah koma mene zata tayashi addu'a (Ayya MD fa yakamu ga safiyya💃 mu bata masan meyake ba) _________ _____ B'angarena kuwa tunda natashi ba kowa adakin, dan haka wanka nayi kozan ji karfin jikina, Nama manta dakin ummah halima nake, saida nabude wardrobe zan dau kaya, Natina fita nayi kaitsaye dakin buhaisa na nufa, ina shiga ta rungume ni sis kin tashi kenan? Tun dazu zan tasheki ummah tace kar wanda yatadaki, Umm ciwon kaine fa kuma ya sauka, Haka dai kice sis kije kishirya ki fito mi dinner, Okay! Doguwar rigar buhaisa nasa dayake tsawon mu daya, Tayi min dai_dai amah takama ni kasancewar nafita kiba, Sallah nayi na danyi karatun alQur'ani sai a azkhar, Buhaisa ce tashigo Tom ustaziya inkin idda kifito ke muke jira, Hararar ta nayi wace ustaziya? Kemana tanada fada ta fita dagudu tana dariya, Murmushi nayi nima na bita, Duk ahalin gidan na zauna a dinning area amah banda dady, Tun daga nesa Yaya saif ya zubeni da ido ko 'kiftawa har naja kujera na zauna, Ina dagowa naga niyake kallo, Nasan za'a rina dan naji alamun ana kallona, Harara wasa na mishi ina turo bakina cikin shagobba naceYaya uhm! kallon fa, Murmushi kawai yayi yacigaba da cin abicin shi, Kasancewar ba Wanda yajimu sai buhaisa da naga tana dariya kasa_kasa, Har ummah halima tace lafiya buhaisa ko duk murnar ganin safiyya ne? Kai tadaga tana kallona nikuma na harareta, Haka dai mu gama cin abicin, Mu dawo parlour ana fira, Waini "safiyya meya hadaki da matar can ne? Duk abinda yafaru na fada mata har dukan da abba yamin, Waikina nufin har yanzu malam ibrahim na dukan ki, Ato gaskiya bazai yiwuba bazata saboba ya karyamin 'ya a alhaji yadawo, Matar nan dai batada da Imani tarabani da yar uwata kuma so take tarabani daku, Sai kuka, Ya Allah duk inda 'yar uwata take Allah yasa tana cikin koshin lafiya, Allah ka baiyana Mana ita, Da ameen duk muka asa danni yanzu nasaba, Kinzo gidannan kenan in Allah ya yarda, Kuje ku kwanta dare yayi kusan zaku fita aiki, Saida "Safe muyi mata mutashi mu fita Dan anty hajara ma ta tafi daki, Muna zuwa nayi alwala kwanciya bacci, ina addu'a buhaisa kecewa waike meye tsakaninki da Yaya saif ne? Saida na shafa nace ikon Allah wani Yaya saif din? Yaya saifu mana kokina nufin bakiga irin kallon da yake miki bane, Ummm nashiga uku ni safiyya waikeda "Isha meke damun kune wai, Nafada ina kallon ta............✍️ _(😎 To ga yayah saif ga MD da alamufa Yaya saif naciki koya zata kaya🤔)_ https://chat.whatsapp.com/CiFQHB3CNkRJ8gmX6banlC 🌹 RAYUWATA 🌹 Story and written✍️ Bilkeesu .S. Aliyu 💞(Billy pinky)💞 🤝 Amanar nazari writer's association📚 [07070260240] WhatsApp number or call 📚 NAZARI WRITERS ASSOCIATIONS📚 EPISODE🌷1️⃣6️⃣▶️1️⃣7️⃣🌷 Meye na kirawa kanki shiga uku? Dan ance yaya saif din na sonki, Umm bazaki gane bane wallahi sis, Me Ishan tace mikine? Barzancen kawai! Wallahi baki isaba saikin fada, Murmushi nayi tare da cewa, San gulma to basai kinji ba, Haba sis please kidafamin mana, Umm wai MD take cewa sona yake, Dariya tayi inma hakane_inma-bahaka bane munriga shi ehhee, Tafada tana fari da iddo, Nima murmushi nayi tare da addu'a konciya bacci, naja blanket na rufe har fuskata, Saida safe, Allah yakaimu lafiya, Wai kin kira yaya Ansar kuwa, Ohh my God nafada ina fitowa daga bargon, Waya nadauka zankira shi dare yayi sosai, Sis kibari kikirashi gobe maybe ma yayi bacci, Umm hakane kuma Allah yah kaimu goben lafiya. Ameen! ______--------______ Zaune take a kujera bedroom din nata alamun waya take, Koda majeed yashiga Bata yankeba, Shima da alamu yagane dawa take wayar, Zama yayi kusa da ita yana daura kanshi a cinyarta, Wayar ta cigaba dayi tana shafa sumar kanshi, Sallama take da Wanda suke wayar, yazare wayar yana kaita kunne shi, Barka da dare papa yafada kasa_kasa, Banji abinda nacikin wayar yake fada, Naga dai yayi murmushi wanda inba ka kura mishi iddo ba bazaka gane yayiba, Papa Allah yakaimu lafiya, Shine abinda ya furta basu wani dade ba ya ajiye wayar gefe, Muje kayi dinner! "Ammiii ya Kirata cike da shagobba, "Na'am" Auta taje ta amsomin Madara ta aguri granny, Yau bazakai dinner bane? Uhm zanyi wani aikine, Tom Allah yabada sa'a ka kwanta da wuri kagaji dayawa, Insha Allah, Yafada yana gyara kwanciyar shi acinyar ta tare da lumshe ido, Yana haurawa sama azima tace auta yaushe yaya Majeed yadawo ne? Dazu taba ta amsa lafiya! Ooh a'ah bakomai! Okay, Auta nabarin gurin ta dakko waya, Can gefe takoma da alamu waya zatayi, Hello zaituna, Banji me aceba daga can b'angare ba, Tace albishirinki, Shiru tayi, Can kuma ta kyalkyale dariya, Yaya majeed fa yadawo, Shiru tayi alamun tana sauraren ta, Ke nima ban saniba yanzu na ganshi nake tambayar auta, Ki kwantar da hankalin ki sai goben kyazo, Shiru takuma yi tana murmushi, Tom Allah yah kaimu goben, Daganan ta yanke wayar takoma parlour, Su cigaba da fira, Majeed ne ya fito alamun masjid zashi Dan isha'i ake kira, Barka da fitowa yaya Suka hada baki gurin fada, Hannu kawai ya daga musu ya fita a parlour, Kai tsaye masjid ya nufa, Kasancewar masjid din acikin gidan yake, Bayan ya fito kai tsaye part din shi yanufa, Kamar yadda yabarshi haka yake saidai da alamu angyara shi dan kuwa sai kamshi yake, Bai tsaya parlour ba yawuce bedroom yadade sannan ya fito parlour, Hannun shi ri'ke da waya da laptop, Zaune yakai kan sopa yana daura laptop din asaman cinyarshi, Lasa keypads din laptop din yake, cike da kwarewa, da alamu wani aiki yake Mai mahimmanci, Wayar sace tafara vibration alamun shigowar kira, Kamar bazai dauka ba can kuma maiya tuna yadaga, Shiru yayi, Okay, Subari ma hadd'u gobe, Shine abinda ya furta yana ajiye wayar, Yayi nisa a aiki saiga auta nan, hannun ta rike da karamin tire mai d'auke da jug, sai mug da cukali karami Da sallam ta'karasa parlour bai d'agoba yadai amsa mata sallamar ciki-ciki har tak'araso, Tabble din dake tsakan kanin kujerar dayake ta dari tire, Barka da hutawa yah majeed, Hannu kawai ya daga mata, Guri tasamu ta zauna tana kallon wani Indian film da akeyi, Zubamin madara ya fada batare da ya d'agoba,, Mikamai tai data zuba akaramin mug tabashi, Kana takoma tacigaba da kallon tana satar kallon shi kadan_kadan, Tunda yaga ta zauna yasan akwai wata kasa, "Auta Na'am" yayah,, Mekiki bukata ne? uhm, Kusa dashi tamatsa tana murmushi, "Yah majeed waya nakeso asanja min, Uhm saimai? Account dina yayi kasa tafada cikin shagobba, Uhm saime? Shikenan! Okay kifada ma "Yusuf kalan wacce kikeso kudin kuma zan miki transfer, Thanks yayanah,, Madara takara mishi ta fice daga part din, Fuskarta dauke da murmushi, Shima murmushin yayi ya cigaba da akinshi, ________---------_______ 💗💗💗 Kaduna B'angaren ummah halima kuwa, Koda dady yadawo tafada mishi cewa yayi, Ganina bai kamata safiyya tadawo gidan an yanzuba sbd yanzu ta girma ta mallaki hankalin ta, dole bakomai za'a sassauta mata bakamar daba, Kuma dudu saura kwana nawa tai aure, In Allah yakawo nagari, Baikama ki ri'ka Sagar mata da gwiwa ba, Yarinyar akwai hankali da hakuri kinsan kuma duk mai hakuri a RAYUWAR Nan bazai taba faduwa ba, Kikara kwantar mata da hankali kinji, Hakadai ummah halima ta hakura dan taga hakan shine dai-dai, Around 8:30 safiyya ta farga kasancewar dama ta tashi tayi sallah komawa tayi, Gefen ta takalla ba "Buhaisa kana takai kallon ta ga agogo, Ido tazaro tana durowa, Kai tsaye bathroom ta nufa, Sanye ta fito daure da towel, Da karami a hannun ta tana goge gashin kanta, Dan Safiyya batasan kitso kwata_kwata Wardrobe ta nufa ta dakko bakar jallabiya, Tasaka, Kana takarasa gaban mirro lotion, kawai ta shafa sai kwalli, da lips gloos, Fita tayi kanta ba dan kwali sbd ta wanke kan tanaso ya bushe, Ummah halima ce kawai a parlour ganin yadda tafito ne yasata sakin baki, Wato ke safiyya har yanzu baki dena barin kannan naki ba kitsoba, Kuma bana hanaki zama ba dan kwali ba koh, Ummi wanke kan nayi shiyasa nabarshi yasha iska, Okay bari buhaisa ta dawo saikuje kitso "Ummii" tafada cikin shagobba, "Na'am please basai naje ba tana rausayar dakai, Shikenan jekiyi breakfast kannan ya bushe sai na tufkemiki, Uhm kawai tace tanufi dinning amah badin taso ba, Bayan tagama tafara tufkemata ummi please kimin kalba next week sai buhaisa tarakani amin kitson Dan Allah, Uhm Allah yashirya ki da wanna halinaki bari na miki kalba Amah ki tabbata anmiki kamar yadda kifada, Insha Allah ummi! Har tagama mata suna fira, Takuma fadamata yadda suyi da dady, Ai bakomai ummi nifa nasaba da halinsu, Hakadai takara kwantar mata da hankali da sake yimata nasiha.. kitchen su shiga ta tana tayata aiki kasancewar masu aiki basa musu girki, _________ B'angaren MD kuwa Koda yaje gurin aiki da murnar ganin safiyya amah sai ya tuna ya bata hutu fah, Hakadai ya aikin ba nutsuwa Allah yasama dai taji sauki, yafada yana shafa fuskar shi, har sutashi gurin aiki yana tunanin ta dan haka kai tsaye gidan su yanufa, Daya dade da sanin sah, Ya dade bakin get din kafin ya aika yaro akirata, To inta fito me zance mata uhm meyasa yau bakizo gurin aiki ba, kai aa kawai nazo dubaki ne yesss shikadai yake surutun shi har yaron ya dawo wai gatanan, 1k yaba yaron shikuma yatafi kusan 20 minutes saiga anty Waleeda ta fito acin mayafi da da dauri, Bai lura da fitowar taba saida ta kwan-kwasa glss din motar, Budewa yayi tare da fadin baiwar Allah lafiya, Cikin yau'ki tace bakai ace kana kirana ba, Ooh sorry safiyya nake nema, Dan inkin shiga ki turomin ita, Kallon sama da kasa tamai mai ooh ka Bata ai banan bane gidansu, Kallon rashin fahimta yabita dashi ai naga kuma nan gidan, Kai malam nacema bannan bane haba tafada tana kama hanyar koma gida rai a bace, Mamaki yakama shi to amah ai naga dai Nan ne gidan yafada yana kara kallon gidan, Hakadai yaja mota ya tafi badin yaso ba, Zuciyar shi cike da kewarta, __________ Yayah saif ne yafara dawowa sai anty hajara, Buhaisa karshe lokacin tuni sunyi dinner itada ummi Dan har baccin rana ma tasata tayi, Bayan kowa ya shirya su fito parlour suna fira yayah saif shima yadawo daga massalaci, Shima zama yayi ana hirar dashi, Buni_buni kadan yana kallon safiyya, Har anty hajara ta lura dashi ummi ce ta fito Dan haka dinning area suka nufa, Safiyya ce tayi saving nasu tana zuwa buhaisa ta zauna,, Dariya anty hajara tayi sufara cin abicin, Itama buhaisa batai magana ba ta zuba tana hararar ta, Parlour su dawo ana Hira har dady yadawo motsi kadan tayi idon yah saif akanta, har dai ta gaci tace yah saif please kallon fa tafada tana harara shi, Ka badaya kallon shi sukai kanshi ya sun kuyar cike da kunya, daga bayama tashi yayi ya koma ciki......................✍️ (Waishin 🧐dawa azima take waya ne komai zai faru tsakanin anty Waleeda da md🤭) Kudai kawai saimun hadu a page 18&19 danjin yadda zata kaya🥰 *🌹 RAYUWATA 🌹* *Story and written✍️* *Bilkeesu .S. Aliyu* _💞(Billy pinky)💞_ *🤝 Amanar nazari writer's association📚* *[07070260240]* _WhatsApp number or call_ *📚N .W .A🖊️* *EPISODE 🌷1️⃣8️⃣⏪1️⃣9️⃣🌷* *Abuja____--___* B'angaren yah majeed kuwa Koda auta ta fita aikin shi ya cigaba, bayan ya gama ya maida hankalin shi a tv yana kallon film din da sukeyi yana shan madarar sa kamar baya so. Har saida film din yakare sannan ya shige ciki. Maimakon kwanciya bathroom ya wuce ya hada ruwa mai d'umi cikin bathtub tare da zuba kayan kamshi kala_kala. Sanan yashige ciki Saida yayi minti ashirin cur ruwan na ratsashi ya sanan ya shiga gurin wanka ya dauraye jikin shi. Bayan ya fito shafa'i da wutiri yayi sanan ya shirya yayi kyau sosai cikin shigar tasa kamar wanda ba kwanciya zaiyi ba . Ga wani uban kamshi da yake kamar kanfanin hada turare kamar ba dare ba. Sumar nan tasha gyara hakama kwantaccen gashin sajan sa sai wal'kiya yake ya kwanta luf-luf ya sake fidda taswirar duguwar fuskar sa. Saida ya tabbatar ya gama komai sanan ya nufi bed wanda a lailayeshi da farin bedsheet. (Kirari nayi ga ubangiji mahalincin wannan hallitar kaskiya dole aso mai kyau dan shi mutum ne da yasan ha'kkin tsara ado. ya iya saka sutura ta zauna tsaf ajikin sa kuma ya haskata tamkar dan shikadai ake saka kaya irin su) Addu'a konciya bacci yayi sanan ya kwanta, *Washegari....* Sanye yake cikin riga da wando gajeru da alamu daga gorin mutsa jiki ya fito jikin jike da gumi gafen shi karanshi ne ke biye dashi wato cucu. Yusuf ne ya karaso da sauri yana mika mishi towel amasa yayi yana goge zufar data jikashi ruwa Hafiz yake niyar zuba mishi a karamin mug hannu yasa ya amshi goran ruwa ya kafa abaki kadan ya rage yana zubama cucu abaki, Kaitsaye kofar da zata sada shi da baban parlour shi yanufa da alamu gurin ma a part din shi yake, Dan gurin motsa jikin ma kanshi abun kallone koda yashiga Yusuf biye dashi ciki yashiga kana ya fada bathroom ya hada ruwa mai d'umi cikin bathtub tare da kayan kamshi kala-kala sanan yashiga. Bayan ya fito close d'insa ya nufa fitowa yayi cikin shigar riga da wando rigar mai kamar rigar sanyi dan har hula tana da ita agaban rigar anyi zanen heart da pink din zare sai kyalli take shikuma wandon dogo ne daga kasa anmishi wata zuga ga wani uban kamshi da yake kamar kanfanin hada turare kamar ko yaushe sumar nan tasha gyara. (Masha Allah shine abinda nafurta🤫) Kaitsaye parlour ya fito "Yusuf yace barka da fitowa ranka yadade" hannu kawai yadaga mishi kana ya zauna a daya daga cikin sofa. Gaisawa suyi da shi kana yake bashi bayanin duk abinda yafaru lokacin bashi, kasancewar badashi sukai tafiyar ba da "Taheer ne" ranka yadade auta tayimin maganar waya jiya dan har nasa zuwa anjima za'a kawo mata. "Wai harta fadama? "Eh rankaya dade tun jiya takirani ai. "Okay" Wayan shi tafara Kara dauka yayi kasancewar ringing din dayasa ma "Ammiii na daban ne shiyasa. Majeed kana inane breakfast ya kamalla Kai ake jira. Ammii yanzu zan fito insha Allah, "Okay" sai kazo tana fada tayanke kiran. Ga badaya 'yan matan gidan suna dining area suna breakfast, Bako sallama tashigo parlour. Sanye take cikin riga da wando wanda su kamata sosai, Fuskarta tushe da wani tan fatsetsen glass, wanda baka iya ganin idon ta, Tayi rolling da wani karamin mayafi, Haka takalmin kafarta shima mai tsini, sai taunar cingam take yana kara kas-kas Hannun ta rike da karamin akwatu. Gaba daya 'yan matan kallon ta suke masu Jan tsaki nayi, masu murmushi nayi. azima ce ta taso da gudu ta rungume ta. Welcome sis tafada tana rike mata hannu, Sai ayna dake zaune itama tace welcome! Tana dauke kanta. Dukan su da kallon rainin hankali ta bisu tana karasawa tsakiyar parlour, Wato ace har yah "Aj ya dawo ba wacce ta kirani ta fadamin saboda ba'kin ciki. to gani nazo, Tafada cike da masifa. feenah ce taja tsaki tare da cewa wace ke agurin shi da har sai ankiraki dan ya dawo? Cike da rainin hankali tayi maganar batare da ta dago ta kalleta ba. Wacce ni kike tambaya? Ido feenah ta kashe mata alamun eh. Wacce zai aura! Oooh ai basai anfada Miki ya dawoba kina matsayin wacce zai aura. Ai saidai muji agurinki yah majeed zai dawo koh? Tafada cike da rainin hankali ta na kallon zaituna. Auta dake jinsu takaici duk ya isheta. sai hauka suke akan Wanda sam besan sunayi ba. Ayna ce tai dariya tacigaba da danna wayar ta. Takaici ne ya ishi zaituna ta dago daniyar yima feenah masifa azima ta rada mata magana akune. Ke kikama kanki bansan rashin kunya Sonki ne bayayi besan ma kinayi ba. Zaituna tafada cike da masifa. Oooh ashe ke yasan kinayi fa tunda har maganar aure anyi koh. Tafada suna fashewa da dariya itada aynah, Aifa zaituna ta harzuka parlour ya cike da hayaniyar su bakajin komai sai zage-zage suna tona ma juna asiri. Ammiii ce take sak kowa daga upstairs, ta hade cikin wata hadda'd'iyar shadda sai kyalli take. Wacce tasha dinki irin na zamani. Aa hayaniyar me nake jine tun dazo? Ba wanda ya dago ya kalleta, saima Kara kami da sukai har ana shirin fara dambe. A nutse yake sa'kkowa daga upstairs d'in cikin nutsuwa gami da nagarta sai zuba 'kamshin mayun perfumes d'insa yake. 'Kamshinsa ne ya shiga rige-rigen shiga 'kofofin hancin su, Azima dake kusa da zaituna tai saurin tsungulin ta, Gaba daya ido su zuba mishi tunkan ya idda saukowa. Ammiii murmushi kawai tayi ta wuce dinning area din. Wanda autace kadài akai sai basma, Wani kallo ya watsa musu dan saida hantar cikin su ta kada. Kana ya wuce dinning din ba tare da yasake kallon suba. Yana karasawa ya rungume Ammii tare da cewa, good morning first love! Morning handsome I hope katashi lpy Alhamdulilah! Ammiii nahh! Yafada yana kaiwa zaune kusada kujerar Ammii. Kuma tunsa taja bazaka saki wannan fuskar bane. Murmushin gefen baki yayi yana kallon ta, Kai Ammii nah! Aiko kamar zuciyar zaituna da feenah zata fado. Ba masuba har su auta, Dan murmushi gawan da bai sabayi kyau yake mai. Suma kujera suja suna sinne kai ita ko zaituna har zuma take gurin gaishe shi, Morning kawai yace ya fara cin abicin shi Suma sauran gaida shi suyi Kai kawai ya daga musu kasancewar in yana cin abicin baya magana ___________ *Kaduna🌸* "B'angaren mom kuwa jiran safiyya kawai suke ta dawo su ci ubanta. dan gyaran gidan ma basuyi ba jira suke ta dawo tayi, Amah shiru kamar an aiki bawa garinsu. Anty Waleeda ce tace mom kinga yarinyar nan ba dawowa zatai ba, Kuma kinsa Abba ya daketa maybe tana gidan wannan kanwar uwar tata. Hakane wallahi kinga Har na manta da halima ai uban nata zai dawo da kafarta zata dawo dan ubanta, "Har kwana biyu shiru safiyyah Bata dawo ba" aiki na neman gagarar mom dan anty Waleeda cewa ma take bata iya aiki ba. Yaune ma mom ta zage tadan gyara gidan azuciyar ta tana tsinema safiyyah da tanan ai da ita zatayi har hango irin dukan da zatama yarinyar nan take inta dawo" "Kasancewar Abba bashi agarin ne da tuni tasa ya dawo da ita " "Mom ce zaune a parlour ta daura kafa daya kan daya tana dana waya" Yaron ya shigo wai ance safiyya tazo a waje. Injiwa? wani ne mai mota. Okay kace gatanan" Wani murmushi makirci mom tasaki tana Kiran anty Waleeda" "Haka ta karaso dawata fingilar riga iya gwiwa ta tsaya mata aka tana wani 'bata fuska mom gani" Kije ana kiranki a waje kuma ki sanja wanan kayan kidan fesa turare. "To kawai tace ta fice saigata anci doguwar riga da mayafi sai kamshi take kai tsaye wajen ta nufa gurin MD" "Shigowa tayi ranta a 'bace mom dama waccan yarinyar yazo nema akace ni" "Yakuyi dashi? Duk yadda suyi da MD ta fada mata kuma ni wallahi mom yamin ina son shi" "Kwantar da hankalin ki zanyi bincike akanshi in yayimin yadda nake so shikenan" "Amah fa mom nidai gaskiya yayimin sosai k kingan shine ga kyau ga aji da kingan shi kisan daga gidan madara ya fito" "Niji bari yarinyar nan ta dawo tafada mana ko waye shi" "Uhm mom" "Na'am" "Wallahi kamar safiyyah yanzu tafara rainaki fa, kinga da komai dukan daza amata ba inda take zuwa, amah yanzu har tasamu zarrar maida Miki martani inkina mata magana mata" "Shiru mom tayi nawani lokaci kamar mai nazari, kuma fa hakane amah ban nida ita zanje asake mata wani sabon kollin ne" yauwa mom koh kefa ni wallahi na kosa abba ya dawo ya dakko ta dan nagaji da cin garin kwaki, da fara da mai" ________________ "Around 8:00 Sutashi kasancewar yau ba aiki, Safiyyah cema ta tashi buhaisa, wanka tafara shiga koda ta fito saida tasake tashin buhaisa kana tashiga, ita kuma tafara shiyawa" "Tare su fito waya ma'kale a kune ta Tana waya da yah Ansar har su iso parlour yah saif na satar kallon ta kadan-kadan. Ita tama saba da wannan kallon nashi Dan haka bata nuna alamun tasan yana yi, Zama tayi su cigaba da waya har yake cema ta Sunday ta koma gida shima wanan week din yaso dawowa amah yanzu sai next week, Amah yah maiyasa bazaka dawo din ba? baki a gida nikuma basan ciwon kan wanan matar! Please yah Ansar ka dawo mana. Tafada cikin shagobba, a'ah kibari sai next week din insha Allah. Tom yaya nah Allah yah kaimu Da haka sukai sallama" "Gaisawa suyi da yah saif da anty hajara wace take zaune tana danna waya, Fira suke har Ummah halima ta fito itada Abba gaishesu suyi cikin girma mawa kana su wuce dinning area" Bayan sun kammala ita da buhaisa su kwashe komai su gyara, kana su koma parlour suna fira anan nema Abba yake cewa gobe za'a sa ranar anty hajara dan haka yah saif kar yaje ko ina, Haka dai safiyyah itada buhaisa suke ta murna da tsare-tsaren biki kamar ansa har yah saif nasaka musu baki anty hajara da kunya ta isheta tashi tayi takoma sama tana murmushi" "Dariya buhaisa tayi uhm waifa kunya taji meye na kunya anan wallahi da nice ba kunyar da zanji tafada tana fari da ido, Ungo taki nan wato da kece ba kunyar da zakiji koh ai dama tafiki kunya. Ummah ce tafada tana ma buhaisa da kuwa, dariya suka sa gabaki dayansu, Kai ummi nifa bahaka nace ba tafada tana turo baki" Allah dai yashirya minke cewar Abba yana murmushi, Da ameen duk suka amsa, ana murmushi" "Har abba ya fita suna hira itama anty hajara daga baya ta fito a cigaba da ita, yah saif please yau ka kaimu shopping wallahi kayan kwalliya na sunyi kasa. Sai dai safiyyah ce tafada sai muje ya fada yana kallon safiyyah, Uhm a lallai yah saif to gaka gatanan ita take cewa tana so taje shopping wai turarukan ta sunyi kasa. Koba haka bane? tafada tana kiftama Safiyyah ido da rausayar dakai, Eh hakane! Dariya anty hajara tayi tace gulman mu kawai, Ku gama gulmar ku kuzo ku same ni, Kai anty hajara mune gulman mu Safiyyah tafada cike da shagobba" "A'ah kugama zaku dawo ku sameni ne ai" "Duk dariya suyi su maida hankalin su kan yah saif, Kar anty hajara tai musu gwabi, Itama bata sake cewa komai ba dan tasan halin 'kannan nata. tom shikenan ku shirya sai muje after asahr preyer. Yauwa yah saif su hada baki gurin fada. Daga baya ma kan anty hajara su koma suna mata tsiya tun tana samu su baki har ta koma saidai tai musu murmushi" "Tsaf ta shirya cikin doguwar riga ta material red, Kayan sun mata kyau, ta dauko fari hijjab tana niyar sawa buhaisa ta turo kofa" "Kan bala'i menake gani haka? Wai gowa tayi tana dubawa a ina? Bata rufe bakiba taji buhaisa ta kwace hijjab din wallahi baki isah kinsa hijjab ba. Tsaki Safiyyah tayi tana cewa uhm sai kiyi Dan Allah ni bani, Banza tayi da ita ta nufi wardrobe duk hijaban ciki ta kwashe tana niyar ficewa. safiyyah tace ina kuma zaki? ban sani ba tafada tana ficewa da gudu tana dariya itama ta rufa mata baya dan ta gane nufin ta, Haka sukai ta zagaye parlour nan kamar wasu yara, "Wai 'kalan ku kuwa kunga Safiyyah da buhaisa Allah yashirya min ku mekuma ya faru? "Wai ummi kaleta fa shopping yah saif zai Kai mu, wai shine hijjab zata sa kullum tana manne da hijjab shine nace tasa mayafi wai a'ah kuma fa ummi hijaban duk ba wankka ku bane bama guga. "Takare sa maganar tana kallon safiyyah da ta tsaya tana hararar ta" "Kinga safiyyah kisa mayafi kema kya huta da sa hijjab din nan. Tom ummi! Yauwa ko kefa, jeki sawo mayafin kafin ya fito. Gwalo buhaisa tamata kingani fa ummi gwalo take min, Ke buhaisa kibar mata gwalo nace ma tasa Hijabin hajara ai, Sorry ummi! Tafada tana sake mata gwalo tai sama da gudu tana dariya. Baya safiyyah ta rufa mata Naga randa zaku Dena wannan abin kamar wasu yara cewar ummi tana murmushi. (Like nida sis Waleeda 😅) "Tsaf su fito gunin burgewa cikin doguwar riga ta material red, Sai ma dai-dai cin mayafi da tayi rolling dashi tsaf ta fito kamar wata balarabiya, "Haka su iso shop rite din shiga suyi yah saif ya dauki keken yana jah sukuma suna sawa, safiyyah dai rabin kayan data dauka turaruka ne sai kayan za'ki dan ita buhaisa tafi auki a gurin kayan kwalliya. "Haka sugama da ganan su wuce gurin Shan ice cream da yawo, Da ganan ya ajesu gida ya wuce gurin kallon ball. *Washegari...* Kasancewar jiya mun gaji bamu tashi da wuri dan tunda muyi salah mu koma. Anty hajara da ummi ne suyi breakfast bayan sunga ma anty hajara tazo ta tashemu, bathroom nashiga nayi wanka buhaisa ta shiga, Tare mu fita muna dariya" "A dinning area mu sa mesu muma can mu nufa" "Muna gama wa mudawo parlour muna fira har Abba ya fita shida yah saif baki sunzo, muje mukai musu drinks da snack's" "Har Isha tazo aiko nayi murna na rungume ta su gaisa da ummi da anty hajara daga baya ma bathroom mu wuce. Aikuwa musha shafta ta bamu labarin MD buhaisa dai bata so wai tana Taya yah saif kishi" "Ansa ranar auren anty hajara nan da wata daya zamu sha biki tun ranar mu fara tsararen biki" "Ina sallah yah saif ya kirani ni Isha ta dauka suka gaisa, ta bani lokacin na idar kasancewar anguwa za muje yau" _______________ *Abuja🤍* "Kowa part din su yanufa itakuma zaituna part din granny tayi. Aa ke kuma daga ina da wannan tsinan nun kaya? " "Kai tsohuwar nan daga gida mana" "Amah zakiyya na ganin ki kifito haka? _____ "Yah majeed na Shirin fita office suna sallama da Ammii. saiga addah nan a'ah my son yaushe andawo ne ba azo an gaishemu ba? Birkitatun idon shi ya dago yana kallon addah, Sorry addah yanzu nake shirin shigowa. Yafada kamar bai son magana, Aa my son bakomai wallahi ai gajiya ce to yah hanya? Alhamdulilah! munsame ku lpy? Yafada yana shirin barin parlour" "Wai dama bakaje ka gaishesu ba da kaje gaida granny? "Uhm lokacin sallah ne yaye shiyasa, "Yafada alamun ya gaji da maganar, murmushi kawai Addah tayi.............✍️ *Please🙏 comment and like 👍and share fissabilah👏👏👏* *🌹 RAYUWATA 🌹* *Story and written✍️* *Bilkeesu .S. Aliyu* _💞(Billy pinky)💞_ *🤝 Amanar nazari writer's association📚🖊️* *[07070260240]* _WhatsApp number or call_ _📚N.W.🖊️_ *Book 1 📖* *Page 20&21* "Yanzu zakaje ka gaishesu ne koh sai ka dawo? "Saina dawo yanzu time ya kure" "Allah yah tsaremin Kai ya dawo da kai lafiya Allah yabada sa'a" "Ameen yah Allah cewar Addah, shima Ameen yace yana sunbatar goshin ta kana ya fice cikin nutsuwa, dolene inka kaleshi ka 'kara kallo . Tunda ya fito compound din gidan tight security d'in dake zagaye da harabar wurin suka wani irin kamewa tare da sara mishi, Had'i da gaishe shi" "Hannu kawai yadaga musu tare dace wa kun tashi lpy? Cikin harshen turanci. Bai jira amasa warsu ba ya nufi" "Gurin shegun manyan car's d'in dake jibge wuri guda su nufa shida security d'insa. Zu'ke'kiyar ba'kar motar da juseph ya fiddo, Wanda ko makaho ya shafa yasan eh lallai kudi yayi aiki wurin siyenta. Dan sai wani irin kyalli da sheke take mai daukar ido. Gatan dai bata cika hayaniya ba kuma Bata mamaye waje ba. Tsaf take kala da yanayin matasan zamani irinsa dake gara kan nera bisa ga damar da ubangiji ya basu." "juseph ne ya bude masa motar ya shiga sanan Yuoseef ya shiga suma sauran security d'in shiga nasu suyi su fita a jere susa motar da Aj yake a tsakiya juseph ke driving" "Kai tsaye company su nufa" "Ganin katon company dasu zo yasani furta masha Allah gaskiya company ya hadu ga girma, a saman company dauke yake da wani tambari Mai kamar tauraro irin tambarin dake jikin motocin shi" "Har ciki su shiga guys d'insa su bude Mai motar, Saida yadau tsawon lokaci kafin ya fito gaba daya ma aikantan sai girma mashi suke." "office din danake kyautata zaton nashine, dan yafi ko ina tsaruwa, kuma security's ne aciki da wajen shi. ya shiga youseef beye dashi" ✨🤍✨ Uhm dan Allah meye ai bin wanan shigar granny? bama wannan ba ace yah majeed ya dawo amah baki gayama mummy ba? "To ban fada ba kinga daga ke har uwar taki inbaku rabu dani da zancen Abdulmajeedu ba wallahi zan saba muku. Kedashi kwata-kwata baku dace da juna" "Kamar zaituna zatai kuka tace granny kina nufin nida yah Aj bamu daceba?" "To banda abinki inake ina Abdulmajeedu? jikifa yara ba tarbiyya, jifa shigar dake jikin ki da sunan wayewa, shiyasa yaran 'kauye sufiku hankali wallahi. Takare maganar tana cigaba da damun furar ta," "Zaituna nashirin sake magana, granny ta zuba mata wani kallo, wuce ki bani guri kin wani tsayamin aka" "Harara itama tazuba ma granny tana wuce bedroom din ta," "Kwafa granny tayi tacigaba da abin da take tana mita" "Tana shiga ta danna ma mummy kira wayar na fara ringing ta fashe da kuka. Aikuwa mummy na dauka taci karo da kukan zaituna, nanfa hankalin ta ya tashi an ta'bamata shalele. Kinga ya isa haka fadamin meya faru? Nanfa ta shirya karya da gaskiya tafada mata, kuma granny ma wai nida yah Aj bamu daceba takai karshen maganar tana sake fashewa da kuka" "Kinga ki kwantar da hankalin ki, wallahi indai ina numfashi a doron kasar nan bamai auren majeed sai ke, Inko kiga baki aure Shiba to saidai bana numfashi wallahi. Bari Yaya ya dawo" "Yauwa mummy na shiyasa nake kara sonki wallahi sosai Allah ya barmin ke" ____🤍💗 "B'angaren Ammii kuwa bayan Aj ya fita ne take karaba addah hakuri. A'ah aminiya bakomai Nima jiya basma take sanar min ya dawo, kuma yau ina Shirin zuwa saiga fennah tashigo raibace, nake tambayar basma wai fada suke da zaituna. Yaushe zaituna nan tazo gidan nema? "Saida Ammii taja numfashi kana ta bude baki tamkar Bata son maganar tace. Okay nima fitowa ta kenan natar suna yi maybe yau tazo, Fitowar majeed nema sudena. Takai karshen maganar kamar bata so" "Ai kinsan yaranan sai addu'a wallahi Allah dai yashirya Mana" "Ameen yah Allah" "Daganan su cigaba da firar su irin ta aminai" _____________ *Kaduna✨* Tsaf su shirya cikin bakar abaya wacce ama kolliya da farin duwatsu sai takalmi Mai dan tudu. Safiyyah datai rolling din gale saita fito kamar balarabiya" "Sallama suyima ummi anty hajara na musu tsiya aikuma yawo salamu alaikum jiya an fita yauma haka. Dariya suyi su fice suna mata gwalo. Eyye zaku dawo kusa menine har ke ishan. tafada tana daga murya dan su jiyo ta da kyau" "A motar Isha mutafi. Kai tsaye gidan anty zainab muje antyn Isha. aikuwa taji dadi sosai anan muka dade dan sai gabda magrib mukoma gida. Isha tayi-tayi Dani naje na gaida momy nace mata insha Allah gobe kan natafi zan zo. Badin taso ba ta ajemu bakin get ita kuma ta karasa gida kasancewar anguwar su daya" "Koda mushiga ba kowa a parlour cikin sanda mu wuce sama Dan kar ummi taji mu tace yanzu mu dawo. Gab da zamu shiga daki saiga anty hajara nan. murmushi tayi tana fadin ummi! aida gudu mushige muna dariya. Itama murmushi tayi ta koma daki" "Saida muyi sallar isha'i sanan mu fito parlour lokacin ma dady ya dawo amah Banda yah saif. Muna cikin dinner ya dawo, shima nandin ya nufo. nice farkon tashi aikuwa ina zama yah Ansar ya kirani, munsha waya har nake sanar mai gobe zan koma gida, da kuma sa ranar anty hajara. yace ai ummi ta fada mishi, Har su gaisa da buhaisa da ganan muyi sallama. Yau bamu wani dade muna fira ba kowa ya tafi daki, koda mu shiga ma bamiyi wata fira ba nida buhaisa kasancewar mungaji ko bacci yake ji, *Washegari....* A hankali take bude idanun ta tasauke shi akan agogon dake ma'kale a bangon dakin bakin ta dauke da addu'a tashi daga bacci A round 8:30 ai da sauri ta duro a gadon Kai tsaye bathroom ta shiga bata wani dade ba ta fito da alamun wanka tayi duban ta takai kan bed din amah ba buhaisa alamun ya riga ta tashi. Wanka tayi lotion kawai ta shafa ta saka doguwar riga mai dan santsi da hula kana ta fito parlour. "Bayan sun gama breakfast, su tafi gidan su Isha, ai kuwa taji dadi sosai taja su suje su gaida momyn ta daganan su shige ciki fira su sha kamar baza su hadu gobe ba. Buhaisa ce dai yau haushi takeji safiyyah. zata tafi gida, saida suyi sallar ashar sanan su koma gida. "Kasancewar yah saif ne zaikaita" Tsaf tashirya cikin atamfa riga da siket Wanda d'inkin ya zauna daram ajikin ta kamar dan ita ayi, kasancewar tafi buhaisa kiba, shiyasa kayan su kamata sosai, gogaggen Hijabin ta tasaka hadi eyeglasses, facemask dinta kuma ta mayar jaka ta fito. Aikuwa buhaisa ta cika tai fam kamar zata fashe da kuka anty hajara ta tasata a gaba tana tono ta. Saidai da tasata kuka, daga baya su koma lallashin yar auta. Koda safiyyah ta fito itama lalashin tayi, ki kwantar da hankalin ki, bikin anty hajara fa yazo Kinga tun ana saura sati biyu zanzo to kinga ai na kusa dawowa. Badi taso ba yah saif yace kinga tashi mu tafi kar yamma ta cikayi. Sallama suyi da ummi da anty hajara kana su tafi. Har kofar gida ya kaita shirin fitowa take taji ya rikemata hannun ta waigowa tayi tana Mai zuba mai hararar da ita kanta bata san ta Mai ba, "Hannun ya saki yana dan wayan cewa, tafiya zaki ba sallama? Ko kinyi kewarsu ne? Ya jera mata tambayar ajere. "Kai kawai ta daga mishi tare da cewa kadan. "Kiyi kewar tasu? "Uhm "Tom shikenan sai yaushe kuma? "Yatsun hannun ta tadaga mai guda biyu tare da cewa week. "Two weeks? ya fada yana kallon safiyyah. "Uhm "Yar kurma kenan wato na isheki koh Tom shikenan sai munyi waya. "Baki tadan turo jin ya kirata da yar kurma, Amah batace komai ba saida ta fita hannun ta rike da murfin motar kana tace. "Thank you yah saif Saida safe, ka gaidamin da sisy nah please. Ta hada hannu wan ta alamun roko. "Baki ya saki yana kallon ta, saida ta rufe murfin motar, kana ya dago da sauri har takai bakin get. Saida yaga shigarta ya sauke ajiyar zuciya kana ya tada motar ya tafi. "Saida motar shi ta tafi ta dago daga leken da take tana sauke ajiyar zuciya, ga baki daya tsoran shiga take amah haka ta dake tai sallama a kofar parlour. "Gabaki dayan su suna zaune a parlour daga mom har anty Waleeda da yah safwan dashi ba zaman gidan yake ba sai baby. "Aikuwa da gudu baby tazo ta rungume ni nima rungume ta nayi muna kara sawa cikin parlour. Tunda nayi sallama su zuboma kofar ido harna karasa ina gaida mom, "Abin mamaki saida na ta'bata ta d'ago firgigit. Kuma ta amsamin harda tambaya ta yasu ummi, Amsa wa nayi ina gaida yah safwan shima dai amasa wa yayi tare da cewa ina kishiga ne safiyyah? "Naje gidan ummi ne . "Oooh shiyasa abincin ma sai anga dama akeyi a gidan kenan? Bance komai ba na tashi na nufi anty Waleeda na rungume ta, duk da tana tureni amah ban damu ba dan ba karya nayi kewar su. Yadda nai tsam mani hakan ce ta kasance Dan parlour dai sai addu'a wallahi. Ina mamakin san jiki irin na mom da anty Waleeda. "Bedroom nashiga na barsu da mamakin dawo wata, dan itafa mom batai tsammani zan dawo ba. To shima dai bedroom din sai addu'a dan yama fi parlour datti, Jaka tana ajiye ina Mai leka bathroom wayo Allah, na furta ina mai fitowa da sauri. Parlour na fito na wuce kitchen na dauko kayan shara, bedroom din na share tare da yin mopping. Na koma bathroom shima share shi nayi abin takaici ga pad nan haka duk na hada na share kana na wanke bathroom din. "Saida akira magrib na gama aikin, yah safwan nata min sannu da yake shi ba halin mom ya biyo ba. "Around 4:00 Natashi, raka'a atul fijir nayi kana nai sallah asuba tare da azkhar, nafara karatun alQur'ani ban wani dau lokaci ina yiba natashi nafara gyaran gidan kafin karfe 7:00am nagama komai har girki, Wanka nayi har na fito anty Waleedah bata tashiba bare tayi sallah tashinta na kumayi, me hali baya fasa halinsa dan yauma masifa ta hauni da ita kyaleta nayi na cigaba da kintsawa. "Tsaf na shirya cikin less pink wanda amai ado da fararen duwatsu, dinkin riga da siket, simple makeup nayi dan kuwa daga fouda, sai kwalli, da lips gloos, and maskara, da na taje eyelashes dina dashi aifa ya fito gadar-gadar Masha Allah, kalba na hade na daure da ribom, Parlour na fita dan na karya bakowa a parlour sai yah safwan, gaisawa muyi tare mu karya dan shima zai fita gurin aiki, Jeki dako mayafi na ajeki, Tom yah safwan. Gogagen milk hijjab nasaka da face mask da eyeglasses sai plate shoe shima pink waya ta nadauka nasaka a hand bag na fita, Su anty Waleeda suna ta sharar bacci harna mu tafi Muna zuwa ya bani 1k godiya na mai ina karasawa ciki. Yauma Isha ta rigani zuwa ban dade da zuwa ba mu fita gabatar da program din ranar Thursday da ba muyiba. "Bayan mun gama mukhtar yake cemin MD na kirana, Kai tsaye office din nashi na nufa ina shiga, PA dinshi da sai cin magani take ta min iso gurin shi, ban damu da kallon da take minba na karasa da sallama. "Tsaye na ganshi sai zagaye office din yake, Nima tsayawar nayi ina furta, good afternoon sir! Nuna min gurin zama yayi shima yana kai zaune. Jin ya kafeni da ido ya sani na dago daniyar magana dan nifa na tsani kallo, shikuma ya kware indai gurin kallo nane. Yah jikin naki? Ya jefomin tambayar da saida na dago na kalleshi. Ai naji sauki! Nafada ina kasa da idona . Masha Allah! Dama dalilin da yasa na kiraki ina son magana dake ne, Uhm inajinka na fada cike mamakin wacce magana zaiyi dani. "Cikin bazata matukar bazata na d'ago ina kallon shi jin maganar da banta b'a tsammani daga gare shi ba. "Wallahi safiyyah ina son ki ina burin ki zamo uwar y'a'yana tun randa na ganki naji ina sonki wallahi, tinanin ki ya hanani bacci, har gidan ku naje acemin Wai banan bane gidan, ko sawa nayi yau tayi please kar kicemin aa. Ya karasa maganar kamar zaiyi kuka idon shi na tara kwalla. Ni wallahi dariya ma yabani da tausayi gami da kunya. "Na baki lokaci safiyyah kije kiyi tunani da kyau, Insha Allah duk abinda kika yanke zan amsa da hannu biyu, amah kimin adalci please. Ya 'karasa maganar cike da magiya. Kai kawai na gyada mishi na fice daga office din, Kai tsaye office din mu na nufa, mu cigaba da abinda muke, gabaki daya tunanin maganar nake. to ya akai ma yasan gidan mu, haka dai har atashi takardun dazan kaima ma cewa nayi Isha takai mu hadu a mota, Koda ta tambayeni cewa nayi bakomai na wuce. Da ta dawo take sake tambaya ta, meya faru naji MD yace intaya shi rarrashin ki? Bakomai! Na fada irin banson wata tambayar, Amah safiyyah baki da wata aminiya data wuce nida buhaisa, haka nima bani da wata aminiya sama dake, kinsan bana boye miki damuwa ta. amah some time kina boye min damur ki bana takura ki da dole saina ji, shikenan. Ganin taji haushi kuma nima fa banyi adalciba, hannun ta na kama, kiyi hakuri kinji sis wallahi ba haka bane, nafad'a mata duk yadda muyi da shi. "Uhmm safiyyah ta kira kinsan menene? "Aa saikin fada isha" "Wallahi ki amince ta ko ina MD ya can-can ci a soshi. Don mutum ne nagar tacce wanda yasan ya kamata mai ilimi. A taikaice wallahi koni MD yace yana so tuni zan amince ba kiga yadda PA ta mutu akanshi ba amah bata gaban shi. Please kidai kara tunanin amah wallahi kun dace da MD sosai. "Murmushi nayi tom sisy nah nagode sosai muje to" "Itama murmushin tayi never mind sis nidai fatana ki amince wa bawan Allah nan, Tafad'a tana tada motor, Har kofar gida takawo ni kana ta wuce tana kara rokona murmushi kawai nayi na shiga bakina dauke da sallama. Mom ce da anty Waleeda kawai a parlour, ko firar mai suke ina shigowa suyi shiru dan ko sallamar basu amsa ba, To nasan hali tunda basu san mahimmanci taba. Gabanta naje ina fadin good evening mom, murmushi kwance a fuskata. Sanin ba amsawa zatai ba yasa na mike na wuce bedroom. Tom dama yaudin fa gaskiya na gaji. kasancewar program biyu nayi ga kaina har juyawa yake. Bathroom na shiga na wanke kana nayi wanka tare da dauro alwala, Bed nafada ina sauke ajiyar zuciya ga yunwa na kwakular cikina, amah nasan ba abinda zan samu a gidan nan, nikuma bazan iya girki ba dan kaina ciwo yake. Ganin fa zan cutu yasa na tashi, mayafi na daura akan towel din na fito kai tsaye kitchen na nufa. "Kamar yadda nai tsam mani hakan ce ta kasance dan kuwa bakomai hattana miyar basu rage ba, Garin kwaki na jika da Madara na zuba gyada, na fito duk da kallo su bini anty Waleeda na dariya kasa-kasa har nashige" ________ *Abuja🤍* Motocin shi ne su shigo gidan kai tsaye parking lot su nufa ajere su tsaya, kasancewar parking lot din akwai girma. Da sauri Samuel ya Kara so ya bude mai motar. yadau tsawon lokaci kafin ya fito gaba daya kamewa suyi har ya bargun youseef beye dashi, Kai tsaye ta babban parlour yabi. Aikuwa gaba daya 'yan matan gidan suna zaune, wasu sunyi group din fira, wasu waya, wasu chat, wasu koma iya su biyu ne, wato zaituna da azima kenan dan yanzu ma riga da wando ne ajikin ta. "Da sallam ciki-ciki ya shiga dan inba kallon bakin shi kayiba ba zaka ce yayi magana ba. Gaba ki dayan su nutsuwa suyi, Barka da dare yah Aj su hada baki gurin fada. Da kallo ya bisu daya bayan daya, "Ke" Ya furta tamkar mai ciwon hakori, Zaituna da tasan da ita yake tace Na'am yah Aj tana nufo inda yake tana wani rangwa d'a. Tom bema san metake ba dan hankalin shi bashi gareta, "Karna dawo na ganki a haka. Yafada yana haurawa upstairs, Me feenah zatai itada aynah inba dariya ba har da shewa. Zaituna da ranta yayi ko loluwar baci itama b'angaren granny ta nufa dan ta gane nufin shi ta cire kayan jikinta kenan. "Shiko kaitsaye dakin Ammii ya nufa. Haka yayi ta zuba mata shagobba san ransa saiki rantse shine auta kamar ba Wanda gaba daya yaran gidan ke tsoro har ma manyan shakkar sa suke. "Zakai dinner ne yau ko aa? Tafada tana kallon shi. "A'ah auta ta amso min Madara a gurin granny ita zansha" Tom dayake itama tasan halin nashi baya son cin abinci bare kuma na dare ya gwamace yasha Madara ko coffee. "Saida safe yayi mata yabi ta wata kofa da Kai tsaye part din shi zata kai shi............✍️ 🌹 RAYUWATA 🌹* *Story and written✍️* *Bilkeesu .S. Aliyu* _💞(Billy pinky)💞_ *🤝 Amanar nazari writer's association📚🖊️* *[07070260240]* _WhatsApp number or call_ _📚N.W.🖊️_ *Book 1 📖* *Page 20&21* "Yanzu zakaje ka gaishesu ne koh sai ka dawo? "Saina dawo yanzu time ya kure" "Allah yah tsaremin Kai ya dawo da kai lafiya Allah yabada sa'a" "Ameen yah Allah cewar Addah, shima Ameen yace yana sunbatar goshin ta kana ya fice cikin nutsuwa, dolene inka kaleshi ka 'kara kallo . Tunda ya fito compound din gidan tight security d'in dake zagaye da harabar wurin suka wani irin kamewa tare da sara mishi, Had'i da gaishe shi" "Hannu kawai yadaga musu tare dace wa kun tashi lpy? Cikin harshen turanci. Bai jira amasa warsu ba ya nufi" "Gurin shegun manyan car's d'in dake jibge wuri guda su nufa shida security d'insa. Zu'ke'kiyar ba'kar motar da juseph ya fiddo, Wanda ko makaho ya shafa yasan eh lallai kudi yayi aiki wurin siyenta. Dan sai wani irin kyalli da sheke take mai daukar ido. Gatan dai bata cika hayaniya ba kuma Bata mamaye waje ba. Tsaf take kala da yanayin matasan zamani irinsa dake gara kan nera bisa ga damar da ubangiji ya basu." "juseph ne ya bude masa motar ya shiga sanan Yuoseef ya shiga suma sauran security d'in shiga nasu suyi su fita a jere susa motar da Aj yake a tsakiya juseph ke driving" "Kai tsaye company su nufa" "Ganin katon company dasu zo yasani furta masha Allah gaskiya company ya hadu ga girma, a saman company dauke yake da wani tambari Mai kamar tauraro irin tambarin dake jikin motocin shi" "Har ciki su shiga guys d'insa su bude Mai motar, Saida yadau tsawon lokaci kafin ya fito gaba daya ma aikantan sai girma mashi suke." "office din danake kyautata zaton nashine, dan yafi ko ina tsaruwa, kuma security's ne aciki da wajen shi. ya shiga youseef beye dashi" ✨🤍✨ Uhm dan Allah meye ai bin wanan shigar granny? bama wannan ba ace yah majeed ya dawo amah baki gayama mummy ba? "To ban fada ba kinga daga ke har uwar taki inbaku rabu dani da zancen Abdulmajeedu ba wallahi zan saba muku. Kedashi kwata-kwata baku dace da juna" "Kamar zaituna zatai kuka tace granny kina nufin nida yah Aj bamu daceba?" "To banda abinki inake ina Abdulmajeedu? jikifa yara ba tarbiyya, jifa shigar dake jikin ki da sunan wayewa, shiyasa yaran 'kauye sufiku hankali wallahi. Takare maganar tana cigaba da damun furar ta," "Zaituna nashirin sake magana, granny ta zuba mata wani kallo, wuce ki bani guri kin wani tsayamin aka" "Harara itama tazuba ma granny tana wuce bedroom din ta," "Kwafa granny tayi tacigaba da abin da take tana mita" "Tana shiga ta danna ma mummy kira wayar na fara ringing ta fashe da kuka. Aikuwa mummy na dauka taci karo da kukan zaituna, nanfa hankalin ta ya tashi an ta'bamata shalele. Kinga ya isa haka fadamin meya faru? Nanfa ta shirya karya da gaskiya tafada mata, kuma granny ma wai nida yah Aj bamu daceba takai karshen maganar tana sake fashewa da kuka" "Kinga ki kwantar da hankalin ki, wallahi indai ina numfashi a doron kasar nan bamai auren majeed sai ke, Inko kiga baki aure Shiba to saidai bana numfashi wallahi. Bari Yaya ya dawo" "Yauwa mummy na shiyasa nake kara sonki wallahi sosai Allah ya barmin ke" ____🤍💗 "B'angaren Ammii kuwa bayan Aj ya fita ne take karaba addah hakuri. A'ah aminiya bakomai Nima jiya basma take sanar min ya dawo, kuma yau ina Shirin zuwa saiga fennah tashigo raibace, nake tambayar basma wai fada suke da zaituna. Yaushe zaituna nan tazo gidan nema? "Saida Ammii taja numfashi kana ta bude baki tamkar Bata son maganar tace. Okay nima fitowa ta kenan natar suna yi maybe yau tazo, Fitowar majeed nema sudena. Takai karshen maganar kamar bata so" "Ai kinsan yaranan sai addu'a wallahi Allah dai yashirya Mana" "Ameen yah Allah" "Daganan su cigaba da firar su irin ta aminai" _____________ *Kaduna✨* Tsaf su shirya cikin bakar abaya wacce ama kolliya da farin duwatsu sai takalmi Mai dan tudu. Safiyyah datai rolling din gale saita fito kamar balarabiya" "Sallama suyima ummi anty hajara na musu tsiya aikuma yawo salamu alaikum jiya an fita yauma haka. Dariya suyi su fice suna mata gwalo. Eyye zaku dawo kusa menine har ke ishan. tafada tana daga murya dan su jiyo ta da kyau" "A motar Isha mutafi. Kai tsaye gidan anty zainab muje antyn Isha. aikuwa taji dadi sosai anan muka dade dan sai gabda magrib mukoma gida. Isha tayi-tayi Dani naje na gaida momy nace mata insha Allah gobe kan natafi zan zo. Badin taso ba ta ajemu bakin get ita kuma ta karasa gida kasancewar anguwar su daya" "Koda mushiga ba kowa a parlour cikin sanda mu wuce sama Dan kar ummi taji mu tace yanzu mu dawo. Gab da zamu shiga daki saiga anty hajara nan. murmushi tayi tana fadin ummi! aida gudu mushige muna dariya. Itama murmushi tayi ta koma daki" "Saida muyi sallar isha'i sanan mu fito parlour lokacin ma dady ya dawo amah Banda yah saif. Muna cikin dinner ya dawo, shima nandin ya nufo. nice farkon tashi aikuwa ina zama yah Ansar ya kirani, munsha waya har nake sanar mai gobe zan koma gida, da kuma sa ranar anty hajara. yace ai ummi ta fada mishi, Har su gaisa da buhaisa da ganan muyi sallama. Yau bamu wani dade muna fira ba kowa ya tafi daki, koda mu shiga ma bamiyi wata fira ba nida buhaisa kasancewar mungaji ko bacci yake ji, *Washegari....* A hankali take bude idanun ta tasauke shi akan agogon dake ma'kale a bangon dakin bakin ta dauke da addu'a tashi daga bacci A round 8:30 ai da sauri ta duro a gadon Kai tsaye bathroom ta shiga bata wani dade ba ta fito da alamun wanka tayi duban ta takai kan bed din amah ba buhaisa alamun ya riga ta tashi. Wanka tayi lotion kawai ta shafa ta saka doguwar riga mai dan santsi da hula kana ta fito parlour. "Bayan sun gama breakfast, su tafi gidan su Isha, ai kuwa taji dadi sosai taja su suje su gaida momyn ta daganan su shige ciki fira su sha kamar baza su hadu gobe ba. Buhaisa ce dai yau haushi takeji safiyyah. zata tafi gida, saida suyi sallar ashar sanan su koma gida. "Kasancewar yah saif ne zaikaita" Tsaf tashirya cikin atamfa riga da siket Wanda d'inkin ya zauna daram ajikin ta kamar dan ita ayi, kasancewar tafi buhaisa kiba, shiyasa kayan su kamata sosai, gogaggen Hijabin ta tasaka hadi eyeglasses, facemask dinta kuma ta mayar jaka ta fito. Aikuwa buhaisa ta cika tai fam kamar zata fashe da kuka anty hajara ta tasata a gaba tana tono ta. Saidai da tasata kuka, daga baya su koma lallashin yar auta. Koda safiyyah ta fito itama lalashin tayi, ki kwantar da hankalin ki, bikin anty hajara fa yazo Kinga tun ana saura sati biyu zanzo to kinga ai na kusa dawowa. Badi taso ba yah saif yace kinga tashi mu tafi kar yamma ta cikayi. Sallama suyi da ummi da anty hajara kana su tafi. Har kofar gida ya kaita shirin fitowa take taji ya rikemata hannun ta waigowa tayi tana Mai zuba mai hararar da ita kanta bata san ta Mai ba, "Hannun ya saki yana dan wayan cewa, tafiya zaki ba sallama? Ko kinyi kewarsu ne? Ya jera mata tambayar ajere. "Kai kawai ta daga mishi tare da cewa kadan. "Kiyi kewar tasu? "Uhm "Tom shikenan sai yaushe kuma? "Yatsun hannun ta tadaga mai guda biyu tare da cewa week. "Two weeks? ya fada yana kallon safiyyah. "Uhm "Yar kurma kenan wato na isheki koh Tom shikenan sai munyi waya. "Baki tadan turo jin ya kirata da yar kurma, Amah batace komai ba saida ta fita hannun ta rike da murfin motar kana tace. "Thank you yah saif Saida safe, ka gaidamin da sisy nah please. Ta hada hannu wan ta alamun roko. "Baki ya saki yana kallon ta, saida ta rufe murfin motar, kana ya dago da sauri har takai bakin get. Saida yaga shigarta ya sauke ajiyar zuciya kana ya tada motar ya tafi. "Saida motar shi ta tafi ta dago daga leken da take tana sauke ajiyar zuciya, ga baki daya tsoran shiga take amah haka ta dake tai sallama a kofar parlour. "Gabaki dayan su suna zaune a parlour daga mom har anty Waleeda da yah safwan dashi ba zaman gidan yake ba sai baby. "Aikuwa da gudu baby tazo ta rungume ni nima rungume ta nayi muna kara sawa cikin parlour. Tunda nayi sallama su zuboma kofar ido harna karasa ina gaida mom, "Abin mamaki saida na ta'bata ta d'ago firgigit. Kuma ta amsamin harda tambaya ta yasu ummi, Amsa wa nayi ina gaida yah safwan shima dai amasa wa yayi tare da cewa ina kishiga ne safiyyah? "Naje gidan ummi ne . "Oooh shiyasa abincin ma sai anga dama akeyi a gidan kenan? Bance komai ba na tashi na nufi anty Waleeda na rungume ta, duk da tana tureni amah ban damu ba dan ba karya nayi kewar su. Yadda nai tsam mani hakan ce ta kasance Dan parlour dai sai addu'a wallahi. Ina mamakin san jiki irin na mom da anty Waleeda. "Bedroom nashiga na barsu da mamakin dawo wata, dan itafa mom batai tsammani zan dawo ba. To shima dai bedroom din sai addu'a dan yama fi parlour datti, Jaka tana ajiye ina Mai leka bathroom wayo Allah, na furta ina mai fitowa da sauri. Parlour na fito na wuce kitchen na dauko kayan shara, bedroom din na share tare da yin mopping. Na koma bathroom shima share shi nayi abin takaici ga pad nan haka duk na hada na share kana na wanke bathroom din. "Saida akira magrib na gama aikin, yah safwan nata min sannu da yake shi ba halin mom ya biyo ba. "Around 4:00 Natashi, raka'a atul fijir nayi kana nai sallah asuba tare da azkhar, nafara karatun alQur'ani ban wani dau lokaci ina yiba natashi nafara gyaran gidan kafin karfe 7:00am nagama komai har girki, Wanka nayi har na fito anty Waleedah bata tashiba bare tayi sallah tashinta na kumayi, me hali baya fasa halinsa dan yauma masifa ta hauni da ita kyaleta nayi na cigaba da kintsawa. "Tsaf na shirya cikin less pink wanda amai ado da fararen duwatsu, dinkin riga da siket, simple makeup nayi dan kuwa daga fouda, sai kwalli, da lips gloos, and maskara, da na taje eyelashes dina dashi aifa ya fito gadar-gadar Masha Allah, kalba na hade na daure da ribom, Parlour na fita dan na karya bakowa a parlour sai yah safwan, gaisawa muyi tare mu karya dan shima zai fita gurin aiki, Jeki dako mayafi na ajeki, Tom yah safwan. Gogagen milk hijjab nasaka da face mask da eyeglasses sai plate shoe shima pink waya ta nadauka nasaka a hand bag na fita, Su anty Waleeda suna ta sharar bacci harna mu tafi Muna zuwa ya bani 1k godiya na mai ina karasawa ciki. Yauma Isha ta rigani zuwa ban dade da zuwa ba mu fita gabatar da program din ranar Thursday da ba muyiba. "Bayan mun gama mukhtar yake cemin MD na kirana, Kai tsaye office din nashi na nufa ina shiga, PA dinshi da sai cin magani take ta min iso gurin shi, ban damu da kallon da take minba na karasa da sallama. "Tsaye na ganshi sai zagaye office din yake, Nima tsayawar nayi ina furta, good afternoon sir! Nuna min gurin zama yayi shima yana kai zaune. Jin ya kafeni da ido ya sani na dago daniyar magana dan nifa na tsani kallo, shikuma ya kware indai gurin kallo nane. Yah jikin naki? Ya jefomin tambayar da saida na dago na kalleshi. Ai naji sauki! Nafada ina kasa da idona . Masha Allah! Dama dalilin da yasa na kiraki ina son magana dake ne, Uhm inajinka na fada cike mamakin wacce magana zaiyi dani. "Cikin bazata matukar bazata na d'ago ina kallon shi jin maganar da banta b'a tsammani daga gare shi ba. "Wallahi safiyyah ina son ki ina burin ki zamo uwar y'a'yana tun randa na ganki naji ina sonki wallahi, tinanin ki ya hanani bacci, har gidan ku naje acemin Wai banan bane gidan, ko sawa nayi yau tayi please kar kicemin aa. Ya karasa maganar kamar zaiyi kuka idon shi na tara kwalla. Ni wallahi dariya ma yabani da tausayi gami da kunya. "Na baki lokaci safiyyah kije kiyi tunani da kyau, Insha Allah duk abinda kika yanke zan amsa da hannu biyu, amah kimin adalci please. Ya 'karasa maganar cike da magiya. Kai kawai na gyada mishi na fice daga office din, Kai tsaye office din mu na nufa, mu cigaba da abinda muke, gabaki daya tunanin maganar nake. to ya akai ma yasan gidan mu, haka dai har atashi takardun dazan kaima ma cewa nayi Isha takai mu hadu a mota, Koda ta tambayeni cewa nayi bakomai na wuce. Da ta dawo take sake tambaya ta, meya faru naji MD yace intaya shi rarrashin ki? Bakomai! Na fada irin banson wata tambayar, Amah safiyyah baki da wata aminiya data wuce nida buhaisa, haka nima bani da wata aminiya sama dake, kinsan bana boye miki damuwa ta. amah some time kina boye min damur ki bana takura ki da dole saina ji, shikenan. Ganin taji haushi kuma nima fa banyi adalciba, hannun ta na kama, kiyi hakuri kinji sis wallahi ba haka bane, nafad'a mata duk yadda muyi da shi. "Uhmm safiyyah ta kira kinsan menene? "Aa saikin fada isha" "Wallahi ki amince ta ko ina MD ya can-can ci a soshi. Don mutum ne nagar tacce wanda yasan ya kamata mai ilimi. A taikaice wallahi koni MD yace yana so tuni zan amince ba kiga yadda PA ta mutu akanshi ba amah bata gaban shi. Please kidai kara tunanin amah wallahi kun dace da MD sosai. "Murmushi nayi tom sisy nah nagode sosai muje to" "Itama murmushin tayi never mind sis nidai fatana ki amince wa bawan Allah nan, Tafad'a tana tada motor, Har kofar gida takawo ni kana ta wuce tana kara rokona murmushi kawai nayi na shiga bakina dauke da sallama. Mom ce da anty Waleeda kawai a parlour, ko firar mai suke ina shigowa suyi shiru dan ko sallamar basu amsa ba, To nasan hali tunda basu san mahimmanci taba. Gabanta naje ina fadin good evening mom, murmushi kwance a fuskata. Sanin ba amsawa zatai ba yasa na mike na wuce bedroom. Tom dama yaudin fa gaskiya na gaji. kasancewar program biyu nayi ga kaina har juyawa yake. Bathroom na shiga na wanke kana nayi wanka tare da dauro alwala, Bed nafada ina sauke ajiyar zuciya ga yunwa na kwakular cikina, amah nasan ba abinda zan samu a gidan nan, nikuma bazan iya girki ba dan kaina ciwo yake. Ganin fa zan cutu yasa na tashi, mayafi na daura akan towel din na fito kai tsaye kitchen na nufa. "Kamar yadda nai tsam mani hakan ce ta kasance dan kuwa bakomai hattana miyar basu rage ba, Garin kwaki na jika da Madara na zuba gyada, na fito duk da kallo su bini anty Waleeda na dariya kasa-kasa har nashige" ________ *Abuja🤍* Motocin shi ne su shigo gidan kai tsaye parking lot su nufa ajere su tsaya, kasancewar parking lot din akwai girma. Da sauri Samuel ya Kara so ya bude mai motar. yadau tsawon lokaci kafin ya fito gaba daya kamewa suyi har ya bargun youseef beye dashi, Kai tsaye ta babban parlour yabi. Aikuwa gaba daya 'yan matan gidan suna zaune, wasu sunyi group din fira, wasu waya, wasu chat, wasu koma iya su biyu ne, wato zaituna da azima kenan dan yanzu ma riga da wando ne ajikin ta. "Da sallam ciki-ciki ya shiga dan inba kallon bakin shi kayiba ba zaka ce yayi magana ba. Gaba ki dayan su nutsuwa suyi, Barka da dare yah Aj su hada baki gurin fada. Da kallo ya bisu daya bayan daya, "Ke" Ya furta tamkar mai ciwon hakori, Zaituna da tasan da ita yake tace Na'am yah Aj tana nufo inda yake tana wani rangwa d'a. Tom bema san metake ba dan hankalin shi bashi gareta, "Karna dawo na ganki a haka. Yafada yana haurawa upstairs, Me feenah zatai itada aynah inba dariya ba har da shewa. Zaituna da ranta yayi ko loluwar baci itama b'angaren granny ta nufa dan ta gane nufin shi ta cire kayan jikinta kenan. "Shiko kaitsaye dakin Ammii ya nufa. Haka yayi ta zuba mata shagobba san ransa saiki rantse shine auta kamar ba Wanda gaba daya yaran gidan ke tsoro har ma manyan shakkar sa suke. "Zakai dinner ne yau ko aa? Tafada tana kallon shi. "A'ah auta ta amso min Madara a gurin granny ita zansha" Tom dayake itama tasan halin nashi baya son cin abinci bare kuma na dare ya gwamace yasha Madara ko coffee. "Saida safe yayi mata yabi ta wata kofa da Kai tsaye part din shi zata kai shi............✍️ 🌹 RAYUWATA 🌹* *Story and written✍️* *Bilkeesu .S. Aliyu* _💞(Billy pinky)💞_ *🤝 Amanar nazari writer's association📚🖊️* *[07070260240]* _WhatsApp number or call_ _📚N.W.🖊️_ *Book 1 📖* *Page 20&21* "Yanzu zakaje ka gaishesu ne koh sai ka dawo? "Saina dawo yanzu time ya kure" "Allah yah tsaremin Kai ya dawo da kai lafiya Allah yabada sa'a" "Ameen yah Allah cewar Addah, shima Ameen yace yana sunbatar goshin ta kana ya fice cikin nutsuwa, dolene inka kaleshi ka 'kara kallo . Tunda ya fito compound din gidan tight security d'in dake zagaye da harabar wurin suka wani irin kamewa tare da sara mishi, Had'i da gaishe shi" "Hannu kawai yadaga musu tare dace wa kun tashi lpy? Cikin harshen turanci. Bai jira amasa warsu ba ya nufi" "Gurin shegun manyan car's d'in dake jibge wuri guda su nufa shida security d'insa. Zu'ke'kiyar ba'kar motar da juseph ya fiddo, Wanda ko makaho ya shafa yasan eh lallai kudi yayi aiki wurin siyenta. Dan sai wani irin kyalli da sheke take mai daukar ido. Gatan dai bata cika hayaniya ba kuma Bata mamaye waje ba. Tsaf take kala da yanayin matasan zamani irinsa dake gara kan nera bisa ga damar da ubangiji ya basu." "juseph ne ya bude masa motar ya shiga sanan Yuoseef ya shiga suma sauran security d'in shiga nasu suyi su fita a jere susa motar da Aj yake a tsakiya juseph ke driving" "Kai tsaye company su nufa" "Ganin katon company dasu zo yasani furta masha Allah gaskiya company ya hadu ga girma, a saman company dauke yake da wani tambari Mai kamar tauraro irin tambarin dake jikin motocin shi" "Har ciki su shiga guys d'insa su bude Mai motar, Saida yadau tsawon lokaci kafin ya fito gaba daya ma aikantan sai girma mashi suke." "office din danake kyautata zaton nashine, dan yafi ko ina tsaruwa, kuma security's ne aciki da wajen shi. ya shiga youseef beye dashi" ✨🤍✨ Uhm dan Allah meye ai bin wanan shigar granny? bama wannan ba ace yah majeed ya dawo amah baki gayama mummy ba? "To ban fada ba kinga daga ke har uwar taki inbaku rabu dani da zancen Abdulmajeedu ba wallahi zan saba muku. Kedashi kwata-kwata baku dace da juna" "Kamar zaituna zatai kuka tace granny kina nufin nida yah Aj bamu daceba?" "To banda abinki inake ina Abdulmajeedu? jikifa yara ba tarbiyya, jifa shigar dake jikin ki da sunan wayewa, shiyasa yaran 'kauye sufiku hankali wallahi. Takare maganar tana cigaba da damun furar ta," "Zaituna nashirin sake magana, granny ta zuba mata wani kallo, wuce ki bani guri kin wani tsayamin aka" "Harara itama tazuba ma granny tana wuce bedroom din ta," "Kwafa granny tayi tacigaba da abin da take tana mita" "Tana shiga ta danna ma mummy kira wayar na fara ringing ta fashe da kuka. Aikuwa mummy na dauka taci karo da kukan zaituna, nanfa hankalin ta ya tashi an ta'bamata shalele. Kinga ya isa haka fadamin meya faru? Nanfa ta shirya karya da gaskiya tafada mata, kuma granny ma wai nida yah Aj bamu daceba takai karshen maganar tana sake fashewa da kuka" "Kinga ki kwantar da hankalin ki, wallahi indai ina numfashi a doron kasar nan bamai auren majeed sai ke, Inko kiga baki aure Shiba to saidai bana numfashi wallahi. Bari Yaya ya dawo" "Yauwa mummy na shiyasa nake kara sonki wallahi sosai Allah ya barmin ke" ____🤍💗 "B'angaren Ammii kuwa bayan Aj ya fita ne take karaba addah hakuri. A'ah aminiya bakomai Nima jiya basma take sanar min ya dawo, kuma yau ina Shirin zuwa saiga fennah tashigo raibace, nake tambayar basma wai fada suke da zaituna. Yaushe zaituna nan tazo gidan nema? "Saida Ammii taja numfashi kana ta bude baki tamkar Bata son maganar tace. Okay nima fitowa ta kenan natar suna yi maybe yau tazo, Fitowar majeed nema sudena. Takai karshen maganar kamar bata so" "Ai kinsan yaranan sai addu'a wallahi Allah dai yashirya Mana" "Ameen yah Allah" "Daganan su cigaba da firar su irin ta aminai" _____________ *Kaduna✨* Tsaf su shirya cikin bakar abaya wacce ama kolliya da farin duwatsu sai takalmi Mai dan tudu. Safiyyah datai rolling din gale saita fito kamar balarabiya" "Sallama suyima ummi anty hajara na musu tsiya aikuma yawo salamu alaikum jiya an fita yauma haka. Dariya suyi su fice suna mata gwalo. Eyye zaku dawo kusa menine har ke ishan. tafada tana daga murya dan su jiyo ta da kyau" "A motar Isha mutafi. Kai tsaye gidan anty zainab muje antyn Isha. aikuwa taji dadi sosai anan muka dade dan sai gabda magrib mukoma gida. Isha tayi-tayi Dani naje na gaida momy nace mata insha Allah gobe kan natafi zan zo. Badin taso ba ta ajemu bakin get ita kuma ta karasa gida kasancewar anguwar su daya" "Koda mushiga ba kowa a parlour cikin sanda mu wuce sama Dan kar ummi taji mu tace yanzu mu dawo. Gab da zamu shiga daki saiga anty hajara nan. murmushi tayi tana fadin ummi! aida gudu mushige muna dariya. Itama murmushi tayi ta koma daki" "Saida muyi sallar isha'i sanan mu fito parlour lokacin ma dady ya dawo amah Banda yah saif. Muna cikin dinner ya dawo, shima nandin ya nufo. nice farkon tashi aikuwa ina zama yah Ansar ya kirani, munsha waya har nake sanar mai gobe zan koma gida, da kuma sa ranar anty hajara. yace ai ummi ta fada mishi, Har su gaisa da buhaisa da ganan muyi sallama. Yau bamu wani dade muna fira ba kowa ya tafi daki, koda mu shiga ma bamiyi wata fira ba nida buhaisa kasancewar mungaji ko bacci yake ji, *Washegari....* A hankali take bude idanun ta tasauke shi akan agogon dake ma'kale a bangon dakin bakin ta dauke da addu'a tashi daga bacci A round 8:30 ai da sauri ta duro a gadon Kai tsaye bathroom ta shiga bata wani dade ba ta fito da alamun wanka tayi duban ta takai kan bed din amah ba buhaisa alamun ya riga ta tashi. Wanka tayi lotion kawai ta shafa ta saka doguwar riga mai dan santsi da hula kana ta fito parlour. "Bayan sun gama breakfast, su tafi gidan su Isha, ai kuwa taji dadi sosai taja su suje su gaida momyn ta daganan su shige ciki fira su sha kamar baza su hadu gobe ba. Buhaisa ce dai yau haushi takeji safiyyah. zata tafi gida, saida suyi sallar ashar sanan su koma gida. "Kasancewar yah saif ne zaikaita" Tsaf tashirya cikin atamfa riga da siket Wanda d'inkin ya zauna daram ajikin ta kamar dan ita ayi, kasancewar tafi buhaisa kiba, shiyasa kayan su kamata sosai, gogaggen Hijabin ta tasaka hadi eyeglasses, facemask dinta kuma ta mayar jaka ta fito. Aikuwa buhaisa ta cika tai fam kamar zata fashe da kuka anty hajara ta tasata a gaba tana tono ta. Saidai da tasata kuka, daga baya su koma lallashin yar auta. Koda safiyyah ta fito itama lalashin tayi, ki kwantar da hankalin ki, bikin anty hajara fa yazo Kinga tun ana saura sati biyu zanzo to kinga ai na kusa dawowa. Badi taso ba yah saif yace kinga tashi mu tafi kar yamma ta cikayi. Sallama suyi da ummi da anty hajara kana su tafi. Har kofar gida ya kaita shirin fitowa take taji ya rikemata hannun ta waigowa tayi tana Mai zuba mai hararar da ita kanta bata san ta Mai ba, "Hannun ya saki yana dan wayan cewa, tafiya zaki ba sallama? Ko kinyi kewarsu ne? Ya jera mata tambayar ajere. "Kai kawai ta daga mishi tare da cewa kadan. "Kiyi kewar tasu? "Uhm "Tom shikenan sai yaushe kuma? "Yatsun hannun ta tadaga mai guda biyu tare da cewa week. "Two weeks? ya fada yana kallon safiyyah. "Uhm "Yar kurma kenan wato na isheki koh Tom shikenan sai munyi waya. "Baki tadan turo jin ya kirata da yar kurma, Amah batace komai ba saida ta fita hannun ta rike da murfin motar kana tace. "Thank you yah saif Saida safe, ka gaidamin da sisy nah please. Ta hada hannu wan ta alamun roko. "Baki ya saki yana kallon ta, saida ta rufe murfin motar, kana ya dago da sauri har takai bakin get. Saida yaga shigarta ya sauke ajiyar zuciya kana ya tada motar ya tafi. "Saida motar shi ta tafi ta dago daga leken da take tana sauke ajiyar zuciya, ga baki daya tsoran shiga take amah haka ta dake tai sallama a kofar parlour. "Gabaki dayan su suna zaune a parlour daga mom har anty Waleeda da yah safwan dashi ba zaman gidan yake ba sai baby. "Aikuwa da gudu baby tazo ta rungume ni nima rungume ta nayi muna kara sawa cikin parlour. Tunda nayi sallama su zuboma kofar ido harna karasa ina gaida mom, "Abin mamaki saida na ta'bata ta d'ago firgigit. Kuma ta amsamin harda tambaya ta yasu ummi, Amsa wa nayi ina gaida yah safwan shima dai amasa wa yayi tare da cewa ina kishiga ne safiyyah? "Naje gidan ummi ne . "Oooh shiyasa abincin ma sai anga dama akeyi a gidan kenan? Bance komai ba na tashi na nufi anty Waleeda na rungume ta, duk da tana tureni amah ban damu ba dan ba karya nayi kewar su. Yadda nai tsam mani hakan ce ta kasance Dan parlour dai sai addu'a wallahi. Ina mamakin san jiki irin na mom da anty Waleeda. "Bedroom nashiga na barsu da mamakin dawo wata, dan itafa mom batai tsammani zan dawo ba. To shima dai bedroom din sai addu'a dan yama fi parlour datti, Jaka tana ajiye ina Mai leka bathroom wayo Allah, na furta ina mai fitowa da sauri. Parlour na fito na wuce kitchen na dauko kayan shara, bedroom din na share tare da yin mopping. Na koma bathroom shima share shi nayi abin takaici ga pad nan haka duk na hada na share kana na wanke bathroom din. "Saida akira magrib na gama aikin, yah safwan nata min sannu da yake shi ba halin mom ya biyo ba. "Around 4:00 Natashi, raka'a atul fijir nayi kana nai sallah asuba tare da azkhar, nafara karatun alQur'ani ban wani dau lokaci ina yiba natashi nafara gyaran gidan kafin karfe 7:00am nagama komai har girki, Wanka nayi har na fito anty Waleedah bata tashiba bare tayi sallah tashinta na kumayi, me hali baya fasa halinsa dan yauma masifa ta hauni da ita kyaleta nayi na cigaba da kintsawa. "Tsaf na shirya cikin less pink wanda amai ado da fararen duwatsu, dinkin riga da siket, simple makeup nayi dan kuwa daga fouda, sai kwalli, da lips gloos, and maskara, da na taje eyelashes dina dashi aifa ya fito gadar-gadar Masha Allah, kalba na hade na daure da ribom, Parlour na fita dan na karya bakowa a parlour sai yah safwan, gaisawa muyi tare mu karya dan shima zai fita gurin aiki, Jeki dako mayafi na ajeki, Tom yah safwan. Gogagen milk hijjab nasaka da face mask da eyeglasses sai plate shoe shima pink waya ta nadauka nasaka a hand bag na fita, Su anty Waleeda suna ta sharar bacci harna mu tafi Muna zuwa ya bani 1k godiya na mai ina karasawa ciki. Yauma Isha ta rigani zuwa ban dade da zuwa ba mu fita gabatar da program din ranar Thursday da ba muyiba. "Bayan mun gama mukhtar yake cemin MD na kirana, Kai tsaye office din nashi na nufa ina shiga, PA dinshi da sai cin magani take ta min iso gurin shi, ban damu da kallon da take minba na karasa da sallama. "Tsaye na ganshi sai zagaye office din yake, Nima tsayawar nayi ina furta, good afternoon sir! Nuna min gurin zama yayi shima yana kai zaune. Jin ya kafeni da ido ya sani na dago daniyar magana dan nifa na tsani kallo, shikuma ya kware indai gurin kallo nane. Yah jikin naki? Ya jefomin tambayar da saida na dago na kalleshi. Ai naji sauki! Nafada ina kasa da idona . Masha Allah! Dama dalilin da yasa na kiraki ina son magana dake ne, Uhm inajinka na fada cike mamakin wacce magana zaiyi dani. "Cikin bazata matukar bazata na d'ago ina kallon shi jin maganar da banta b'a tsammani daga gare shi ba. "Wallahi safiyyah ina son ki ina burin ki zamo uwar y'a'yana tun randa na ganki naji ina sonki wallahi, tinanin ki ya hanani bacci, har gidan ku naje acemin Wai banan bane gidan, ko sawa nayi yau tayi please kar kicemin aa. Ya karasa maganar kamar zaiyi kuka idon shi na tara kwalla. Ni wallahi dariya ma yabani da tausayi gami da kunya. "Na baki lokaci safiyyah kije kiyi tunani da kyau, Insha Allah duk abinda kika yanke zan amsa da hannu biyu, amah kimin adalci please. Ya 'karasa maganar cike da magiya. Kai kawai na gyada mishi na fice daga office din, Kai tsaye office din mu na nufa, mu cigaba da abinda muke, gabaki daya tunanin maganar nake. to ya akai ma yasan gidan mu, haka dai har atashi takardun dazan kaima ma cewa nayi Isha takai mu hadu a mota, Koda ta tambayeni cewa nayi bakomai na wuce. Da ta dawo take sake tambaya ta, meya faru naji MD yace intaya shi rarrashin ki? Bakomai! Na fada irin banson wata tambayar, Amah safiyyah baki da wata aminiya data wuce nida buhaisa, haka nima bani da wata aminiya sama dake, kinsan bana boye miki damuwa ta. amah some time kina boye min damur ki bana takura ki da dole saina ji, shikenan. Ganin taji haushi kuma nima fa banyi adalciba, hannun ta na kama, kiyi hakuri kinji sis wallahi ba haka bane, nafad'a mata duk yadda muyi da shi. "Uhmm safiyyah ta kira kinsan menene? "Aa saikin fada isha" "Wallahi ki amince ta ko ina MD ya can-can ci a soshi. Don mutum ne nagar tacce wanda yasan ya kamata mai ilimi. A taikaice wallahi *🌹 RAYUWATA 🌹* _Story and written✍️_ *Bilkeesu .S. Aliyu* _💞(Billy pinky)💞_ *🤝 Amanar nazari writer's association📚🖊️* *[07070260240]* _WhatsApp number or call_ _📚N.W.A🖊️_ _*_Masu comment gaskiya comment dinku yana sani nishad'i sosai*_ *_Kuna cikin zuciyar Billy pinky kuna dabbane wallahi my fans_🥰🤗💃💃* *22&23* "Kamar ko yaushe ba abinda parlour yake sai kamshi mai sanyaya zuciya mai shaka, Youseef dake biye dashi ya ajeye mishi laptop wayoyin shi, tare da furta sir baka bukatar komai? "No youseef kaje Saida safe" "Thank you sir Allah ya tashemu lafiya" "Ameen" Ya amsa asaman labba. "Bedroom ya nufa Koda ya shiga zama yayi a gefen bed yana bin ko wacce kosurwa da kallo kamar mai san ganin wani abu, Mikewa yayi ya fara zame kayan jikinsa domin shiga wanka. Yaja tsawon lokaci kafin ya fito sanye da bathrobe ash calour sabuwa dal dan yadda take wani maski-maski zai tabbatar da hakan karamin towel dake hannun sa ya kai kan ji'ka'kiyar sumar kansa mai tsawo data kwanto masa har fuskar sa. Kai kace ya hada jini da larabawa, Tamkar bashi kadai bane a dakin fuskar sa adaure ba alamun rahama a cikin ta. Gurin mirro ya nufa hand dryer din dake gaban mirror ya jona a socket, cikin 'kan'kanin lokaci ya kammala gyara ta, lotion ya shafa sama-sama sai sprays dinsa masu shegen kamashi sanan ya nufi close d'insa, fari pyjamas mai shegen kyau da laushi sai boxer shima dai sabo, tsaf yayi shirin nasa ya koma gaban mirror yayi wakan tsaddadun turarukan baccin sa masu kamshi kamar ba dare ba, Kai tsaye parlour ya nufa tsit yake sai karar tv da yake ta aiki, zaune yakai kan sopa, madarar da auta ta kawo masa yanab wanka, ya zuba a cikin karamin mug yana sha yana aiki a laptop. Sai 12:pm ya wuce bedroom ya haye bed ya kwanciyar sa kace wanda bashi da wata damuwa a rayuwar sa, saida yayi addu'oin kwanciya bacci ya lumshe idanun sa, kafin wani dogon lokaci ya fara sauke numfashi a hankali alamun yayi bacci. _____✨✨ Koda zaituna tashiga granny na ganin yadda tashigo rai bace, yasa ko kallon ta batai bahar ta shige bedroom din ta. Koda auta tazo amsar masa madara saiga tanan ta fito wai tabata takai mishi, a'aa kibarta takaimi shi ita ya aiko, kuma kinsan halinshi basai na fada miki ba, inba so kike daga ke har ita ranku ya baciba. Kinga habibah ga madarar can acikin fridge ki dauka ki kaima sa, Tom granny auta ta fad'a tana tashi, Madarar ta dauka kana tai musu saida safe. Granny ce kawai ta amsa amah zaituna tsaki tayi tana tashi, Kinga wallahi in baki fita min hanciba zan feto ki, ya zaki zo mun daki kina min tsaki kamar dangin tsaka, akan wanda besan ma kinai ba, kinsan Allah ko yasan kinayi zan hanashi auranki, tinda ku baku da kunya, daga ke har uwar taki kallon ku nake. A batace ba sai baki da take turowa tashige daki, Kwafa granny tayi taciga da kallon Indian film din da akeyi, yadda ta kafe tv da kallo zaka dauka tasan me akeyi, lokaci-lokaci takan ja tsaki da fad'in tirr. (Hajiya granny tamu dama ina ke ina kalon Indian film😂) "Koda taje kaimai madarar taga bashi a parlour, ta d'an zauna daga taji shiru ta ajiye mai takama kanta, mezata zauna tayi wayace tun rana an kawo mata ita kud'i kuma taji alert. ___________ *Kaduna✨* Kadan nasha garin kwakin na ajiye shirin kwanciya nake saiga Kira, Bakuwar number ce kamar bazan dauka ba dan kuwa Saida ayi 2 miss call kana na dauka. "Assalamu alaikum" Cikin mamaki na ciro wayar ina kara dubawa kamar fa muryar MD nakeji, jin ance Safiyyah yasa ni maida wayar ina amsa mai sallama, "Zakiyi mamaki ina na samu number ki koh?" "Uhm" "Agurin Isha na amsa, kin koma gida lafiya? "Lafiya lau" Mum dade muna wayar shike firar nikam Iya kaci nace uhm, uhm-uhm, kamar wata kurma. Bayan munyi sallama, yah Ansar da tunda muke wayar ya kirani na kira, "Assalamu alaikum Yaya nah" Wa'alaikis Salam little sis yakike? Lafiya lau alhamdulila! Kin koma gidan ne? Eh yah na dawo tun jiya yauma har gurin aiki naje" Masha Allah komai dai lafiya? Alhamdulilah! yah Ansar ya aiki? Mundad'e muna waya kam, har yake cemin ranar Friday zai dawo, naji dad'i sosai dan kuwa kamar na jawo ranar tazo, Koda muyi sallama bathroom na shiga na dauro alwala, kwanciya nayi ina karanto addu'oi kwanciya bacci ban wani dade ba kowa ya daukeni. Yauma kamar ko yaushe bayan na gama duk aikin gidan dan har breakfast nayi, tsaf nashiya cikin jar abaya mai ratsin fari, wace amah ado da fararen duwatsu, sai takalmi mai dan tudu white, ribbon nasa na daure kaina, mayafin abayar nasa nai rolling da face mask da eyeglasses sai takalmi mai dan tudu white, wayata Dana saka a hand bag ce tafara ringing, hello yah safwan" "Kifito mutafi" Bai jira me zance ba ya yanke Kiran, Har gurin aiki ya kaini ya bani 1k, godiya na mishi, ina shirin shiga saiga motar Isha nan tare mu shiga da ita Kasancewar yau munada program akan matasa, mu'az yazo mutafi domin fara gabatar da program din, tini babban bakon mu ya iso, dan haka cikin kan-kanin lokaci mu fara kasancewar an gama shirya komai. Motsi kadan idon MD akaina dan har ya fara takurani da wannan kallon nashi, Koda mu gama cafeteria mu nufa domin cin abinci bayan munyi order muna cikin cin abinci saiga MD, kujerar kusa dani yaja ya zauna, hakan da yayi yaba ma kowa mamaki, kasancewar MD akwai jiji da kai gami da miskilanci dan haka suke mai kallon mai girman kai, ban dago na kalleshi ba naci gaba da cin abicina, da Isha su gaisa yasa amishi order, sai a lokacin na gaishe shi dan banso yau mu hadu dashi ba. Aikuwa murmushi kwance a fuskar shi ya amsa, Shiya biya kudin order bance komai ba sai Isha ce ta mishi magana, a gurin mu barshi mu tafi. Isha ce yau ma takai ni har gida, mun dade muna fira a mota kana ta tafi ni kuma na shiga. _________ *Abuja🤍* Cikin nutsuwa gami da nagarta yake sa'kkowa daga mata'kalar benen, Sanye yake cikin sute black sai neck tie golden, takalmin kafar sa da yake black kolliyar shi ta kasance golden, sumar nan tasha gyara ta kwanto masa har fuskar sa, hannu ya kai yana matsar wa, ga wani kamshi da yake mai saka nutsuwa, tun kan ya karaso 'kamshin sa ya riga shi isowa, gaba daya suna dining area har Ammii, ido su zuba mishi a sace har ya 'karasa yaja kujera kusa da Ammii ya zauna, Cikin girma mawa yake gaishe ta itama cikin farin ciki ta amsa mishi, suma gaishe shi suyi cike da girma mawa tunda yace lpy bai sake amsawa ba, to dama shi haka yake 'kar-'karin amsawa dai lpy. Shiya fara tashi a dinning din sai zaituna yau dai balefi doguwar riga ce ajikin ta, "Majeed harka gama? "Uhm Ammii zanje na gaida granny ne" "Okay jiya dama da naje gaishe ta take tambaya ta nace ka tafi company tom inka fito kaje ka gaida su addah" Saida fuskar sa ta canja, kai kawai ya d'aga mata kana ya nufi part din granny. "Murmushi tayi tasan because tace yaje ya gaida su addah ne yasa shi bata rai" Granny dake zaune kamar ko yaushe ta zuba ma tv ido, ba kamar jiya ba yau program take kalla na gidan tv haske inda safiyyah suke gabatar da program akan matasa A dai-dai lokacin da Majeed ke shigowa da sallama ciki-ciki, a dai-dai lokacin safiyyah ta sake magana cikin zakin muryarta. Shawara ga matasa ya kamata ama tsayin ka na matashi kari'ke martabarka ta matashi, wanda a yanzu haka yayi 'karanci ga matasan mu, kullum idanun su akan 'yan mata, burin yin kudi kota halin 'ka'ka, daukar shaye-shaye a matsayin wayewa, raina na gaba dasu saboda suna jin tashen balagar samartaka, rashin yin biyayya ga iyaye saboda jahiltar wayewar zamani, da kaga ka kai tsawo shikenan iyayenka sun zama abokan wasanka, fifita ilimin boko fiye da na addini, Dan Allah taya za'a samu nasarori a RAYUWA? Kalilannefa a cikin ku masu irin wannan 'kya'kya'kywan tunanin, 'karancin su yasaka kowa ganin tamkar babusu. Dan Allah matasan mu ku gyara please, kune ginshi'kin kowacce al'umma, daku duniya take alfaharin, kudena shaye-shaye, domin kullum ruguza ku yakeyi, ya ruguza 'kasashenmu da al'ummar mu, ku Dena zina, kullum durkusar daku take da 'kaskantar daku, ku dena barandar siyasa inba hakaba kullum a 'yan turin mota zaku 'kare, Dan girman Allah ku farka daga nauyayen baccin daya d'auke ku, ku daidai ta RAYUWAR ku, nutsu kuyi karatu, ku daina karatu domin burin aiki, karatu wata katangace a gareku, idan kun kammala koba aiki ku nemi sana'a kudena girman kai, 'kila wannan sana'ar itace mafi alkairi a gareku amah kullum burinku 'katon office why? "Dan Allah ku sanja ku zama jarumai" A hankali ya sauke ajiyar zuciya yana me janye idanun sa akan tv daya kafe safiyyah dasu har tagama jawabi, baya ganin fuskarta sosai, kasancewar sanye take da eyeglasses sai facemask dinta data jawo kasa dan da kadan ya wuce bakin ta, Masha Allah masha Allah gaskiya yarinyar nan na matukar birgeni, ka duba fa yanda take jan hankali ga matasa bama iyasu ba kawai, da ace matasan mu zasu dauki shawar ta ai sun sauya da yawa, Allah yamiki albarka d'iyar, nan kaima Allah yabaka mace irin wannan" Da ameen yah amsa asaman labba kana su gaisa, Yauma kamar fadi Saida ta kuma mishi maganar aure aikuwa ya hadde fuska yace, kinga granny please kidena min maganar, nan wallahi banaso dan ni har yanzu banga wacce tamin ba, yakai karshe yana sauke ajiyar zuciya. Nifa bana son iskanci meye wani pilis kace kome oho, nifa in bazaka mun hausa ba to kamin shiru basan wannan cakod'addiyar hausar nan taka. Takai karshen maganar tana balla mishi harara, Murmushin gefen baki yasaki tare da fad'in, ayya sorry my granny tafad'a yana mikewa saina dawo, Fuska ta sake hadewa jinya 'kara mata turanci, saida ya kama handle din zai fita tace Allah yah tsare ya bada sa'a. "Ameen ya amsa a saman labba kana ya fice, kai tsaye part din uncle Abdullah ya nufa a parlour duk ya same su har uncle Abdullah yana shirin fita, zama yayi su gaisa kana su gaisa da mama matar shi kenan, Tare su fito uncle abdallah ya tafi shi kuma ya shiga part din uncle sulaiman, su ma dai a parlour ya same su addah sai kuma Umma amarya. Cikin fara'a su gaisa da addah, ita kuwa Ummu amarya irin miskilan matan nan ne haka su gaisa ba fara'a, koda ya tashi zai fita da wani kallo me kama da harara ta bishi har ya fice. (Toh🤔ke kuma ummah amarya yada haka) Fuskar nan a daure kamar wanda a aikowa sakon mutu, Kallon shin yakai kan agogon dake daure a tsin-tsiyar hannun sa kirar diamond, Time ya tafi da yawa gashi yau aikwai abubun da yake sonyi da yawa maybe ma tomorrow zai bar kasar, Gashi ya dawo baije yaga yadda abu-buwan shinsuke ta fiyaba duk da youseef ne tsaye a kan komai. Tsaki yasake ja akaro nabiyu, Har ya isa babban parlour, Da youseef ke jiran sa. Youseef na zaune suna gaisawa da Ammii, shima koda ya shigo sallama suyi da Ammii ta bishi da addu'a har lokacin 'yan matan gidan na parlour. zaituna kam ita tashi ma tayi tabi bayan shi, aikuwa fennah ta hade rai jira kawai take taga dawowar zaituna. Ammiii kai kawai ta girgiza ta tashi ta haura upstairs, Koda ya fito tini motocin daza su fita an shiryasu, kasancewar sunji ogan nasu shirune ma su fito suna jiran fitowar sa, youseef biye dashi gaba daya kamewa suyi su na gaishe gaisawa suyi ya shiga mota, because tini Yuoseef ya bude mishi, a jere motocin suka fice. Kaitsaye wani katafaren company su nufa, masha Allah shine abinda nafurta gaskiya company ya had'u, A saman shi an rubuta AA SARAKI MOTORS, da manya baki idan blue ta kawo, sai pink, sai red, kalolidai da yawa. __________ *Kaduna✨🤍* Tini na amshi soyayyar MD because MD ya can-can ci a soshi, Soyaya muke cike da aminci dan har a gurin aiki sun lura da haka, PA d'insa ce dai haushi kamar ya kashe ta, to ban masan tanayi ba saidai naji ana fada, Iyakacin ta harareni bana nuna ma nasan tanayi. Yau Friday cikin farin ciki na tashi because yau yah Ansar zai dawo, gurin aiki ma jinake kamar kar naje, Amah haka natashi nafara aikin gidan, bayan nayi sallah nai azkhar da karatun alQur'ani, Tsaf nagama komai na gyaran gidan dan kuwa har breakfast nayi, Yau so nake in ma yah Ansar girki mai dadi, shiyasa na'kiyin miyar dan nasan muddin mom tasan yah Ansar zan ma girki wallahi ba barina zatai ba, Bayan ko kayan abincin shike siya, wataran yah safwan inya gadama yayi cefane amah ba a sanran mom ba, Tsaf nashirya cikin doguwar riga ta atamfa, pitet sai goggagen hijabi na saka har kasa sai facemask da eyeglasses sai plate shoe, A gurguje na shirya saboda yah safwan na jirana, Turaruka kwai na fesa sai hand bag dana dauka nasaka waya ta aciki na fita, Ina fita parlour naga Abba da mom Abba na karyawa da alamun yau fitar wuri zaiyi, Danni rabon danasa Abba a idona ma na manta. Har kasa na duk kusa ina gaishe shi, Yau kam da d'an fara'a a fuskar shi ya amsa, harda min addu'ar Allah yabada sa'a, cikin farin ciki na d'ago ina kallon Abba, kwallar data taru a idona ban bata dama zubowa ba, Ameen yah Allah Abba nah, Ganin yadda mom ta hade girar sama da ta kasa tana kallon Abba, murmushin takaici nayi nafice a parlour dan bata dago ta kalleni ba bare in saran amsawa, To da yake yanzu ma wasan buya muke da ita, tace min waya zo nemana, nace bansani ba kuma nasan akan MD take magana, da yazo lokacin dana tafi gidan ummah halima. Har gurin aiki ya kaini koda ya ajeni na shiga ciki dan Isha yau tarigani zuwa, Office din MD naje domin ance yana nema na, da harara PA din tasa ta bini har na shige, Koda nashiga gashe sa nayi tare da fad'in gani sir. Murmushi kawai yayi tareda nuns min gurin zama, ba musu na zauna ina gyara fuskata, ganin yadda nayine yasa, Yafara min bayanin program din da zamu yi ranar Monday, "Please baby ki nutsu kiduba da kyau, "Insha Allah nafada ina ficewa daga office din. Yau da wuri mutashi aiki kasancewar yau Friday, Har gida MD ya kaini kasancewar yanzu shike maidani gida yace Isha ta huta. Kuma har yanzu mom batasan shike kawoni gida ba, Har nakai hannu kan handle din kofar najita a rufe, juyowa nayi ina kallon sa ganin shima kallon nawa yake yasa nai 'kasa da kai, meya "samekine yau naganki cikin farin ciki baby? "Uhmm maybe yanada nasaba because yah Ansar zai dawo. Wow, baby shine baki fad'amin ba? "Sorry farin ciki ne yasa na manta afwan" "Shikenan dama inaso na tambayeki amah naga kin kosa ki tafi mayi waya kawai" Okay kawai nace murmushi kwance a fuskata, Bye nace ina fita a motar, saida nashiga gida sanan yatada motar ya tafi. Koda nashiga bakowa a parlour, naji dad'i hakan kuwa, bedroom nashiga kaya kawai na cire nasaka doguwar riga mara kauri, Kitchen nashiga girki nafara mishi cikin kan kanin lokaci nagama na gyra kitchen, har lokacin banji motsin su mom ba dan alama ya nuna basu gidan, nakin shi naje nakara gyara shi duk kan natafi gurin aiki na gyara nasaka tsin-tsiyar kanshi. Koda nakirashi ma yana cikin kaduna ya kusa 'karasowa. Bathroom nashiga nai wanka koda na fito doguwar riga nasa nara nauyi, Ina gaban mirror inasa turare saiga kiran Buhaisa, bayan mun gaisa take cemin inan zuwa gobe sisi! Allah yah kaimu amah dai zani islamiya kinsan wancen week din banje ba? Nima sai yamma zanzo saboda wannan shugiyar matar! Kai sis mom dince shegiya? "Ai tamafi haka wallahi" "Umm Allah ya shirya yaufa yah Ansar zai dawo. "Eh yafada ma ummi dalilin zawana da yamman kenan kinga ko dare nayi ya maidani" "Hakane tom Allah yah kaimu goben ki gaidamin ummi da anty hajara jiyama miyi waya da ita" Ameen tom zasuji, amah amah yah Ansar dinfa ko kuna wayane? Uhmm munayi" Da gaka muyi sallama da ita. Tunda shigowar mota nasan yah Ansar ne naje na dako mishi jaka, Shikuma ya shiga wanka, kafin ya fito na shirya mishi abinci, koda ya fito zaman ci yayi, muna fira irin ta yayah da kanwa saiga mom nan kamar an jefota, motar uban wa nake gani a gidan nan ? Ko kulata banyi ba bare innu na nasan tanayi, sumar tsaye tayi tana bin yah Ansar da kallo. __________ *Abuja 🤍* Kasancewar yau dady zai dawo sai aiki ake a gidan, gaba daya 'yan matan gidan ma suna part din Ammii har Addah ma nacan, da mama, amah ba banga umma amarya ba, masu aiki kam sai kai kawo suke. Wata motace tashigo gidan ko parking bata gama dai-dai tawa ba ta kashe motar ta fito. dattijuwar matar data fito wacce kamar su daya sak da zaituna sai kuma uncle sulaiman, fuskar nan kwata-kwata ba alamun fara'a acikin ta, cikin shiga ta alfarma, security dake harabar gidan sai gaisuwa suke mi'ka mata amah bata dago ta kallesu ba bare susa ran amsawa, Taku take cike da izza hadi da takama kamar wata sarauniya, tinda tashi go main parlour gaba daya su zuba mata na mujiya, wasu kam mamakin ganin tane ya bayyana 'kara-ra a fuskar su...............✍️ _Taku har kullum da ko yaushe_ _🤝 Amanar haske writer's association📚🖊️_ *Please🙏 comment and like and share fissabilah👏👏* *🌹 RAYUWATA 🌹* *Story and written✍️* *Bilkeesu .S. Aliyu* _💞(Billy pinky)💞_ *🤝 Amanar haske writer's association📚🖊️* *_[07070260240]_* _WhatsApp number or call_ *📚N.W.A🖊️* 🅿️➖24&25 Dagudu zaituna tazo ta rungume ta, "Oyoyo mummy" Sai time din tasaki murmushin gefen baki tana shafa kan 'yar tata, kujera mai zaman mutum daya ta zauna ta d'ora kafa daya kan daya. gaba daya 'yan matan dake parlour suka gaisheta cike da girma mawa, ta amsa fuska a tsuke, zaituna kuwa na ma'kale da ita kamar wata jaririya. (Too🤔 da alamu ke majeed ya gado a miskilanci, duk da dai Ammii ma ba daga nan ba kamar jinin sarauta) Barka da zuwa su addah da mama su mata, ta amsa cike da isah tana ma Addah wani kallo. Ammiii ce ke sauko daga upstairs cikin shiga ta alfarma, shadda ce sai maiko take, taji aiki sai wal'kiya take dinki abuja bubu, sai k'amshi take zubawa kamar wacce tai barin turare, ga wata uwar sar'ka da dankune, abun hannu, harma da zobe sai zuba kyalli suke daganin su na gold ne, waya ma'kale a kunne ta, har ta karaso ta zauna, yanda duk subita da ido har mummy sai tabe baki take zai tabbatar maka da tayi kyau, " A'aa zakiyya yaushe ki zone? " Umm wallahi yanzu nazo naga Yaya ma bai 'karaso ba " " Oooh tom sannu da zuwa ai ya kusa shigo wa " " Okay " Kawai mummy tace tacigaba da latsa wayar ta, Fira Ammii suke da su mama har papa ya dawo. Gabaki dayan su harabar gidan su fita, kyakkyawan dattijo daya fito daga mota fuskar sa kwance da murmushi, Kamar su daya da auta dan da gani kamar sa ta d'ako, taje da gudu ta rungume shi tayi tana zuba mishi shagobba, itada su azima, bayan sun shiga ciki zama yayi ya gaisa da kowa, kana yace bara na dan watsa ruwa yafada yana mikewa, " To Yaya a fito lafiya cewar mummy. " ya amsa da ameen ya nufi upstairs Ammii tabi bayan shi" wani kallo mummy ta bisu dashi me kama da harara. sai lokacin ta nufi part d'in granny zaituna beyi da ita, suma su addah part din su nufa. 'yan matan kuwa ba wacce ta tashi saima fira dasu dora, har auta da bakinta ya'ki rufuwa saboda farin ciki. Ranar duka family a mai parlour suyi dinner, ana fira cikin farin ciki, anka cire granny, da yah majeed da kwata-kwata bangan shiba, da alamun bashi ma a kasar, ita kuwa granny tana ji da kafarta, Bayan duk sun kamala da dady dasu uncle sulaiman kai tsaye part granny su nufa har matan nasu, fira suke cike da farin ciki, da nishad'i, saidai k'alilan a cikin su da sai kalura zaka gane nayin fuskar su, Sallama suyi mata kowa ya nufi part din shi, because dare yayi, "Mummy dan Allah kima dady magana auren mu nida yah Aj, wallahi mummy jinake kamar in rufe idona inga na zama matar shi, takai karshen maganar hawaye na zubo mata. Gabaki daya hankalin mummy ya tashi, itafa a rayuwa ta tsani taga hawayen diyar ta tilo kwallin kwal, Ki kwantar da hankalin ki ai wallahi indai inada rai majeed bashida wata mata sai ke, meyasa kike tada hankali kine wai akan abinda kisan bazai gagare niba, Yanzu dare yayi zuwa gobe za muyi magana da yayan, ki kwantar min da hankalin ki kiji dear, " Tom mummy nah " " Tashi kije ji kwanta " *Washegari...*ma gabaki dayan su tare suyi breakfast, bayan sun gama masu zuwa gurin aiki su tafi mazan su da matan su. Mummy ce dai tunda su gama bata tashi a parlour ba, itada 'yan matan gidan, har dady ya wucce dakin shi, shigarsa baifi da minti arba'in ba tabi bayan shi, Da sallama tashiga tana bin 'kayatacen parlour nashi da kallo dayaji kayan more rayuwa, sai k'amshi yake mai sanyaya zuciya, wannan gyaran Ammii ne dan ita macece wacce tasan mahimmanci tsafta, kuma take bata muhimancin, shiyasa k'amshi da yake part din ta daya ne dana yah majeed. Bakowa a parlour sai sautin k'ira'ar dake tashi a TV, kujera tasa mu ta zauna ta daura k'afa daya kan daya tana bin ko ina da kallo, B'angaren su amah suna zaune suna fira da dady suji sallamar mummy, koda su fito suma zama suyi dady yace, " Zakiyya ce ashe? " Eh Yaya nice dama magana zamu yi tafada tana kallon Ammii " " Oooh to bara na baku guri Ammii tafada tana mi'kewa " " Aa yi zaman ki Bilkeesu, dady ya fada " " Yaya barta ta bamu guri maganar mai mahimmanci ce, ta karasa maganar tana bin bayan Ammiii da kallo da tuni takai kofa. Shidai dady kai kawai ya gyada tare da fad'in, " ina sauraren ki " "Dama Yaya akan maganar majeed ne, ace yaro ya girma har yanzu ba aure duk ga sa'oin shi na dangi kowa da yaron shi,ba daya ba ba biyu ba, amah Yaya haka zamu zuba mishi ido yana abinda yake so. kaima ai zaka so ganin jikokin ka tunda Bilkeesu tayi majeed, tayi habiba, shikenan shiru akeji da alamu ma s, "Hannun da dady ya daga mata ne yasa ta hadiye maganar data ke son fada ta daro da fad'in" Yaya ai gaskiya ce wallahi, in baida buduwar ma ai mu saimu zaba mishi ba ma zuba ido muna kallon shi yana abinda ya gadama ba, ga 'yar uwar shinan zaituna sai hada shi da ita ai baya k'i jinin shi ba, itama kuma tana mutukar sonsa, kaga Yaya sai ayi tuwona maina, akara kulla zumunci wallahi. Dafa irin auren 'kauye ne da tini majeed yanada jika wallahi bama 'ya ba, Hajja ma kullum fadan ta akan rashin auren shi, ga uban dukiya ai yasamu magaji nan kusa shima ya huta. Amah Yaya gaskiya ya kamata a duba magana ta sosai, kuma wallahi zaituna na mutukar son shima tunda kamar tsoran matan yake, ina bashi ita bazai damu ba kuma 'yar uwar shi, koya kagani Yaya? Takai karshen maganar tata murmushi kwance a fuskata tana kallon dady ganin kamar ya gamsu da maganar ta. Okay shikenan zakiyya kije zanyi tunani, kuma zan tun tubi su sauran da kuma hajja duk yadda mu Kai shikenan, Nima rashin auren nashi na damuna, amah inkiyi dubi da kwata-kwata becika samun zama ba, yau yana can gobe nan, kuma auren ma kwata-kwata bashi a gaban shi ne, anya kuwa zai amince? "Dady yakai karshen maganar damuwa kwance a fuskar sa" " To Yaya yazai yi in bai amince ba a dole ma saiya amince, tunda in mun zuba mishi ido to wallahi bayi zaiyi ba, tunda shima yana shirin kamawa d'abi'ar turawan nan wallahi, kuma daka kyale hajja in komai ya kamalla shikenan ni zan fara mata magana. " A'ah kinsan hajja ce ya kamata tariga kowa ji, Allah dai ya zaba abinda yafi zama alkairi " " Ameen yah Allah Yaya bari naje a huta lafiya Allah yakara nisan kwana " __________ *Kaduna✨* Oho ashe kaine ka daowo dole ka cike mana tsakar gida da waccan shegiyar motar, "Barka da dawowa mom" "Kai dakata ban bukata, ke kuma tunda Yayan naki zai dawo shiyasa ki tafi bakiyi miyar ba koh? kinga safiyyah ki fita idona in rufe, kuma abincin in shikadai kima to yadena ci yaje waje ya siya dan da yunwa na dawo. Tunda tafara maganar har takai karshe ban kalleta ba itama saida ta ida sanan ta karoso parlour tana bin ko ina da kallo, Da gudu baby tazo ta rungume yah Ansar kanta ya shafa tareda cewa baby kin girma, "Fuska ta rufe alamun jin kunya kai yah Ansar a hakan primary 6 fa nake" "Eh mana baby daga primary 6 din basai jss ba? "Ke dalla zoki wuce banza mara zuciya wuce muje twssss" ta fizgi hannun baby tana turjewa zata kwace bata saurare taba su shige bedroom din ta. Kai kawai yah Ansar ya girgiza ya cigaba da cin abinci shi muna fira, Ranar har sha biyu muna fira yah Ansar har na bashi labarin MD, kodama ya kira maganar daya ce zamuyi cewa nayi mayi waya da safe. *Morning* Bayan nagama komai na aikin gidan dana sabayi, dan har breakfast munyi nida yah Ansar because shi zai kaini. Tsaf nashirya cikin goggagun uniform din islamiya ta, na daura nik'ab sai eyeglasses da nasa alQur'ani na dauka na fice, Yah Ansar ne ya kaini har islamiya, ya zauna su gaisa da yah sayyadi mu because abonkin shine daganan kuma ya tafi. Koda nashiga class mu gaggaisa da yan ajinmu suke min korafin rashin zuwana waccan week din, nace wallahi naje anguwa ne shiyasa. ________ B'angaren MD kuwa tunda safiyyah ta amshi soyayyar shi kullum fuskar nan cikin fara'a, har momyn shi ta lura, "Waini Suraj Mike damun kane naganka kwana biyun nan cikin Koda yaushe cikin fara'a, kodai wani abun kasamu a gurin aiki naku? "Duk yadda suyi da safiyyah ya fada mata "Waikana nufin wacce take program akan matasa Suraj? " Eh momy ita " "Alhamdulilah momy ta fada tana daga hannun ta sama gaskiya naji dad'i sosai Allah ya tabbatar da alkairi Zan ma Abba ku magana sai aje ayi magana da manya, Dan abinda na dade ina jirane ace ka fito da matar aure. Tunda 'yan matan dangi da yawa na sonka ka'ki, to Allah ya amshi addu'a ta" Mennat ma cikin farin ciki take taya yayan nata murna, harda ya bata number safiyyah. _______ "Mom wai kuwa kinsan safiyyah yanzu ba wannan kawar tata bace ke kawo ta gida? Anty Waleeda tayi maganar cike da gulma tana kallon mom. "K ban gane mekike nufi ba inba k'awar tata ba to kenan takoma karunwanci ne komai? "To mom wama yasani, nidai jiya bayan kin tafi Nima na fito zan tafi gidan su lubna naga ta fito a wata mota, kuma bata Ishan bace, ke kinga kallon da murmushin da take yine? da kingani kinsan ba mace bace, dan naga kamar ma namiji na hango aciki to da yake glass din me duhune banga waye a cikiba, dan saida ta shiga ya tada motar, wallahi kidau mataki a kanta. Yadda mom ta rike baki tana bin anty Waleeda da kallo zakasan tashiga mamaki ne. "Mekike nufi ne Waleeda kina nufin safiyyah tafara karunwanci ne shine zan dau mataki? aini dazata bi duniya dana fijin dadi wallahi. Dan yadda na tsani uwar ta haka na tsaneta, keni yanxu ma nafi tsanar ta akan kowa wallahi. "Uhm mom kenan, ai Ni nafiki tsanar ta bakiga kanwata bace amah tafini cigaba kigafa aiki take niko ina zaune, Kuma kinsan ustaziya ce shine har kike tinanin zatayi wani karunwanci, kedai kawai mom ki tsaya kiyi bincike akanta wallahi, tunkan abi ya Miki nisa." "Ehh kuma hakane, to amah ai ustazan sunfi iya iskanci" "To nidai mom nafada miki, kuma akan wanan wanda yazo neman ta, wallahi mom kullum son shi ninkuwa yake a zuciyata kisan abun yi" "Ki kwantar da hankalin ki zansan abunyi jiyama gurin na kan kwari muje nida mama, to bamu sameshi ba amah asatin nan zan koma" "Assalamu alaikum" Buhaisa data shigo tun dazu take sallama su mom suna can kwaryar daki suna kullin su ta fito tanabin buhaisa da kallo. "Ina yini" "Daban wuniba kya ganni, kekuma daga ina ? "Oooh sorry nashigo miki gida ba neman izni safiyyah nake nema" Buhaisa tayi maganar da cike da rainin hankali tana wani murmushi, Dan tasan sarai mom ta ganeta kawai tsabar wulakanci ne. "Tsaki kawai mom taja tashige bedroom. Itama buhaisa tsakin taja kasa-kasa tashige bedroom din su safiyyah. *Evening* Koda nadawo islamiya a gidan nasami buhaisa, aikuwa tacika fam. "Ke shine ki'ki dawowa kinsan wannan shegiyar matar daba mutunci ne da itaba tana gidan " "Sorry sisi wallahi matsala asamu mun biya gaida wata 'yar ajin muce da bata da lafiya shiyasa, amah afwan" "Shikenan ya wucce, waikin san ma iskanci da matar nan tamin ne? Aa amah sisi please mubar zancen mom kinji, Yasu ummi da anty hajara da yah saif? "Uhmm duk suna lafiya sunce a gaishe ki, damafa anty hajara ta fito da anko ne, yah saif ma harya suyo mana, kinga yanzu saura dinki gobe zamuje mukai, because biki yazo. Yayi tom Allah yasaka da alkairi ya kaimu lafiya, kuje kawai da Isha tunda ni nakusa zuwa ma gidan, kinga some time kaya ma kai daya akemana da kadan nafiki jiki" "Ameen yah Allah sisi nah tom yayi, sauran shirye-shiyen kuma saikin zo saimu k'rasa koh" "Eh hakam yayi amah meda-me yakamata ayi kisan nifa bansan wannan abun" Eyye to wallahi baki isaba, kinga fige wannan ustazanci zakiyi gefe in mungama kya dawo dashi wallahi. Haba sisi nah, kunyar wa zakiji, kauyawa day ne, sai bredal show, sai fulani, sai kamu, kawai za'ayi anan acan Abujan za'ayi dinner, bayan kai amarya. "Hmmm Allah yakaimu lokacin sisi " "Ameen yah Allah ki kefa" "Murmushi kawai nayi mu cigaba da fira har yah Ansar ya dawo mu koma dakin shi muna fira, bayan magrib ya tafi kaita, nikuma nadan gyara mai dakin na nufi bedroom din mu. Yauma mun dade muna fira kana na tafi na kwanta, har lokacin anty Waleeda kamar ma bata a gidan. MD ya kirani musha soyayyar mu a waya, muna shirin sallama yace, "Amm baby su alhajina zasuzo fa maybe next week din nan dan haka ina bukatar ganawa da Abba yaya za'ayi kenan". Da sauri na d'ago kaina kamar yana kallona, cike da kunya ga kwalla ta tarumun a ido, "Baby kinyi shiru? "Uhm yakama kafara ganin yah Ansar dai first kafin Abba nake ga" "Sosai ya sauke numfashi mai nauyi, kana ya amsa da, "okay hakan ma yayi, zan bari to sai gobe masamu yah Ansar d'in" Daga haka mukai sallama" *Monday morning* Yauma kamar kullum around 6:00 am natashi bayan nayi sallah da azkhar da karatun alQur'ani. Nafara gyaran gidan, dan na makara, cikin kan-kanin lokaci nagama komai, saidai ban musu miyar ba, dan har yah Ansar ya kamamin wani abun. kasancewar indai yana gidan yana tayani saidai mom ta hana shi, Tsaf nashirya cikin riga da siket dakin ya zauna min daram ajikina, simple Make up nayi danko iyakar fauda, sai kwalli, da lipstick, and maskara, da na taje eyelashes dina dashi ya fito gadar-gadar, sai girata da take a ciki na taje. Turaruka na nafesa masu mutukar kamshi, sai plate shoe danasa, gashina dana tsafe nake son zuwa gun kitso tunkan ummi ta ganni dashi atsefe na daure da ribbon, sai yayi kamar nayi a cuci dashu. Goggagen Hijab nasaka har kasa danko d'an kwali bansa ba, sai face mask, da eyeglasses, na dau hand bag d'ita da waya ina ficewa a dakin, dan yau anty Waleedah ma ba'a gidan ta kwana ba. Kamar ko yaushe yauma parlour tsit yake har mutafi, Saida yakaini har kofar shiga kana ya bani 3k, godiya na mishi nace please yayah kabari nakira Isha ku gaisa. Da "okay" ya amsa min nashiga da dan sauri dan kiranta, a hanya mu hadd'u nace Isha kizo ku gaisa da yah Ansar. "Kai Quee hijjab da gaske? "Dariya nayi nace kinsan zan miki karyane ai" "Sorry ni wallahi kunyar yah Ansar d'in nan nake ji wallahi" "Kinji kamar wani saurayinki anya Isha anya? "Ke dalla basan iskanci muje" Murmushi nayi muje su gaisa kana mu shiga ciki shi kuma ya tafi gidan ummi. "A hanya mu hadd'u dasu mu'az dan yau ma tare zamu yi program, duk gaishe su nayi, cikin tsokana suke tono na. "Kai Quee hijjab yau kin makara fa MD zaiciki tara gaskiya, dan baza'a yi san kai agaban mu atoh kiya kukace? Yafada yana kallon su mukhtar. Nida su isheni ma nace kwaji dashi wain Quee hijjab sabon sallo kenan mutafi mubar su, daga baya suma su shigo. MD da tunda na shigo ya zubamin ido na gaisar. kana mufara gabatar da program din............. __________ *Abuja🤍* Mummy na fita tasaki murmushin samun nasara ta wuce part din granny, dantasan ita kad'ai ce zata bata cikas, Bilkeesu ko zataji da ita dan ita irin maccen nan ce me kawaici. Tunda ta shigo granny ke binta da kallo, ganin yadda tashigo sai murmushi take bata ma lura datana parlourn ba, a'a zakiyya daga ina haka naga sai fara'a kike kamar wacce za'asa a aljannah? Firgigit ta d'ago tana kallon ta, kana ta sauke boyayyiyar ajiyar zuciya, abinka da goggagiyar 'yar bariki sai cewa tayi. "Hajja bakomai kawai dai wani abu natuna" takai karshen tana zama kusada granny. Kallon ta tayi cike da nazari sai kawai ta girgiza kanta ta maida hankalin ta kan program din da akeyi. Ita kuma tashige daki domin sanar ma da d'iyar tata labari me dadi. _______✨ Koda mummy ta fita dady nazari ya shiga, har Ammii ta shigo besani ba saida ta taba shi, yasauke numfashi zama tayi kana tace. "A'a lafiya kuwa naga na barka k'alau na dawo na ganka kuma sai a hankali? "Hmmm lafiya lau zauna muyi magan da "to" ta amsa kana ta zauna tace, "nima dama inaso muyi magana" "Okay to fara kawai" "Maganar dama akan auren majeed ne. kaga hajja kullum cikin fad'a take wai mumu daure mai gindi akan aure saidai mu lalabashi, toni ma abun yana damuna, shine na yanke hukuncin a had'ashi aure da feenah, 'yar wajen Addah wato d'iyar sulaiman? "Dogon numfashi ya sauke yana kafeta da ido, nad'an tsawon lokaci kana yace. "Kema dai Bilkeesu? Cikin mamaki take kallon shi sannan tace. "Bangane nimaba alhaji wani abinne ya faru? "A'a bakomai kibani Time zanyi tunani" "Tom shikenan amah yarinyar tana mutukar son shine shiyasa, ma amah dai saina ji ta bakin naka" " Okay shima inaga next week d'inan zai dawo " "Eh haka yace Allah yah yadawo dashi lafiya" Daga haka su cigaba da fira cikin nishadi da farin ciki alamun anyi kewar juna. _________ *Kaduna✨* Har kofar gida ya kaini yauma dai mun dade muna fira, yake sannar min sunyi magana da yah Ansar, Cikin jin kunya na dukar da kaina ina shirin fita, "please beb ki waigo mana nasake ganinki tunda rowar fuskar ma akemin, sarkin kunya nikam naga sanda zaki dena jin kunya ta" Murmushi kawai nayi jin yadda idonun shi ke yawo a kaina, nadan waigo kana nace "to ka budemin motar tukunna. Shima murmushin yayi yana budewa kuwa nayi wuf na fice ina daga mishi hannu. " Shima dagamin yayi har na shige kana yaja motar ya tafi " Cikin sand'a nashiga Allah ya remake ni bakowa a parlour dan haka nai wuf nashige daki dan bana so muhadu da mom, banyi miya ba yau. Anty Waleeda ce a dakin tana kallo tunda nashigo ta bini da harara har nashige bayi, Ashe fita tayi, fitowa ta daure da towel kenan ina gaban mirror, saiga sunan sun banka d'o kofar, Hannun Mom dawata katuwar bulala ta nufo kaina waina satar mata kudi , tsabar mamaki tsayawa nayi kawai ina kallon ta, banyi auneba tasakin min ita agadan bayana, "Ke Waleeda dubamin Jakarta ki gani" Mom tafada cikin hargagi, Anty Waleeda na dubawa kuwa saiga kudi sun fado dauri har biyu a jakata, Mamaki yasani cewa wallahi karyane saidai wanine yasamin. "Dan uwarki rufemin bakin ki nice zan miki karya safiyyah, kud'in nawa zaki dauka kinsan yawan su kuwa? Tafada cike da tsawa tana kara lafta min bulala, wani zafine ya shigemi na kwalla kara. Dai-dai nan Abba ya shigo kamar an jefoshu, "Haba Zuwaira lafiya zaki kama yarinya kina duka jikin ta bakaya, baki da hankali ne? Yafada a hassale yana rike bulalar data daga da niyar sake tsulamin. Basuba hattani Saida nashiga shock, dan bayau bane kawai mom ta taba dukana agaban shiba, bama niba har yah Ansar da duka take, baby kuwa kuka kawai take tana bata hakuri. Mom ce takatsemin tunani na Dan cikin hargagi take ma Abba masifa, dafada mishi kud'in ta na sata kuma wallahi saina biya, inba hakaba wallahi saita kaini kitu, saida takai har yafara bata hakuri da lallabata, Ni al amarin ma saiya nemi fasan kai, haka dai yajata da kyar su fice. Anty Waleeda ta dallamin hara mayya kawai to kurwar uwata kur wallahi. Kadan ma kigani indai mom ce wallahi bari Abba ya fita dan ba kyaleki tayiba kiji mada da tsamin jikin ki, wallahi kuma saikin fito da kud'in nan duk idda kikaisu. Saida ta gama zageni tsaf sannan ta fice, kamar iska zata dauke ta dan sam anty Waleeda bata da kiba. Tana fita na dur kushe nasaki kuka maicin zuciya saboda rad'ad'in da ilahiri jikina ke min. Baby ce ta matso tana rarrashina kai kawai nadaga mata nace jeki baby, Koda ta fita da kyar natashi na hau gado na kudun dune da bargo zazzabi me zafi ya rufeni da ciwon jiki, inaji kiran da yah Ansar kema wayata harya gaji ya dena, nasan cewa zaiyi nayi bacci..................✍️ _Taku har kullum da ko yaushe🫶💯_ *🤝 Amanar nazari writer's association📚🖊️* _07070260240, WhatsApp number or call_ *_Please🙏 comment and like and share fissabilah👏👏_* 🌹 RAYUWATA🌹 Story and written✍️ Bilkeesu Sa'eed Aliyu 💞(Billy pinky)💞 🤝 Amanar Nazari writer's association📚🖊️ [07070260240] WhatsApp number or call 📚N.W.A🖊️ 26&27 *Washe gari* Da zazzaɓi na tashi, kota aikin gidan banbi ba, nayi shirin tafiya aiki dan ko breakfast banyi ba, Ina shirin tafiya na hau napep dan ko yah Ansar bana so mu haɗu, sai gashi ya fito, Ƙasa nai da kaina tare da furta "ina kwana yayah? Bai amsa gaisuwar ba sai kallo daya bini dashi, nakara ƙasa da kaina. "Me yake damunki ne Safiyyah? "Bakomai yaya" "Amah naganki haka ko aikin gidan bakiyi ba kuma kisan halin matar gidan? "Muje yaya zan faɗa ma a mota" Na faɗa inayin gaba da kallo ya bini har na shiga kana shima ya shigo, mun fara tafiya dan na dauka ma ya manta cikin muryar shi da bawasa yace. "Inajinki" Duk yadda muyi dasu mom na kwashe na faɗa mishi, kuma wallahi yah Ansar ko sanda na dawo ba kuɗin a jakata, hasali ma saida na cire waya ta a ciki, na ƙare maganar hawaye na zubomin. "Nasani safiyyah ki ƙara hakuri kinji, nawa tace kuɗin nata? "Bata faɗa ba ai kasan saita ƙai yace kuɗin da zai isheta zata faɗa" Murmushi kawai yayi batare da ya sake cewa komai ba har mu iso gurin aiki. "Yanzu ya jikin naki zazzaɓin ya sauka ko har yanzu? "Because basan shan magani nace mishi ya sauka" "Sure" "Yes" "Allah yasa ba kawai kin faɗa bane, Akan maganar ku keda Suraj kuma, nagama duk wani bincike naga ya can-can ta inbashi ke saboda halayen sa masu kyau, kuma ya fito daga gidan mutunci, To Abba ne matsalar, na mishi magana wai mom ta fito miki da wani, kuma shi zai ba dan yafi gamsuwa da tarbiyyar sa dan haka shi baisan wata maganar Suraj ba. In kuma ba hakaba saidai ki bar aikin ki dawo gida ki cigaba da musu bauta. Kuma.. Kuka na sakar masa mai taɓa zuciya. hakan yasa yai shiru ya gagara cigaba da maganar. Ya tsuramin ido kawai, kana ya jawoni jikin sa shima hawaye na tarumai a ido. Amah fa kisan bana son kuka ko Safiyyah. Dagowa nayi a karo na farko ina kallon sa. kana nasake fashewa da wani kukan ganin yadda idon sa ya kaɗa yayi jajur. Ya kake so nayi. Shikenan haka zamu lalace gurin ma wacce bata taɓa tausayin muba biyayya. Kullum burin matar nan wulaƙanta mu. Tun bansan kaina ba nake bauta a gidan nan. Amah ko sau ɗaya ba'a taba min adalci ba innai kuskure. A kullum a banyi ba nake. Ka duba anty Waleeda fa tana kwance. Yaya nagaji jinake kamar na gudu na bar gidan nan...." Shiii!! Karna sake jin wannan maganar a bakin ki. Safiyyah ai wuya bata kisa dan data nayi da tuni bamu. Duk dacan baki kosa ba saida aski yazo gaban gishi. Kwana nawa ya rage miki a gidan. Bama keba da kike mace zaki tafi gidan miji hattani nakusa tattara kayana mu bar musu gidan. Amah dan Allah kar insake jin kinyi wannan maganar. Inki gudu ina zaki. Ki daure ki cigaba da musu abin da suke so. Wata rana sai labari. Akan maganar ki da Suraj kuma, yau zanje gurin Abban su saif na faɗa mishi, da kawu Inusa da kawu mansir kinsan dai Abba yana mutukar tsoran su, insha Allah komai zai tafi daidai" "Ameen yah Allah yayah" "Yauwa jeki karki makara kuma ki kula da kanki sosai, kar kisa wata damu kinji? " Insha Allah saika dawo Allah ya tsaremin kai yaya nah" "Ameen yah Allah lili sis" Kana ya tafi ni kuma na shiga ciki. *In the evening* A parlour nasame su gabaki dayan su cirko-cirko suna jiran dawowa ta. Da sallama na shiga ba wanda ya amsa har ba daya cika yayi fam da alamu an fan fashine. Banyi aune ba naji saukar mari a fuskata. Anty Waleeda ce sai huci take tana bina da kallon tsana. Yadda ta shammace, ni haka nima na shammace ta na bata hagu da dama. Cikin tsanani azaba ta dafe kuncin ta Ni kimara Safiyyah? An mare kin. wallahi duk sanda ki ƙara ɗaga hannun ki da nufin kaishi jikina wallahi saina miki abinda yafi haka... Kasa ƙara sawa nayi saboda marin da mom tamin hagu da dama, duka na take tako ina tana barauniya ki fitomin da kuɗi na dan uwarki. Duk dukan da takemin ban motsaba saida ta am bato min uwata, cikin kaushin murya nace "Wallahi mom badai uwata ba. Cikin fusata ta shakemin wuya. dan da kyar nake numfashi baby kuwa sai kuka take, Abba da tun ɗazu bai motsaba saidai daka kalle fuskan sa kasan baya jin daɗi. Yake kokarin kwata ta a gurin ta, haba Zuwaira ki saketa mana ta faɗa miki inda takai miki kuɗin. da kyar ya kwaceni dan saida tayi taga-taga zata faɗi, niko zube wa nayi a kasa baby ta kawomin ruwa, ina cikin sha domin shi nake buƙata. Ruwan anty Waleeda ta kaɓar ya zubomin a jikina. Ban ɗago na kalle ta ba. sai Abba da yace kowa ya zauna. Kamar mom zatai magana kome ta tuna tafasa ta tsaya a tsaye kamar doki sai jijjiga take. Kai kawai ya girgiza kana ya fara magana cikin ɓacin rai. "Yanzu dan Allah kunfi so kullum maƙwota suna jiyiku kuna faɗa? Twssss aikin banza ina ruwana da wasu maƙwota nidai kuɗina kawai nasani wallahi. Inba haka ba saina kaiku police station acan kwa fitomin da kuɗi na. "Kuɗin naki nawa ne? Yah Ansar daya shigo ya faɗa yana kafe mom da ido. Saida ta diririce saboda kallon da yake mata. "Duba dari da hamsin tunda naga wasu a jakarta" "Okay transfer or cash? "Cash nake buƙata tunda nima cash ta.." Hannu kawai ya ɗaga mata kana ya jah hannu na, mu fice kasan cewar jikina ya dau zafi. Ba wanda yace komai acikin mu dan ni ko hawaye babu a ido na. Har mu iso wani p hospital, ciki mu shiga a gwada ni, Cikin tsoka na doctor fadil yace. "Safiyyah allura fa zan miki itace kawai zatai saurin saukar da zazzaɓin nan. Jin ya ambato allura nai rau-rau da ido, ina kallon yah Ansar daya haɗe fuska, Please doctor ka bani magani kawai. "A'a Safiyyah nasani ko maganin abaki basha zakiyi ba, inma kinsha to ba bisa ƙa idaba, kuma allura itace kawai bani hannun ki na miki. ƙin karasawa nayi saima tsayawa da nayi kamar zanyi kuka ina kallon yah Ansar. "Doctor fadil yimata ina sauri ne" Badin nasoba na runtse idona har a gama hawaye na zuraromin. Saida yah Ansar yayi murmushin gefen baki kana yace. "Allah ya shirya minke safiyyah" Doctor dai ya amsa da ameen daga haka muyi sallama ya biya ya ciri kuɗi, ya mubiya ya siyamin kaza, kana mu wuce. Gida Yanzu yaya haka zaka bata kuɗin? "To ya za'ayi Safiyyah bafa yau tasaba irin wannan abun ba. nidai abinda nake so dake duk inda RAYUWA zata kaiki ki kasance mai hakuri, domin me hakuri ne keda ribar zaman duniya. "Insha Allah yaya" Koda muje tana zaune a parlour tana jiran dawowar mu, daki na shige shi kuma yah Ansar ya bata kuɗin ya wuce daki. Gaba daya yau kowa na gidan da yunwa ya kwana, to baiwar tasu bata da lafiya bare naje na daura musu. nikam yah Ansar ya siyamin kaza ita naci na kwanta. Bayan munyi waya da MD. ______ Yah Ansar yaje ya sami su kawu Inusa da kawu mansir sun. Sunta faɗa dan me za'a takura ma marainiyar Allah, dan kowa ya yabari ummah ta rasu, to har yanzu bata ba labarin ta. daga baya su amince da za suzo su same sa. *Washe gari* Suzo don mun tafi aiki ma har Abban basu same shiba sai office ɗinsa. Su tattauna duk da dai da farko taso tayi tsami a tsakaninsu. Kasancewar Abba yana ganin girman yayan nashi. Da kyar dai ya amince da batin Suraj.. A lokacin mani ina office ɗin MD naje kaima sa aikin daya bani ranar Friday. Kamar kullum yauma sanye nake da hijjab har kasa, akwai mark a fuskata har da eyeglasses. To dama shigar tawa kenan. Indai ka ganni da gyale to ɗan kolin abaya nasa nai rolling. Miƙa masa nayi na maida hankali a wayata, "Masha Allah yayi kyau sosai baby yanzu saura printing. tom ki kasan ce cikin shiri kinji" "Insha Allah" Daga haka na koma office na koma mu cigaba da aiki. *In the evening* Har gida yauma ya kaini. Dan har na fita na manta da jakata, shine ya dakko ya fito ya bani nadan jingina da motar shi. "Amarsu ta ango" daya faɗa yasani dauke kai ina murmushi. Shima karamar dariya yayi yana dawo ta inda na maida kan nawa. Karamar harara nasakin masa ina sake dauke kaina. Yace "Tab irin wannan harara haka amarya ai saiki sa na zube a ƙasa wallahi. Kinga adanamin ita sai nanda 'yan watanni kawai. Kinga inma suma nayi dai kya farfaɗo dani da kanki ba wanda yaji konya gani koh? Dariya ya bani amah kasancewar ba'a ganin bakin nawa sainai murmushi kawai nasake dauke kaina. ________ Anty Waleeda da dawowar ta kenan daga yawan ta. Taci karo da Safiyyah da MD suna shan soyayya zuciyar ta data buga lokaci ɗaya ta dafe tare da furta. "Na shiga uku na Ni Waleeda me nake ganine? Ganin ba me amsa mata tambayar ta kuma intaci gaba da kallon su zuciyar ta zata iya bugawa. Ta faɗa gida hankali tashe tana kwalla kiran. Mom! Mom! "Waleeda lafiya kike kwalla kirana kamar ance miki na mutu ko Abban ku? "Uhmm mom bazaki gane bane wallahi jinake kamar zuciya ta zata fashe" Ta ƙarasa maganar tana fashewa da kuka. Tuni mom ta rikice sai jerama ɗiyar tata tambaya take. amah anty Waleeda sai kuka take kamar. ko wacce ace mom ta rasu. Dai-dai ina shigowa parlour dan basu masan na shigo ba. Mom ta daka mata tsawa tare da cewa. "Ki faɗamin meya faru, me amiki, wani abune ya faru? "Mom safiyyah! "Meya faru da Safiyyah har kike kuka kamar ance ta mutu? "Wallahi mom da zata mutu danafi ko jin daɗi. Wallahi da har sadaka sainayi" Tsabar yadda maganar ta dakeni bansan sanda zafafan hawaye su zubomin ba. Dama tsanar da anty Waleeda tamin har ya kai haka. Mom ce ta katseni tare da cewa "sai jamin rai kike kifadami abinda ya faru" "Wallahi mom ganin ta nayi da wannan wanda yazo gidan nan neman ta. kuma mom kisan tsananin son danake masa mom. Jin zuciyata nake kamar zata buga" takai ƙarshe maganar tana zubewa akasa. "Banza yaushe kizama shasha-shane Waleeda akan namiji kike zubda hawayen ki? To wallahi ni Zuwaira nayi rantsuwa da Allah. indai baki same saba itama bazata same shiba. saidai bana numfashi a doran kasa. (Tofa🤔 ana wata ga wata wai inji masu iya magana) Ban bari mom tasake cewa komai ba na share hawaye tare da sallama. Gaba ɗaya ɗagowa suyi suna kallo na. "Barka da gida mom" Bata amsa ba nima na wuce ciki zuciya tana suya. Dama ƙiyayyar da anty Waleeda take nuna min har takai ace kona mutu saitai sadaka saboda farin ciki. Innalilahi wa'inna ilahiri raji'un wannan wacce irin rayuwa muke ciki. Allah yasa mu dace,, ◼️Alƙawarin Allah yah cika. yau dai iyayen Suraj wato MD sun kawo kuɗi gidan mu. inda naga baƙin halin mom muraran. Dan zage-zage ta dingayi dayima Abba masifar wai an munafunce ta. Ashe bai gaya mata ba sai ganin su kawu Inusa tai. Shine take tambayar sa meya kawosu. Yace mata iyayen wanda yake neman aure nane suka zo yau. Takaici ya hanata sake cewa komai sai ido data zubamishi. Dai-dai shigowar baki saiga abinci da ruwa da lemo yah Ansar na shigowa da su da batan san ina yasame suba. Shiko yah Ansar sanin halin ta yasa ya faɗa ma ummi ta dafa musu. Aikuwa ranar munga tujara. Dan nima da bansan meke faruwa ba ina gurin aiki ina dawowa saida na amshi rabona. Anty Waleeda kuwa kuka take tana zage-zage. Uffan bance ba musuba. An wajen yah Ansar naji komai iyayen Suraj sun kawo dubu 300k suna gun Abba. Bance masa komai ba muciga ba da fira dan bana ma sha'awar shiga cikin gidan. Sai gurin sha ɗaya nashiga anty Waleeda kawai na samu a parlour taci kuka idon nan yayi hulu-hulu. Bance mata komai ba na kama hanya bedroom. Jinayi kawai an shaƙemin wuyan hijabi na tabaya tare da sakin mun duka hannu bibbiyu. Jin numfashi na na barazanar dauke wa yasa na fusgo hijabin na yagaji sanan na waigo ina numfashi da kyar. Anty Waleeda ce tsaye sai faman huci take kamar me shirin dambe. Na mata kallon sama da kasa kafin nace mata cikin mamaki,, Lafiya kuwa baiwar Allah kin shaƙeni haka sai kace wacce na cimiki bashi? Are You oky? "A haukace nake dan uwarki. Wallahi kaɗan ma kigani dan wataran in shaƙe ki saikin dena numfashi zan barki. Dan haka ina gargaɗin ki inhar kina son ranki ki fita sabgar Suraj wallahi. Ki kuma bar ganin ya kawo kuɗi da sunan auren ki. Wallahi indai kiga kin aure sa saidai ina bana raye. Amah inhar ina raye wallahi yadda ban same saba kema wallahi bazaki same saba jaka yar dabba yar gidan mayya. Murmushi kawai nayi mai fadi. wallahi ni dariya ma tabani da tausayi, na wucce ɗaki na barta tana ɗaura min zagi kamar ba dare ba. Bathroom na shiga nayi wanka kana na dauro alwala nai shirin bacci, ba abinda nake sai ƙamshin humura. Sama-sama najiyo maganar Abba ita kuma tana kuka. Baki kawai na taɓe na gyara kwanciya ta ina karanto addu'oi kwanciya bacci dan gobe zanje gidan ummi bikin anty Hajara saura one week. Sai dai kamar kullum saida na tashi nayi ƙiyamul laili daya zame min jiki. Saidai idan banda lafiya, amah ko prioud nake saina farka. ________ *Abuja🤍* Mummy nashiga ɗaki taci karo da zaituna data kafe hoton majeed dake wayar ta da kallo. Har takai zaune kusa da ita bata sani ba har ta amshi wayar kana ta ɗago firgigit. Ajiyar zuciya ta sauke dan har mummy saida ta jiyota kana tace. "Wallahi mummy kin bani tsoro" Tafaɗa a shagobe . "Uhmm zaituna ki kwantar da hankalinki indai majeed ne kamar kin samu. Dan mun gama magana da yaya kuma nasan zai amince hajja ce matsalar amah nasan yadda zanji da ita". Tsabar farin ciki zaituna rungume ta tayi tana zuba ma mahaifiyar tata addu'a. Granny da duk maganar da suke tana jinsu kai kwai ta girgiza ta koma parlour. Dan tunda taga mummy tasan wani abun take kullawa shiyasa tasa mata ido sosai. Yanzu kuma tunda ta gano abinda take shirya wa ai tasan yadda zatai da ita. _______ Yau majeed zai dawo dan haka Ammii dakanta tashiga kitchen tamishi girki sai auta da fennah dasu taya ta. Dan kwata-kwata baya son cin abinci masu aiki, bayan sun gama tasa mama Rabi'ah da auta suje su gyara mai ɗaki kasancewar mama Rabi'ah ke masa gyaran ɗaki. *In the evening* A hankali motocin nashi dasu taso daga airport ke shigo wa cikin gidan, youseef ne daya fito a cikin ɗaya daga cikin motocin ya nufi motar da ogan nashi yake ya bude masa. Saida ya ɗau minti biyar kana ya fito gaba ɗayan shi. Sanye yake cikin suite milk sai neck tie black, sai takalmin kafar sa da yake milk kwalliyar sa data kasance black, sumar nan tashi data sha gyara ta kwanto mishi har fuskar sa. Ga wani ƙamshi da yake me kwantar da hankalin me shaƙa. Yanda su zaituna da fennah su zubamishi ido kamar zasu cinye shi. Zaituna ji take kamar taje ta rungume shi ko zataji sauƙin abinda take ji. Ita dai fennah tana ƙoƙarin danne wa ba kamar zaituna da take nuna wa a fili ba. Da gudu auta taje da niyar rungume shi itada basma tunda ya musu wani kallo su kame suna tura baki. Murmushi youseef yayi kana a hankali yace. "Sorry autar mu" Yana bin bayan sa hannun shi dauke da laptop da wayoyin sa. Sannu da zuwa su zaituna su mishi shi kuma ya wuce part ɗin Ammii. _______ *Kaduna✨* *In the evening* Tsaf na shiya cikin abaya baka mai santsi wacce amah ado da fararen duwatsu manya da kanana. Gashina da tunda na tsefe kallabar da ummi tamini ban sake yin kitsoba na daure da ribbon nai acuci. Rolling nayi da mayafin abayar aikuwa na fito kamar balarabiya. Farin eyeglasses na saka kamar ko yaushe idona ya fito dara-dara, ko marks yau ban saba saboda yah Ansar, Plat shoe nasa kana na dauki jakar dana haɗa kayana, sai hand bag da phone na fice a ɗakin. "Wow my Little sisi kinga yadda kiyi kyau kuwa kamar wata balarabiya? "Uhmm kai yah Ansar kaima dai, ina ni ina balarabiya dan Allah" Nafada a shagobe. Murmushi yasaki kana yace "ki adana abarki kyama Suraj danni yanzu na kusa hutawa da shagobarki" Baki na taɓe kamar zanyi kuka na nufi gurin motar shi na shiga. Shima dariya yayi y biyoni mu tafi. Dai-dai wani shagon ɗinki ya tsaya yace min ina zuwa. Be wani dade ba ya fito hannun sa dauke da leda, ashe ɗinki ya mana nida buhaisa da Isha, kala bib biyu tsabar farin ciki bansan sanda na rungume shi ba. Tun kan mu isa gidan yace min nakira Isha ta kintsa za muje shopping da ita, da to na amsa kana nakira ta, koda muje shiga yayi su gaisa da ummi, buhaisa da ta cika tai fam wai saboda banzo da wuri ba. Hakuri na bata na miƙa ma ummi kayan taitasa mishi albarka.Tafiya muyi mu ɗau Isha a gida. kai tsaye shop rite muje yace kowa ya dauki abinda yake so, kama daga kan takalma jaka da kayan kwalliya. Da turaruka iri ɗaya mu ɗauka. Daga nan ya maida mu gida muyi mishi godiya yace. "Toni dai gobe insha Allah zan koma kuma munyi sallama da ummi sai minyi waya." "Yah Ansar bazaka zo bikin ba? "A'a buhaisa insha Allah zan dawo ranar Friday" Isha da tunda a fara maganar bata ce komai ba. Sai yanzu ne cikin sanyin murya tace. "Tom Allah yah kaimu yasa kaje lafiya kadawo lafiya" Da ameen yah Allah duk muka amsa. Yanda yah Ansar yake bin Isha da wani kallo ita kuma sai ƙasa da kai take. Murmushi nayi kawai dan abinda nake zargi ya kusa zama gaskiya na shida Isha na son junan su aɓoye. To da hakan zai kasance dana fi kowa murna. Sallama muyi mishi mushiga ciki. Tunda mu shiga ɗakin da ake ma anty Hajara gyaran amarya mu tasata gaba da tsokana kamar sa'ar mu. Kamar zatai kuka take kwalla kiran. "Ummi! Ummi! Kizo ki rabani da marasa kunyar yaran nan dan Allah. Wallahi kema Safiyyah kita biyema su buhaisa inadai aure ne kema ai kin kusa, zakiga iskanci wallahi". Jin haka yasa ni zunbura baki cikin shagobba nace kai anty Hajara. Dariya susa gaba ɗayan su buhaisa tsabar dariyar mugun ta harda rike ciki. "matsoraciya kawai ni kutashi kubani guri zanyi waya da my husband" Dariya mu sanya gaba ɗayan mu kai anty Hajara har yazama miji ne ai saiki bari ashafa. "To ko hana ashafa fatihar, kunga Safiyyah in baku wucce ku bani guriba wallahi" Dariya mu sanya tunda muna shirin kara magana saiga ummi nan. Ai da gudu mu fice muna dariya. Tunda kuma mu koma ɗaki su buhaisa su sani gaba wai amaryar MD. Saida su kusa sani kuka kana su rabu dani. Muraka Isha gida mukuma mu dawo. Gabaki dayan su suna parlour harda yah saif suna shan fira. Muna zama muyi anayi damu. anan yah saif ya bamu kayan fitar biki, dan haka muyi zaman tsara yadda komai zai kasance.......✍️ Taku har kullum da ko yaushe 🤝Amanar nazari writer's association📚🖊️ 07070260240, WhatsApp number or call Please🙏 comment and like and share fissabilah👏👏 *_Typing📲_* _What's app channel👇_ https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _WhatsApp group👇_ https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *🌹RAYUWATA🌹* _CREATED AND WRITTEN BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* _💞 Billy pinky💞_ *Nazari writer's asso....📚* [07070260240] _*WhatsApp number or call*_ _Amanar🤝 Nazari writer's✍️_ *Page2️⃣8️⃣➖2️⃣9️⃣* Kaitsaye part ɗin Ammii ya nufa zaune ya sameta, murmushi kwance a fuskata har ya ƙarasa gareta ya rungume ta. Cikin shagoɓɓa yace " Ammiii i miss you " "Miss you so much my son. Ka dawo lafiya? " Alhamdulilah " " Ma sha Allah. Kaje kayi wanka ka huta saika fito kayi dinner " Da "to" ya amsa kana ya fice cikin sassarfa, Youseef yana zaune suna fira da su auta. Fitowar sa yasa shi tashi yabi bayan sa, a parlour Youseef ya yada zango yana shirin shiga bedroom ya waigo yana kallon Youseef kana a hankali kamar mai ciwon baki yace. "Youseef kaje kawai ka huta, zuwa anjima saimu fita" "Okay sir baka bukatar komai? " Babu kaje kawai " Ya faɗa yana shigewa bedroom, ba abinda yake sai ƙamshi mai kwantar da hankali mai shaƙa. zama yayi a bakin tam fatsatsen bed ɗin nashi da a lailayeshi da lallausan bed sheet. Yanda yake bin ko wacce kusurwa ta ɗakin da kallo kamar me neman wani abu. fuskar nan murtur kamar bashi bane ya gama zuba ma Ammii shagoɓɓa, a hankali ya tashi ya nufi bathroom bayan ya rage kayan jikin sa. kusan minti arba'in ya fito sanye cikin, bathrobe pink calour sabuwa dal, ƙaramin towel dake a hannun sa yana goge kwanta ciyar sumar sa. Gaban mirro ya karasa yana ɗaukar hand dryer ya jona a socket cikin cikin ƙan ƙanin lokaci ya kammala gyara ta, lontion ya shafa sai sprays dinsa masu shegen ƙamshi. Kana ya nufi close ɗin sa, riga da wando ya dauko wacce rigar ta kasance mai hula a gaban ta an rubuta TIGER da manyan baki mai kyau da laushi sai dogon wando da boxer shima dai sabo, tsaf ya gama shirin nasa ya koma gaban mirror yayi wankan tsaddadun turarukan nasa masu ƙamshi kamar ba dare ba, ya fito parlour, Kai tsaye masjid ya nufa domin gabatar da sallah. Tare su fito da dady da sauran Uncle's ɗin nasa bayan sun gabatar da isha'i, tafiya suke suna fira cike da Nishaɗi har su karasa babban parlour domin yin dinner. Lokaci-lokaci Majeed kan ɗan runtse ido da shafa gefen kanshi. Gaba ɗaya family zaune suke a kan dinning area domin yi dinner inka cire granny dasu dasu shigo yanzu. Da sallama suka shiga aikuwa su zubo musu ido na ɗan wani lokaci suna dauke idanun su tare da musu barka da zuwa. Inka cire Zaituna data zube Majeed da kallo kamar wata sokuwa. mummy ce data lura da hakan ta zun guro ɗiyar tata tana balla mata harara baki taɗan taɓe saiku ma ta maida kanta kasa tana wasa da abincin dake gaban ta. Gaba ɗaya zama suyi kana cikin girmama wa Majeed ya gaida iyayen nashi fuskar nan dai ba alamun fara'a a cikin ta. wani kallo mummy da umma amarya suke mai kowa datashi fassarar, ita mummy haushin ta tana matsayin uwar sa kuma tana niyar zama surukar shi amah bai nuna alamun ya ma ganta a gurin ba balle ya mata Tata gaisuwar da ban, dan koda ya gaida su Addah bata amsa ba. Itako umma amarya ita tabar wa kanta sani. Bayan sun gama kamar yadda su saba su nufi part ɗin granny domin yin hira. Gwanin ban sha'awa family suke fira, in kacire Majeed daya koma gefe ɗaya yana aiki a laptop kamar dole idonan ya kaɗa yayi jaa, Lokaci-lokaci yakan kai hannun sa kan shi alamun ciwo kan yake mai ko kuma gajiya da zaman gun. Granny da Ammii na lure dashi tausayin jikan nata take daya kasance shi kadai namiji a gaba ɗaya family, tun kan takai ƙarshe a maganar tata ya musu sallama ya fice yana dafe kanshi dake masa tsananin ciwo. Da kallo duk su bishi tausayi kwance a fuskar wasu daga ciki, dan granny da Ammii ma kamar zasuyi kuka har ya ƙarasa fice wa a ɗakin, dady ma kai kawai ya girgiza su cigaba da firar su, fuskar wasu daga cikin su ba fara'a. (🤔 To me kuma yake faru wa dashi ne dasu bishi da kallon tausayi🤭 bari dai nayi shiru mu zuba ido👀) Ita kuwa mummy kawai jira take taji dady yayi magana akan Auren su Majeed, amah shiru har kowa ya kama gaban sa. *Washe gari* Cikin nutsuwa gami da nagarta yake sakkowa daga mataƙalar benan, Tun kan ya ƙaso ƙamshin sa ya riga isowa, gaba ɗaya family zaune suke suna breakfast, da kallo su bishi fuskar su dauke da murmushi har ya ƙara so ya gaida iyayen nasa cike da girmamawa, duk da dai sun gaisa tun a masjid yaja kujera ya zauna kusa da uncle Sulaiman. Suma su Zaituna gaba ɗayan su gaishe sa sukayi cike da girmamawa. Ya amsa fuskar nan a haɗe, Lokaci-lokaci yakan yakan shafa kan shi da runtse ido, Ammii da dady na lure dashi. Shiya fara tashi, cikin damuwa Ammii tace "Majeed ina zaka" a hankali ya ɗago dara-daran idanun sa ya sauke a kanta cikin ya mutsa fuska alamun ya gaji da zaman gun yace, "Ammii zanje gaida granny ne". Ya faɗa yana ɗan fara tafiya, cikin damuwa ta girgiza kai har ya hau upstairs, suma da kallo duk su bishi har ya ɓace ma ganin su. Zaituna ma tashi tayi tabi bayan sa part ɗin granny, Fennah da Azima su bita da harara. Bayan sun gama, kowa ya kama gaban sa masu zuwa gurin aiki su tafi. Majeed kuwa koda ya ƙarasa zaune yasami granny tana kallon tasher haske Tv idan Safiyyah ke gabatar da program, tunda yayi sallama ta ɗago ta amsa mai cikin fara'a yana zama kusa da ita, hankali ta mayar kan Tv shima sanin yadda take mutukar son wannan gidan Tv da kuma program ɗin da suke gabatar wa ne yasa bai sake cewa komai ba ya maida hankalin shi gun, inda Safiyyah yauma take gabatar da program akan taɓarɓarewar ilimi tare da abokin aikin nata. Inda take cewa, *Taɓarɓarewar ɓangaren ilmi a tarayyar Najeriya* ta daɗe ta na haifar da illoli da janyo nakasu ga harkokin ci-gaban ƙasa musamman ma dai yankin arewa,a sabili da yadda darajar ilmin ke ci-gaba da zubewa ƙasa warwas. ƙwararrun masana sun nuna takaicinsu, dangane da matsalolin ilmi daban-daban da suka tattaro suna ciwa hukumomi da malamai tuwo a ƙwarya,al'amarin da ke ƙara nunar da cewa malamai da yawar gaske a Najeriya sun fara yin bankwana da harkan koyarwa sakamakon tsananin talauci da rashin biyan su alabashi bakan lokaci,da kuma wulaƙancin da malaman ke fuskanta daga iyayen yara. Safiyyah ta ci gaba da bayyana rashin jin daɗin ta kan yadda manyan Najeriya ke kwashe 'ya'yansu daga ƙasar suna fitar da su ƙasashen ƙetare neman ilmi. lokaci yayai da dukkanin shuwagabannin Najeriya dake kwashe 'ya'yan su suna zuwa karatu ƙasashen ƙetare da su daina,su dawo mu tattaru wuri ɗaya dan gyara darajar ilmin yaranmu. Duk da cewa a yanzu haka dai kashi 75 % na makarantun jihohin arewa masu zaman kansu na jama'ar kudancin Najeriya ne,kuma akwai baragurbin malamai da yawar gaske dake a makarantun gwamnati suna koyarwa,wannan ya sanya gwamnatin jahar kaduna ta fara yin waje da dukkanin malaman da basu cancanta su koyar a cikin makarantunta dan ya zamo wani mataki na farko na tsaftace harkan koyarwa a dukkanin makarantunta. Haka dai su cigaba da tattaunawa itada abokin aikin nata har su gama, suma masu sauraro sallama. "Masha Allah yarinyar nan tana ƙoƙari sosai saidai fatan Allah ya kareki a duk inda kike Safiyyah" granny tayi maganar tana waigowa tana kallon Majeed yadda ya haɗe fuska bazaki gane ma yasan me granny take cewa ba amah dai ya amsa da "Ameen" asaman labba. Daganan su cigaba da fira wacce rabi ita keyi sai Zaituna dakan sa musu baki data shigo tun suna kallon program ɗin. Sallama yama granny kana ya fice. kai tsaye part ɗin Ammii ya nufa. Koda yaje bata mama Rabi'ah take cemai tana part ɗin dady, saidai ya runtse ido jin ta ambaci dady kamar zai juya sai kuma ya nufi part ɗin nashi Zaune ya se sa shida Ammii shima ƙara sawa yayi yana zama a ƙasa daga can gefe kamar me tsoran wani a cikin su. cikin ladabi yake sake gaida iyayen nasa batare daya ɗago ya kalli dady ba sai shafa gefen kanshi yake dake masa ciwo, magana kaɗan suyi da mahaifin nasa akan kasuwanci lura da halin da yake ciki ne yasa shi cewa. "Majeed kaje ka huta ma ƙarasa maganar a waya zuwa anjima" Kai kawai ya kaɗa ya tashi ya nufi hanyar fita, ganin yadda yake tafiya ne kamar zai faɗi yasa Ammii tashi ta ɗan rungumo sa jikin ta su nufi part ɗin ta dashi. Dady ya bisu da kallo kwalla cike da idanun sa. Kai tsaye bedroom su nufa ya kwanta a gadon ta, kana ta fara mishi addu'a tana shafa mishi a hankali ya fara sauke ajiyar zuciya alamun bacci ya ɗauke sa. Auta dake zaune tun ɗazu ta zuba uban ta gumi tana kallon su, ta sauke ajiyar zuciya tare da cewa "Allah sarki yayah Allah ya baka lfy" da "ameen Ammei ta amsa kana tace. "Kije parlour ki zauna ni zanje gurin dadyn kune saiki riƙa lekowa kiga koya farka" Da "to" ta amsa kana su fita tare Auta ta zauna a parlour Ammei ta wuce part ɗin dady. _________ *Kaduna✨* Shirye shiryen bikin anty Hajara muke ba kama hannun yaro dan yau da yamma za muyi ƙauyawa. Gaba ɗaya yan matan dangin Dady duk sun zo dan kusan sa'annin mune. *In the evening* Buhaisa ce cikin shirin ƙauyawa take kwalla kiran sunan Safiyyah. "Wai Safiyyah mekike nufi ne tun ɗazu muna ta jiranki mun kintsa ashe ke kina nan kina bacci wai ustaziya bazaki gurin ƙauyawa ba, batin kinsan time ɗin Abu nan yayi har ya fara wucewa". Safiyyah da tun da Buhaisa ta fara magana har ta gama tana kallon ta kana ta balla mata harara itama cikin ɗaga murya tace. "Ke dan Allah meye kizo kina mun ihu a ka batin kaina ciwo yake eye?" Buhaisa na niyar magana Isha ta shigo tana faɗin "Wai lfy kuke kuwa ya ke Safiyyah da muke jiran ki naganki haka Bama ki kintsa ba lfy kuwa?" "Kyale yar rainin wayo wai kanta ke ciwo" Buhaisa ta faɗa tana hararar Safiyyah. "Uhmm bawani ciwon kai malama places tashi ki kintsa dan ke muke jira haba dan Allah. Kuta wani abu kamar yara" "Uhmm bazaki gane bane kawai tazone ta sani a gaba tana min masifa" na faɗa ina kallon Buhaisa. "To sorry sisi nah wallahi raina ne ya ɓaci dana ganki a kwance nan amah shikenan please tashi ki shirya". "Dama fa ninayi wanka kaya kawai zansa kuje inna kintsa zan fito". Na faɗa ina kallon su. "Wallahi baki isaba malama kedai kwai kintsa kizo muje" Isha ce tai maganar tana zama, ba tare dana ce musu komai ba nashige bathroom. Cikin ƙanƙanin lokaci na gama shirya cikin kayan ƙauyawa, kasan cewar a harabar gidan za'ayi tuni komai ya kamala kasan cewar masu daya decoretion sun zo sunyi dan sanda ma mu fita anty Hajara na gurin da ƙawayan ta. Haka ayi ƙauye day aka tashi lafiya inda washegari akayi Fulani day. Yau kam ba'ai fama daniba kasan cewar ina mutukar ƙar son fulani day inda muka shirya cikin fararen kayan fulani amar kuma tasa blue. Abun ba'a cewa komai yadda kayan su min kyau dan saida su Buhaisa su matsa muyi hoto aikuwa anyi hotuna kam ba lefi. Shima anyi lpy inda washegari daya kasance day 3 akayi Arabiyan night, kasan cewar sai dare yasa mu fita dan sai gab da magrib mu dawo inda mu kintsa cikin bakar abaya tare dayin rolling ɗin mayafin ta dukan mu aikuwa munyi fito kamar larabawa. Toh shima haka ayi lpy a tashi lpy. Day 4 kuma ayi Bridal shor inda gaba ɗaya muyi ankon kaya purple amah banda amarya shima haka ayi lpy a tashi lpy. Washegari kuma daya kasance day 5 ayi walima amarya tasha kyau cikin les blue inda malamai magada annabawa suyi wa'azi mai kashe jiki da ɓargo anty Hajara kam ansha kuka inda ƙawayan ke mata dariya daga baya su koma lallashin ta. Antashine gab da magrib, dan haka kowa ya tashi muma muje miyi sallah. Gajiyar dana yine yasa na kwanta da wuri dan so nake na huta ko dinner ma yau bazan yiba waya tace ta fara rigging ganin sunan daya fito ɓaro-ɓaro akan screen ɗin wayar wato حببي yasani sakin murmushi na ɗauka da sallama a baki nah, daga can ɓangaren ya amsa min sallamar har ina jiyo sautin murmushin sa, haka mu cigaba da waya cikin soyayya da nisha can yace. "Albishirinki my princess". Ido na lumshe kana nace goro. "an shirya komai tsaf gobe in sha ALLAHU za'a tsaida date. Jinai duk wani iri, amma a ƙasan raina ina farin ciki da hakan. Koba komai ai zan samu ƴancin kaina. Daga nan mu cigaba da fira bajima muyi sallama. *Washegari* Yau ta kasance ana i gobe ɗaurin aure kuma yau za'a sa amarya a lalle mukam tunda mu fita wankin kai dan acan ma amana namu lallen baki da jah sai dai ace Masha Allah kam dan lalli yayi kyau. bamu dawo ba sai gab da magrib. a gajiye mu shiga ciki inda mu tarar parlour cike da baki. gaishe su muyi mu wuce sama inda kai tsaye ɗakin anty Hajara mu nufa. Zaune take tasha lalli ƙawayan ta sun sata a tsaki sai zolayarta suke. Muma zama muyi a ɗaura damu daga baya ma data gaji tashi tayi wai zata amsa waya. Dariya muyi Nabila ke cewa "ba wani waya dama kin dawo" bata kulata ba ta fice muma mu tashi mu nufi bedroom. Wanka nayi tare da dauro alwala bayan na gabatar da sallah magrib ban tashi ba na fara karatun Alqur'ani ko wanne harafi ina bashi haƙƙin sa saida akira isha'i na tashi na gabatar, lokacin yaya Ansar ya kirani a waya da rabon dami waya dashi tun shekaran jiya. Cikin farin ciki na ɗaga tare dayin sallama. Daga ca ya amsamin tare da tambaya ya nake, mun dade muna fira yake cemin ɗazu ya dawo yanzu haka ma yana gida. Cikin shagoɓɓa nace. "Yayah zaka zo nanne yau?" Daga can ina jiyo murmushin sa kana yace. "Safiyyah kenan dare yayi saidai zuwa gobe ran daurin aure insha Allah" "Toh yaya nah Allah ya kaimu lafiya". Da "Ameen" ya amsa kana muyi sallama. Tun muna waya dama md ke kirana sai bayan mun gama na kirasa bai dauka ba sai ya sake kirana. Mun daɗe muna waya tunda najisa cikin farin ciki nasan da walakin goro. Yake cemin. "My princess yau fa ansa rana nan da wata ɗaya insha Allah kina gida na" Dama tuni yaya Ansar ya faɗa min ansa rana, amah bai faɗa min wata nawa ba. Cikin jin kunya nayi ƙasa da kaina kamar yana gaba na nace. "Allah yah kaimu" Da "Ameen yah rabbi" ya amsa kana mu cigaba da waya cikin farin ciki. Buhaisa ce tazo ta kirani wai yayah Saif na kira na. Koda naje ba abinda yamin saima fira dami dashi yanda muke firar nagan shi wani iri cikin damuwa nake cewa. "Yaya Saif baka da meke damun kane nagan ka wani iri?" "Uhmm bakomai kawai dai rabuwa da Hajara ne" "Allah sarki yayah ai sai hakuri haka aure ya gada. Kai da kake babba kai zaka ƙarfafa mana gwuiwa. Please yayah ka kwantar da hankali ka kaji". Tunda ta fara maganar ya zuba mata yana kallon ta a zuciyar sa yace. "Uhmmm bazaki gane bane Safiyyah" (Allah sarki 😥Yah saif) Suna zaune har Buhaisa tazo su cigaba da fira. ________ Ɓangaren mom kuwa tunda a kawo kayan sa rana take ta tasa Abba a gaba tana masifa sai hakuri yake bata amah sam taƙi saurarasa ta yadda take shiga a tannan take fita ba. daga baya daya gaji sai ficewa yayi ya bar mata gidan, inda anty Waleeda ta saka mata kuka. "Wallahi mom in ban sami Suraj ba itama Safiyyah bazata same saba. dan wallahi nafi karfin inrasa abu ita ta samu impossible mom wallahi bazai taba yiwuwa ba" takai ƙarshe maganar cikin tsawa kamar wata mahaukaciya. Ita dai mom da kallo kawai tabi ɗiyar tata cikin sauke ajiyar zuciya tace. "Toke Waleeda banda abinki ai koh bakya son wannan yaron wallahi bazan taɓa barin Safiyyah ɗiyar Amina ta aure saba. kenan ma Amina tafini koda bata raye yanda yaron yake ɗan gidan manya ta aure shi ai Amina tamin nisa tafini, wallahi indai ina raye Amina bazata taɓa finaba ko da yaushe saidai ta kasance a bayana. Ke Safiyyah ma bazan barta tai aure sai dai ta ƙare a me min bauta, daga baya na haɗa da wanda nasan bazai barta ta huta ba. Dan haka ki kwantar da hankalin ki auren ki dashi ba fashi inko baki same saba itama bazata same shiba wallahi. Takai ƙarshen maganar rai bace inda anty Waleeda ta rungume ta tana zuba mata kirari. Wayarta ta dauka tana neman layin Umman ta aikuwa baifi ringing ɗaya ba aka ɗaga daga can ɓangaren, bako sallama ta fara faɗin. "Umma komai fa na shirin lalace wa gashi har ansa rana nan da wata ɗaya bikin wannan matsiyaciyar". Shiru tayi na ɗan wani lokaci tana sauraren mahaifiyar tata, can kuma tace. " Anya Umma na kan kwari kuwa yayi aikin nan cewa fa yayi baza ma asa rana ba balle biki gashi har ansa rana saura biki, gaskiya Umma ki neman mana wani dan so nake nanda gobe komai ya wargatse wallahi". Shiru ta kumayi nadan wani lokaci alamun tana sauraren ta kana cikin taɓe baki tace. "Uhmm tana can gidan wannan ƙanwar uwar tata Halima ana bikin wannan shegiyar yar tata data ƙi aure sai yanzu. Dan wallahi yanzu haka nasan itake zugata duk iskanci da take amah bari ta dawo zan gyara mata zama". "Toh Umma saikin zo ɗin" ta kareshe maganar tana yanke kiran hankali kwance. (Ni koh nace ayi dai mugani☹️) __________ A ɓangare Suraj kuwa wato (MD) musalta muku irin farin cikin daya shiga bata lokaci ne, daga shi har iyayen sa. Inda tuni dangin sa sunji daga ciki akwai yarinyar ƙanwar mahaifinsa dake mutukar sonsa amah shi kwata-kwata bata gaban sa. Aikuwa da suji labari har gida tazo ta zazzage momy ita da ɗiyar tata. Ana haka Suraj ya dawo cikin farin ciki domin ganin mahaifiyar tasa ya tarar su lubna da mahaifiyar ta suma ma momyn sa wulaƙanci. Tsawa ya daka ma lubna tare da sauke mata lafiyayyen mari, ya mata tatas ita da mahaifiyar tata dakyar su fice tare da cin alwashi kala-kala. Kasan cewar momyn tashi macece mai hakuri ta lallaɓa shi da kwantar mai da hankali. ___________💫 Rana bata karya sai dai uwar ɗiya taji kunya inji masu iya magana dan kuwa yau aka daura auren anty Hajara da angon ta Ahmad. Inda bayan daurin aure da gama hotuna a fara shirye-shiryen tafiya da amarya Abuja. Can na hango ƙannin amarya wato Safiyyah da Buhaisa da Isha, gurin su yaya Ansar da yaya Saif dan harda MD ma. inda su haɗe cikin ankon shadda yar uban su pink calour. sunsha make up sunyi kyau saidai ace tabarakallah. Kasan cewar Safiyyah ba gonar kwalliya bace dan saida Ummii ta matsa amata kana ta yarda, aikuwa tayi matukar kar kyau kamar itace amaryar kowa sai yabawa yake. Bayan sun gama gaisawa da MD akayi musu hotona. Ummii ma uwar amarya ta haɗe cikin fitinanne Les ɗin ta ɗan ubansu marron colour and white saidai ace Masha Allah amah fa tasha kyau. Inda ta shiga cikin tsakiyar yaran nata amusu hotuna. kana a fara shirye-shiryen tafiya da amarya. Inda akaita gurin dady ya mata faɗa da nasiha mai ratsa jiki aikuwa taita kuka za'a tafi da amarya da kyar a ɓanɓareta a jikin Ummii ta rungume ta tana kuka. Muko dariya muyi ta mata daganan mu ɗauki hanyar Abuja. Ankai amarya gidan ta lafiya gida yayi kyau saidai ace masha Allah. 8pm mu fara shirye-shiryen zuwa gurin dinner, inda akawo me mana make up bayan angama ma, amarya da ƙawayen ta sai mu. Kasan cewar mu uku ne sai kwalliyar tai sauri, dan danan simple makeup akayi mana, amma komai iri d'aya, dama haka mukeyi, komai namu kullmun iri d'ayane. Munyi k'yau mukayi shiri cikin material blue doguwar riga dan ta matseni da kyar nake motsi, kamar yanda aka tsara sai veil shi kuma pink. Na jujjuya ina kallon kaina a mirror, “kai jama'a nikam bazan iya fita hakaba gaskiya”. Buhaisa dake kwance tana danna waya tad'ago ta kalleni, “kai amma kuma wlhy kayan sun miki k'yau, kinganki kuwa? dan ALLAH ki barsu, kiyi rolling veil naki kawai”. “kai ba Safiyyah kad'aibafa, nima bazan iyaba, after dress zan d'ora wlhy”. Cewar Isha. Dariya Buhaisa tayi, ta tashi zaune tana ajiye wayar, “waiku miyasa k'auyawane sister's, naga a ke6antaccen waje za'ayi?”. “amma kuma dai ai akwai maza kema kin sani”. “to alaranmiya, Ku saka, amma kafin Ku saka ɗin nidai kuzo miyi hotuna”. Gaskiya koni nasan munyi k'yau, kasancewar mud'in fararene, kalolin duk sai suka kar6i jikinmu blue & pink. Wanda bai saniba saiya ce mu 'yan uku ne. dan muna matuk'ar kama da juna, sai dai Buhaisa tafimu haske niku ma nafisu ɗan jiki. Sai da mukad'anyi hotuna sannan muka fito. Inda ƙawayan anty Hajara suyi tace wa munyi k'yau, Kai tsaye gurin taron mu ƙarasa inda abokan ango su ɗi bemu. tunkan mu k'arasa muke jiyo tashin kid'a. wajen dank'am yake da 'yanmata da samari, da yan uwan ango da namu muma, sai abokan ango, Tunda muka shigo akai mana caa da idanu, wasu tsantsar kamarmu ce tajawo hankalinsu kanmu, wasukuma burgesu mukayi, to dama shi taro ya gaji haka. Amarya ta sha kyau sai dai ace masha Allah ita da angon ta Ahmad Nan afara gabatar da shagali sai pictures da'aka d'auka da video, 'yan mata sunata casar rawarsu da samari, mudai muna gefe muna kallo. Dan koda a bukaci muje ba rawar dana yi sudai su Buhaisa sun taka. Inda wani maƙalalle a abokan Yah Ahmad ya nace min, to suma dai su Buhaisa sun sami nasu. gab da magriba taro yatashi lfy, kowa ya kama gabansa. muma gida a maida mu. *In the Afternoon* "Wai dan Allah Safiyyah ku fito mu tafi mana bawan Allah nan tun ɗazu yana can yana jiran mu, kuma kunsan anjima zamu wuce". Buhaisa da tunda ta fara magana saida takai ƙarshe ta tsaya. "Afwan muje dan Allah karkiyi far feson mu mai saurayi". Dariya tayi "eh naji ai ya daɗe yana jiran mu koh" "please ku muje magana nan nu" cewar Isha tana ƙaraso wa inda muke. Dama saurayin Buhaisa ne yace wai ya kamata mu fita waje mu dansha iska. Dani kwata-kwata banyi niyar fita ba dan saida anty Hajara tasa baki kana na shirya. Shine yanzu tazo tana mana aka-aka. Duka baya mu shiga ashe harda saurayin Isha aciki, kai tsaye a wani tanƙamemen shopping mall yayi parking. Masha Allah tabarakallah shine kawai abin dana ke faɗa a zuciya. Wani irin don kulallen ginine mai tsawo da sam baida iyaka gamai kallo. Ganine irin na mutanen ƙetare wanda iya haɗuwa yah haɗu, sai wasu tanfatsa-tanfatsa din glass masu kama da window ko ince kofa. Ginin da yake a dunkule kamar anyi cycle da iya kawai gun da a zagaye, abin kallo, shine a gaba inda yake haɗe da wani wanda ya kasance mai faɗi. Inda nakai kallo na saman wancan ginin dake a dunkule, ajikin sane sunan gurin ke rubuce. *A A SARAKI SHOPPING MALL* Nagani a rubuce da Golding colour, dolene kaga wannan gurin ka tsarkake sunan Ubangiji mai girma da ɗaukaka. tabbas na taɓa jin sunan amah a ina shine na manta. A gaba ki ɗaya parking lot ɗin motoci ne na alfarama, wasu na shiga wasu na fita keda ganin gurin kasan sai dan wane da wane. "Ku muje" maganar da Ishaq saurayin Buhaisa yayine ta dawo dani daga haiyacina daga kallon ginin, bance komai ba mu fito daga motar. Aikuwa muna fira wannan nataccen daya nace min shima ya fito a tashi motar, kallo ɗaya namishi na dauke kaina ina jin gina da motar. Kusa dani ya matso yana cewa "beb muje koh" Ban ɗago ba bale na nuna alamun naji me yace. Buhaisa ce tazo saitin kune na cikin raɗa-raɗa take cewa. "Please Sopy karki bada mu mana, kuma kimsan wulaƙanci ba kyau" Kalmar ƙarshe data faɗa ce ta sani motsawa inda suyi gaba itada Ishaq mu kuma a bayan su su Isha a bayan mu. Kai tsaye cikin katafaren mall ɗin mu shiga.........✍️ _*Taku har kullum da ko yaushe*_ *Billy pinky💞* ing📲* _WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _WhatsApp group_👇 https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 Amanar nazari writer's ✍️ Page 3️⃣0️⃣➡️3️⃣1️⃣ *A A SARAKI HOUSE* "Boss ya kamata fa yau kaje kaga A A SARARI SHOPPING MALL saboda tunda ka dawo baka je kaga meke tafiya ba duk dai ina zuwa amah zuwan naka zaifi. Ina ganin kawai daga can sai mu wuce gurin metting ɗin" Youseef ya ƙare sa maganar yana kallon Majeed cikin fatan Allah yasa ya amince yadda suke kamar yan sama jannatin nan yau suna waccan kasar gobe waccan ya kamata yaje yaga meke wakana kafin su kuma barin kasar. Tunda Youseef ya fara magana har ya gama baice komai ba illa zube shi da rikitattun idanun sa da yayi a hankali ya motsa bakin sa kamar wanda ama tilas yace. "Okay muje" ya faɗa ya miƙewa sai lokacin na kare mai kallo sanye yake cikin sute silver sai ta ciki data kasance black sai neck tie silver. Gashin nan yasha gyara dan ya kwanta masa luf-luf a gadan bayan sa. Ba abinda yake sai ƙamshin mayun turarukan sa masu mutukar ƙamshi da sanya nutsuwa, Taku yake cikin ƙasaita gami da izzah Youseef biye dashi har su fice kai tsaye part din Ammei su nufa inda parlour yake shiru dan haka ya nufi bedroom ɗin ta Youseef dama tuni ya wuce Babban parlour yana jiransa a can. Sallama dauke a bakinsa ya shiga inda ya sami Ammei zaune akan sofa dake cikin bedroom ɗin waya a hannun ta da alama waya ta gama ko kuma zatayi, har gaban ta ya ƙarasa tare da kaiwa kasa yana gaidata cikin fara'a ta amsa tare da kamo hannun sa ta zaunar kusa da ita. "Majeed amah kana shan maganin ka kuwa dan ya kamata ace yanzu komai tsakanin ka da dadyn ku ya wuce amah abin kamar ma gaba yake kuma kace kana sha a ina matsalar take" ta ƙara sa maganar cike da damuwa. Hannun ta ya kama cikin son kwantar mata da hankali yace. "Humm Ammei ki kwantar da hankalin ki insha Allah komai zai wuce kinji Ammei nah" yakai kashe tare da lumshe ido, "Na sani amah nasan halinka fa anya kana shan maganin nan kuwa?" "Uhmm yanzu dai Ammei bar naje Youseef na jirana za muje mall inna dawo sai muyi magana" ya kai ƙarshe tare da sumbatar goshin ta. Tasan dan baya san maganar ne kawai shiyasa zai tafi addu'a tamishi kana ya fice cikin nutsuwa. Yana fitowa Youseef ya samu a parlour kasa shida su Auta da Basma suna fira sai Zaituna dake can zaune akan kujerar mai ɗaukar mutum ɗaya cikin riga da wando sai ƙaramin mayafi, dan dama jiran fitowar sa take tana danna waya, sai su fennah dake can rukunin kujeru White and black suna fira, yana fitowa gaba ɗayan su natsuwa suyi Zaituna dake danna waya ma ajiye ta tayi duk suka gaidashi cikin girmama wa. Kyakkyawar fuskarsa ma abociyar kamewa da tsare gida a haɗe ya amsa batare da ya kalli ko acikin su ba su fice shida Youseef. Da sauri Youseef ya buɗe masa bayan farar zananniyar motar da Samuel ya fiddo, wadda ko makaho ya shafa yasan eh lallai kuɗi yay aiki wajen sayen ta. Dan sai wani irin sheƙi take da ƙyalli mai ɗaukar ido. Gata nan wata ƴar ƙumbula bata cika hayaniya ba, ba kuma ta cika mamaye waje ba. Tsaf take kala da yanayin matasan zamani irinsa da ke gara kan kuɗi ta yanda suke so saboda amincewar UBANGIJI garesu. Sai da ya zauna Youseef ya maida ƙofar ya rufe sannan kowa ya zabura ya shiga mazauninsa. Youseef da Samuel na gaba kamar koyaushe. Securitys ɗin sa na'a wata motar kamar ko yaushe suma. Da dasu uku ma kawai zaiyi fitar. Samuel na ƙoƙarin tada mota ta fito da ɗan saurinta. Kamar kullum tana a cikin kwalliya dake ƙara fidda mata ƙyawunta da bayyana wayewarta. Youseef ne yay ma Samuel nuni daya dakata, dan haka ya tsaya ɗin harta ƙaraso, kallo ɗaya tai musu ta ɗauke kanta, dan direct bayan ta nufa saitin inda Majeed da bai san ma da fitowar tata ba yake. Dan hankalinsa nakan takardun daya ɗauka a gefensa da Youseef ne ya ajiye masa su dan ya duba. Cikin shagwaɓaɓɓiyar muryata data haɗe da gayu ta furta, “My bro.. please zan bika, nasan dai mall zakaje”. Idan kujerar motar nan ta motsa shima ya motsa duk da kuwa muryar tata tazo masa a bazata tunda shi bai san da fitowar tasu ba. Kuma inama tasan da zuwan sa mall. Ƙara narke murya tayi cikin nuna damuwa da shirun nasa ta sake cewa, “Please mana Yaya Majeed na shigo?”. “Kai kana jiran miye?!”. Ya faɗa cikin yanayin fusata batare daya ɗago ba. Ai jikin Samuel har rawa yake wajen murzama motar key dan ko kallonsu ogansu yayi sun san mi yake nufi balle magana da baki. Da wani kalar mayen kallo Zaituna tabi motar, ga wani irin sanyi ƙalau da jikinta ke komawa kamar an zubama bread ruwa. Dai-dai motocin na isa katafaren golden an black gate ɗin gidan da aka wangale musu wasu hawaye masu zafi suka shiga rige-rigen sakkowa saman ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Bata motsasu ba, bata kuma yi yinƙurin barin wajen ba. Ashe turaren da Mommy ta bata duk na ƙarya ne tunda gashi tazo gabansa amma bai kulatan ba. Azizat dake ta bayansu ce laɓe ta tako zuwa inda take bayan ta gama cin dariya, dan tun fitowar Zaituna daga parlour tabiyo bayanta, dama kuma itace ta ɗauke turaren da Mommy ɗin ta bama Zaituna ɗin dan a kunnenta komai ya faru sanda take bata batare da su sun sani ba. Hannunta ta kama kawai tare da janyota ta faɗa jikinta. Rungumeta tayi cikin sigar nuna lallashi batare da tace mata komai ba, sai dai shafa bayanta kawai da takeyi dan babu wani abu da zata faɗa mata kuma wanda ita bata sanshi ba. Sai dai kawai taƙi yarda ne kamar yanda kowa ya sani. Dan tunda yayansu yaface bayayi tofa babu ubanda ya isa cewa yayin sai Ammeinsa, da dady. Bata ganin laifin Zaituna wani lokacin, dan wlhy ko ita inama-inama. Amma yanda tasan yana mata kallon ƙanwa yasa take dannewa kawai. Sun ɗan jima a wajen kafin ta kama hannunta su koma ciki... Kai tsaye basu zame ko inaba sai A A SARAKI SHOPPING MALL gabaki ɗaya ma'aikatan gurin ruɗewa suyi ganin oga da kanshi nan suka fara gaidashi cikin girmamawa tare da kaishi guri na musamman duk lokacin daya zo dama gun yake zama. A ɓangaren mu kuwa saida mu shiga mu sake tabbatar da cewa lallai gurin bana wasa bane dan waje ba komai bane akan cikin inda ya kasance komai da zallar glass akayi, inda ya kasance sama da kasa . gaskiya musalta muku kyau da tsaruwar gurin bata lokaci ne dan zamuci lokaci da yawa amah naba kowa damar ƙiyastawa. (kyau ace kowa yaje ya gani da idanunsa lol😁) mutane ne keta kai kawo a gurin 'yan mata da samari harma da matan aure wasu da mazajen su harda masu jajayen kunnuwa dan ga dukkan alamu sune ma'aikata gurin. Mun shiga 6angaren kayan kwalliya, suce kowa yaza6i abinda yakeso. Nidai nace masa a'a na gode. 6ata fuska yayi yana hararata, ya maida kallonsa ga Buhaisa dasu tuni sun mayi gaba. Ya kalleni yana fad'in “mujeto ni na d'ebar miki”. bance masa komaiba nabi bayansa ganin kamar yayi fushi, da kansa yake za6ar mini duk abinda yadace. Dan iyakar mu ƙasa kiransa ayi awaya ya ɗan matsa gefe domin amsa kiran. Su Buhaisa ma sunacan suna d'auka, kamar ance nabar wajen saina zagaya tabaya, a dai-dai wannan lokacinne shikuma yake tunkarowa shida mutanen shi, da alama yana zagayene kowani abun daban. tafiya yake cikeda nutsuwa da izzah, sai sautin takunsa dakakeji, tunkam ya ƙaraso gareni ƙamshin sa ya riga shi isowa. Waige-waige na fara ban ankaraba saiji nayi natafi suuuu santsi ya kwasheni. Kasan cewar shi mutumne mai yawan tausayi da taimako, da sauri yayo kaina kafin naje ƙasa, Dan yasan fad'uwata a wajen babban had'arine dan ba ƙaramin woya zan shaba danni nama sadak'ar na faɗi ido na runtse kawai ina jiran kaiwata ƙasa. Majeed ya tabbatar idan ya barta ta faɗi zataji mugun ciwo ne, dan haka da saurinsa kuwa ya tarota ta faɗo jikinsa. Jin shiru ban faɗi ba kuma najini kamar kwance a jikin mutum tsabar firgice da tsoratar da nayi yasani buɗe idona dana runtse. Zuruf ya faɗa cikin rikitattun nasa dashima ya kafe fuskata da kallo da sauri na janye nawa. Cikin tashin hankali na fara mutsu-mutsun kwatar kaina, jikina sai rawa ya ke yi. Shikuma yaƙi sakinta dan ya tabbatar yana sakin nata faɗuwar daya gudar mata a farko sai tayi wadda ta fita a yanzu, Duk da tsawan da yayi mata bata nutsuba, sai ma cigaba dayin mutsu-mutsunta nason ƙwacewa takeyi, tuni hawaye kuwa sun fara bimata kumatu, dan a rayuwarta da hankalin kanta kuma hakan bai taɓa faruwa da itaba. Ko hannu bata yarda koda Yah Safwan koh Yah Saif wani ya riƙe mata balle akai ga runguma irin haka. Sai gata yau kwance a ƙirjin wani ƙaton, da ko yayunta basu taɓa aikata haka a gareta ba. Ai dama barinta yayi ta faɗin da wannan abin kunyar......... Saida ya tabbatar ya dai-dai ta yadda koda ya saketa bazata faɗi ba kana ya saketa, ba tare da yace uffan ba yabar wajen, inda su Samuel su take mai baya. A hankali na sauke ajiyar zuciya tare da bin bayan sa da kallo. Su Buhaisa da akan idonsu komai ya faru, sai Youseef daya tsaya ya mata sannu shida ma'aikatan gurin dasu rako shi kana yabi bayan boss din nasa zuciyar sa cike da wasu-wasi. Da sauri su ƙaraso gareni suna tanbayata babudai wata damuwa ko?. “babu komai Alhmdllh”. ‘nafad'a ina gyara tsayuwata’. Kana nace kuzo mu tafi gaskiya dan daga nan ba inda zan motsa sai gida, Buhaisa da Isha ma atare sukace haka ne gaskiya tafiya zamuyi. da kyar mu yadda muje gurin biyan kuɗin su biya nikam danaga bazan iyaba ma waje na fita batare dana musu magana ba. Dai-dai zan ƙarasa gurin motar da muzo, suma su fito ta wata ƙofa alamun suma tafiya za suyi dan mun kusa cin karo dashi na maza naja baya. Raɓani yayi ya wuce yabarni da kamshin turaren shi. , A dai-dai lokacin su Buhaisa su ƙaraso gurin hannu na takama mu wuce mota, a motar da muzo anan mu koma kai tsaye gida mu koma inda anty Hajara tace. "niko ina kujene haka kun daɗe sosai 'yan mata masu samari". dariya su Buhaisa suyi su fara bata labari, "wallahi anty Hajara karkiga yadda gay din ya had'u anya ba Balarabe bane kuwa isha?" Buhaisa tai tambayar tana rike haba "ke saidai ba indiya harfa gashine kwance a gadan bayan sa irin nawani jarumi bani sunan sa nan Safiyyah" Isha ta fada tana kallo na tsaki naja tare da cewa. "Ke kisanshi kuma" dariya suyi Buhaisa na faɗin "anty kinga kuwa yadda Safiyyah tayi wallahi badin daya sake ta tafiya yayiba dayasha masifa dan karkiga yadda ta haɗe fuska. Kamar ba wacce a temakaba". Takai ƙarshe maganar tana hararata kala bance ba saima wayata dana cigaba da danna wa, inajin firar tasu inda duk akan wannan mutumin ne. "Oooh wai A A SARAKI MALL kuje badai nifinku mai Company ne ya temake taba da zata faɗi.?" "Shi kuwa anty wannan A A Saraki nefa da zakiji ana yawan faɗar shi saboda cigaban daya kawoma Arewacin Nigeria inda naji wai duk Arewacin Nigeria harma da kudun bame kuɗin baban shi. Wallahi anty ban taɓa tunanin zan ganshi ido da ido ba sai gashi yau na ganshi danko a mujallah ko gidan TV ban taɓa gannin shiba". Cewar Buhaisa inda Isha tace "ai kisan baya son magana da yan jarida shiyasa" "Uhmm amah fa Allah yayi halitta agunan" Buhaisa da Isha dai sai firar Majeed suke yi inda Isha tace waini kam meye cikakken sunan sane naji anata A A SARAKI koh" Anty Hajara dai dariya tayi tana cewa "ah lallai wannan guy din ya tafinmu daku toh full sunan shidai kamar danaji ana cewa Abdulmajeed Abubakar Saraki" "Wow nice name" suka haɗa baki wajen faɗa inda suka tasani a gaba ganin yadda nasha mur naki cewa komai wai. "Wallahi karkiga yadda ku dace" tsaki naja na shige ciki. Kallo suka bini dashi, Ihsan kawar anty Hajara tace, “Anya yarinyarnan batada aljanu?, ke kowama bai mikiba?, yanzu nan duk had'uwar Majeed Safiyyah tana nufin bai burgeta ba kenan?”. Dariya Buhaisa tayi, sis... Ihsan har yanzu baki gama fahimtar Safiyyah ba na lura, kyagama abinda yafi haka indai daga wajentane. Yanzu hakama tunda kikaji tace haka ko sau d'aya bata kalleshiba wlhy bare tasanma kalarsa. “humm aiko wlhy inabata kalleshiba anyi babu ita kuwa, ruwa ta shata kuma, yo kobabu komai aina bada koda labarine nace nata6a ganinsa ido da ido ko”. ‘cewar Ihsan’. Dariya kawai Buhaisa tayi, su cigaba da firar su inda suka tsaya. inda ni ciki ma nashiga na kwanta dan kaina wani irin ciwo yakemin dama tunda na tashi yau nakeji gabana na faɗuwa. *Washegari* Muyi sallama da Abuja inda dakyar aka ɓanɓaremu ajikin anty Hajara dan haka mu barota tanata kuka danma Yah Ahmad yana gidan, toh mumu dai haka muke shiru kamar kurame har mu isa Kaduna. Dan Isha ko gidan Ummi bata shigaba tace wallahi gida tayi to muma bamu takura mata ba muyi sallama mushige ciki. Inda mu samu duk bakin sun tafi sai ƙalilan na nesa nima dai yau maso tafiya amah Ummi ta hana tace na bari sai gobe. Kasan cewar gaba da magrib mu dawo sallah kawai nayi sai karatu ina zaune akan sallaya har a kira isha'i na tashi na gabatar daganan ƙasa na sauka muyi dinner inda su Yah Saif su dawo musha fira daganan mu wuce mu kwanta. *In the evening* Sanye take saukowa cikin abaya pink sai mayafin ta White da nayi rolling ƙaramar hand bag pink ce a hannu na sai plate shoe pink mai gashi-gashi asaman sa waya kare a kunne ta tana waya da Isha. Buhaisa riƙe da ƙaramin akwatin ta a hannu fuskar nan a haɗe Safiyyah zata tafi ta barta. "Eh kijirani yanzu in zamu wuce da Yah Ansar zan biyo muyi sallama" shiru tayi na wani lokaci kana tace. "Okay saina zo" dai-dai suna ƙara sawa parlour inda Yah Ansar ke zaune shida Ummi suna fira yana jiran ta fito su tafi. Zama muyi muna gaisawa da Yah Ansar Ummi ce ta kalli Buhaisa data haɗe rai tace. "Ikon Allah Safiyyahn zakibi ne dakike niyar sakin kuka" cikin tura baki gaba tace "yanzu fissabilah anty Hajara ta tafi itama Safiyyah danake gani take ɗebe min kewa itama zata tafi ni Allah Binta zanyi". Dariya Ummi tayi tace. "Aikuwa baki isaba nikuma kibarni dawa Saifu da inya fita aiki sai an ganshi baki ba Hajara to bazai yiwu ba. Indai Safiyyah ce tama kusa dawowa nan da zama tunda bikinta ya taho nanda wata ɗaya ne dan bazan barta agun waccan matar ba wallahi dan ba uwar da zata tsinana mata". Takai ƙarshen maganar ranta bacce. Mudai shiru muyi batare da munce komai ba har ta gama sai Yah Ansar ne ya bata baki sallama muyi mata mu tafi Buhaisa kam harda hawaye tonima dai yau ta sani kukan. kai tsaye gidan su Isha muje da take jirana. Har ciki na shiga nabar Yah Ansar a mota yana jirana, koda na shiga mu gaisa da Momyn ta inda tashiga ta kiramin ita, bangajiya na mata muyi sallama nace. "Kinga Isha bari na tafi Yah Ansar na mota yana jirana kizo muje ku gaisa". Murmushi tayi kana tace "a'a ki gaidamin da shi ba saina fita ba" galala nayi ina kallon ta kana nace. "Lallai ma wai ni dan Allah meke tsakanin ki da Yah Ansar ne naga sai wani kunyar sa kikeji anya kuwa Isha". "Uhmm kinga tashi muje dan Allah karkimin wata fassarar Mrs Md" Sallama nayima momy kana mu fita saida na fita nake cewa. "Can muku dai intai wari maji". "Bama zatai ba ai balle kuji". Dariya kawai nayi batare dana ce mata komaiba har mu iso inda motar sa take, tunkan mu ƙarasa ya zubeta da kallo dan saida ta gaishe sa kana ya ɗago yana amsawa murmushi kwance a fuskar sa. Nidai murmushi nayi na shiga ina jiran su gama gaisawa yazo mu tafi. Gida ta koma mukuma mu dau hanyar gida. Koda mu isa gidan nayi a haukace yake kamar wanda yayi wata ba gyara sai can daga gefe akwatina ne dasu sweet, dasu alawa, da drinks, harda su biskit, a watse a ƙasa dukkan alamu kayan sa ranane da'a kawo shine aka wulaƙanta su haka. Yah Ansar ya buɗe baki da niyar yin magana saiga baby nan da gudu tazo ta rungume ni. Tana min oyoyo shine take cewa ai kayan sarana nane da'a kawo shine mom Bata taɓa ba ta barsu a gun, bance mata komai ba sai Yah Ansar ne ya fice na leka ta window naga motar shi ta fice a gidan. Nima kota kansu banbi na shige bedroom, "Yah rabb" shine abinda na furta ganin bedroom ɗin kamar anyi danbe a cikin sa kaina har juyawa yake saboda na tsani naga guri da datti koya yake. Dama nasan za'a rina amah banyi tunanin dattin zakai hakaba. Kitchen na nufa na ɗauko kayan shara, da bedroom na fara kana nazo parlour jin gidan shiru yasa nace koh mom bata nan ne, bayan nagama share gidan gaba ɗaya bathroom na shiga shima na wanke shi abin haushi wai hatta pad ankasa d'auke wa saidai duk sanda na dawo na ɗauke. Haka na gama wanke wa tsaf na fito na fara mopping ina cikin mopping ɗine saiga su mom nan itada Anty Waleeda kodaga ina suke oho. Ko gaisuwar danake ma mom bata amsa bamin sai ciki su shige abinsu duk su batamin mopping din dana gamayi ga bayana ya gaji ga ciwon kai banbi takan gunda su bata ba nashige bedroom wanka nayi tare da dauro alwala. Inda anty Waleeda ta shigo sai habaici take zubarwa ban kalleta ba na tada salah. Bayan na kintsa cikin kayan shan iska na fita parlour saiga Yah Ansar nan shida Mama Hadiza ashe wai can yaje ya ɗauko ta. Kakace a wajenmu, dan ƙanwar kakarmu ce, mahaifiyar su Abba kenan. Ba sosai take zuwa gidan ba saboda wulaƙancin da Mom ke musu. Mu kuma Abba baya barinmu zuwa wajenta, garama Yaya yanzu daya mallaki hankalin kansa yana zuwa abinsa. Nayi murna ƙwarai da ganin mama Hadiza. A take na shiga hidima da ita dan naga alamun mom ko ruwa bata bata ba. Duk da hararar da Mom ke mun banbi takanta ba na shiga hidima da kakarmu. Bayan sallar isha'i kuma Yaya ya sayo mata kayan ƙwaɗayi yazo ga zauna muka sha hira. Dan dole Abba ma yazo ya zauna akayi da shi shima. Mom da anty Waleeda kuwa kowa yay shigewarsa ɗaki sai baby kawai a wajen. Bamu tashi a falon ba sai sha biyu. Abba ko tun sha ɗaya matarsa tazo ta tasashi suka shige ko kunyar mama Hadiza bata ji ba balle mu ƴaƴa. Gado nabarma mama Hadiza su kwanta itada Anty Waleeda Ni kuma na shinfiɗa bargo na kwanta. Sabuwar hira muka buɗe da ita har sai ɗaya sannan barci ya kwasheta. Niko alwala na tashi nayi nai nafilfilina kamar yanda na saba sannan na kwanta. Hakan kuma bai hanani tashi uku da rabi ba na shiga ayyukana. Kafin kace mi na kammala, dan har abinci naima mama Hadiza na saka mata a kula nakai ɗaki dan nasan ba lallai da rana a bata na kirki ba. Gashi ban dawoba lokacin. Kalacin ma isashe na ɗiba mata. Itako tanata mitar yanda nake wannan uban aiki ga fitar safe kuma. Ni dai bance komai ba face murmushi kawai. Yau kam Yah Ansar ya shigo gidan domin gaisheta. Ya ajiye mata kayan shayi da ƙaton bread ɗin ta harda soyayyan ƙwai. Albarka ta dinga saka mana sannan mukai mata sallama muka wuce dan kar mu makara. ◾Mama Hadiza itace ta raba komai na kayan sa ranar nan. Har maƙwafta sai da tasa Baby ta kai ma kowa gida-gida. Sannan dangin su ta ƙulla na kowa daki-daki. Wanda ke anan cikin Kaduna ta saka Yah Ansar ya kaita ta kai ma kowa. Na dangin Ummah kuwa har gida tasa Yah Ansar yakaita ta kaima Ummi. Yah Ansar ma da Yah Safwan ta ɗiba musu. Nima komai sai da ta ɗiba min. Hakama jama'ar gidan kowa da nashi. Kuma kowa zai iya rabama abokan arziƙinsa idan yaso. Amma sai Mom tai biris da nata anan falo har Yah Ansar ya maida Mama bata ɗauke ba daga ita har ƴaƴanta. Abba dai ganin mama Hadiza yasa shi zama ya ƙuƙƙula ya fita dasu wai zai rabama abokansa da ƴan wajen aikinsu. Ya raba ko bai raba ba oho masa. ◽A ranar da nakai ma ƴan office ɗinmu kowa ya sake sanin alaƙata da Suraj wato MD, dan wasu basu ɗauka gaske soyayya muke ba saboda yadda muke taka tsan-tsan dan shi yama rigani rabawa dan iya yan officer ɗin mu kawai ni na bama. *Abuja🤍* ........"Dama Mummy turaren da kika bani ba mai kyau bane ba batin kince ina sawa indai yaji ƙamshin shikenan zai fara sona" Zaituna ce ta tasa Mummy a gaba tana tambayar ta kamar zatai kuka. "Me kike nufi ne Zaituna kina nufin baku haɗu bane ko baki sabane eye". Tai maganar cikin zaro idanu, itama Zaituna cikin taɓe baki tace. "Wallahi Mummy nasa dan saida naga fitowar sa ma nima nasa kuma daga gun kaitsaye gurin sa na nufa amah Mummy karkiga irin wulaƙancin da yamin" ta kai ƙarshen maganar tana fashewa da kuka. "A'a wallahi da sake dan nasan Sakeenat bazata min karya ba akan turaren inma ya kasance karya ne wallahi tamu ce nida ita jeki dakko min turaren dakisa nagani". Ba musu Zaituna ta nufi ɓangaren su domin ɗauko turare, saboda yanzu Mummy ta bar part ɗin granny ta koma part ɗin ta. Koda ta kawo mata wata ashariya Mummy ta mulmulo tana sakin turaren ya faɗi ƙasa ya tarwatse, cikin hargagi ta ɗago kamar zata daki Zaituna. "Uban wa kika nuna ma sanda na baki, kinsan kuɗin dana kashe kuwa akansa kanna same shi shine zaki bari har a canza da wani?". Zaituna data ji tsoro ganin Mummy a haka dan koda wasa bata taɓa zagin taba sai yau aikuwa tasan ba ƙaramin kuɗi ta kashe ba dan Mummy bata da hakuri akan kuɗi. "Mummy Allah sanda na ajiye shi bakowa a ɗakin kuma Allah ba wanda yasan na ajiye shi". Mummy cikin sauke ajiyar zuciya ta zauna a gefen gado tayi shiru na wani lokaci tana kallon Zaituna kana tace. "Kibari zanyi bincike akai duk wacce naga da hannun ta aciki wallahi zan dau tsatstsaura. Mataki akanta. Nasa an kawo min shine saboda naga Yaya ya share magana ta kamar suna tsoran Majeed ɗin shiyasa nake so nayi maganin sa da kaina dan duk sanda yazo hannu na humm". Takai ƙarshen maganar tare da sakin makirin murmushi. Zaituna ba tayata. Azizat dake bakin ƙofa alaɓe tana jinsu tai wani shumin murmushi tare da cewa. "Ai Wallahi muddin inanan bazan bari ki auri Yah Majeed ba" tana gama faɗa ta wuce part ɗin granny.... ⚫ Ɓangaren Majeed kuwa tun da subar Mall gurin meeting su wuce inda dukkan tunanin shi yana gun wannan yarinyar daya rasa ina ya taɓa ganin ta. Daya ga yana takura ma kansa dan shi mutum ne wanda bai shiga abinda bai shafesa ba dan haka ya fige tunanin ta arai har su isah gida amah jefi-jefi takan faɗomai arai dan har Youseef ya lura da hakan. Bai zarce ko inaba sai part ɗinshi dan bebi ta babban parlour saboda yasan yanzu parlourn cike yake da 'yan matan gidan. Youseef biye dashi hannun sa riƙe da wasu Golding din leda mai dauke da tambarin Mall ɗinshi har su isha parlourn sa na kasa. Zaman su ba daɗe wa bayan ya sallami Youseef akan yaje ya ɗan huta saiya dawo shima ya tashi ya nufi bedroom, Kai tsaye bathroom ya shiga ya dau kusan 40 minutes kana ya fito sanye da bathrobe blue color hannun sa ɗauke da ƙarami yana guge kwantar ciyar sumar sa dake kwance har gadan bayansa. Bayan ya gama komai na al'adar rayuwar sa haka zalika ya shirya cikin kayan bacci farare tas ga ƙamshin dayake kamar ba dare ba ya fito parlour saboda yau bazaiyi dinner ba. Waya ya ɗauko ya shiga kiran granny bugu ɗaya ta dauka. Jin shiru yasata cewa. "inbaka da abin faɗa ne zan kashe waya ta kana cinye min kati ehe" Yanda tayi maganar saida yasa shi sakin ƙaramin murmushin gefen baki kana ya motsa bakin sa kadan kamar mai tsoran ajishi yace. "Please granny kiba wani ya kawomin madara" yakai ƙarshen maganar da alamun ya gaji dan da gani bayasan doguwar magana. Granny data taɓe baki daga can tace. "kasan banson wannan turancin naka dan Allah meye wani filis kace ne komai nifa in bazaka fito kayi magana ba zan datse kirana". Tana wani ballama wayar harara kamar yana gaban ta. Zaituna dake kusa da itadai sai kunshe dariya take ga wani farin ciki da take ciki na zataga rabin ran nata dan yau tun safe bata ganshi ba. Daga ɓangaren Majeed kuwa hannu yakai kansa dake dan masa ciwo kaɗan-kaɗan tare da jinjina rigimar granny da sarai yasan ta gane me yake nufi amah ta basar. "Humm in bazaki bani bane nasa anemo minla wani wajen ke komai sai kin ma mutum gori". Kasan cewar yasan hakan ne kawai zaisa ta kyale sa shiyasa, aikuwa granny cikin zaro idanu tace. "Rufamin asiri ni Maryamu ace na hana jikana guda ɗaya madara yo Allah na tuba meye wata madara? Bari nasa a kawo ma yanzu". Ba tare data jira me zaice ba ta yanke kiran. Murmushin gefen baki yayi kana ya jawo wayar sa yana da nawa. ..........Zaituna ce tace. "granny kawo na kaima Yaya madarar dan nasan yana can yana jira yau koda ya dawo bai shigo babban parlour ba". Tunda Zaituna ta fara magana har ta gama granny kallon ta take cikin taɓe baki ta fara kwalla kiran sunan Rabi'ah". Cikin nutsuwa mama Rabi'ah ta fito daga kitchen ta ƙarasa gurin granny. "Dama zance ne kiɗan zuba ma Abdulmajeedu madara ni kafar nan ta matsamin basan tashi dan Allah a kula sosai". Da "to" mama Rabi'ah ta amsa tana wuce wa kitchen, cikin ƙanƙanin lokaci ta gama haɗa ta ta kawo granny, Zaituna ta umarta data Kai masa tare da zuba mata gargaɗi. Kai tsaye part din ta nufa yana zaune a kujerar yayi crosing ƙafarsa ɗaya akan ɗaya da ganin sa duniyar tunanin ya faɗa. Dan saida ta ajiye a ƙaramin table ɗin dake tsakiyar kujerar da yake takai zaune ƙasa kusa da kafar sa tare da kure kyakkyawar fuskarsa da kallo. Jin kamar motsi kusa dashi yasa shi buɗe idanun sa a hankali yana binta da kallo dan bata masan ya buɗe idon ba dan ta lula duniyar tunanin. Tsawar daya daka mata ne yasa ta firgigit ta dawo daga tunanin data fada tana kwabe fuska, ta buɗe baki da niyar magana ya daura hannun sa asaman labban sa tare da nuna mata kofa. Sanin halinsa da baya son musu yasa ta fita da sauri hawaye na zubowa a idanun ta, kai kawai ya girgiza kana ya haura sama domin wanke bakinsa sbd zaisha madara. Bai dadewa ya dawo ya zuba a ƙaramin mug yana sha a hankali, cikin lokaci kaɗan ya gama sha ya koma kan laptop yana danna wa kafin Youseef yazo. A hankali yake jin bakon yanayi a kansa tun yana daure wa ya daiji abin bana wasa bane ya tashi a hankali zai nufi bedroom jiwa ta kwashe shi ya zuɓe a ƙasa. Matar dake labe a bayan kofa ta saki wani makirin murmushi da sauri ta bar part din.................................✍️ (Toh fah🤔🤔 inji mai tallan totuwa a birnin totoh🤨) *Taku har kullum da koh yaushe* *Billy pinky💞* Typing📲* _WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _WhatsApp group_👇 https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *✨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION✨* *T.M.W.A.✍️* ✨✨✨✨✨ 💪😊 *TUNANI MAI ZURFI KAFIN RUBUTU SHINE TAKEN MU, RUBUTU MAI FAD'AKARWA DOMIN AL'UMMA,AL'K'ALAMIN MU ABIN AL'FAHARINMU, RUBUTU BAIWA CE GA WANDA ALLAH YA BAWA,TAKENMU SHINE HASKAWA A CIKIN AL'UMMA DA FIKIRAR DA ALLAH YA MANA, TAURARU A DUNIYAR MARUBUTA.* ✨✨✨✨✨ 💪😊 *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 *Amanar taurari writer's asso..✍️* Page 3️⃣2️⃣➡️3️⃣3️⃣ ................ Youseef ne ke shigowa part din shida Samuel kasan cewar neman da boss ke musu tunkan su ƙaraso cikin parlour su hango kamar mutum kwance a ƙasa. Cikin tashin hankali su ƙarasa inda su tarar da Majeed kwance a ƙasa ga wata kunfa dake fitowa a bakin sa danko motsi bayayi. Cikin tashin hankali Samuel ya nufi shi yana kiran boss, shiko Youseef da kingan sa yana cikin tashin hankali ya shiga kiran doctor ɗin gidan ring biyu tayi ya dauka. Ba tare daya jira mai zaice ba ya fara bashi ummarni, doctor fadil jin yadda Youseef ke magana cikin tashin hankali yasan ba ƙaramin abu bane ya sami Majeed. .........cikin ƙan-ƙanin lokaci saiga su doctor fadil da gadon nan da ake daukar marasa lafiya, shida sauran doctor's din. Sunyi shiga ɗimuwa ganin halin da Majeed yake ba ɓata lokaci su nufi hospital din dake cikin gidan dashi, babban hospital ne acikin gidan dan koh wani asibitin ma albarka ga kwararrun ma aikata masu jajayen kunnuwa Hausa wan kaɗan. Kai tsaye Emagency aka nufa dashi domin bashi temakon gaggawa dan tuni gabar ta fara aiki ajikinsa kasan cewar ta mai karfi. Kasancewar darene yasa a gidan ba wanda ya san Majeed na asibiti, sai ma'aikatan gidan dake kaikawone suga sanda a fito dashi cikin tashin hankali suka nufi part din granny dan sun san gaba ɗaya family yanzu suna can. Kuma ganin ba ko ɗaya acikin sune ya tabbatar musu da ba wanda ya sani, dan uncle Sulaiman ma bai daɗe da shiga cikin ba. Aikuwa shigar ɗaya daga cikin ma'aikatan cikin parlour tare da sallamar sace ta dawo dasu daga firar da suke, hankali su mayar kan sa inda Mummy tayi ƙofa ta mike cikin daka tsawa tace. "Me haka kai kuma zaka faɗo ma mutane daki bayan hakan dokace?". Cikin in ina yace dama.. dama.. Alhaji.., tsawar data daka masace tasa shi kasa ƙarasa maganar jiki na rawa dan tsawar ta mutukar gigita sa. kuma kowa yasan halinta dan gaba ɗaya ma'aikatan gidan tsaron ta suke harma daga wasu daga cikin gidan kasan cewar yadda take shinfiɗa mulki a gidan. Hannun data nuna masa ne tare da zaro masa ido alamun ya fice yasa shi dawowa daga tunanin daya tafi. Har yana yin tuntube gurin juyawa zai fita, Dady ya kira sa tare da tambayar sa meke faruwa, granny kuwa harara kawai takai ma Mommy suna maida hankalinsu kansa baki ya buɗe zaiyi magana kenan wayar dady ta fara ringing ganin Youseef ne yasa yasake tabbatar daba lafiya ba, hannu ya daga masa yana ɗaukar wayar. Batare da sun gaisa ba ya faɗa mishi suna cikin hospital Majeed ba lafiya. "Innalilahi wa'inna ilahiri raji'un" kawai dady ke maimaita wa, inda gabaki ɗaya family wasu daga ciki su shiga damu suna kallon dady dan son jin meke faru haka. Cikin tashin hankali dady ke tambayar Youseef meke damun Majeed ɗin dan yasan shine kawai dalilin dake sa Majeed ya kwanta a asibiti amma yanzu meya same sa. Daga can ɓangaren Youseef cewa yayi. "Gaskiya dady jikin ba daɗi dan har yanzu doctors na ciki basu fito b..". Dady baima Bari ya gama jin maganar Youseef ba ya fara ƙoƙarin fita dan tuni dama ya tashi a tsayema yake waya da Youseef ɗin. "Haba bukar ina kuma zaka kuma meye faru ka barmu cikin kokwanto kuma kana shirin ficewa ba tare da kace komai ba?." Maganar da granny tayice tasa dady juyowa. "dan Allah ku gafarceni Hajiya wallahi tsananin tashin hankali ne yasa na manta ya cancanta kusani albashi Mahaifiyarsa. Majeed ne yanzu Youseef ya kirani wai suna asibiti bashi da lafiya". Yana gama maganar yabar ɗakin yayinda su uncle Abdullah su rufa masa baya. Granny kuwa salati tayi ta sanar da ubangiji tare da cewa. "Nashiga uku ni Maryamu meke faruwa da Abdulmajidu har da kaiwa kwanciya a asibiti Ni Yar nan jikan nawa guda a'a wallahi ba Lafiya". Granny ke maganar cikin tashin hankali tana nufar kofa danko takan hijabi batabi ba ta fice. Adddah ce ta matso kusa da Ammei data kasa cewa komai sai binsu take da ido. "Kinga Aminiya tashi muje muga ya jikin nasa ba zama zamuyi ba". Ta faɗa tana kama hannun Ammei ba musu tatashi tasaka hijjab suka fice, to dama Yan matan gidan tuni sun fice dan Zaituna da Auta dady na fita subi bayan sa cikin tashin hankali. Suma sauran sun tafi sai mama ce da Umma amarya suka bi bayan su Adddah. ...............A ɓangaren su Majeed kuwa tunda doctor's su shiga dashi suke ƙoƙarin ceto numfashin sa amah Abu ya faskara da kyar da temakon Allah suyi nasarar ceto numfashin inda kuma suka koma kan gubar dan ba ƙaramar poison ayi amfani ba gurin cutar dashi. Dan badin an fara masa temakon gaggawa ba kuma asibitin acikin gidan yake da komai zai iya faruwa. Yayinda su dady hankalin su yake a tashe dan basu san halin da yake ciki ba, kowa na familyn ka gani kasan bashi cikin walwala dan ba'a gane cikin kowa acikin su. Yayin da granny ta daga musu hankali daga baya ma komawa tayi tana zagaye bakin kofar, ita kuwa Ammei na zaune kamilar mace kenan mai kawaici da hakuri bazaka taɓa ganin damu a fuskar ta ba saidai ƙasan zuciyar ta addu'a kawai take ma yaron nata dan tasan shi kuma Allah ya haɗa shi da jarabawoyi iri-iri acikin wannan a hali, sai dai kawai addu'a. Su Zaituna kuwa daka gansu kasan suna cikin damuwa alabashi Auta da Zaituna dan damuwar su tafi fitowa fili sai Fennah. Su Youseef kuwa da sauran yaransa suna zaune jigum-jigum kowa fuska ba walwala. ...........har dare ya tsala gidan gaba ɗaya ya dau shiru sai hasken daya haske gaba ɗaya gidan dan idan kana cikin sa bama za kasan dare yayi ba. Amma har lokacin shiri kake ji doctor's basu ce komai ba idan wannan ya fito yana share gumi anan granny dasu dady zaauje suna tambayar ya jikin nasa amma amsar ɗaya ce su cigaba da addu'a. Umma amarya ce cikin ranta ke mitar gajiya da zaman gun datayi tashi tayi cikin daure fuska tace. "Toh Ni zan danje ciki Allah ya bashi lafiya". Yayin da uncle Sulaiman ke aika mata da wata harara tare da nuna mata ta zauna, sarai ta fahimci me yake nufi amma ta basar tana kama hanyar barin hospital din. "Ke ke ina zaki haka?." Granny tayi maganar tana bin Umma amarya da wani mugun kallo, cikin jin takaicin wannan tsohuwar ta juyo fuska haɗe tace. "Hajiya zan ɗan shiga ciki ne Allah ya bashi lafiya". Ta ƙarasa maganar tana gafe da kanta dan tasan halin wannan kinibabbayir tsohuwar. Cikin zazzaro ido granny tafara managa. "Eyye wato ciki zaki shiga ki kwanta bakiji kunya ba ke? Jikana na nan rai a hannun Allah amma kina faɗin ciki zaki ki kwanta, kina ganin kowa na gidan anan dan nasan har masu aiki tunda su san bashi da lafiya suma bazasu runtsa ba dan sun san mahimmanci sa amma saike toh bari kiji tun wuri ki koma ki zauna dan muna nan daku har gobe idan dame niyar tashi bisimilah". Tana gama maganar takoma bakin kofa tana zagaye. Cikin jin takaicin granny Umma amarya ta bita da wani mugun kallo ƙasa-ƙasa tana tura baki gaba haka ta nemi guri ta zauna gefe guda tana hare-hare. Murmushi kawai Mama tayi tana girgiza kai, shiko Uncle Sulaiman harara kawai yake aika mata dan yaji daɗi da granny ta hana duk shi bataji maganar saba. A hankali doctors suke fitowa da Majeed dake kwance a gadon daukar marasa lafiya kai tsaye wani ɗaki na musamman suka nufa dashi yayin da granny tabi bayan su. Dr Fadil ne ya dakatar da ita kana su shiga dashi granny har tayi niyar yin tujara sai kuma tai ƙofa taja tunga a bakin kofa. Basu daɗe ba su fito dan sai share gumi suke su dady ne su nufeshi suna tambayar Ya jikin nasa, saida Dr Fadil ya nisa kana ya fara magana. "A gaskiya Alhaji jiki da sauki amma fa da matsala". cikin tashin hankali granny tace. "meye matsalar meya sami jikana" "Granny ki kwantar da hankalin a yanzu haka jikin nasa da sauki kuma mun shawo kan matsalar". "Humm" granny ta sauke ajiyar zuciya kana tace. "Kaga fito ka faɗa mana meye matsalar meye same sa". "Maganar gaskiya abun ya bani mamaki dan kuwa poison a samishi a wani abu yasha kuma yana da mutukar illa ajikin ɗan Adam dan zai ɗauke shi tsawon shekara yana kwance ko ɗan yatsa bazai iya ɗaga waba daganan kuma sai mutuwa dan kwata-kwata bashi da makari. Saboda haɗarin sa gaba ɗaya a hana saida shi a ko ina dan duk wanda agani dashi hukunci yake dauka mai tsanan... "Nashiga uku na ni Maryamu" granny dake yashe a ƙasa ce ke maganar jin ana niyar kashe mata jika. "Yanzu wacce Yar iskar ce ke niyar kashe min jika? oo ni Yar nan me Abdulmajidu ya muku ne kuke niyar kashe min jika? kun haɗa shi da mahaifinsa amma hakan bai muku ba sai kun rabashi da duniyar wayyo Allah na bukar kamani kamani naje naga ɗan nan karsu ƙara sa shi". Ta ƙara sa maganar tana fashewa da kuka, shikuwa dady tsabar maganar ta dake sa ya kasa koda motsi a gurin Ammei dai nacan bata taso ba amma duk abinda ake cewa tana ji dan bata da tacewa saidai tai ta mishi addu'a dan wannan familyn nasu sai addu'a kawai. Uncle Abdullah ne yace. "yanzu doctor kana nufin wannan gubar mai hatsari aka sama My son kuma a cikin gidan nan". "Nima shine abin tambayar taya za'a sami wannan gubar a cikin gidan nan". Cewar Uncle Sulaiman yana kallon Dr Fadil, jinjina kai Dr yayi kana yace. "Toh wannan ne kuma ban sani ba amma zanso naji meyaci na ƙarshe kuma koh zan iya samun shi domin nayi goji akan sa nagani". Zaituna dake shirinyin magana Granny dake kuka ta rigata, "maganar gaskiya Abdulmajidu madara yasha kuma madarar daga gurin na ta fito, dan tunda ya kirani nasan yace yana bukatar madara nasan ba abinda yasha kuma daga ita baya shan komai. Haka zalika madarar mai tsafta ce". Takai ƙarshe tana sake fashewa da kukan dayafi nada. Tunda afara maganar har a gama acikin su Addah ba wanda baiyi jimamin hakan ba. amma sai dai mutum ɗaya dana lura tunda akayi maganar binciken akan madarar fuskar ta tacanja dan gaba ɗaya ta maida hankali akan wayar ta, tana danna wa kasan cewar dokar granny taba wanda zai fita agun. Gefe kadan ta matsa tana waya ga dukkan alamu da mai aiki take waya cikin bada ummarni take maganar. "Kinyi abinda nasaki". shiru tayi tana sauraren abinda ake faɗa, daga can ɓangaren ta ce. "Ranki ya daɗe komai done dan suna fita dashi na ɗauke komai". "Okay". Kawai tace tana kashe wayar tare da sakin wani murmushi kana ta koma inda ta taso. (Niko nace kin manta abu ɗaya akwai CCTV camera a part din 🤣) yayin da su Uncle Sulaiman da su Youseef su nufi part din Majeed domin ɗakko madarar da ace yasha domin ayi bin cike akan ta. Koda suje an duba sama da ƙasa ba'a ga madara ba kuma dai doctor Fadil yace gubar bata daɗe wa ajikin mutum take fara aiki dan bata ɗaukar 10 minutes bare ace tun a waje ya sha, har sun fito zasu wuce Youseef da tun ɗazu yake ta waige-waige idonsa ya sauka akan mug din daya faɗi ƙasan table ɗin dake tsakan kanin kujerar daya zauna. Tsaidasu yayi kana ya tsuguna ya dauko duk ga madarar nan ta zuɓe da alamu da'a zo ɗaukar wacan ba'a lura da itaba, "yauwa kawo wannan ɗin zaiyi bari a gwada". Cewar doctor Fadil ajiyar zuciya su sauke a tare kana su fice a part din su nufi hospital. *Kaduna ✨* ..............Yauma kamar kullum tun kafin asuba na tashi duk wani aiki danake na gama shi kafin a kira sallah bayan nayi sallah tare da tilawar Alqur'ani. Tsaf na shirya cikin bakar abaya mai sulɓi an mata ado da fararen duwatsu ɗan kwalin abayar nasa nayi rolling dashi na fito tsaf kamar balarabiya. Yadda abaya ta ta kasance baka haka takalmin dake kafata ya kasance black mai dan tudu. haɗaɗɗiyar humura ta mai sanyin ƙamshin nakasa sai turaruka na masu sanyin ƙamshi irin na mata, kasan cewar niɗin ma'abociyar ƙamshi ce a ko ina akuma koda yaushe. Sai facemask black da eyeglasses white dana sa. Dama tuni nayi breakfast dan haka bakar jakata na dauka sai phone na fice a ɗakin nabar anty Waleeda na sharar baccin ta dan banjin ko sallar asuba tayi. Napep na tare mu wuce dan Yah Ansar ya koma shikuma Yah Safwan dama ba kwana yake a gidan ba. Koda muje kuɗin sa na ciro na bashi akuma dai-dai lokacin motar MD ta tsaya na ganshi amma sai nayi kamar ban gansa ba na nufi hanyar shiga ciki cikin takuna da mutane ke fassarawa da yanga wasu suce girman kai. Da haka har ya ƙaraso inda nake ya koma muna jerawa. "Good morning" shine kawai abin dana furta batare dana kallesa ba. "Uhmmm beb da shine zaki wuceni bazaki tsaya mu gaisa ba kohhh?". Jin yadda yayi maganar ne yasani daga manyan idanu na da wasu kan kira da kamar na mage aikuwa su faɗa cikin nashi a hankali na janye nawa, kana nayi ƙasa da kaina ina sakin ƙaramin murmushi mai ɗan sauti ta cikin facemask ɗina kana nace. "Humm bafa haka bane kawai daiii". Yanda ya tsireni da kallo ne yasa nayi shiru batare dana ƙarasa maganar ba. "Kawai dai me?" "Na tafine amma ai zamu gaisa". "Uhmm beb kenan batin ma kona kiraki baki zuwa sai akan aiki". "Sorry hakan ai shine dai-dai koh?". Na faɗa ina langabe kai tare da kallon shi, saida yayi murmushi kana yace. "Uhm hakane beb muje toh". Tafiya mu fara kaida ka ganmu kasan mun dace da juna, PA da tun farkon zuwa na tana kallon duk abinda ke faru tsakanina da MD haka take jin zuciyar ta kamar zata fito girjin ta dan a haukarta son shi take shikuma baima san tana yiba. Ta kusa da ita mu wuce muna cigaba da hirar mu irin ta masoya, dan saida ya rakani har office din mu kana ya wuce nashi cikin takunsa na nutsuwa, dan MD gayene Wanda ya san darajar gayu da iya daukar wanka gashi miskili shiyasa su PA su mace akansa. Tabbas idan nece muku bana son MD nayi karya dan inajin son shi acikin zuciya ta. Sanda na shiga office ma acan na tarar da Isha inda members ɗin office din mu ketamin wasa wai gaba ɗaya na canja MD nidai murmushi kawai nayi ina kaiwa zaune a kujera marks ɗin fuskata na cire na aje gefe tare na sake gyara eyeglasses din idona na fara aiki a lap top dan akwai wani program da zamu gabatar yau. Isha kuwa fita tayi don kaima MD wasu takardu dan haka na fara aikina cikin nutsuwa. _______ Mom____ "Mom yanzu fissabilah haka zamu cigaba da zuba ido akan yarinyar nan kince zaki gurin malam amma kinje yace baza ai bikin ba amma har yanzu shiru tunda gashi har anyi sa rana yanzu bikin fa kwata-kwata bai wuce 3 week's ba haba mom. in bazaki iyaba kubarni ni na dau mataki akan yar iska dan wallahi Suraj na wane ni kaɗai dan Ni akayi shi. Mom data zuɓe anyi Waleeda da ido kamar wacce ta faɗa duniyar tunani ta sauke ajiyar zuciya tare da cewa. "Waleeda baki san irin ciwo da rad'ad'in dana ke jiba akan Auren yarinyar nan aini ba Suraj ba Auren ne kwata-kwata bana so tayi na fiso ta ƙare a gidan nan kawai dan tamin bauta, ai indai inada rai jinin Amina bazai taɓa samun Salama ba shima Ansar ɗin bakiga mu yake ma bauta ba komai na gidan nan ai yanzu akan sa yake ban da haka wallahi da tuni nasa an batar min dasu kamar yadda na ma uwar su Amina tana rayene ma kota mutu oho". "Yauwa mom dan Allah duk yadda zakiyi kiyi akan auren nan, kuma kisan ma wata matsalar mom?" "A'a saikin faɗa". "MD mom zai kuwa amince dani dan rannan dana tare sa mom karkiga wulakanci da yayimin wallahi shiyasa zuciya ta ke rawa". Kamar zata fashe da kuka tayi maganar tana kallon mom. "Kinji banza dama akace miki haka zamu barsa? Ke nida duk yadda zanyi ki mallake sa ai saina yi abin dama yasa kijini shiru da maganar akwai abinda nake shiryawa ne sai kuma Umma da tace na jirata banda haka ai da tuni an rufe babin". "Wayo Allah mom gaskiya naji daɗi sosai momy nah shiyasa nake ƙara sonki". "Kawo kunnen ki kiji shirin dana ke akan su" cewar mom ba musu anty Waleeda ta masa mom ta fara gwargwada mata maganar dani kaina banjin me suke cewa bale na fada muku. Da haka 'ya da uwar suyita zance irin makircin da zasu kulla ma Safiyyah. ________🔷🔷🔹🔹🔷🔷______ Sultan ne yazo mu fita domin gabatar da program. Inda tuni ba kuwar mu tazo dan haka mu fara gabatar wa. Ya ku matasa! Shin me ya sa ba sa faɗa muku sirrinkan nasararsu, sai ci dai su kawo muku Maudu’in Jayayya? Ya ku Matasa! Shin me ya sa ba sa ware awa ɗaya ko a sati ne, su koya muku wani abu da zai kawo muku sauƙin rayuwar da mu ke ciki? Ko kasuwanci kake ko dako, Ustaz ne kai ko Comrade, ɗalibin ilimi ne kai ko ɗan siyasa, ka ware lokacin nazari, bincike, karatu, da koyon sabon ilimi mai amfani na zamani da zai dace da ci gaban rayuwarka. Ka daina yadda wasu suna kawo maka Skip to content. Haqiqa abin alfahari ne da kuma birgewa yadda wasu zaqaquran matasanmu a soshiyal midiya suka dage ga ba da himma wurin canza tunanin jama’ar Arewa, musamman matasa ‘yan uwansu daga akasin wayewa zuwa ga wayewar a harsunan Turanci da Hausa. Alhamdulillahi kuma ana ganin alamun nasara a kan hakan. Wannan juyin juya hali ne na tunani, wanda kuma shi ne a’ala. Allah ya saka mu su da alheri. Sai dai kuma an ce mutum tara yake, bai cika goma ba. A tare da wannan himma na wad’annan matasa namu, akwai buqatar sanya mu su linzami don jan hankalinsu game da sha’anin addini da kimiyya, cewa yayin da dukkan masu wayewa suke yabawa ci gaban da kimiyya ya kawo wa duniya, to kuma kada hakan ya sa a raina gudunmuwar da shi kuma addini ya kawo wanda ya ma fi na kimiyyar. Ba wai don kawai Allah ya ce walal-aakhiratu khairun laka minal uulaa (lahira ta fi alheri a gare ka a kan duniya) ba, addini a qashin kansa, ba tare da la’akari da Musulunci ne ko Kiristanci ba, yana ba da gudunmuwa ga tarbiyyar d’an Adamu ta hanyar tsara masa rayuwa da d’ora masa dokokin mu’amala. Wannan tsari na rayuwa yana koyar da mutum ladubba, abin da ita kuma kimiyya ba ta ma sansu ba. A warware, abin da nake qoqarin cewa shi ne, kimiyya na koya wa d’an Adamu yadda zai yi rayuwar jin dad’i ta hanyar qere-qere da zaqule-zaqulen bincike mai amfani da ma mara shi, addini kuma na koya masa yadda zai yi mu’amala da mutane ‘yan uwansa cikin tsari da rayuwa mai ban sha’awa. Idan aka taqaita zance a hakan kawai, a awo irin na masu hankali, na qarshen ya fi alheri a kan na farkon. Domin dai shi ne ginshiqin rayuwa. Za a iya gudanar da rayuwa ko da babu ilimin kimiyya, amma ba za a iya gudanar da ita ba idan babu mu’amala mai kyau a tsakanin jama’a. Da wannan nake ce wa matasan nan namu masu himma, yes, muna buqatar qara qaimi daga wannan jibgewar da muka yi, don mu ma mu zama aqalla qannan Turai a ci gaban qere-qere, amma kuma, bisa la’akari da irin gudunmuwar da addini yake badawa wajen ha’b’baka nagartar halayyar bani Adama, wanda shi kuma kimiyya ba ya yi, to bai kamata mu kuma mu fi karkata ga ra’ayoyin Turawan ba, wad’anda tsanarsu ga addini da kuma ganin birgewarsu ga ci gaban kimiyya, sun kitsa mu su yawaita aikin aibata addinin da kushe shi tare da kambama ilimin kimiyyar sama da komai duk kuwa da taqaitawarsa a komai d’in. Ma’ana dai kada azar’ba’bi ya kai mu ga biye mu su wurin kushe addini a kai-a kai tare da kambama kimiyya a samansa. Kowanne na da muhallinsa. Na’am, gazawa wurin amsa tambayoyin qurilla na mufakkirai da kuma zaluncin Coci a zamanin daular Romawa, na daga cikin dalilan da suka sa Turai ta tsani addini ta kuma juya masa baya. To amma gare mu mu Musulmi fa? Shin haka abin yake? Sam ba haka ne a wurinmu ba! Daga cikin ilmukan Musuluncin namu ne aka samu na kimiyyar, kuma almajiran Musuluncin ne suka bunqasa shi har ma duniyar yau take amfana daga gare shi. Ga wasu ‘yan misalai: 1- Duk da qoqarin sauya tarihin ilimin lissafi na Algebra da Turai ke yi wurin d’aukaka sunan Diophantus (Masanin Lissafi na Girka) a kan na Khawarizmi, zuwa yau d’in nan fomular da aka sani kuma ake amfani da ita a wannan ‘bangare na lissafi, ta Khawarizmi ce. Shi kuma d’aya ne daga cikin almajiran Musulunci. Cikakken sunasa shi ne, Muhammad Ibni Musa Al-Khwarizmi. Ya yi rayuwa a zamanin Ma’amun, d’aya daga cikin halifofin Abbassiyya, wajejen 820 Miladiyya. A wannan lokaci, Turai na cikin duhu. 2- Ibni Sina, wanda Turawa suka malkwad’a sunansa zuwa Avicenna, wala’alla don kada Musulunci ya yi alfahari da irin gudunmuwarsa ga ilmukan kimiyya da falsafa, uba ne ga ilimin likitancin zamani. An ce ya rubuta litattafai sama da 40 a kan fannin likitanci kawai wad’anda har zuwa yau d’in nan ake komawa gare su. Littafinsa The Canon of Medicine, kundi ne na ilmukan cututtuka da magungunansu (encyclopedia). Shafin Wikipedia ya ce shi ne littafin da aka riqa amfanin da shi a jami’o’in Turai a zamanin tsakiya na wayewar Turai d’in (Medieval Era), wajejen qarni na 15 ke nan. Kazalika shafin ya ce an sake wallafa littafin a shekarar 1973 a birnin New York. Ibni Sina shi ne, Abu Ali Al-Ḥusayn Ibn Abd Allah Ibn Sina. Ya yi rayuwa a zamanin daular Abbasiyawa. A wannan lokaci Turai na cikin duhu. 3- Shafin yanar gizo na Aljazeera ya wallafa wani bincike da ya yi a kan abin da ya kira “Science in A Golden Age” wato Ilimin kimiyya a zamanin shuhurar ilimi na Musulunci. Shafin ya nuna irin ilimin Physics d’in da Ibni Haytham ya fitar a littafinsa, Kitabul Manazir (The Books of Optics), wanda ya rubuta sama da shekaru 1,000 da suka gabata. Shafin na Aljazeera ya ce, littafin mujalladi bakwai ne, kuma ya ragargaji ra’ayoyin Plato da Euclid a kan wata matsala ta ilimin Physics da ta shafi haske da gannai, kuma ra’ayoyinsa ne gaskiyar da duniya take amfana da shi a yau. Ibni Haytham shi ne Abu Ali Al-Ḥasan Ibn Al-Ḥasan Ibn Al-Haytham. Ya yi rayuwa a zamanin daular Abbasiyawa. A wannan lokaci Turai na cikin duhu. Ke nan ashe dai, mu a Musulunci, addini bai yi abin da masu kimiyya za su tsane shi ba, qarewa ma, Malaman Musuluncin ne suka fitar kuma suka bunqasa ilimin na kimiyya a zamunansu. Ga hujja: Kimanin shekara dubu d’aya da d’ari hud’u wata ayar Qur’ani daga cikin suratul Hadid ta ce: “Kuma muka saukar maka da qarfe, a cikinsa akwai cutarwa mai tsanani, kuma da amfani ga mutane…” Wannan ilimin kimiyya ne. Domin da qarfe ake qera bindiga da takubba da nukiliya, kuma da shi ake qera mota, da jiragen qasa da na sama da na ruwa. Ke nan tabbas akwai cutarwa a cikinsa kuma akwai amfani. Qur’ani ya fara fayyace hakan. Hatta ilimin yadda za a sarrafa shi qarfen da wasunsa na daga sinadarai a kimiyyance yana tattare da dai shi addinin ne ta hanyar ingantattun hadisan da aka ji daga Manzon Allah (sawa), ko shiryayyun halifofinsa da suka sha daga Manzon (sawa). Wata ruwaya ta zo a Nahjul Balagha cewa: “Wata rana Imam Ali (as) yana ga’bar kogin Furat sai ya ce wa Sahabbansa: ‘Da na so zan iya fitar mu ku da haske da wuta daga wannan ruwan.’” Masana sun fassara hakan da cewa wutar lantarki yake nufi, wato “Hydroelectricity.” Hakan ne ko ba haka ba, wannan dai ya nuna yana da masaniya a ilimin qere-qere mai wuyar fahimta tun a wancan zamani wanda mutumin yau ke kira kimiyya. Me kuma ya sa bai yin ba? Wala’alla domin gudun fitinuwar mutanen lokacin ne saboda tsukewar fahimtarsu a lokacin. Kazalika an ruwaito shi (as) Biharul Anwar yana cewa: “Shin kuna jin cewa Allah bai yi wata halittar bayan ku ba ne? Wad’annan taurarin da kuke gani a sama suna da birane kamar yadda kuke da shi a wannan duniyar.” Kafin a haifi Galilio da kusan sama da shekara dubu, Imam Ja’afar Sadiq (as) yana da shekara 11 ya tabbatar da cewa duniya ce ke kewayawa a nata tsarin da tsaikon. Ya kuma yi sauran d’imbin zantuka da sai bayan sama da shekaru dubu ne ilmukan kimiyya ke aminta da su. Duk wannan yana nuna mana cewa a cikin wannan addinin namu na Musulunci, muna da komai, kawai dai mu ne ba mu sani ba, don haka muke yabawa na wad’anda suka sata daga gare mu kuma suka yi sa’ayin bunqasawa. A kan haka nake qarqare zancena da jan hankalin matasan nan namu masu himma da cewa, idan addini a wurin Turai abin qyama ne saboda zaluncin da ya yi wa kakaninsu da gazawarsa a amsa tambayoyin masu zurfafa tunaninsu, to mu a wurinmu abin alfahari ne saboda ya zo mana da komai, har ma da wanda ba mu tambaya ba. Don haka kimiyya daga addini take ba kishiyar ta ba ce. Rashin sanin hakan gazawarmu ce ba gazawar addinin ba. Allah ya qara wa wad’annan matasa himma da qwazo da basira wurin tattaunawa da fitar da abin da zai amfani al’ummarmu, ba abin da zai raunana mata imani ba......................✍️ *Taku har kullum da ko yaushe* 🤝*Amanar taurarin writer's association📚* _*Yawan comments and like yawan typing*_ 😜 *Typing📲* _WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _WhatsApp group_👇 https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 ✨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION✨* *T.M.W.A.✍️* *Amanar taurarin marubuta writer's....✍️* Page 3️⃣4️⃣➡️3️⃣5️⃣ ................Bayan mun gama gabatar da program inda muyi sallama da bakuwar mu na koma office mu ciga ba da aiki. Kasancewar yau da wuri mu tashi aiki sallama muyi da Isha MD ya ɗauke ni mu wuce, a tunani gida zamu sai naga ya dau wata hanyar daban kamar bazan ce komai ba dan tunda mu fara tafiya ba wanda yayi magana tun bayan gaisuwar da na mishi. Ɗagowa nayi da niyar kallon sa a dai-dai lokacin shima ya ɗago yana kallon na a hankali na ɗan juyar da kaina gefe ina murmushi inda shima murmushin yayi tare da cewa. "Wai duk kunyar nan ta meye da ake kasa hada ido dani uhm beb ? Nan fa da 3 week's kin zama tawa sai yadda naso nayi dake fah" Murmushi nayi tare da cewa. "Ai saika bari time ɗin yayi koh" kureni yayi da kallo na wani ɗan lokaci kana yace "uhm aiya kusa". Murmushi kawai nayi tare da cewa. "Tom Allah ya kaimu amma yanzu ina zamu naga ka dau wata hanyar da ban". Da "ameen" ya amsa kana yace. "Saida ke zanyi". Ya faɗa tare da jiyowa yana kallo na murmushi kawai nayi batare da nace komai ba, kana yace. "Wasa nike miki kinji zan kaiki ki gaida momy nah ne dan ta matsamin nakai mata ke ta gani kinga yau kuma mun tashi da wuri shiyasa nace bari muje. Amma ya kigani?". Saida na danji wani abu a zuciya jin yace zani gaida mahaifiyar sa amma ban nuna maiba sai kai dana daga mishi ina lumshe ido. Murmushi yayi mu cigaba da tafiya cikin kankanin lokaci mu isa gidan. "Màsha Allah" shine abinda na furta ganin irin kyau da tsaruwar gidan inda kai tsaye parking lot ya nufa tare da yin parking kana ya maido da hankalin sa kaina tare da cewa. "Babe muje koh". Kallon sa nayi ganin shima ni yake kallo yasa nai ƙasa da nawa murmushi kawai yayi yana fice wa daga motar, har inda nake ya zagayo ya buɗe min tare da matsawa gefe, ba musu na fito inda kai tsaye cikin gidan mu shiga. Zaune suke a cikin babban parlour inda mu shiga bakin mu dauke da sallama shine a gaba ni kuma ina binsa a baya kaina a ƙasa har mu ƙarasa cikin parlour. Dattijuwar matar dake zaune a kujera mai ɗaukar mutum uku kamar su ɗaya dashi sak kamar an zana ga dukkan alamu itace momy, sai wata da baza mu wuce sa'anni ba zaune kusa da momy wato mennat ƙanwar sa kenan dan duk suna kama da juna sai dai ita mennat ba sosai suke kama ba. Gaba ki ɗayan su fuskar su kwance da murmushi inda mennat tunkan mu idda shigo wa tazo da ɗan gudun ta ta rungume ni tana mun barka da zuwa tare da kama hannu na ta nufi kujera dani. Tana niyar zaunar dani a kujerar a hankali na zame na zaune a ƙasan shimfiɗaɗɗen cafet ɗin dake malale a cikin parlour mai taushe. fuska ta ɗan bata tare da nuna min kujerar alamun in zauna, ka faɗa na make tare da marairaice fuska alamun nanma yayi, ba musu ta barni itama ta nemi kusa dani ta zauna. Momy da tun shigowar mu ba tace komai ba sai murmushi da take yi tana kallon mu nida mennat har mu zauna sai kana tace. "A'a ɗiyata yada zama a ƙasa? Tashi ki koma kujera ai nan gida ne". Murmushi kawai nayi ina ƙasa da kaina tare da cewa. "Momy nan ma ai yayi". Murmushi kawai tayi tare da girgiza kai dan tasan ba tashi zanyi ba. A hankali na matsa kusa da ita tare da gaishe ta cikin girma mawa, itama cikin fara'a ta amsa min tare da riƙe hannu na cikin nata tana murzawa a hankali. "Oooh sai ance ki kawo mata ruwa kenan koh mennat kin zauna kawai kina zuba surutu". Cewar momy tana kai duban ta ga mennat data zauna sai jana take da hira nidai ina amsa mata da eh ko a'a dan gaba ɗaya kunya nikeji dan tuni momy ta maidani kusa da ita tana jana da hira. "Sorry my mom wallahi gaba ɗaya murnar ganin tane yasa na manta ban kawo mata ko ruwa bane afwan antynah". Tana gama faɗar haka ta tashi, kai kwai momy ta girgiza tare da cewa. "Allah dai ya shirya min ke". Da "ameen" mu amsa harta kawomin ruwa da drinks har da abinci toh ruwan dai kawai nasha cox gaba ɗaya MD ya zuɓeni da kallo ganin sai fira muke da momy kamar dama mun saba. Nikam kasan cewar magana tamin akan aikina shiyasa na saki jiki da ita muna fira dan saida ta sani dole naci abincin kadan kana ta barni mu taho, inda ta haɗa min shatara ta arziki naki ashe shi ya amso. Har kofar gidan mu ya kaini kasan cewar magrib ta kusa, sallama muyi kana ya zagayo tare da buɗen mi kofa sai da naja wani lokaci kana na fito, hannu na ɗaga mai tare da nufar get har na kai hannu kan kofar naji ya kira sunana. "Safiyyah" cak na tsaya da buɗe kofar tare da waiga wa ina kallon sa da shima ni yake kallo. "I love You". "I love You too". Ina faɗa na shige gida da sauri, murmushi yayi tare da lumshe idanu kana ya shige mota ya bata wuta yabar anguwar. ____________ *Abuja🤍* A ɓangaren Majeed kuwa jikinsa alhamdulilah dan yaji sauki sosai yanzu haka ma yana part din Ammei, dan dady ya hana ayi bincike akan gubar da asama Majeed yayin da hakan yayi ma wasu daga cikin su daɗi wasu kuwa sun so ayi binciken amma dady ya hana, dan da kyar granny ta yadda dan tace sai anyi bincike an gano wake son kashe mata jika. Haka dai granny tayi ta gama amma dady ya kashe maganar ba yadda su iya haka su hakura. ⚫Kwance yake akan cinyar Ammei sai shagoɓɓa yake zuba mata itakuma tana lallaɓa shi Auta dake gefe sai dariya take. Gaba ki ɗayan su zaune suke cikin parlour Ammei inda suke kallon program ɗin da Safiyyah take gabatarwa akan Tarbiyya. Tunda ta fara magana yayi shiru yana saurare yayin da Ammei da Auta gaba ɗaya hankalin su yana kan TV, shiru yayi nawani lokaci kamar mai nazarin maganar da Safiyyah take yi itada da abokiyar aikin ta. Yanda take bayani akan TARBIYYA cikin nutsuwa kasan cewar yau ba facemask a fuskar ta iya kacin eyeglasses ne kawai yasa ake iya ganin fuskar ta tar. Bayan sallama da tayi tare da gabatar da bakuwar tata ta fara magana cikin zazzakar Muryar ta mai saka nutsuwa ga mai sauraro, dan Allah yayi baiwa agurin Allah ya bata murya mai cike da wani kalar sirri a ciki. *TARBIYYA A ƘASAR HAUSA* Kalmar tarbiyya, ararriyar kalma ce daga Larabci (التربية aka Hausantar da ita. Kalma ce magamaiya, wacce ke iya ɗaukar ma’ana ta renon jikin yaro; hanyoyin kyautata ruhi da kuma koyar da kyakkyawar cuɗanya da jama’a. Abin da ake nufi a nan shi ne cewa, tarbiyya ta shafi gangar jiki, ruhi da kuma yadda mutum yake cuɗanya da sauran jama’a, a al’ummance da kuma ɗaiɗaiku. Ƙololin buƙatar tarbiyya ita ce gina cikakken mutum mai amfanar da kansa da kuna waninsa. Bisa la’akari da wannan faffaɗar ma’ana da wannan kalma take da ita, rubutun zai taƙaitu ne wajen yin magana a kan abin da ya shafi ruhi da kuma cuɗanya. Zai yi magana bakin gwargwado a kan ma’anar tarbiyya, manufarta, amfaninta, masu bayar da ita, jerin wasu kyawawan halaye da kuma yadda Bahaushe yake bayar da tasa tarbiyyar, da sauransu bakin gwargwadon iyawa. *Ma’anar Tarbiyya* Saboda zamowar kalmar tarbiyya mai tushe a Larabci, zan kawo ma’anarta a Larabce da cewa, “Ita ce ayyukan ɗaukakowar halittu, wato ƙarawa mutum mutumtaka domin ya samu kaiwa cikakkiyar daraja matabacciya a jiki da aiki da ruhi da kuma cuɗanya”, Abu Hamza (2013). Daga wannan ma’ana za mu iya fahimtar cewa, tarbiyya reno ce. Saboda dukkan abubuwan nan da aka ambata suna ƙunshe cikin reno. Shi kuwa reno ana yin sa ne mataki-mataki. Sai dai ya fi zafi a tsakanin ranar farko ta haihuwa zuwa shekara uku. A wannan tsakanin komai yi wa mutum ake yi. Ɗawainiyoyin suna fara raguwa ne bayan an yaye mutum wato daga watanni 15 na haihuwa zuwa shekaru 2. Daga wannan mataki yawancin yara sukan fara yi wa kawukansu wasu abubuwan kamar ci da sha da sauran ƙananan abubuwan rayuwa. Daga wannan mataki na yaye kuma, sai a shiga kiwonsa, da ma’ana ta lura da zirga-zirgarsa ƙut-da-ƙut har zuwa kamar shekaru 5 ko 6, idan zai kai kansa mahallaka ko dai a ce da shi bari, ko kuma a je a ɗauke shi ko a janye shi da sauransu. Idan ya haura shida kuma, to ya fara kai wa matakin da zai fara cuɗanya da wajen gida, sai kuma ya shiga makaranta. A makarantar ma renonsa ake yi, saboda a koyar da shi ne alaƙoƙin da suka shafi rayuwarsa ta duniya da kuma ta lahira, iya tsawon karatunsa da ma rayuwar baki ɗaya. Saboda haka idan muka koma kan waccar ma’ana ta tarbiyya muka ciro kalmomin cewa, ayyuka ne da ke ɗaukaka halitta, za mu gan su cikin wannan ɗan taƙaitaccen bayani game da reno da na yi. Ana kuma iya cewa, tarbiyya ita ce horas da yaro kyawawan halaye domin ya zama mutum nagari. Ko kuma a ce, hanya ce ta nuna wa yaro yadda zai tashi da kyawawan halaye ababen yabo a cikin jama’a. *Manufar Tarbiyya* Babbar manufar tarbiyya ita ce samar da mutum mai kyawawan halaye ababen yabo domin ya zama mai amfanar da kansa da kuma waninsa. *Amfanin Tarbiyya* Amfanin tarbiyya ba zai ƙidayu ba, amfaninta na ƙarshe; wato maƙurar amfanin nata shi ne mutum ya samu kansa a gidan Aljana a lahira, a nan duniya kuma ya zama son kowa, ƙin wanda bai samu ba. Waɗannan gajiyoyi da za a ci; duniya da lahira, su ne maƙura, sai kuma wasu ɗaiɗaikun abubuwa da zan lissafo kamar haka: Numfashi ta sauke tare da gyara eyeglasses din idanun ta, kasan cewar tabar facemask dinta a office a hankali ta cigaba da magana cikin nutsuwa gami da kamala. Tsarkake Halaye: Tarbiyya tana tsarkake halayen mutum ya zama mai kyawawan halaye. Sauƙin Rayuwa: Kyakkyawar tarbiyya tana saka mutum ya rayu, rayuwa mai sauƙi. Saboda zamowarsa mai wadatar zuci. Farin Ciki: Mutum mai cikakkiyar tarbiyya akan same shi cikin annashuwa a mafiya yawan lokutansa. Saboda koda wani abu can gefe ya ɓata masa rai, to yasan idan ya zo yin hulɗa da wani wanda abin bai shafe shi ba, sai ya danne wancan ɗacin a ransa shi kaɗai. Girma da Ɗaukaka: Kyakkyawar tarbiyya tana ɗaukaka darajar mutum a idon mutane a nan duniya, haka nan ma a wajen Ubangiji Mai Girma da Buwaya. Kwarjini: Kyakkyawar tarbiyya tana saka mutum ya zama mai kwarjini. Matakan Bayar da Tarbiyya Akwai matakai ko hanyoyi da ake bi wajen bayar da tarbiyya da suka haɗa da nuni, lura, umarni da kuma hani. Nuni: Abin da ake nufi da nuni a nan shi ne aikata aiki a aikace, wanda daga nan shi wanda ake tarbiyantarwa zai gani ya koya. Tirƙashi, masu iya magana sun ce; “Idan mutum ya ce zai baka riga, to duba ta jikinsa”. Wannan magana ta zo daidai da faɗin Larabawa cewa; “Maras abu baya bayar da shi”. Saboda haka dole ne mai bayar da tarbiyya ya zama mai tarbiyya. Wannan hanya ta bayar da tarbiyya ita ce mafi tasiri da kuma muhimmanci wajen bayar da tarbiyya. Saboda haka dole ne masu bayar da tarbiyya; iyaye, malaman makaranta da sauran jama’a suma su zama masu tarbiyya. Misali. ...... dole iyaye su zama masu tsafta a aikace, kafin su dasa halin tsafta a zukatan ‘ya’yansu. Idan yaro ya tashi ya ga iyayensa suna share gida tsaf-tsaf, basa barin kwanon abinci da dauɗa, basa jefar da sutura ko’ina a ciki da wajen ɗaki, to a haka shi ma zai girma mai kula da tsafta. Kuma zai tashi shi tsafta ya sani bai san ƙazanta ba. Saboda haka da zarar ya fara zuwa makaranta malaman makaranta ba za su wahala da shi ba. Umarni da Hani (Kwaɓa): Umarni shi ne a riƙa gaya wa yaro yi kaza. Misali, idan yaro ya tsoma hannun hagu cikin kwanon abinci, ko ya riƙe abinci da hannun hagu zai kai bakinsa, sai a gaya masa cewa, wannan ba shi ne hannun cin abinci ba, ga na cin abinci nan. Da haka zai gane hannun dama dana hagu. Shi kuwa hani shi ne kore abu. A wannan gaɓar kuma yana nufin kare ko dakatar da yaro daga aikata aikin da ba mai kyau ba. A cikin wannan misalin dana kawo a sama, akwai gaurayen hani da kuma umarni. Yaro ya tsoma hannun hagu domin cin abinci, sai aka hana shi; wato aka dakatar da shi daga cigaba da amfani da hannun hagu. Sannan aka gaya masa; wato aka umarce shi da amfani da hannun dama. Lura/Kula: Lura ko kula, suna ɗaukar ma’anar saka ido a kan kai-komo na yaro; wato zirga-zirgar yara. Wannan hanya ta lura, cikamakonta shi ne kwaɓa. A nan, iyaye za su saka ido sosai game da zirga-zirgar ‘ya’yansu, duk lokacin da suka ga wata baƙuwar halayya maras kyau, sai su yi maza-maza su ɗauki matakin da ya dace tun kafin ta zama jiki. Da zarar yaro ya fara fita wajen gida domin zuwa makaranta; wato daga shekaru uku zuwa sama, to fa dole iyaye su riƙa lura da shi sosai, saboda yanzu kuma ya je ya gwamutsa da sauran yara daga gidaje barkatai. Saboda haka idan iyaye basu saka lura ba, to tarbiyyar ‘ya’yansu sai ta koma barkatai. MUHIMMANCIN TARBIYYA Tarbiyya tanada matuqar muhimmanci. A duk lokacin da dan adam bai samu tarbiyya ta musulunci ba to lallai zai iya komawa mai dabi'a kamar ta 'dabba'. ANNABI S. A. W yana fada a hadisi cewa: ﻣﺎ ﻧﺤﻞ ﻭﺍﻟﺪ ﻭﻟﺪﻩ ﻣﻦ ﻧﺤﻞ ﺃﻓﻀﻞ ﻣﻦ ﺃﺩﺏ ﺣﺴﻦ "Uba bai bawa Dan shi/Yar shi kyauta mafi falala ba fiye da kyakykyawan ladabi/tarbiyya". ........... Zuciya da gangar jikin sa ba abinda take so sai kwadayin son ganin fuskar ta a hankali cikin ya sauke idanun sa dake farare tar akan TV a kuma dai-dai lokacin Safiyyah ta d'ago domin sallama da masu sauraro. Aikuwa akan kyakkyawar fuskar ta ma abociyar kyau da kwarjini idanun sa su sauka. Yadda zuciyar sa tayi wani tsalle a girjin sa kamar zata fito cikim mamaki yake sake kallon ta yayin da ita kuma ta cigaba da sallama da masu sauraro. "Yah rabb" shine abinda ya furta wani tari yana sarƙafeshi jin yadda zuciyar sa take masa. "Lafiya Majeed meya faru". Cewar Ammei duk ta ruɗe da sauri Auta ta dauko ruwa tare da balle bakin gorar tana Shirin tsiyaya masa ya amshi gorar inda ya kafa bakin sa saida ya shanye kana ya koma kujera ya lafe dan ya bar jikin Ammei ma. Sannu suke masa yana ɗaga kai inda ya maida idanun sa kan TV, a zahirin gaskiya baza kace TV yake kallo ba dan sam idanun sa ma a lumshe suke amma a baɗini tar idanun sa suke akan kyakkyawar fuskar Safiyyah yara sa me ke shirin faruwa dashi ne akan wannan yarinya. Yanda take motsa dan ƙaramin bakin ta dake ɗauke da lipstick mai kalar pink yake kallo gaba ɗaya ya faɗa duniyar tunani dan duk firar dasu Ammei suke baima sani ba haka yayi luf kamar me bacci. Yanda su Ammei keta yabon Safiyyah da sa mata albarka kasan cewar duk family suna mutukar son program ɗin ta dan baya wuce su. Ba abinda Ammei take fata da addu'a sai Allah yaba Majeed mai irin halin wannan yarinya dan yanzu *RAYUWAR* sai a hankali. Hankalin t mayar kan Majeed daya labe kamar me bacci amma ita tasan ba baccin yake ba. "Majeed yaushe zaka fito da matar aure ne". Jin maganar yayi a bazata don haka cak ya dawo daga duniyar tunani daya tafi yana d'ago rikitattun idanun sa dasu dan surka sai su bada wata kala daban yana kallon Ammei dasu. Hararar wasa Ammei ta bishi da ita tare da cewa. "Bar kallo na da wannan idanun naka". Fuska yaɗan kawar tare da shagobe ta yana kallon ta batare daya yi magana ba. "Kaga Majeed ya kamata ka farka a baccin da kake tuni ka girma ka isa aure sa'oinka kowane gasu nan da yaran su ba ɗaya ba ba biyu ba amma kai ka tsaya mene?". Yanda ya wani shagobe fuska kamar ba shiba kana yace. "Nifa Ammei Allah cikin matan banga wacce tamin b..a". Ya ƙarasa maganar a rabe jin zuciyar sa ta tuno mai da Safiyyah. "Toh tun wuri kasan abunyi dan mun gaji da ganin ka haka in kuma dadyn ku ya samoma da kasan to ko a cikin ƙannin kane ai yayi koh". "Uhmm Ammei jan raini ne ai, nidai ku barni insha Allah na kusa kinji Ammei nah". Ya ƙarasa maganar yana kwantar da kanshi a kafadar Ammei. Murmushi kawai tayi tare da girgiza kai dan tasan indai ta halin Majeed za'abi tofah bazai ba. "Nadai na faɗa ma tukafin dadyn ku ya waigo gareka kasan abun yi". Auta da tunda afara maganar ba tace komai ba sai yanzu tace. "Allah yah Aj nima na kosa nayi anty amma ka ƙi yin aure yaya". Kamar zatai kuka ta idda maganar dan Auta cikakkiyar yar shagobba ce. Harara ya zuba mata tare da cewa. "Yaushe na zama abokin wasan kine habibat harda ana min magana kina samin baki?". Dan shi baya ce mata Auta dan yace har yanzu shine Auta shiyasa duk shagoɓɓar Auta indai yanan bata yi sai dai tabar mai. Kamar zatai kuka tace "Yaya nah Allah ba haka bane am very sorry". Batare daya ce komai ba ya girgiza kai kawai tare da zame wa ya kwanta a cinyar Ammei yana kafe TV da ido. duk da tuni Safiyyah ta gama program ɗin ta dan wani shirin ma suke. gani yake kamar zai ganta amma shiru a hankali ya lumshe ido yana faɗa wa duniyar tunani Safiyyah. Time ɗin daza ta faɗi a shopping mall ya taima keta yanda fuskar ta tai bayyana tsoro ƙarara da yanda ta runtse idanun ta sai ƙaramin bakin ta datake motsawa kamar mai addu'a yake tuna wa. A hankali murmushi ya subuce mishi. Ammei da tunda ya kwanta take binshi da kallo ganin sai murmushi yake yasa ta ƙara kallon sa dan tasan abune mai wuya yasa Majeed murmushi. amma yanzu haka kawai sai murmushi yake kamar wanda abashi kyautar wani abun tunda bayi yake ba. "Majeed lafiya naga sai murmushi kake kodai ka samomin suruka ne wannan murmushi haka". Saida gaban sa ya faɗi jin Ammei tace yana murmushi dan baima san yana yiba, kasan cewar sa namijin duniya bai nuna mata ba sai kallon ta da yayi tare da lumshe ido cikin shaguɓe fuska yace. "Ammeiiii". "Na'am". "Bafa murmushi nike ba kawai wani abu na tuna shine". Yayi maganar yana sauke numfashi alamun ya gaji da maganar. "Humm wai nikam Majeed kaje kuwa Kaduna ka gaida Amma?" . "Yah rabb" ya fad'a yana dafe koshi kana yace. "Sorry Ammei banje ba amma insha Allah zani" "Yaushe?". "Cikin week din nan insha Allah". "Allah yasa" Shiru suyi na dan lokaci sai Auta da Ammei ne ke fira can Majeed ya tashi ya wuce wani bedroom din shi dake part din Ammei, da kallo su bishi har shige kai kawai Ammei ta kada su cigaba da hira da Auta. Koda ya shiga kan bed din shi dake lailaye da white bedsheet ya fad'a tare da lalubar wayar sa number Youseef ya fara kira bugu biyu ya ɗauka cikin girmama wa yayi sallama. Bayan sun gaisa Youseef yace, "boss akwai wani abu da kake bukata ne?". "Hmmm dama wani bincike nake so kaimin kuma kai da kanka nake so basai wani yayi ba". "Okay inajinka". "Akan wata yarinya dake aiki a gidan TV haske a Kaduna ". Ya idda maganar yana lumshe ido, daga can ɓangaren Youseef tuni ya gane wace boss ɗin nashi kuma aminishi yake nufi amma sai ya basar tare da cewa. "Okay boss meye sunan ta" Saida ya sauke ajiyar zuciya kana yace. "Humm S.... Sohfeeyarh". Ya idda maganar yana lumshe ido. Saida Youseef ya saki ƙaramin murmushi jin yadda boss ya faɗi sunan, kana yace "insha Allah bani nanda anjima". Sallama suyi yana gyara kwanciyar sa tare da lumshe ido ya faɗa duniyar tunani............. ____________ *Kaduna ✨* .............. Shirye-shiryen tafiya gidan Umma Halima nake dan ta matsa kasan cewar bikin saura 2 week's ne inda a ɓangaren MD ma shirye-shiryen suke da mama Hadiza taso naje gidan ta tamin amma kasan cewar umma Halima ta riga ta sai ta hakura. Nikam tsakanina da Abba muna nan yadda muke in batin gaisuwa dake haɗani dashi, haka su mom da anty Waleeda ba abinda ya ragu saima abinda ya karu, dan kwata-kwata yanzu ba abinda yake haɗani da anty Waleeda saboda biki nata matsowa su kuma sunyi sunyi dai sunga ba abinda ya sauya na daga biki saima shiri da ake yi dan haka sun zuba ma sarauta Allah ido kawai baby ce sai Yah Safwan dan shi bama zaman gidan yake ba. Kasan cewar yaya Ansar ya dawo shiyasa yanzu sai dai dana dawo gurin aiki ko Islamiyya ina gurin shi wataran ma har fita muke shaƙa tawa. Yayin da tsakanina da MD soyayya muke mai tsafta da tsayawa arai haka ahalinsa suna nuna min so dan wataran ma da Mennat yake zuwa dan kawai tazo guri na, dan haka shakuwa ce sosai a tsakanin mu. Tsaf yau na shirya bayan na gama duk wani aiki na gidan dana saba cikin blue Black ɗin abaya na shirya da mayafin ta fari dan yah Ansar yana waje yana jirana. Hand bag d'ita na ɗauka da waya ina shirin fitowa naci karo da anty Waleeda sai cika take tana batsewa tabbas naji zafi sosai amma haka na daure tare da cewa. "Sorry anty Waleeda bansan kina gurin ba". Yanda ta bini da wani kallo tsana tare da jan wani shegen tsaki kana tace. "Okay da kike shirin tafiya yawon naki uban wa ki barma yayi miki girki". Danne zuciya ta nayi kana nace "sorry kin ɓata ba yawo zaniba ziyara zani girki kuma ku bari dana dawo zan dafa muku ku ci tunda ba daɗe wa zanba just 2 week's ne fa". Na idda maganar ina sakin murmushin rainin hankali. Ba tare dana Jira me zata ce ba na raba ta gefen ta na wuce wata na barta tsaye baki sakeke tana kallo na. Ina fita dama yaya Ansar na mota yana jirana dan haka kai tsaye mu dau hanyar anguwar Rimi...........✍️ *Taku har kullum da ko yaushe* 🤝*Amanar taurarin writer's association📚* _*Insha Allah book one ya kusa sauka kuyi hakuri plzzzzz da jina shiru kwana biyu amma insha Allah ko farkon azumi ne zanyi ƙoƙarin karasa muku book 1 bayan sallah in Allah ya nufemu da kaiwa lpy sai a daura da book 2 ina gaya maku yanzu fa za'a fara wasan kudai ku kasan ce dani cikin littafin*RAYUWATA* _Billy pinky✍️* *Typing📲* _WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _WhatsApp group_👇 *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 ✨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION✨* *T.M.W.A.✍️* *Amanar taurarin marubuta writer's....✍️* *TEAM HAZIKAI BIYAR✨* Page 3️⃣6️⃣➡️3️⃣7️⃣ ................horn ya danna baba mai gadi ya buɗe mana mu shiga inda kai tsaye a parking lot a tsaya. Bayan gama dai-dai ta parking fitowa yayi tare da buɗe min kofa. Muka jera gunin ban sha'awa sai cikin parlour bakin mu ɗauke da sallama. Ummi ce sai Buhaisa tare da wata mata fara tar da ganin ta 'yar kwalliya ce, zaune a parlour suna fira cike da farin ciki. A tare su ɗago suna amsa mana sallama yayin da Buhaisa tazo da gudu tana rungume ni. Murmushi nayi jin tana niyar kada ni, a hankali nace. "Sake Ni kar ki karasa ni dan ba karfi garen ba". Sakin nawa tayi fuskar ta kwance da murmushi kana tace. "Kai amarya a hakane har zan kada ke guda nawa nake". Batare dana ce mata komai ba jin ta ambaci amarya sai ma hannun ta dana kama tare da ƙarasa wa kusa da Ummi. Shikam yah Ansar tuni ya zauna suna gaisawa dasu Ummi, kusa da Ummi na zauna ƙasan lallausan cafet ɗin dake malale a parlour tare da gaida su ita da matar dake zaune a kujerar kusa da ita, inda tuni Buhaisa ta shigar min da kayan dana zo dasu. Yah Ansar bai wani daɗe ba yama ummi sallama tashi nayi nabi bayan sa domin muyi sallama. Ina fita ya kalleni tare da marairaice fuska. Cikin mamaki nace. "Yaya nah maiya faru nagan ka haka?" Kai ya kawar tare da cewa. "Zo ki rakani". "Amma Yaya nah ina?" Harara ta yayi tare da cewa. "Bazaki ba dai kenan?" Kallon sa na sake yi kana na shiga dan bana son masa musu. Bai tsaya ako inaba sai a kofar gidan su Isha. inda tsabar mamaki nama kasa magana saima kallon sa nake inda shi hankali sama yana kan waya da kuma dukkan alamu da Isha yake waya yana shaida mata gamu a waje. Ban dawo daga mamakin dana tafiba saida naga Isha ta fito inda kai tsaye motar da muke ta nufo. Tafin da yaya Ansar yamin a fuska ne ya dawo dani a tunanin dana tafi tare da cewa. "Kallon fah?" Kai kwai na girgiza ina sakin murmushi tare da cewa. "Ba komai". Shima murmushin yayi tare da buɗe motar dan tuni Isha ta iso, tare mu fita cikin murmushi ta rungume ni tare da faɗin. "Amarya ce da kanta". Hararar wasa na mata tare da cewa kodai ke. Murmushi akwai tayi tana gaida Yah Ansar amsawa yayi tare da binta da kallo da ita ma shi take kallo, Inda ni Safiyyah na saki baki ina kallon ikon Allah. Gyaran murya nayi tare da cewa. "Toh mudai zamu tafi dan yaya kasan halin ummi". "Sis bazaki shiga ki gaida momy ba?" Isha ta faɗa tana marairaice fuska. "Kiyi hakuri daga gidan ummi fa muke saboda yaya ya kosa ya ganki ya dakko ni Ko ummi bata san munzo ba amma insha Allah zanzo ki gaidamin ita". "Tom shikenan sis saina zo". Cewar Isha yayin da yah Ansar dai sai kallon mu yake. Sallama mukai mata kana mu shiga mota dan ya maida ni. "Hmmm yaya yaushe akaimin wannan ɗan waken zagayen?" Na faɗa ina kallon shi murmushi yayi tare da cewa. "Allah sarki lili sis surprised naso na miki". Ya faɗa hankalin sa nakan titi. "Wow Yaya naji daɗi sosai kuma hakan shine burina kuma ka cikamin shi nagode sosai". Murmushi shima yayi dai-dai lokacin da mu iso kofar gidan sallama muyi kana ya tafi ni kuma Na shige ciki. Inda ummi ke tambaya ta nace mata fita muyi kana take cema matar dake zaune kusa da ita da tun da mu shigo Mu gaisa da ita. "Toh luba ga tanan zaku iya farawa yau ko sai gobe". Kallon ta takai kaina tare da cewa. "Ai ina ganin Hajiya yau kawai zamu fara saboda lokaci, yau saura two weeks kice kuma baza mu kai haka ba kinga kam saidai a fara yau". "Eh hakane Allah ya bada sa'a ke Safiyyah sai kije ki kintsa zuwa anjima zaku fara". "Tom Ummi" shine kawai abin da na faɗa na tashi na shiga ciki inda Buhaisa ta tasani a gaba tana min tsiya. Labari na bata tsakanin soyayyar Isha da Yah Ansar. "Haba biri yayi kama da mutum danni tuni wallahi na harbo jirgin su tom Allah yasa alkairi saura Yah Saif". "Ameen yah rabb Allah sarki Yah Saif mun rabu da gaisawa". "Hmm kedai kawai ki bar Yah Saif inda kika ganshi wallahi". "Saboda me meke da munsa?" "Wallahi sopsy ban sani ba amma kamar yana cikin damuwa saidai mu taya sa da addu'a kawai". Saida na sauke ajiyar zuciya kana nace. "Allah ya yaye mishi abinda ke damun sa". Buhaisa ta amsa da "ameen" kana mu cigaba da wata firar. _________ *Abuja🤍* *A A SARAKI HOUSE* ................."Hajiya ya kamata fa mu sauya taku dan wallahi komai ya kusa kwace mana ke ya kike gani da an bari anyi binciken nan dafa shikenan kashin mu ya bushe?" "Humm bazaka gane bane wallahi Ni kadai nasan irin tashin hankalin dana shiga lokacin ga wannan rigimam miyar tsohuwar da anbiye ta ta a da yanzu wani zancen ake ba wannan ba, amma dai mun tsallake sai mu sake shiri". "Toh yanzu ya kike gani za'a yi?" Dariyar mugun ta tasaki tare da cewa. "Yaron ya cika taurin kaine inaga kawai mu tafi plant B shima in bai samu ba sai mu tafi plant C Dan shi dai da wuya ya tsallake ko waye shi kuwa". Shima dariyar yayi yana kallon ta tare da cewa. "Daɗi na dake kema muguwa ce kanki akwai kawo wuta, dan haka plant B din kawai za'a tafi kinga kafin ya bar ƙasar nan kawai sai a gama komai idan kuma bai samu ba sai a tafi plant C din kwai". Dariya su sake saki a tare, tare da tafawa kamar ba mace da namiji ba sannan su cigaba da tsara shirin su. ✨🤍✨🤍✨ ..........Gaba ɗaya idanunsa da ƙyaƙyƙyawar fuskarsa na kan screen ɗin laptop ɗin cinyarsa da takardun hannunsa. Fuskar nan ciɗin-ciɗin babu alamar sassauci kamar wanda ke cikin ɓacin rai. saman Centre table ɗin daya ajiye ƙafafunsa masu tsananin tsafta da haske. Gashi cas babu wani girma sosai irin na maza. Dan wata macen ma sai ta fishi girman ƙafa. Youseef ne ya shigo bakin sa ɗauke da sallama inda kai tsaye kujera ya samu ya zauna tare da cewa. "Barka da hutawa boss". Kai ya jin jina ya cigaba da aikin da yake a laptop saida ya dau kusan 20 minutes kana ya maida hankalin sa kan Youseef tare da cewa. "Friday zamu je Kaduna". Shine kawai abin da ya faɗa ya maida hankalin sa kan laptop. Inda shikam Youseef ya ɗago yana kallon boss din nashi kuma Aminin sa kana yace. "Amma boss me zamuje yi Kaduna?" "Oooh kasan bani da dangi acan koh". Majeed ya faɗa yana zuba ma Youseef hararar wasa. Inda shiku ma Youseef ya saki murmushi tare da cewa. "Allah sarki Ammah zatai baki kenan ranar Friday". Ya faɗa yana ɗan kasa da kai, Majeed ne yace. "Okay kaida mekake nufi" Yar dariya yayi tare da cewa. "Na ɗauka....s". Hararar da Majeed ya wasa masa ce yasa shi kasa ƙarasa wa yana dariya. Cikin silent voice ɗinsa yace . "Youseef Allah ka fita idona ". Murmushi kawai yayi tare da cewa. "Boss fatan ka duba bayanan akan binciken da kasa nama dan tuni na turama?" "Yes" "Toh amma boss nayi mamaki da ace bikin ta yazo". "Ba abun mamaki bane ai hakan" "Toh Allah ya zaɓa abinda yake alkairi". Da "ameen" Ya amsa a saman labba inda Youseef ya cigaba da faɗin. "Boss yaufa kana da meeting 11:00pm dan tun 5:30pm suke a cikin garin Abuja". "Na sani kaje kuyi kawai dan yau banjin zani ko ina". Cikin mamaki Youseef ke kallon sa kana yace. "Amma boss kasan fa muhimmanci baƙin nan dan zasufi jin daɗi idan kaine". "Kawai kuyi dasu ɗin dan bani a yanayin haɗu wa da kowa yau". "Okay Allah yah karoma lpy da kwanciyar hankali, nabar ka lpy". Cewar Youseef dan yasan tunda yace yaje ɗin tofa baza Shiba, dan dagani ran sa ma a ɓace yake amma ya dangan ta ɓacin ran a akan waccan dalilin. ✨💞✨💞✨ ............"amma Alhaji ya kamata fa akan wannan matsalar dake tsakanin ka da Majeed ta wuce yanzu dan wallahi abun na damu na, ka duba fa shakuwa da kaunar dake tsakanin ku a da amma yanzu zama guri ɗaya ma ku gaisa ya gagara balle aje ga hira". "Hajiya bilkeesu kenan baikai ga yadda nikeji ba a zuciya ta ba, nayi iya yina amma abu yaci tura da kamar yayi sauk'i amma yanzu gaba ma kawai abin yake ƙarawa. Kuma yana shan maganin?" "Toh a cewar sa dai yana sha amma lokacin daya dawo nan da zama gaskiya kamar ba'a amfani dashi, Tom amma ni kafin ya bar part din nan nasa yayi amfani dashi sosai duk da dai sai nayi fama dashi yake sha". "Tom Allah ya kawo sauki dama akwai maganar dana ke so muyi dake akan Majeed ɗin". " toh Alhaji ina sauraren ka". "Daman akan batun nan ne". "Màsha Allah an samu nasara?" "A'a kam dan anrigamu sai dai hakuri". Cike da damu Ammei ke kallon dady kana cikin sanyin muryata Mara hayani ta fara maganar dani kaina banjin me suke cewa, dan haka ne tattara alkalami ✍️📝na nace bari mu leƙa Kaduna muga halinda mom suke ciki. _________________ *Kaduna✨* A ɓangare mom fa abu gaba ɗaya ya cabe mata dan dawowo gida tayi ta tarar ba Safiyyah inda anty Waleeda ke sheda mata ta tafi gidan ummi halima, anan fa hankalin mom ya tashi dan taga alama wannan abun fa ba fasa shi za ayi ba. Gashi gaba ɗaya ta gaza gane kan ɗiyar tata ga nakan kwari yace abu bazai tabbata ba amma gashi yana niyar tabbata dan haka bataga ta zama ba. Zaune take ta zabbaga uban tagumi inda parlour yake kaca-kaca kamar anyi dambe a cikin sa, gefe guda kwofu nan tea din dasu Shane baje a gurin amma har yanzu ba a kwashe suba sai kudaje ne keta binsu. Tana wannan tunanin har Umman ta tashigo bata sani ba dan ba kowa a gidan sai ita kaɗai, anty Waleeda kuwa tunda ta karya ta fice a gidan bata dawo ba, shiko Abba ko karyawa baiyi ba ya fice wai yana da aiki a office. Saida umman ta ta gama ƙare mata kallo kana tashigo har ta zauna a kujerar kusa da ita bata sani ba saida ta kai hannu ta taɓa ta aikuwa firgigit ta d'ago tana kallon mahaifiyar tata. "Ikon Allah ni A'i tunanin me kike yi ne haka Zuwaira tun ɗazu sai sallama nake amma hankalin ki bashi a jikin ki". Ajiyar zuciya ta sauke tare da kallon mahaifiyar tata fuska ɗauke da damuwa tace. "Umma wallahi gaba ɗaya na kasa samun sukuni akan maganar auren yarinyar nan ki duba fa umma har yanzu shiru, bayan kuma anyi aikin nan amma abu yaci tura ga Waleeda kullum cikin min maganar take". Ajiyar zuciya umma ta sauke kana tace. "Daɗi na dake rashin hakuri ai tunda kiga na kwantar da hankali na kema ya kamata ace naki ya kwanta, dan nakan kwari baya magana biyu ballema irin kuɗin da muke zuba mishi ai dolle asamu biyan buƙata, dan haka ki kwantar da hankalin ki aure baza ayiba inko anyi toh bazamu barta ta zauna lafiya ba". A hankali mom ta sauke ajiyar zuciya fuskar ta ɗauke da murmushi tace. "Shiyasa nake yinki umma nifa inson samune aure ne bana so naga tayi, nafiso ta ƙare a meyi min bata dan ko kaɗan bana so naga jinin Amina yana hutawa. Yanzu umma Bama wannan ba intai auren wazai ringa mana gyaran gida, da girki, dan itafa Waleeda ba iyawa zatai ba shiyasa na fison ko auren zatai akaita gidan da yake da maiko". Saida umma tayi murmushi kana tace "toh baga su Safwan ba in suyi aure matan ba sai suyi miki bauta ba". "Hakane kuma fa umma Waleeda inta dawo zan turo miki ita sai ake can ɗin da ita". ta faɗa tana dariya. Da haka su cigaba da tattaunawa itada mahaifiyar tata inda kisan ba uwarta ba anayi ana dariya. 🤍💞🤍💞🤍💞 Shirye-shirye biki ake ba kama hannun yaro daga ko wanne ɓangare, musamman ma daga family ango dan shine auren dasu mumy za suyi na farko dan daga Suraj sai Mennat. Dan haka ita kanta Mennat ba'a barta a baya ba dan ta shirya ma bikin Yayan nata sosai dan ma ta wani ɓangaren tana gun amarya. Haka ɓangaren Ummi ma shirin aurar da ɗiyar yar uwar tata take, dan duk wani abu daya kamata uwa tayi a bikin yar ta toh Ummi tayi shi saidai fatan Allah ya kaimu ranar lpy. Batun aiki kuwa tun ranar data zo gidan Ummi tai sallama da gurin aiki sai kuma bayan biki angama shan amarci. Yayin da tuni mai gyaran jiki ta fara nata aikin tun ranar datazo. Wani irin gyaran jiki mai ban mamaki luba ta fara min ɗan gaske. Tunda na shiga bedroom din Ummi ko falo an haramta min fita, hakama wayata an kwace gyara kawai nake sha ciki da waje, ni kaina abin har tsoro yake bani. Abubuwan da ake danna min ina sha kuwa kamar zasu sanyani amai nake ji. Shiyyasa dana faki ido sai na zubar. Ga wani irin mahaukacin ƙamshi da ko yaya na motsa sai kaji waje ya buɗe. Fatata yayi wani irin ƙyau na tashin hankali. Sau ɗaya Luba ke bani damar yin waya da RK a rana. Shima na minti goma kawai. Duk wani abu na bashi damar yaje su tattauna da su Buhaisa, ga Isha, ga Nusaiba yarinyar uncle ɗin su Buhaisa, harma da Mennat ƙanwar sa. _______★ A ɓangaren ango wato MD shiri yake dan kai tsaye zance yafi amarya ƙaguwa, dan gurin aiki tuni ya mishi ƙaura kace shine amaryar daka kalleshi ko da yaushe yana cikin farin ciki. Komai ya kammala saidai jiran ranar kawai. inda yaune gidan su ango ke shirin miƙa lefe gidan su amarya. Kasancewar lefen gidan Abba za'a kaishi dan haka Ummi tuni tayi shirin tafiya gidan dan ita rabon ta da gidan ma ta manta. Tsaf ta shirya dan tuni tasa masu aiki da Buhaisa harma da ita kanta sun shiga kitchen domin shirya ma yan kawo lefe a abinci, dan tasan indai ta Mom Za'abi tofa za'aji kunya dan haka komai tasa an fita dashi ansa a motar Yah Saif danshi zai kaita. Daga ita sai Maman Isha suka tafi dan tasan dole za'a samu wasu mutumen daga dangin Abba zasu zo, dan Aminiyar tace baji ba gani, sai Buhaisa data maƙale saita bita dan ita anty Hajara sai satin biki ya shiga zata zo. dan haka daga Safiyyah sai Luba dake mata gyaran jiki sai kuma masu aiki aka bari a gidan yayin da su kuma Yah Saif ya tafi kaisu. Koda suje gidan ilai kuwa yadda Ummi tai tsammani ba kowa acikin sa sai Mom da anty Waleeda sai wata ƙanwar mom ɗin da mahaifiyar ta dan da alamu zuwa gidan yar Tata baya mata wuya, tun kafin agama shigo da kayan dasu zo dashi saiga dangin Abba nan suma sunzo a mota, batare da Ummi ta tsayaba kai tsaye suyi sallama acikin parlour, dan gaba ɗaya angama shigar musu da kayan dasu zo dashi. baki mom su saki suna kallon yaran dake shiga da kayan cikin parlour kafin Mom ta jefoma yaron tambayar. "Wannan kayan daga ina". Amsa yaron ya bata dacewa. "Wata Hajiya ce tace a shigo dasu". Ba tare da ya gama basu amsa ba su Ummi su shigo bakin su ɗauke da sallama. Wani kallo aka shigarma juna tsakanin Mom da Ummi batare da sun amsa musu sallamar da suyi ba, Ummi ce tai janye idonta akanta tare da sakin wani miskilin murmushi tana ƙarasa wa cikin parlour su Buhaisa da Maman Isha biye da ita inda kai tsaye kujera su samu tare da karka ɗewa dan tayi datti ba lefi, su zauna kowa bakin sa ɗauke da bisimilah. Shirune ya ratsa parlour sai kuma kana nun tsaki dake tashi ƙasa-ƙasa daga ɓangaren su Mom yayin da ko daga ido su Ummi basuyi ba saima hankalin su dasu mayar kan waya sai Buhaisa dake bin parlourn da kallo dan a mutukar har mutse yake tako ina. Zaman su ba daɗe wa saiga dangin Abba nan su Mama Hadiza da anty Maryam yarta dake aure acan kawo harma da matan su kawu Bala sun shigo. Aikuwa tuni parlourn ya dauka aka fara gaishe-gaishe tsakanin dangin Abba dasu Ummi yayin da Mom ko ido bata daga ta kalle suba saida mahaifiyar ta ta zun gureta dan koba komai ai itama dangin tane. Sai lokacin ta gaishe da dangin Abban koma ince dangin ta tunda auran zumunci ne tsakanin ta da Abban. Tunda kuma su gama gisawa ta tsuke bakinta tayi shiru batare da ko tayin ruwa tayi musu ba, anty Waleeda kuwa ko kallo basu isheta ba saima tashi da tayi tana harare-harare tare da taunar cungum ta shige bedroom din su. Duk da kallo su bita yayin da Mama Hadiza ta kada baki tace. "Oooh ni yar nan kace kema A'i nan kuka yo". Saida ta tabe baki tare da cewa. "Eh munzo taya ku amsar lefen yar tamu ne". Itama Mama Hadiza saida tayi murmushi kana tace. "Anko gode". Daga hk bata sake cewa komai ba sai kan Ummi data koma tana tambayar ta. "Wai ni mai babban suna bata nan ne nasan data nanan da tuni an cike mana gaba da kayan shaye-shaye dana ciye-ciye". Murmushi Ummi tayi kana cikin girmama wa tace. "Ai Safiyyah ta kwana biyu a gurina ko zata dawo sai biki ya rage kaɗan" "A'a màsha Allah dama ta faɗa min lokacin dana ce Maryam zata mata ɗan gyaran jiki tace ai tana gidan kima. Toh Allah Ubangiji ya saka miki da mafificin alkairi amma tabbas kinyi hallaci dama wannan shine zumunci ai". Da "ameen" dukka suka amsa inka cire mom da komatsen ta da sai baki kawai suke tab'e wa. "Au Niko nace Zuwaira fatan dai abincin ya kammala?, dan nasan bakin nan na gab da isowa". Mama Hadiza ce ta kuma faɗa tana mai kafe mom da kallo. Cikin ya tsina mom tace. "Mama wanda abincin kuma?. Ta sake jefa ma mama Hadiza wata tambayar itama fuska haɗe take bata amsa da. "Abinci mana na yan kawo kayan lefen Safiyyah koh shi Ibrahim ɗin bai faɗa miki bane". Saida ta wani taɓe baki kana tace. "A gaskiya ba'a faɗa min ba, dan haka ni yau koh girki banyi ba gari ma mu jika mu s....". Tsawar da mama Hadiza ta daka mata ce tare da ɗaga mata yasa tayi shiru tare da cewa. "Wato kedai Zawaira bazaki canza wannan baƙin halin naki ba?, aiko ɗin ki fitar da mijinki kunya kyasa y'ar taki da ƙanwar taki su tayaki ayi girki nan amma tsabar is...". Ummi ce ta katse ta ta hanyar nuna mata abincin dasu zo dasu harma da drinks da duk wani abu daya kamata aba baƙi na fita kunya. Aifa nan mama Hadiza harma da matan su kawu Bala su shiga da mata albarka ita da zuri'arta, inda mom rai bace ta tashi fuuu tashiga daki zuciyar ta na kuna inda ƙanwar tata yabi bayan ta. Duk abin nan da ake ko sau ɗaya umma mahaifiyar mom bata ce ta tafi a sauke ba, Dan jitake kamar ta tashi ta bar gidan toh amma ta riga tace sunzo amsar akwati ne. Dole ta cigaba da zama badin taso ba........... To lefen dai Safiyyah ya iso gidan Malam Ibrahim. Gida fa cike da ƴan gulma musamman ta fannin mom dan harda kawayen ta kace bikin Anty Waleeda dan wannan dai badin Allah suzo ba, anzo ne ayi sa ido. ga akwatina jerarru na kece raini da ƴar gata kawai ake kaima set biyu shaƙe da kayan alfarma na gani na faɗa. Babu wanda zaice lefen nan bai birgesa ba. Sai dai anga tsagwaron hassada daga Mom dan ta kasa haɗiye komai. Harda zage-zagenta wai ai saurayin Anty Waleeda ne na kwace da asiri. Kuma ba kowa ke kawo min asirin ba sai Ummi. Ba tare da koh daga kai Ummi tayi ba ta kalleta saima Buhaisa ce datai niyyar magana Ummi ta dakatar da ita ta hanyar harara. Ai kuwa ta sami amsa dai-dai da ita dan Mama Hadiza da matan kawu Bala saida suyi mata tatas......... kowa na shirin kama gaban sa dan Mama Hadiza cewa tayi kawai Ummi su ɗauke lefen ta tafi dashi can gidan ta, dan yanzu itace ai mahaifiyar tata. Batare da Ummi tayi mata musu ba aka ɗauke lefen daga gidan sun wuce da shi can gidanta. Acewarsu barinsa gidan Abba bazai yiwu ba su Mom zasu iya salwantarwa saboda basu da isashen mutunci. Ashe ko hasashen su Mama Hadiza yay dai-dai. Dan su Mom sun shirya mummunan ƙudiri kuwa akan lefen nan aka ɓata musu shiri............✍️ *Typing📲* _Follow my WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _Follow my WhatsApp group_👇 https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 *✨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION✨* *T.M.W.A.✍️* *Amanar taurarin marubuta writer's....✍️* *TEAM HAZIKAI BIYAR✨* Page 3️⃣8️⃣➡️3️⃣9️⃣ ..................Su Ummi sun dawo lpy da kaya niki-niki dan mota biyu ma su kayi, inda ni abin ma yaɗan so ya bani mamaki amma ba abun mamaki bane sanin halin mom. Na tarbe su cike da fara'a inda kai tsaye Ummi tasa su Rabi shiga mata da kayan can parlourn Abba ita kuma ta haura sama domin hutawa. Buhaisa ke bani labarin duk yadda akayi naji baƙin ciki kwarai da gaske da abun da Mom din takeyi, koba komai aini ɗin a matsayin ɗiyar ta nake amma bakomai Allah ya ganar da ita inme gane wace. Ina shirin magana waya ta tafara haske alamun shigowar kira dan a silent take, murmushi nayi ganin Suraj ke kiran dan kwata-kwata ba muyi waya dashi ba. Hannu nakai da niyar ɗaukar wayar Buhaisa ta ɗauka tare da cewa. "Ango Ango kasha kanshi". murmush yayi mai sauti kana yace. "Na'am bestyn mu ya ranki". "Fari tasss". Cewar Buhaisa tana dariya, shima dariyar yayi kana su gaisa cikin barkonci dan dama haka sukeyi da ita sannan yace. "Ina ginbiyar tawa ne?". "Ga tanan tayi wani iri kamar wanda in akai maka ita ta tafi kenan dan kwana biyun nan haka take har yar rama tayi, yanzu ma lallaba maka ita nake dan jiya ma take cemin gaskiya na sami Ummi na faɗa mata itafa ta fasa aur.....". Wayar dana fisge ce a hannun ta tare da zuba mata harara ya hanata karasa maganar da take sonyi tare da kyalkyalewa da dariya tana ficewa a dakin. Nima murmushin nayi tare da kai wayar kunne na. Murya kamar zaiyi kuka yace. "Babe da gaske wai?" "Uhm uhm fah". "To yayane?" Ya sake faɗa cikin sanyin murya, nima cikin shagoɓɓa nace. "Sharrin bestie nefa kawai". Ajiyar zuciya ya sauke mai karfi tare da faɗin "Alhamdulilah" ni saima yaso bani dariya wato shi harya yadda da zancen Buhaisa, Katsemin tunani yayi wajen cewa. "Babe kinsan meye". "Uhm uhm" "I swear I love you Soo much please don't leave me alone babe". Saida gabana ya faɗi jin yadda yayi maganar tamkar zaiyi kuka ni saima ya bani tausayi, nima cikin sanyin murya nace. "Insha Allah muna tare FARSI" "Allah yasa sai nakejin kamar....." "Kamar me". Na faɗa cike da shagoɓɓa idona cike da kwalla. Dariya yayi tare da cewa "ba komai babe" Nima jin haka sai nai murmushi. Shiru muyi na wani ɗan lokaci kowa na sauraren bugun zuciyar ɗan uwan sa can naji yace. "Bebeee" "Uhm" "Kinyi dinner" "Uhm" "Yauwa tom yanzun ki tashi ku dan yi hira da bestyn mu dan bana son kiyi baccin yamma kinga magrib ta kusa nikuma zan shiga gurin momy ne". "Tom kagaida min da ita" "Zataji insha Allah" Da haka mukai sallama ina shirin fita parlour saiga Luba nan hannun ta ɗauke da wani ɗan mug inda ta mika min tare da cewa. "Oya maza shanye ki bani kofin". Yadda kisan zanyi kuka anty Billy haka na kafa kai inasha cikin two minutes na shanye dan abun cikin mai daɗi ne. Kana na bata ita kuma tayi murmushi ta fice inda na rufa mata baya...... ____________ *Abuja 🤍* *A A SARAKI HOUSE* ............. Monday tushen aiki kasan cewar Monday ranar aiki ne . Gaba ɗaya family zaune suke a dinning area dake babban parlour cikin shirin aiki mazan su da matan su suna breakfast inka cire Yah Majeed sai kuma granny da sam bata yadda da zaman dinning ba a cewar ta tafison taji ta Mike kafa. Amma daga kan Uncle Sulaiman, Uncle Abdallah, Dady, Ammei, Addah, Mommy, Mama, sai anty Amarya, sai kuma Yan matan gidan da ko wacce hankalin ta yake akan bama cikin ta abinci wasu kuma anayi ana latsa waya. duk da doka ce kana cin abinci kana latsa waya to amma ba wanda yasa dokar a gun Dan da alama ma bai fito ba. Tsit ka ke jin gun ya dau shiru sai karar spoon dake tashi dan wasu da yawa a cikin su sun kusa gama cin abincin. Tun kafin su ganshi mayataccen ƙamshinsa daya gama manne jikinsa da komai nasa ya iso hancinansu. Gaba ɗaya sun zuba ma hanyar da suke kyautata zaton ta nan mamallakin kamshin zai fito. A hankali ko yake sakko wa daga upstairs din cikin nutsuwa gami da nagarta. Yayi matuƙar ƙyau cikin Maroon suit sai long sleeve shirt fara tas. sai da zuciyar Zaituna da finnat ta ɗan motsa da wasu daga ciki. Kai tsaye Ammei ya nufa da itama ta zuba mishi ido fuskar ta ɗauke da murmushi.        “hannun ta ya sumbata yana mai ɗan bata side hug. Sai kuma murya ƙasa-ƙasa ya furta, “Good morning my everything”.       Murmushi Ammei ta sake masa, tana mai amsawa da, “Ka tashi lafiya ?”.         “Alhamdullahi Ammei nah”.     “Masha ALLAH”. Zaune yakai kan ɗaya daga cikin kujerun dinning din kusa da uncle Abdallah. Ya fara gaida iyayen nasa cikin natsuwa gami da girmama wa, suma su amsa masa cike da kulawa. Kana ya koma kan matan suma ko wacce fuska ɗauke da murmushi su amsa mishi. Haka kannin nashi shima su gaidashi cike da girmama, yayin da hannu kawai ya daga musu kana cikin coll vioce ɗin shi yace "kun tashi lafiya" daga haka bai sake cewa komai ba, suma bayan sun amsa basu sake magana ba dan sun san iyakar amsawar kenan. Mama ce ta dube shi cike da kulawa tace. "My son har yanzu shiru kak'i fito mana da matar aure kuma gaskiya ni jika nake so". Dariya su sanya gaba ɗaya inka cire shi Majeed ɗin daya kara haɗe tashi fuskar, da kuma wasu daga cikin su da dariyar ba takai zuciya ba. "Faɗa mishi dai Mama ni kaina nagaji da zuba ido kamar ma tsoron matan yake". Cewar Anty Amarya. Yayin da cikin taɓe baki Mummy tace. "In tsoran matan yakeji basai a zaɓa mishi a cikin dangi ba". "Aaa ku dena takuramin ɗa haba dan Allah kamar ba iyaye ba". Cewar Addah Kana ta waigo tana kallon Majeed cike da kulawa tace. "My son please mu basu kunya kafin sabon wata ya shiga dan naga sa idon ya fara yawa". Murmushi yayi irin na gefen baƙin nan tare da gyaɗa mata kanshi dake dan masa ciwo sama-sama kasan cewar zaman su guri ɗaya da dady tare da furta. "insha Allah" asaman labban kana ya tashi ya koma can cikin parlourn inda kai tsaye rukunin kujeru Black and White ya nufa tare da ɗaura kafa ɗaya kan ɗaya. Duka da kallo suka bishi har Ammei da tunda su fara mishi tsiya batace komai ba saidai kowa da nashi manufar kallon da yayi mishi. Inda Addah ta katse su gurin kiran sunan Zaituna. "Na'am Addah". Saida Mummy ta d'ago dan gani me za'a sa Zaituna. Yayin da Addah tace. "Yauwa Zaituna haɗa ma my son breakfast din shi ki kaimai". Da "toh" ta amsa farin ciki kamar zai mata me danji take kamar ta rungume Addah dan farin ciki, kana ta mike ta haɗa mishi duk wani abu da tasan nashine, kasan cewar Ammei ke mishi girki dan baicin na masu aiki. Ta nufi inda yake bakin ta ɗauke da sallama. Doguwar riga ce a jikin ta ta bacci amma sai dai bata matseta ba sosai saboda tasan halin shi dan tuni ya hana su sa matsatsun kaya. Harta dire tiren data haɗu mishi breakfast din akan table ɗin dake tsakan kanin sofar da yake bai ɗago ba. Kana ta fara ƙoƙarin haɗa mishi komai dan tsaf sunsan halin yaya na su akan abinda yake so da wanda baya so. Yadda ta duko sosai kusa dashi ga wani uban turare data bula a jikin ta dan har hannun ta na gogar kafadar shi, kana ta kashe murya tare da cewa. "Done!" Wani kallo ya watso mata da yasa hajin cikin ta kada wa, cikin sauri kuma tabar gun ta nemi guri ta zauna a kan lallausan cafet ɗin dake shimfide a cikin parlourn. Ammei ce ta kalli Finnat cikin kulawa tace. "Au Finnat ɗauki madarar nan ki kaima yayan ku kinga Zaituna ta manta da ita. "Toh Ammei" Finnat ta faɗa tare da ɗaukar jug din ta nufi cikin parlourn bakin ta ɗauke da sallama. inda Zaituna ta ɗago tana binta da wani irin kallo mai kama da harara itama ramawa tayi kana ta ajiye mai tare da zuba wa a ƙaramin mug ta nemi guri itaka kan cafet ta zauna. Saida ya mula dan kansa kana ya ɗago ya fara da madara duk da haka kusan hankali sa na'a kan laptop ne dan da alama wani aiki yake mai mahimmanci. Youseef ne ya shigo cikin shirin sa nafita aiki kai tsaye dinning area ya nufa inda ya samu su dady na shirin tashi dan gama wayar su kenan da Uncle Kabeer dake can Saudiya, gaishe su yayi cikin girmamawa su amsa mishi cike da kulawa. Ammei ce ta faɗa mishi inda Yah Majeed yake dan shima tunda yaga dady yasan toh fa ba Majeed a gun Kai tsaye cikin parlourn ya nufa inda ya sameshi zaune yana breakfast yan mata biyu zagaye dashi ko wacce da kallon da take mishi kamar zasu cinye shi. Shi abinma saiya nemi bashi dariya amma ba tare da yayi dariyar ba yayi sallama tare da zama a ɗaya daga cikin kujerun. Bayan sun gaisa da Majeed suka su Zaituna su gaidashi. Youseef bai wani daɗe da zama ba Majeed yah kammala breakfast din, ba tare daya kalli kowa acikin su ba ya ƙarasa gurin Ammei inda take zaune a set ɗin kujeru masu white and purple. Har kasa ya duƙa tare inda ta shafa kanshi tare da mai maganar dani kaina banjin me take cewa, amma da alamu harda addu'a take mai. Yanzu kam fuskar tashi adan sake take ba kamar ɗazu ba cikin nutsuwar shi ya fara tafiya yana mai daga mata hannu, Youseef biye dashi bayan sunyi sallama da Ammei, inda Mama ma ta bishi da addu'a dan daga ita sai Ammei a parlourn dasu Zaituna Addah ta tafi gurin aiki anty Amarya ma haka sai Mummy data shige part din granny su dady ma basu daɗe da tafiya ba. Harya kai kofa Ammei ta kira sunan shi bai waigo ba amma ya dakata daga tafiyar da yake. "Kaje kun gaisa da Hajja kuwa?" A hankali ya juyo kamar me ciwon wuya kana ya girgiza mata kanshi murya ƙasa-kasa yace. "Ammei munyi latti saina dawo". Kai kawai itama ta jinjina mishi tare da cewa. "Allah yah tsare". Ya amsa da "ameen" a saman labba suna idda ficewa shida Youseef. Zaituna da finnat na binshi da kallo kamar su hana shi tafiya toh amma ya su iya............... _____________ *Kaduna ✨* ...............Mom tace "Toh ni ba wannan ba, Murja shirye shirye dai sai gaba yake a gidanmu don yau ma aka kawo lefe karkigan shi..." Murja tace "Saura sati ɗaya fa Zuwaira, ba sai a xuba ido ba a ga ikon Allah, idan fa mutum ya fiye axar6a6i da kyar ya dinga ganin abubuwa yanda yake so, ke dai kawai ki xuba masu ido ki daina damun kan ki, auren nan ance ko an daura bai fi na minti goma ba in ma an daura kenan to me xai dameki, ni ba san halin malamin nan nawa tunda na gaya miki shike min aiki kuma kice na kaiki tunda naku shiru, dan haka kawai mu zuba ido mu gani, amma gaskiya malam yana da gaskiya sosai, duka duka nawa ya amsa wajen mu..." Mom ta sauke ajiyar xuciya tace "Ban son in sakankance ne da maganar mutumi a xo ayi abun nan Ina ji Ina gani, wllh da na shiga uku, shi sa gwara in buga nan in buga can, yanxu ma xan je gidan Hajiya Balaraba" Murja ta tabe baki tace "Toh ni dai sai mun yi waya amma da kin hakura ki jira mu gani koda ace baiyi ba bayan an daura zamu iya gurgude shi koh" ajiyar zuciya Mom ta sauke tare da cewa. "Tom shikenan sai munyi wayar Aminiya". Daga haka suyi sallama. ________★ Yau anty Hajara ta sauka a garin Kaduna dan tare ma su taho da Yah Ahmad kasan cewar jirgin safe su biyo yasa su sauka da wuri, an shirya musa tarba sosai dan Ni lokacin dasu zo ina ciki Luba ta hana ni fitowa sai bayan nayi wanka da ruwan data haɗa min daya ji turaruka dan ba abinda nake sai kamshi ko yaushe kuma dashi nake wanka dan haka kamshi ya kama jikin na sosai dan ko abu na taɓa sai kaji kamshi. Bayan fitowa ta wanka na kintsa cikin abaya marron sai dan kwallin ta. ba abinda na shafawa fuskata sai mai na fito domin musu sannu da zuwa dan koh parlour Luba ba barina na figo take ba, sai dai innaci sa'a in kuma Ummi taganni tace na koma daki shiyasa zaman dakin ya gundire ni sosai. Sosai anty Hajara data kara kyau da yar kiba ta tasani a gaba tana zolayata ita da mijin ta Yah Ahmad. Nikam tun ina sunne kai har idona ya fara tara kwalla dan Buhaisa ma taya su take yi sun taranmin su duka. Fitowar Ummi cikin shiga ta alfarma yasa na koma jikin ta ina sakin kuku, cikin lallashi take tambaya, "waya taɓa min ke Safiyya". Su anty Hajara na nuna mata ina kara sakin wani kukan dani kaina nasan na shagoɓɓa ne. Murmushi itama Ummi ta saki irin na manya dan sak Safiyyah ba abinda ta bari na kamanni yar uwarta Amina. sai dai ace ita ta dara Safiyyah haske amma komai nata ta ɗauko cikin son danne kewar yar uwar tata saboda gaban siriki take duk da dai kamar ɗan ta yake. Da ƙuwa Ummi tama Buhaisa dake dariya ƙasa-ƙasa tare da cewa. "Kinci gidan ku wato kece kisa min 'ya a gaba koh?". dan su anty Hajara tunda ta fito suja baki suyi shiru sai Buhaisa ce baki yaƙi mutuwa. Cikin dariya tace "Allah Ummi bani kadai bace harda su yah Ahmad ma". Ta idda maganar kuma tana kwabe fuska. Dariya su sanya gaba ɗaya sai Ummi da tayi dan murmushi kawai inda Yah Ahmad yace "kai Autas harda sharri" cikin dan zaro ido Safiyyah tace. "Laaaa Allah Yah Ahmad ba sharri bane" dariya su kuma yi wannan karon harda Ummi sai dai Tata bata kai tasu ba. Sannan tace "Rabu dasu kiji Auta ai Bama kulasu kuma zasu zo su sameni ne dukan su". Daga haka kuma kowa ya saki jiki aka sha fira danshi dai Yah Ahmad baya surkuta da Ummi, gashi akwai wasa da dariya itama a fannin ta hakan ne saidai dan nauyi kaɗan. Suna haka Yah Saif ya dawo yadda ya samesu cikin farin ciki har Safiyyah data zake kamar ba Amarya ba ana fira da ita, dan Safiyyah akwai surutu idan ta samu fira saidai kasan cewar ta taso ne cikin gidan dako damuwar kama baza a zaunar dakai ajiba balle aje ga babin hira. Kallon ta yake irin kallon nan dake nuna tsantsar soyayyar da yake mata amma kash wani ya riga shi, ya riga shi a lokacin da yake gab da faɗa mata. Ya tabbata ya rasa Safiyyah har abada toh yaushe ma ya rage mishi ya dena ganin ta tunda bikin dududu kwana nawa ya rage 5 to 4 nefa, "Yah Allah". Ya faɗa yana dafe kanshi inda gaba ɗaya su ɗago su zuba mishi ido saboda maganar karshe da yayi ta fito fili. Tambaya su shiga jira mishi idan ba tare da yace komai ba ya samu guri ya zauna cikin son boye komai yake ma su anty Hajara sannu da zuwa. Suma yadda suga yayi suna basu sake tambayar sa ba. Sai Buhaisa ce data gir giza kai zuciyar ta cike da tausayin ya'yan nata dan tuni ta gano yayan nata son Safiyyah yake amma Suraj ya ruga saidai hakuri. Toh a bangaren Ummi ma hakan take dan tuni ta gano son da Yah Saif yake ma Safiyyah ita kanta zata so yarinyar 'yar uwar ta ta dawo kusa da ita toh amma me haka Allah yake ikon sa sai dai suyi fatan Allah yasa alkairi amma komai ya kare kuma. Around 4:pm Yah Ahmad yabi jirgi ya koma Abuja inda yabar anty Hajara anan dan ita tazo kenan sai kuma bayan biki shima dai yace insha Allah zai shigo ranar bikin. Adaren kuwa munsha hira da anty Hajara dan har Abba ya dawo muna hira daga baya kowa ya nufi gurin kwanciyar shi. ________★ Washegari Suraj yazo kawo min kayan da zansa a gurin dinner da walima da kamu dan nace nifa bana son wasu events iyakacin walima, kamu, sai dinner da yace abokan sa sun shirya ma za'a yi hadin naso ba na yarda dan Buhaisa har haushina tasoji itada Isha, acewar su su kadai su san yadda su shirya ma bikin nan amma wai na musu cikas nidai bance komai ba sai hakuri dana basu. Da kyar Luba ta yadda tabarni zanje gunshi saida Ummi tasa baki kana ta yarda. Nayi kyau sosai cikin abaya k'irar Saudia baka daga ciki nasa wandon Jen's Blue da farar riga data min kyau. Dan kwallin abayar kawai nayi rolling a kaina dan ko turare ban saba saboda kamshin daya gama maye jikina ga wani irin glowing da fata ta take. babu jimawa ta fita. Tunda ta fito ya zuba mata ido, sai ya zam tana takune tamkar da bugawar zuciyarsa. ALLAH ya jarabcesa da son wannan halittar ƙwarai da gaske. Yana kuma fatan mallakarta nan da kwana uku kacal. Safiyyah ta tsani kallo, dan haka sai da ta masa tsogumi akan kallon ƙurillar da yake matan. Baice komai ba face basarwa yana sakin murmushi. Itama sai ta bata ce komai ba kawai ta shiga gaishesa. Ya amsa mata da kulawa, kana su shiga ciki bayan sun gaisa da Ummi dan bai wani jima ba ya bata kayan daya kawo mata yama Ummi sallama yayin da ita kuma ta fita raka shi. Juyowa yayi a hankali yana kallon ta kana cikin sayin murya yace "Babe" da "na'am" na amsa kana na ɗago aiko idanuna su faɗa cikin nashi da shima kallo na yake yi, kallo muke ma junan mu mai wuyar fassarawa. Nina fara janye nawa idon tare da yin ƙasa da kaina, murmushi yayi kana ya katse shurin namu ta hanyar faɗin. "Please babe ki kulamin da kakin sosai Please". ya haɗe hannun shi alamun roko🙏🏽 , kai kawai na daga mishi tare da cewa "insha Allah". Ba wani hira mukaiyi mai yawa ba dan time ɗin da Luba ta dibamin bashida yawa dan haka bai wani daɗe ba ya tafi. Har bakin get na rakashi dan saida yama motar sa key sannan na shigr ciki cike da kewar sa. Kodana shiga ciki matsamin Ummi tayi akan sai mun shiga parlourn Abba naga kayan lefe na, ba yadda na iya na tashi mu hau sama harda su anty Hajara dan itama bata gani ba. Toh ba abinda za'a ce saidai ace Masha Allah dan tabbas MD sunyi bajimta sosai dan sun zuba kaya sosai dan wannan fa shi ake kira da akwatin yar gata. Kayan da ya kawo min na events Buhaisa ta shigo dasu suma dai komai yayi sai dai ace Allah ya kaimu lokacin. Ba wani daɗe wa mu kayi a parlourn Abba ba mu fito kasan cewar ni Luba na nemana dan gobe nema Walima.......................✍️ *Typing📲* _Follow my WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _Follow my WhatsApp group_👇 https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 *✨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION✨* *T.M.W.A.✍️* *Amanar taurarin marubuta writer's....✍️* *TEAM HAZIKAI BIYAR✨* Page. 4️⃣0️⃣➡️4️⃣1️⃣ .....................Ina ciki Isha tazo can na jiyo hirar su itada Buhaisa ji nayi kamar na fito amma ba dama, dan tunda bikin nan y rage saura kwana ki kaɗan Luba ta kara kaimi akan da duk da da dinma anyi amma fa na 'yan kwanakin nan yafi na da. Dan Sosai take min gyara na fitar hayyaci, ciki da waje ga wani uban ƙamshi na bala'i a dukkan motsina. Ko guri na gitta saika ji kamshi ya zauna kaman nice zaune agun. Fatata kuwa wani irin santsi da take da walƙiya abin ba'a magana. Gaba ɗaya ji nake a jikina komai ya canja. Hatta gashina, ƙafafuna da tafukan hannuna gyara Luba ke musu na musamman Dan hatta baki da lips ba'a bari ba.. ________________🖤🤍 A bangaren gidan su Suraj kuwa koda yan kawo lefe su koma sun faɗi irin karrama sun da ayi a gidan su Safiyyah sai kuma maganar ta Mom data tsaya ma ƙanwar maman Suraj a rai. Da take cewa, "ai saurayin yar tane ayi mata kwace da asiri" koda ta tambayi yayar tata saita Bata amsa da. "bakin ciki ne kawai Zubaidah kinsan halin kishi irin n mata, kuma ita Safiyyah maman ta bata a gidan dan wayar gari ma ayi aga bata a gidan kuma dai zargin da ake itace ta koreta, toh kinga kuwa ai komai zata iya faɗa". "Wallahi kuwa yaya shiyasa tunda muje tana kace a kujera sai habaice-habaice take". Murmushi kawai mumy tayi tare da cewa, "shiyasa nake mutukar son yarinya nan wllh, gata da nutsuwa dan duk wanda ya same ta a matsayin mata kam ya dace," da haka su rufe hirar Safiyyah da samata albarka yayin da sosai suke shirya biki na ƙerewa sa'a dan daga uwar angon har uban agon wannan shine zasu fara aurar da ɗan su na fari shiyasa kowa ka gani yana cikin farin ciki da kuma shirin bikin. Daga Mumy har anty zubaidah basu da wani lokaci na kansu dan sun shiga busy sosai akan bikin. Itama dai Mennat ba'a barta a baya ba, gurin shirye-shiryen bikin yayan nata dan jefi-jefi take samu ma ta tabo amarya. dan ita kanta ta maida kanta busy ne a cewar ta ai daga shi ba wani biki da za'a sake yi a gidan sai nata. Toh ta ɓangaren Suraj ma shirye-shirye suke ba kama hannun yaro shida abonka sa. dan har wata yar ƙwarya- ƙwarya walima su haɗa mishi bayan daurin aure sai kuma dinner da duk sudin ne dai su haɗa. Dan acikin abokan nasu kusan shine baida aure shiyasa suke a shirye a harkar bikin dan su Al'ameen babban abokin sa nema yaso rako shi gurin Safiyyah lokacin da zai kawo mata kayan events din Amma fir MD yace aa dan shi akwai shi da kishi acewar sa zasu gama kalle mishi mata tun kafin ta shigo, haka su gama zolayar shi su hakura. _______________🖤🤍 ............Gidan Abba fah abu ya musu yawa dan gaba ɗaya Mom itada ɗiyar tata hankalin su a mutukar tashe yake ganin biki ya matso kwata-kwata saura 2 days ga gaiyata ta walima da a aiko musu daga gidan Ummi gobe in Allah ya kaimu. A lokacin da invitetion ɗin ya iso ga Mom bayan gama karan tawa da tayi, wata irin a Shari'a ta lailayo ta dire ma ɗiyar kawu Bala Kafin ta yaga shi tai mishi gutsi-gutsi ta watsa mata, tare da zuba mata gargaɗi akan ta fice mata a gida kafin ta fito ta same ta. Itako Bahijja cikin sauri ta fice tana dariya da hali irin na Mom dan su kam ba abinda zai hana su zuwa gurin walimar harma da kamun, karo su kusa yi da anty Waleeda da duk ta rame a tsaye dama ita abu ba aukiba duk ta kara zabge wa dan Allah ya jarabce ta da mugun son Suraj gashi ana shirin ɗaura mai aure da ƙanwar ta ƙanwar tata ma wacce tafi tsana sama da komai a duniyar nan dan yanzu wata irin tsanar Safiyya take ji dan ji take ko wuka a bata ace ta kashe wani a duniyar nan kai tsaye Safiyyah zata daɓa ma dan yanzu haka ji take kamar ta bita gidan Umma Halima ai duk wacce za ayi toh amma ba dama dan ko gidan bata sani ba tasan dai suna a anguwar rimi ne shi kadai kawai ta sani game da su. Tana a wannan tunanin ne har ta bangaji Bahijja bata sani ba da kallo kawai Bahijja ta bita har ta shige cikin parlourn. Kai kwai ta girgiza tare da furta. "Allah ya shirya". Kana ta fice a gidan. Kamar wacce a jefo cikin parlourn anty Waleeda ta shigo inda ta sami Mom zaune sai uban huci take, da gudu ta karasa ta faɗa jikin ta tana sakin wani marayan kuka, hankalin Mom duk ya tashi haka take rarrashin yar gwal ɗin Tata da mata alƙawaruru ka iri-iri da rantse-rantse akan batin fasa auren nan. Ita abun haushin ma tunda Safiyyah ta bar gidan bata sake dawowa ba, toh amma tasan dai iya wuya sai dai a dawo gidan ubanta ayi bikin koh, toh anan zata nuna mata ainihin ta dan saita sa an batar mata da ita a duniyar kamar yadda ta battar da mahaifiyar ta. Fatan dai Allah yasa kar suzo da wannan ƙanwar uwar tata Halima. Haka su cigaba da tsine ma su Umma Halima har Yah Safwan ya dawo gidan shigowar sa baisa sunyi shiru ba, saida ya kai zaune kana yace, "amma Mom bikin yarinyar nan Safiyyah yazo ban saniba kuma baki faɗa min ba?". Ya tambaye ta yana kafeta da ido itama cikin fusata tace, "Ban faɗa ba idan ƙanwar uwar kace kota ubanka sai inji". "Kai Mom ƙanwata cef.....a". Tsawar data daka mishi ce yasa shi ɗago wa yana kallon ta dan shi sak Abba ya dakko bashi da faɗa ko kadan, itama cikin tsawa tace, "karka sake kiranta da ƙanwar ka dan duk duniyar nan Baby ce kawai ƙanwar ka sai kuma Waleeda antyn ka amma inba suba baka da wasu kanwa ko yaya". Baki ya buɗe da niyar yin magana ta katse ta hanyar cewa, "bace min da gani shashasha mara kishin kanshi dana uwar sa". Bace komai ba cikin sanyi shi ya wuce dakin shi, su kuma su raka bayan shi da harara kamar ido zai fado. A ɓangare Abba ba wani shiri da yake yi na mahaifi zai aurar da ɗiyar shi, saida su kawu Bala su mishi tatas tare da kawo mishi invitetion ɗin bikin dasu bugo a matsayin su na iyaye, kwarai da gaske Abba yaji daɗi sosai dan har fuskar shi ta nuna toh shine fah harya fara raba ma abonkashi na kasuwanci invitetion ɗin dan sai yanzu ma yake ji a jikin sa na zai aurar da ɗiyar tashi. Rabon ma daya ganta tun da tazo tace mai zata gidan Umma Halima da rabon da ya taka Kafa yaje tun sanda yaje amso Safiyyah bayan batar mahaifiyar ta da Umma Halima ta ɗauke ta. Saidai jefi-jefi suna haɗu wa da Abban su Buhaisa. Shi sai yanzu yake jin rashin kyauta warsa na watsar da Umma Halima toh amma wataran tasa gane kanshi yake kwata-kwata. Toh shima ya Ansar gobe yake saran shigowa cikin garin na Kaduna dan duk wani abu daya kamata mahaifin yayi toh yayi shi ba tare da shi kansa Abban ya sani ba harma dasu Safiyyahn. Dan yadda zai aurar da Yar ƙanwar tasa da yake mutukar kauna. _______________🖤🤍 Washegari Laraba walima ce ta yamma ce, ƙarfe huɗu za'a fara Gaba ɗaya gidan na Ummi cike yake da baki kasan cewar yau ne walima, Safiyyah nacan cikin bedroom din Ummi Luba tazo damai kwalliya domin yima amarya, duk dai yau ba mai yawa za ai mata ba. Amma kafin ayin ma tasha turare harda na tsiya, kai Luba tasan sirrin ƙamshi, tsaf aka kwalliyeta aka sakata ta shirya cikin wata fitinanniyar shadda yar uban su wacce ta kasan pink color kai da gani kasan an kashe kuɗi sosai gurin ɗinkin ta. Matuƙar ƙyau Safiyyah tayi kam kamar ka saceta ka gudu. Ga wani ƙamshi mai azabar daɗi tana bulalawa. Anan harabar gidan aka shirya walimar, dan tabbas gidan su Ummi babbane matuƙa ta yanda basa jin ko ɗar idan sabga ta tashi. Dan koda bikin Anty Hajara duk wani events anan akayi inka cire irinsu dinner. Sosai walima ta ƙayatar dan iya mata ne kawai, dan Ummi akwai jama'a tun daga kan kawaye harma da dangin Abban su Buhaisa dan suna mutukar son ta sasai. sai malamai magada annabawa da aka gayyata suka zuba lectures masu ratsa jiki da saka nutsuwa musamman akan ma'aurata da shi kansa ma zaman auren da daɗin dake cikinsa da ƙalubale. Alhamdullah walima ta kasance cikin aminci, amarya Safiyyah tasha kuka jikinta yayi sanyi sosai, dan har su Isha dake kusa da ita dasu tasa ta da tsokana shiru sukai dan suma fa nasihar ta ratsa su, dan idan ta haɗa da lectures na nasihar iyaye da gargaɗi da wannan ya sake tabbatar mata da aure ba wasan yara bane. Dan duk abinda akace IBADA ne to lallai dole ne ka shirya da shiri na musamman. Dole ne ka yarda da dariya a cikinsa da kuma kuka a wasu lokutan, ita aljanna bata samuwa a kwance, kamar yanda kasan baka samun kuɗi a cikin mafarkinka sai ka motsa ka nema. Idan har duniya da take ba komai ba bata samuwa a garemu cikin sauƙi, taya zamu yi tunanin aljanna samunta zai kasance mana mai sauƙi.  (ALLAH kasa mu ɗin ƴan aljanna ne🙏🏽.)        Ba lectures ce kawai ta gudana a wajen ba, anci ansha tare da raba souvenirs masu ƙyau da ɗaukar idanu. Bayan kammala walima amaryar jibi Safiyyah ta koma ciki, yayin da ƙawayen ta yan islamiyyar su harma dana gurin aiki su fara shirin tafiya kasan cewar magrib tayi. Sallama suyi ma Ummi da Amarya kana su tafi sai kuma Allah ya kaimu gobe Kamu, suma 'yan dangin su Abban su Safiyyah tafiya suce zasuyi Ummi tace a'a suyi zaman su sai gobe tunda akwai kamu, amma ina Mama Hadiza tace gida zasu tafi sai koh 'yan matan irin su Bahijja su zauna. Hakan da Mama Hadiza ta faɗa baima ƙanwar Mom daɗi ba dan taso taga kwal uwar daka. toh amma ai goben ma ƙafarta ƙafarsu ta samu naba wa yar uwar ta labari dan ko yanzu saida ta ɗauki hotuna a cewar ta gani da ido yafi labari. ______________🖤🤍 Washe gari Alhamis kuma ana gobe ɗaurin aure Kamu ne, na rana ne ƙarfe 3:00pm za'a fara. Tunda gari ya waye su Buhaisa basu koma bacci ba dan Isha ma nanta kwana sai su Bahijja. Kasan cewar yau ne ana gobe ɗaurin aure gashi kuma yau za'ayi Kamu, dan ma bikin ba anan gidan Ummi za ayi ba can gidan su Safiyyahn zasu koma bayan an gama kamu. Bayan gama duk wani aiki daya kamata suyi subar ma masu aiki su ƙarasa sauran su kuma su dungu ma zuwa gurin wankin kai da lalli. Kusan ƙarfe 12:30pm su Mama Hadiza su iso da tawagar ta harda ƙanwar Mom da Yayar ta guda ɗaya umma Rabi, dama wasu daga cikin 'yan matan jiya anan su kwana. Da Hibbah, da Bahijja, sai Salma anan su kwana dan tare ma su tafi gurin kunshi dasu Buhaisa. Zuwan su ba daɗe wa saiga anty Fatima nan ƙanwar Abba dake aure a Abuja itama da yaran ta uku biyu sa'ar Safiyyah ne Nabila kuma taɗan girme su, dan daga Abuja nan ta taho tunda Mama Hadiza tace mata suna can, kuma dama suna mutumci sosai da Ummi dan har bikin Anty Hajara taso zuwa amma lokacin sunyi tafiya ne. Nabila, Ikram, Yasmeen, sune yaran ta sai babban namiji. Sosai Safiyyah tayi farin ciki, dan ba wasu ƙawaye bane da ita dan ma 'yan gurin aikin su sunada kara sosai suma kuma ba duka ba. Kamar wasa saiga Yah Ansar da baby wai ta maƙale saita biyu shi shi kuma ganin Mom batanan kawai yace ta shirya yazo ya kawo ta. Aiko zabar farin ciki haɗe su nayi duka na rungume ina murna. An musu tarba ta mutun tawa dan Ummi ba daga nan ba gurin karrama bako yayin da su kuma su shiga saka mata albarka. Gurin karfe biyu saiga dangin su Buhaisa nan sunzo ma Ummi kara kace bikin Anty Hajara harda yaran su dan duk ƙawayen su Safiyyahn ne su kuma saba sosai kasan cewar tana zuwa suma kuma suna zuwa nan su haɗu. Sai wasu daga cikin kawayen Ummi wasu kuma sai zuwa anjima zasu shigo. Kai saidai fa ace Masha Allah dan gida fa ya ciga da dangi tako ina. Hummm kunga Safiyyah kuwa, nace kuga Safiyyah kuwa tayi ƙyau harta gaji, ga ƙunshi ja da baƙi an zuba mata. Karku yadda kunshi nan ya zauna raɗam akan farar fatar ta da sai sheƙi tana wani glowing mai ɗaukar ido, hummm 😌 gaskiya ba'a magana dan kunshin yayi mutukar kyau yadda bakwa tsammani. Ga gashi yasha wanki yasha gyara tubarkallah Masha Allah, dan Allah yama Safiyyah baiwar gashi ga tsawo ga cika sai ɗaukar ido yake. Ƙamshi kam hmmm ba'a magana nace ba'a magana hajiya ko kina nesa da ita matukar ta gitta sai kin jishi. 2:00pm su Buhaisa suka dawo daga gurin kunshi da gyaran kai dan harda anty Hajara dan haka suna dawowa ciki su shiga kota kan amarya basu biba suma su fara nasu shirin inda ganin su Yasmeen dasu Tasleem yasa su rungume juna ana ihun murna. A ɓangaren amarya fah ana can ana kintsa tane dan wata irin shegen kwalliya mai natsuwa akema Safiyyah, komai dai-dai misali ba'a cika shi da shirme ba. Dan mai kwalliyar ƙwararriya ce tun daga Abuja Luba ta ɗakkota dan komai daya shafi amarya itace keyi. Matar ta gogu da sanin takan duniya ne ƙwarai da gaske. Ƙarfe 2:50pm an gama shirya amarya Safiyyah cikin doguwar riga na lass pitch and white color daya tsaru mutuka ga wani ɗinki dan ubansu na doguwar riga Fitet gown. Tun daga sama zuwa gurin cinyar ta a matse take sai da aje dai-dai cinyar ta a saki rigar ta wani buɗe har ƙasa ta wani irin fidda ainahin surarta tamkar zane a takarda dan har ƙasa take jah ta baya. Ga wani fitinannen ɗaurin data kashe mata shi a kanta mutukar zaunuwa ɗaurin kan Safiyyah ya zaunu, ga wata tamfatsetsiyar Sarƙa da ƴan kunne zuwa bangles suma sun haɗu haɗu ta musamman. dan ƙareriyar sarƙa ce da akama ma wani irin adon fararen stones, sai wani irin mayafi mai net dashi ma akasa fatan ɗin less din ayi mai kwalliya dashi shima pitch color, ga wani hadadden takalmi mai shegen kyau bashi da tudu sosai data sa sai ya zauna mata dagwas a kafa ya rabba. Dole ka kalla wannan amaryar ka sake kallo dan takai zama abin kallon. Ita kanta sai take jin kamar ba ita ba. Lokacin da Luba da anty Hajara da itama tuni ta kintsa suka fito da ita falo. sumar zaune tawagar Mom suyi dan da zasu iya rantse wa da Allah badin sun san Safiyyahn itace amarya ba da kai tsaye zasu ce ba ita bace, aran su kuwa imagine suke inama ace Anty Waleeda ce a haka. su Buhaisa da zaman su kenan suma cikin nasu shirin aikuwa suka shiga faɗin, “Woowww!!“ Suna miƙewa. Kafin kace mi hasken camara ya fara hasketa tako ina. kansu su anty Hajara sai hotuna suke zuba mata haka su Yasmeen. Sosai tai ƙyau komai ya fita da fitarsa, sai ƙamshi take zabgawa kamar a kamfanin turare. Tuni dama dangin ango sun zo dan haka kai tsaye harabar gidan su Mami (maman su Isha) itada wata farar mata kyakkyawa itama makotan su Ummi ne kuma kawar ta ce sosai baji ba gani itada Mami Hajiya A'isha su fita da ita, dama tun kan a fita da ita bayan hotunan dasu gama sha aka rufe mata fuska da net ɗin dake a matsayin mayafi. Tunda Safiyyah ta fito Ummi ta tsaya cak tana ƙare mata kallo gaba ɗaya kamannin yar uwar ta take hango a jikin Safiyyah, a hankali ta goge kwallar data gangaro mata a ido kafin idon mutane yakai kanta, sai dai ta makaro dan tuni Safiyyah da ake ma hoto tagani aida dan gudunta ta ƙarasa ta rungume ta itama tana niyar sakin kuka. Cikin sauri ta ɗago ta tare da girgiza mata kai alamun kartai kukan tana ɗauke mata guntun hawayen daya gangaro mata zuwa kumatu rungume ta ta sake yi tana raɗa mata magana a kunne dayasa ta sakin guntun murmushi. Gaba ɗaya gurin tafi ya ɗauka kama daga dangin amarya har na angon. Sosai harabar gidan tasha decoration irin na gargajiya daya mutukar ƙawata gurin. Haka 'yan mata ne sosai a gurin kowa ce dana ta gayun, daga ɓangaren ango har dana amarya sun haɗe yayin da ba ɓata lokaci a fara abinda ya tara su. Alhamdulilah an gama Kamu cikin aminci dan komai fa ya kayatar kayatarwa ta musamman kama daga dangin ango dana amarya kam an rabu cikin farin ciki da nishadi sai dai fatan Allah ya kaimu goben lpy. Toh kusan abu na social media ga Kamu ya tara manyan mutane harma da yaran kuma zamani na kowa wayar sa, TUNI KAMU NA SHAHARARRIYAR YAR JARIDAR NAN WATO *SAFIYYAH A IBRAHIM* TA GIDAN TV HASKE DAKE WAYAR DA KAN MATASA DA KUMA JAN HANKALI GA IYAYE AKAN TARBIYYA. ya shiga zagaye social media. Toh mudai sai dai fatan Allah yasa alkairi. _________________🖤🤍 *Abuja 🤍* ..................gaba ɗaya familyn zaune suke a part din granny kasan cewar duk dare bayan gama dinner can suke zuwa wataran ma can suke yi inka cire Yah Majeed. Zaune suke cikin farin ciki da anna shuwa ana hira wasu kuma na wata sabgar tasu daban daka kalli granny kasan tana cikin farin ciki na haɗuwar familyn nata, inka cire uncle Kabeer dake can Saudiya da iyalan sa shima kuma ana waya dashi kullum. Hira tayi hira tsakanin mayan yayin da kuma yaran ko wacce ta dukufa kan wayar ta sai masu hirar suma jefi-jefi. Cikin zaro ido Auta ta ɗago tana kallon granny ga dukkan alamu wani abun mamakin ta gani, har tana harɗewa wajan cewa, "laaaa granny kinga yau ake Kamun Safiyyah ta gidan Tvn haske". Gaba ɗaya ido su zuba mata suna kallon ta, cikin waro ido itama granny tace, "Na shiga uku na ni Maimunatu Kamu fah kice aure zatayi?". Kafin Auta tayi magan Basma ta amshe da faɗin, "eh granny aure zatai dan yadda najima gobe ne ɗaurin auren shirin faɗa nake ma Auta ta rigani". Kasa cewa komai granny tayi sai sallallami da take yi Azima ce itama cikin nata salon yangar tace, "kai granny naga duk kin tada hankalin ki saika ce wacce akace iskanci take, aure nefa dan gaba ɗaya social media ta ɗauka sai hotunan tane ke trending". Itama granny cikin hayayyako wa tace, "Ina ruwan kine dani". Kana ta koma kan Auta tare da cewa, "wazata aura" shiru Auta tayi alamun nazari kafin tace komai Azizat tace, "MDn gurin aikin su naji kamar ana cewa". Haba granny ta sake riƙe wa tare da cewa, "Ooo Ni maimuna". Zaituna kuwa a zuciyar ta cewa tayi, "kaji tsohuwar nan da fitinar tsiya ina ruwan ta nema oho saika ce tana da wanda zata aura mata ne". Toh ba iya granny maganar auren Safiyyahn ya taɓa ba harda su Addah. A dai-dai lokacin da zai shigo parlourn na granny yaji kalmar Auta tamkar wanda a doka da guduma haka yaja ya tsaya cakk.....................✍️ *Typing📲* _Follow my WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _Follow my WhatsApp group_👇 https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 *✨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION✨* *T.M.W.A.✍️* *Amanar taurarin marubuta writer's....✍️* *TEAM HAZIKAI BIYAR 💪✨* Page. 4️⃣2️⃣➡️4️⃣3️⃣ ..............Kamar zai shiga ko me ya tuna sai kuma ya nufi part din shi Youseef dake biye dashi da shima yaji zancen nasu Auta kai kwai ya girgiza yabi bayan sa domin ajimai kayan shi. Kai tsaye upstairs ya haura nan ma bai tsaya ba ya shiga ƙoƙarin zame kayan jikin sa domin yadda kansa ke sarawa ba abinda yafi buƙata sama da ruwan sanyi. Towel ya ɗaura kana ya shige bathroom din, tsawon minti arba'in da biyar ya dauka kana ya fita sanye da bathrobe white color sabuwa dal, ƙaramin towel dake a hannun sa yana goge kwanta ciyar sumar sa. Gaban mirro ya karasa yana ɗaukar hand dryer ya jona a socket cikin cikin ƙan ƙanin lokaci ya kammala gyara ta, ko mai bai shafa ba sai sprays dinsa masu shegen ƙamshi yasa. Kana ya nufi close ɗin sa, tsaf ya fito cikin jallabiya fara tar ga dukkan alamu sabo ce. tsaf ya gama shirin nasa ya koma gaban mirror yayi wankan tsaddadun turarukan nasa masu ƙamshi kace ba dare bane. Duk wannan shirin da yake kana kallon fuskar sa zaka fahimci bashi da walwala sam, duk da dama ba ma'abocin murmushi bane amma yanzun fuskar sa a mutukar tamke take ba walwala sam. Tuna tare su taho da Youseef yasa shi dafe kai tare da addu'a Allah yasa bai tsaya jiran sa ba ya tafi dan shi ɓacin ran da yake ciki ne yasa ya manta bai tsaya ya sallame shiba. Dan shi mutum ne me mutukar mutun ta ɗan adam, ko ya yake koda kuwa wanda ke aiki a ƙarƙashin sa ne, bare kuma wannan da yake Aminin shi da bashi da wani amini sama dashi a faɗin duniyar nan inka cire su Dady. Cikin nutsuwar sa da izza da koda ace yana cikin damuwa ba lallai ka gane ba yake sauko wa daga upstairs din nashi, aikuwa can ya hango Youseef kishin gide a kujera yana waya sai uban murmushi yake. Shi sai abinma ya nemi bashi mamaki duk da dama yasan Youseef king of love ne shi kuma ta yadda halinsu ya ban banta kenan da nashi. Ya daɗe tsaye a yana kallon Youseef da sauraron shi amma kwata-kwata bai san ma ya fito ba (danya yi nisa sosai a kogin love❤️😂) jin Kamar tsayuwar mutum a bayan sa ne danshi sai yanzu ma ya farga da kamshin turaren shi aikuwa yana waiga wa yaga Yah Majeed tsaye kikam kamar wani soja yana kallon shi. Dariya ce taso kufce ma Youseef sai kuma ya danne baiyi ba sai murmushi da yayi kana yace, "Sorry my beb bani 1 hours plzzz". Ban San me ace mai daga can ɓangaren ba yadai cire wayar a kunnen shi. Ganin yadda ya kafe shi da ido yasa shi saurin miki wa tare da ƙame wa kamar wani soja, sun kuyar dakai yayi alamun jin kunya kana yace. "I'm sorry Sir". Sai kuma ya kwashe da dariya ya koma kujera ya zauna yana cigaba da dariyar shi. Majeed madai murmushi yayi mai sauti tare da kaiwa zaune kusa da Youseef ɗin, duk da cikin ɓacin rai yake saida Youseef yasa Nishaɗi dan ya tuna masa baya ne lokacin suna yara. Cikin silent voice ɗin sa dake fita da ɗan amo yace, "Ina can ina jimamin nabar ka kai ɗaya ashe kai kana nan ana abinda a saba. Allah ya shirmin kai Youseef wata ka kuma samo wa kenan?". Dariya Youseef yayi tare da amsa wa da "ameen" batare daya bashi amsar tambayar shiba, hakan ya tabbatar masa da watan ya kuma samu, kai kawai ya girgiza tare da cewa, "Adai ringa jin tsoron Allah, in kana tunanin Amma bata da wata toh Ammei nada Auta". Murmushi mai sauti Youseef yayi kana yace, "Allah boss bafa yaudara bane kawai dai fashion love ne". " Ummm" Kawai yace alamun karshen zancen kenan, shima Youseef ɗin murmushi yayi ganin boss din ya saki jikin shi akan ɗazu dasu shigowa part din. Shima cikin sanyin murya yace, "Boss Wai ya batun zuwa Kaduna ne?" Shiru yayi na wani lokaci kafin ya buɗe baki kamar baya so yace, "Bari muga zuwa gobe". "Allah kaimu lpy" ya amsa da "ameen" asaman labba ba wata hira suyi ba yamishi sallama ya fice shikuma ya haura sama domin kwanciya. Ya daɗe yana juyi a gadon amma baccin ya gagara ɗaukar sa dan ba abinda yake sai tunani daga baya ma bathroom ya shiga ya ɗauro alwala ya fara gabatar da nafila...... ________________🖤🤍 Washegari ta kama Friday gaba ɗaya familyn suna a dinning area suna breakfast inka cire Dady da Majeed, shi dady bayama ƙasar shi kuma Majeed yana part din sa, har su gama breakfast bashi ba alamar sa, gaba ɗaya hankalin wasu daga cikin 'yan matan bashi a jikin su na rashin ganin abin son nasu musamman ma Zaituna. kuma shiru Youseef baizo ba alamun maybe yau bazai fita aiki ba. Addah ce cikin yar dumuwa tace, "wai nikam ina my son ne naga kwata-kwata yau bai fito ba". Ta faɗa idon ta akan Ammei da itama duk ta damu dan gaba ɗaya hankalin ta na akan upstairs kozai sauko amma bai sauko ba harsu kammala breakfast din wasu daga cikin family ma duk sun fita aiki. Mummy ce ta taɓe baki tana cigaba da danna waya anty Amarya kam ta fita gurin aiki haka Mama itama bata a parlourn. Cikin danne damuwa Ammei tace, "Nima dai naga bai fito ba gaba ɗaya yau banjin ma yaje masallaci inba kota kofar part din shi yabi ba". Mummy da takaici ya tirnike tace, "ikon Allah wai nikam Majeed ɗin ƙaramin yaro ne kome har dan bai fito ba zaku wani bi ku damu saika ce yaron da baisan kansa ba". Mama da fitowar ta kenan daga kitchen taba Mummy amsa da, "Eh Majeed ba ƙaramin yaro bane amma ko kece a matsayin ki na babar shi in kikai wannan lokacin baki fito ba dole a nemeki aji ko lafiya". Kafin ma Mummy data shaƙa ta bata amsa tace, "Ke Auta maza jeki part din nasa ki duba mana ko lafiya ko zamu sami su kuni". Da "to" Auta ta amsa kana ta miki ta nufi upstairs zuciyar ta cike da sake-saken ko Yayan nata yana lpy kuwa. Kwafa Mummy kawai tayi ba tare daya sake cewa komai ba. Yayin da Addah ta sauke ajiyar zuciya, Ammei dai ba tace komai ba dan ita irin matan nan ne wanda sam magana bata dame taba dan zan iya cewa ma Majeed ita ya gado gurin mulki da rashin son magana dan shi harya ma fita. Zaituna kuwa ji take inama ace ita Mama tace taje taga ko yana lpy, amma ya zatayi. A ɓangaren Auta kuwa koda ta isa part ɗin nasa haka yake tsittt dan kwata-kwata ba haske a parlourn saina hasken rana ɗaya fito, amma gaba ɗaya fitulin a kashe suke alamun ma bai sauko parlourn ba. Kasan cewar makunin a farkon shigowa yake yasa Auta danna shi aikuwa gaba ɗaya haske ya mamaye parlourn. Tsaf yake tamkar ba'a zauna a cikin shiba ga wani irin kamshi mai sanyi dake tashi, saida ta gama ƙare ma parlourn kallo kana ta nemi guri ta zauna a kujerar dan tasan halin yayan nata ba'a shiga mishi daki kai tsaye, kuma tunda taga bashi a parlour tai tunanin ko yana bedroom ne. Zama tayi na 5 minutes shiru bai fito ba a hankali ta nufi upstairs din nashi takai gurin 3 minutes a bakin kofar bedroom ɗin sa kafin ta fara knocking, Amma shiru dan ko motsi bata ji kusan 5 minutes ta tura kofar cikin sand'a ta shiga. Dind'um ɗakin yake dan komai na wuta a kashe yake inka cire ehsin dake kune dan gaba ɗaya dakin ya dau wani irin sanyi mai shiga cikin jiki, saida Auta ta ɗan matse jikinta saboda sanyi cikin tsanani tsoron dake gudu a zuciyar ta ta fara ƙoƙarin kunna wutar ɗakin dan zaman yayan nata cikin duhu ga sanyi tasan me yake nufi. Can ta hango shi kudundune cikin blanket sai uban tsumar sanyi yake yi, ai da sauri Auta ta nufi gurin ehsin ta kashe dan ita kanta da shigowar ta kenan ɗakin sanyin ya fara damun ta bare shi daya kwana cikin sa. Kafin cikin sauri hartana harɗewa ta nufi gadon, bargon daya rufe jikin sa dashi ta yaye inda wani uban hucin zafi ya buso mata a da sauri ta saki bargon tana niyar barin ɗakin, cakk ta tsaya saboda tozali da tayi da hoton wata kyakkyawar baiwar Allah a cikin system ɗin sa dake ajiye a kan side drower. Kur tayi tana ƙare mata kallo inda take sanye cikin White hijjab face din ta sanye da facemark sai eyeglasses dan siriri fari tar shima. Yanda zuciyar ta ke tsillo a kirjin ta yasa ta koma wa dabas ta zauna tare da maida system ɗin kan cinyar ta tare da zoming ɗin photon dan sake tabbatar da wacce take tunani ce ko wata daban. "Kwarai kuwa Safiyyah ce" Ta faɗa a fili sai kuma cikin sauri da kama baki ta waiga tana kallon shi dan ita tsabar kiɗimar ma da tayi na ganin photon Safiyyah a system ɗin yaya Majeed ɗin yasa ta manta da bashi da lafiya, amma waiga War da tayi yasa tunanin ta ya dawo jikin ta. "Habibah ki nutsu yanzu ba lokacin tunani bane" ta ai faɗa a zuciyar ta ai cikin sauri ta diro a gadon tai kofar fita. Kome ta tuna oho sai kuma ta dawo ta kashe system ɗin kana ta rufeta kafin ta sake fice wa a ɗakin. Cikin sauri take sakkowa a down stairs tunda kafin ta iso yadda su Ammei su hangota ya basu tabbacin babu lafiya ai basu ma bari ta ƙaraso ba su tashi subiyo ta. Amma banda Mummy Dai-dai tana karsowa ta faɗa jikin Ammei tare da sakin kuka. Cikin tashin hankali Ammei ke tambayar ta "lpy meya sameshi?" Cikin kuka take ba Ammei amsa da, "Ammei yana kwance cikin duhu da alamama baya numfash.....i" kasa ƙarasa wa tayi saboda sakin ta da Ammei tayi ta bi bayan su Zaituna dan sune a farkon fara wucewa jin batun Auta. Yanda Auta tabar shi haka su same shi aikuwa ko numfashi bayayi cikin tashin hankali Ammei ta haye kan Royal bed din da yake kwance kansa dake a pillow ta maida kan cinyar ta tana hura mishi iskar bakin ta yayin da tuni Addah ta nufi compood domin kiran doctor Fadil dan bata majin yana cikin gidan. Cikin Sa'a kuwa ta same shi dan shigowar sa kenan ɗaukar wasu takardu daya manta dasu zai wuce ai nihin hospital din da yake aiki suci karo da Addah. Ganin ta cikin tashin hankali ya nufi ta yana tambayar ta lpy ita cikin sauri take bashi amsa yazo Majeed ba lpy. Baima tsaya wata magana ba ya koma cikin hospital din dan dakko kayan aiki bai ja wani dogon lokaci ba yabi bayan ta zuwa part ɗin nasa ta wata kofa inda kai tsaye can zaka nufa. Koda su ƙarasa lokacin Mummy ma tashigo dan shirin nasu yayi yawa shiyasa ta biyo su, umarni ya basu dasu ɗan fita su bashi guri zai duba shi, babu musu su fito har Ammei da kansa ke a cinyar ta. Ya kai kusan 1 hours sannan ya fito fuska da damuwa Zaituna da Auta ne su fara shiga ɗakin kana sauran yan matan subi bayan su. Ammei ce tace, "ya jikin nasa Dr Fadil". Cikin sauke ajiyar zuciya yace, "Hajiya ki kwantar da hankalin ki ba wani abu bane amma dai zamuyi magana da Alhaji insha Allah, zan aiko da magungunan da zaisha yanzu na masa injections tare da drip. Daya kare sai a cire mishi insha Allah zai samu sauki". Shiru tayi tana kafeshi da kallo na wani lokaci kafin tace, "Allah yasa inajin yau ma zai shigo". Daga haka cikin ɗakin nasa ta koma inda ta tarar dashi kwance hannun sa sanye da drip irin babban nan da alamu ya samu bacci dan sai ajiyar zuciya kawai yake sauke wa fuskar nan tayi fayau irin na mara lpy. Daga can gefe ta koma ta zauna dan su Addah da Mama duk suna a kusa dashi ne inda cikin dattakon ta tace ma Auta' "Auta maza kije ki faɗa ma Hajja Yayan ku bashi da lpy dan kar ayi lefi" da "toh" Auta ta amsa kana ta tashi Basma tabi bayan ta su fice a ɗakin. ____________🖤 A ɓangaren granny kuwa tana can tana faɗa wai yau kwata-kwata Majeed bai shigo ya gaishe ta ba Mama Rabi na bata hakuri amma bata fasa ba, shigowar su Auta da Basma baisa ta dena ba sai ma harara data bisu daita. Gaishe ta su fara yi kana su gaida Mama Rabi inada granny ta amsa tana ɗauke kai kace Majeed ɗin ne a kusa da ita. Kana cikin faɗa tace, "Lafiya kuzo ku zauna fuska ba annuri gaba ɗayan ku? Atoh ni kunsan bana son wannan ɗan iskan miskilancin da wancan yake neman ya koya muku, inba hira ya kawo kuba ku tashi ku bani guri kafin na fatatta ke ku". Ta idda maganar tana kwafa cikin sanyin murya Auta tace, "Kai granny Yah Majeed nefa yau kwata-kwata bai fito ba toh shine Mama tace naje naga ko lafiya toh d nake sai natarar dashi baya numfashi.....". "Innalilahi wa'inna ilahiri raji'un nashiga uku ni Maimunatu sumafa kice abdulmajidun?" Granny ta jehoma Auta tambaya Basma ce tace "Eh granny amma doctor ya duba shi yanzu haka ma yasa mishi drip maybe Around 11 ya kare." Granny da tayi shiru tana sauraren su Basma saida takai aya kana cikin sanyin jiki tace ma Auta "jeki ɗakko min mayafina naga halinda jikana ke ciki". Da "toh" Auta ta amsa kana ta shiga cikin bedroom din Bata fi 3 minutes ba ta fito ruke da mayafin granny sawa kawai granny tayi kana ta fice su bita a baya. Koda su ƙara sa kuka granny taso farawa Addah ta lallashe ta tare da cewa su fita su dan bashi guri yasha iska kar motsinsu ya tashe shi, hakan kuwa akayi dan gaba ɗaya ma parlourn su koma yayin da Mummy ta koma ɗakin ta ya zama saura Mama da Ammei da granny sai su Zaituna Addah kuma taje kitchen domin haɗo masa abincin kafin ya tashi. Jefi-jefi Auta ko Zaituna kan leka wa koya farka amma dai har lokacin bai farka ba ana haka saiga Youseef yazo, dan tunda yaji boss din shiru yace maybe tafiyar nan bazata yiwu ba gashi yaita kiran wayan sa ba'a picking. Aikuwa koda Ammei ta sanar masa bashi da lafiya ba ƙaramin tashi hankalin sa yayi ba dan sam bai kaunar wani abu ya taɓa masa boss ɗin nasa. Shiga yayi har lokacin bacci yake bai farka ba dan haka bai wani daɗe ba ya fito......................... _________________🖤🤍 *Kaduna ✨* ...............A gidan Ummi fah kowa ya kama gaban sa sai ƙalilan na 'yan matan da basu tafi ba suma kuma shirin tafiya gidan su Safiyyah suke yi, hatta Ummi itama can zataje dan da tace ita bazata waccan gidan ba a gidan ta zatai na taron a matsayin ta na uwar amarya. Toh amma Abba ya zaunar da ita ya mata nasiha mai ratsa jiki da nuna mata mahimmancin yin bikin acan tunda hatta ma ɗaurin auren ta acan yake. Tabbas nasihar ta shige ta dan ta gano duk abinda mijin nata ya faɗa gaskiya ne, da isha'i Yah Saif da Yah Ansar zasu maida su can. Ta ɓangaren Amarya kuwa tun bayan tashi a Kamu ciki ta koma itada Luba domin shirin tafiya gidan su Safiyyah. Bayan gama shirya ta cikin wata bak'ar abaya da ama kwalliya da fararen stones haka shima takalmin ƙafarta baƙi ne sosai tayi kyau sai uban kamshi take yi kamar ba dareba. Gurin Abba Ummi ta kaita aiko Abba ya mata nasiha mai ratsa jiki dan ba abinda take sai kuka dan jin Abban su Buhaisa take kamar nata Abban, bayan gama mata nasiha kana ya ɗaura da kwantar mata da hankali da nuna mata muhimmanci aure da kuma hakuri, danshi aure sai anyi hakuri komai ma a RAYUWAR nan sai kayi hakuri kawai zaka ci ribar zaman duniya. Yayin da tuni Yah Ansar yazo dan haka shida Yah Saif suka kwashe su sai gidan su Safiyyah. Dama tun bayan gama Kamu su mama Hadiza su tafi can gidan ɗin aikuwa suna zuwa da kanta ta buɗe ɗakin Ummah (maman su Safiyyah) su gyara shi tsaf kamar da mutum dan komai na Ummah ya nan ba abinda a ɗauka amma saidai ba mai shiga ɗakin dan ko Mom tayi mitar amma ta hakura shi kanshi Abban ba shiga yake ba. dan tace anan su Ummi zasu zauna da Amarya. aiko abin yama Mom zafi dan sai habaice-habaice take yarwa, su kuwa suyi kunnen uwar shegu da ita su fara shirin ɗaura girki dan tarbar su Ummi a cewar su yanzu basu da lokacin ta sai an ɗaura tukun na. Aiko anan aka sauke su Ummi har hawaye ta share dan kace yar uwar tata tana a gidan ne. Kasan cewar dakin two bedrooms ne a ciki sai parlour dan har dakin Mom shima haka yake, hakan da mama Hadiza tayi kam yasa Ummi jindadi dan dakin zai ishesu yadda suke so kasan cewar itama nata bakin na nan tafe gobe yanzu daga ita sai anty Hajara ne sai Luba sai kuma ƙawayen su Safiyyah sai su Isha da Buhaisa. Abinci a kawo musu mai rai da lafiya yayin da Safiyyah take jinta kamar ba ita ba dan komai ji take ya sauya mata wai yau ita ce amarya ita abun ma saitaji sa kamar wani al mara toh amma wannan kaɗan daga cikin hukuncin ubangiji. Sanda Mom taga Safiyyah saida zuciyar ta ta motsa, dan sak yarinyar ta koma uwar tane aiko ko gaisuwar da Safiyyah take mata bata amsa ba tai waje fuuuu kamar zata tashi sama. Number Murja ta nemo tare da danna mata kira bugu biyu t dauka hira suke ƙasa-ƙasa dani kaina banjin me suke cewa kana ta yanke tana sakin wani makirin murmushi.............. _________________🖤🤍 *Abuja 🤍* Around 11am Majeed ya farka lokacin drip ɗin saura kaɗan ya ƙare, a kuma dai-dai lokacin suke shiga gaba ɗayan su dan ganin ko drip din ya ƙare, ganin yadda yake buɗe ido tare da lumshe wa ya tabbatar masu daya farka, aiko cikin farin ciki su ƙarasa gare shi kowa na jera masa tambayar ya jikin nasa. Ido kawai ya lunmshe kana ya buɗe ba tare da yace komai ba ya yunkura, jin kansa yake ya masa nauyi dan har yanzu yana jin ciwon kan ƙasa-ƙasa. Youseef ne ya jawo fillo ya jingina da fuskar gadon kana shi kuma ya jingina bayan sa. Hannu yakai zai fizge drip din Ammei ta rike hannun tare da girgiza masa kai, fuska ya shagoɓɓe kamar zaiyi kuka Mama ce tace "haba Majeed Please ka barshi ya ƙarasa". Ba tare da yace komai ba ya koma jikin fillon ya lafe tare da lumshe ido. Cikin yan mintuna drip din ya ƙare bayan Youseef ya cire maa drip ɗin taimaka masa yayi ya mike domin watsa ruwa yayin da tuni Addah tasa Finnat haɗa masa ruwan wankan, kai tsaye bathroom ɗin su nufa a dai-dai kofar bathroom din Youseef ya tsaya yayin da shi kuma ya ƙarasa da kansa. Gaba ɗaya fita suyi a bedroom din su koma parlourn ƙasa yayin da akabar Auta tana gyara masa ɗakin sai Zaituna da taki fita a cewar ta zata taya su. Harsu gama bai fito ba dan haka Auta ta kama hannun ta su fice. Fitar su ba daɗe wa ya fito sanye cikin bathrobe ash color inda kai tsaye colose ɗin sa ya nufa. Tsaf ya fito cikin jallabiya fara tar sai wannan farin mayafin Irin na Larabawa da suke sawa musamman in sun sa farar jallabiya. Tsaf ya fito kam gaban mirror ya matsa bayan ya gama ma kansa barin fitinannun turarukan sa masa masu mukar daɗi ga sumar sa datasha mutukar gyara ta kwanta a gadon bayan sa kace balarabe ne tsaye a gaban mirror. Fuskar sa tayi fayau irin na mara lafiya. Kai tsaye parlourn ƙasan shima ya nufa zaune ya samu su a parlourn inda tunda ya sakko shi su zuba ma ido fuskar su fal mamakin shi, mutumin da bashi da lafiya ne ke cikin shirin tafiya masallaci, duk dai da shi dama haka yake komai ciwon da yake mutukar zai iya tashi yayi tafiya toh fa ba abinda zai hana sa zuwa masjid. Sannu su ciga ba da jera masa inda hannu kawai ya ɗaga musu kai tsaye kusa da Ammei ya nufa tare da ɗaura kansa a kafadar ta inda yake magana ƙasa-ƙasa dan shi kowa yasan indai yana ciwo toh fah a zumin magana yake. Ammei ce ta umarci Auta data haɗa masa abincin saboda ko karya wa baiyi ba. Nuni tayi masa da dinning area akan yabi bayan Auta fuska ya shagwabe kamar zai kuka inda ita ma ta daure tata fuskar tare da ɗauke kanta, dolle yasa yabi bayan Auta shidai Youseef na boye dariya. Koda ya gama cin abincin sallama ya musu domin ta fiya masjid addu'a sosai Ammei ta bishi da ita inda dai-dai zai fita yaci karo da granny. Baya taja tana ƙare masa kallo daga sama har ƙasa kana ta fara tambayar sa shida bashi da lpy ina kuma zashi amsa Youseef ya bata da masjid zasu aiko fah nan ta fara faɗa yadda ta shiga ba nan take fita ba shiko Majeed tuni yayi gaba abin sa. Shima Youseef bayan wayan daya mata yabi bayan sa inda tuni driver ya fito da dalleliyar sabuwar motar da zasu tafi da ita.........................✍️ Typing📲* _Follow my WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _Follow my WhatsApp group_👇 https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 *✨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION ✨* *T.M.W.A✍️* *Amanar taurarin marubuta writer's.......✍️* *TEAM HAZIKAI BAKWAI 💪✨* Page. 4️⃣4️⃣➡️4️⃣5️⃣ ...............*RANA BATA KARYA INJI MASU IYA MAGANA SAI DAI UWAR ƊIYA TAJI KUNYA* Na yarda da batun masu hikimar zance. Domin kuwa nima da kaina na yarda wannan rana tawace kam. Sannan in har Mom na amsa sunan uwa a gareni to taji kunyar kuwa. dan ko yau take Jumma'at ranar da donbin mutane da yawa ke so da jinkirin jiran zuwan ta toh yau fah gashi Allah yayi. Kowa ka gani na dangin na wannan ranar ya tashi ne cikin farin ciki inka cire Mom da ita da maƙaraban ta dan a kallo ɗaya zaka mata ka gano tsantsar tsagoron hassada a shimfide a saman tam fatsetsiyar fuskar ta da kwata-kwata a cikin ba alkairi. Misalin ƙarfe 10 daka shigo anguwar dole ka shaida ana biki danfa ta fara cika, dan ma ɗaurin auren sai bayan an saukko daga sallar juma'a za ayi. Amma duk da haka anguwar ta cika haka gidan ma ko ina cike da mata. Ɗakin Ummi aiko cike yake da baki manyan mata wanda daka kalle su kasan eye lallai nera tayi kuka a jikun nan su dan yadda Ummi take yar gayu yar kwalisa haka mutane nata suke. Daga can tsakar gida kam taro yay taro gida ya kacame da hayaniya irin ta biki, anan ɗakin ƙawayena na zagaye dani. Wasu na hotuna wasu na kwalliya, dan yan gurin aikin mu su min kara sosai wasu daga cikin su duk sun zo, wasu na hirarsu akan batun dinner da za'ayi bayan an kai amarya. Dan can gidan su Suraj ɗinne suka shirya. Luba ce da Mamy (maman Isha) su sani na shirya bayan wanka dana sake sha da wasu turaruka Allah ni kaina na fara gajiya da kamshin nan yayin da su Buhaisa sai yabawa suke. Tsaf a shirya ni cikin wata fitinanniyar shadda Read color dataji uban aiki ga wasu stonos sai walwali suke yadda ɗin kin ya zauna daram a jikina zaka tabbatar da eh lallai nera tayi kuka, dan ko kusan yadda Jan abu yake ma fara fata kyau. Ga wani fitinannen ɗauri da ta kashe minshi mutukar zaunuwa ɗaurin ya zaunu, fannin sarka da 'yan kune da bangles ba'a magana sai plat shoe da shima ya kasance Ja mai shegen kyau da tsada dana sa aiko ba karamin kyau ya sake yiba kasan cewar jan lallin dake zane radam a ƙafa ta sai bakin daya kasance kadan, wani irin mayafi ne shima daya kasan ce Ja mai shara-shara sai fararen Stones dasu mishi ƙawanya inda kai tsaye a kaina a ɗaura min shi amma bai rufe fuska ba andai sakaya minshi ajikin ɗaurin da akai min. Aiko na fito fes dani kamar fure a tsakiyar lu'u lu'u. nan take hasken Camera na waya ya shiga kaikawo akaina hatta mai kwalliya tamin pics iri-iri nikam araina ji nake kamar na fisge wayar na goge su. Nan take wasu suce sai sun tura ma ango ciki koh harda Buhaisa ban tanka musu ba sai murmushi kawai d nake yi dan lokacin tuni su Mamy sun fice da gani sai ƙawaye na dasu sani a tsakiya tabbacin daka shigo zaka sheda amarya sai kuma mai makeup da itama sai gobe zata koma Abuja saboda Luba ta dakko tane har sai bayan an gama biki zata koma. Shiyasa itama tana cikin jerin ƙawayen Amarya kafin lokacin kuma dinner. Kiran da Yah Ansar yazo yamin ne ya sakani saka gyale na rufe har fuskata. Shine ya kama hannuna har falon baƙi. Tunda muka fito kuwa gidan ya sake ruɗewa da buɗe-buɗe. Ni dai kaina na ƙasa a cikin gyale dan haka kawai sai naji ina jin kunya kowa. Ban ida daburcewa ba sai da muka isa falon baƙi. Dan ganin kaf kawunaina na ɓangaren uba harda Abba da Abban su Buhaisa. Sai gwagganni da innoni suma dai duk suna nan na kusa sosai, saboda a gaskiya ta dangin Abba muna da family sosai. A tsakkiyarsu Yah Ansar ya zaunar dani ƙasan carpet. Shima sai ya nema waje ya zauna. Kawu Bala ne ya fara min da nasiha mai ratsa jiki. Kafin sauran ma su dinga karɓa ɗaya bayan ɗaya. Daga baya suka koma faɗa da gargaɗi, yayinda ni kuma nike sharɓan kuka ta cikin gyale. Dan babu abinda ya tadamin hankali sai jin muryar Yah Ansar na rawa alamar karaya sanda yake min addu'ar zaman lafiya a gidan aurena. Abba ma dai yamun tasa a taƙaice, daga baya kiran wayarsa da akai ya nema excuse ya fita, da alama kuma kiran da akai masan nada matuƙar muhimmanci ne. Dan naga sai da ya fara magana da Kawu Bala suka miƙe tare suka fita. Fitar tasu bai hana iyayena cigaba da mun nasiha ba, sai da suka gamsu sun min yanda suke buƙata kafin suka sallaman Inna Binta ta kamani ta maidani ciki, dan mazan zasu wuce massalaci ne daga can kuma za'a ɗauro aure. Dole sai da aka sake min kwalliya bayan nayi sallar azhar saboda na ɓata fuskar dan kukan da nasha. Kaya na canja zuwa wani fitinannen less Green daya ji uban ɗinki dan uban su doguwar riga. Ga ƙamshi irin na amare ƴan ƙwalisa ina zubawa. Acan ƙasan zuciyata kuwa jina nake duk wata iri kamar yanda aka san duk amarya da shiga irin wannan yanayin a irin ranar nan. Lokacin da ƙarfe biyu ke cika maza suka fara dawowa alamar an ɗauro auren gabana sai ya shiga wani irin luguden daka da sauri-sauri. Wani irin tsoro da fargaba na ratsa min cikin ɓargo da jijiya har ina jin wani kalar sanyi-sanyi duk da kuwa uban zafi ake zugawa a gari. Ƙawayena sun shiga min shaƙiyanci da buɗa a saman kai, dan Buhaisa da uban gudu ta shigo bedroom din tana kwalla kiran sunana harga Allah na ɗauka wani abun ne ya faru aiko cikin sauri na mike ina tambayar ta meke faru wa, ai bata tsaya bani amsa ba sai rungume Ni da tayi tana faɗin "Sisy nah an daura" sai kuma ga Isha dasu Yasmeen gaba ɗaya sai suka haɗa ni su rungume ni suna murna, sai na samu kaina da sakin hawaye masu zafin gaske da ban san dalilin yinsu ba. Shin murna da farin cikin mallakar matashin saurayi ƙyaƙyƙyawa ɗan ƙwalisa mai cikar kamala da dattako irin Suraj ne, ko kuwa fargabar rabuwa da ƴan uwana ne. a lokacin sam na kasa ganewa. Na gagara banbance komai a yanda ya dace na fahimcesa. Sai ma wani sabon bugun zuciyar da na sake ji sakamakon shigowar aunty Fatima kamar a firgice tana kiran Ummi data shigo tana miƙamin fura a kofi da aka dama wai na sha. Koda Ummi ta tambayeta lafiya, sai tace mata su Kawu Bala ne ke kiranta kuma sunce tai sauri dan kamar dai akwai wata matsala. Da saurin kuwa ta fita alamar itama tana a cikin ruɗanin ne.. Na cigaba da zama kamar butun butumi a tsakkiyar ƙawayena daketa hotuna abinsu batare da su sun fahimci kamar akwai abinda ke faruwa ba. Danni su Buhaisa harsum isheni da hotuna dan tun ina biye musu harna koma na zauna. Muna nan dai hayaniyar gidan na sake ƙaruwa alamar mutane na sake cika gidan ƙananun magana suka ɗan fara fitowa. Sai dai anƙi a fito da komai a fili ana ta son basar da mutane dai. Abinda ya ɗan fara tsayamun a rai shine rashin zuwan Suraj gidan. Dan a burikan mu akwai zuwa hotuna bayan ɗaura aure da yace zasuyi shi da abokansa da kuma ni da ƙawayena da ƴan uwana. Amma dai zuciyata nata tausata akan masa uziri, dan maybe mutane sun masan yawan da hakan bazai yiwu ba ya cika wannan alƙawarin. Wannan tunanin yasa na danne zuciyata na ajiye wannan batun a gefe. Isowar masu kiɗan ƙwarya karfe 4:00pm bayan hotunan da aka gama yi tsakanin duka family na mu. yasa Anty Fatima zuwa ta fita dani a ɗakin ni da ƙawayena. Sosai gidan ya cika da mutane har sai da naji ƙwalla ta cika min ido. Dan tunowa da nayi da Ummah. Ko a wajen kiɗan ƙwaryar ma duk da ba rawa nake ba tsaye kawai nake tsakiya ƙawaye na da su Buhaisa ƴan uwana masu rawar zagaye da ni sai da dinga shigowa ana min liƙi, wasu kuma sukanyi hoto dani a waya harda masu video. Kusan karfe Biyar sai ga Ummi riƙe da hannun Yah Saif da Yah Ansar wai sai sun min liƙi. Kallo ɗaya na musu su duka biyun na fahimci sunyi kuka. Dan idanun Yah Ansar jajur suke. Na Yah Saif kuwa har sun kumburo saboda fari ne kamar Buhaisa. Hankalina ne ya tashi a take nima idanuna suka ciko da ƙwalla ina binsu da kallo. Amma sai suka ƙi yarda mu haɗa ido sai liƙi da sukemin kawai ana ihu kawunansu a ƙasa suna murmushin da ni kaɗai na fahimci na yaƙe ne. Duk yanda naso riƙe kukan nawa hakan ya gagara, bamma san sanda na riƙo hannayensu su duka ba cikin nawa. Dole suka kalleni a tare. Kukan na sakar musu kawai na faɗa jikin Yah Ansar. Shima sai Yah Saif ya rungumemu mu duka biyun yayin da Ummi ta haɗe mu duka ta rungume aiko a tare mu saki kuka mai tsuma zuciya. A take wajen yay tsitt, wasu na ganin mun birgesu da fassara abin namu da tsananin shaƙuwa ne da soyayyar juna. Wasu ko da suka san wani abu dake ɓoye sai suke jin tsananin tausayinmu da jin karaya suma. Nan take aka ringa tuno alkairan Ummah gare su nan masu share kwalla nayi kukan zuci nayi da musu addu'a. Dole dai Yah Ansar ya jamu muka fita daga filin Saboda gaba ɗaya kuka ya sarke Ummi dan ba abinda take tunowa sai yar uwar tata. Nan Mama Hadiza ta jamu zuwa ɗakinsa ta dinga lallashinmu da mana nasiha. Haka kawai maganganun nata sai suke ta min kai da kawo dan na gagara fahimta da fassara wasu nikam. Kiran Yah Ansar da akai a waya ne ya sashi miƙewa ya fita. Babu jimawa ya dawo yay kiran Yah Saif suka fice.. Acan ƙasan zuciyata kam ina jin babu daɗi saboda rashin ganin duk jama'ar gidan a cikin sha'anin bikin nawa. Dan yaran duka babu wanda na gani har Baby da su Yah Safwan Gara ma ita Mom ɗin bayan ɗaura aure sanda Yah Ansar yazo ya fita dani ɗin nan zuwa falon baƙi na ganta ita da wasu ƙawayenta a tsaye sunata faman dariya da alama akwai abinda suke tattaunawa a tsakaninsu............... ___________🤍🖤 *Abuja* ..........A hankali mutocin nashi ke dai-dai parking a parking lot din dake gidan, cikin sauri Muktar ya fito tare da buɗe ma Boss din nasu kofa. Bai ɗau wani lokaci mai tsayi ba ya fito a motar, kamar yadda ya fita cikin kayan nasa irin na larabawa duk da shima tamkar balaraben yake haka yanzu ma cikin su ya dawo duk dama masallaci Jumma'at suka je. Kamar ɗazun dai haka ma yanzu fuskar tasa take a tamke kwata-kwata ba fara'a a cikin ta. Amma duk da haka baka isa gane cewa yana da damuwa duk dai da haka yake ko yaushe fuskar sa ba fara'a, su kansu yaran nasa sun lura Boss din nasu bashi a yana yin walwala yau kasan cewar sun sanshi kamar yunwar cikin su. Dan yau ko gaisuwar da suke mishi bai amsa ba illah hannu kawai ya ɗaga musu. Muktar ne dake wannan tunanin a zuciyar sa ya dawo ganin harma ya nufi kofar main parlour yayin da Youseef ke biye dashi. Kofar ya buɗe da kansa kana ya tura kansa ciki tare dayim sallama ciki-ciki. 'yan matan gidan ne kawai zaune a parlourn ko wacce da abinda take yi, kamshin turaren sane sai kuma sallamar Youseef dashi yayi da karfi ya fargar dasu cewa sun dawo. Duka ido su zuba ma Yayan nasu ko wacce a cikin su da irin tunanin da take. Sannu da zuwa su masa inda tunkan dama ya iso ya gama ƙare ma kowa a cikin su kallo hannu kawai ya ɗaga musu yayin da su shiga gaida Youseef daya samu guri shima ya zauna a ɗaya daga cikin kujerun parlourn. Amsa musu yayi da kula wa yayin da Majeed ya haura upstairs part din Ammei. Zaune ya same ta a bedroom din ta kan abin sallah da alama addu'a take dan ita Ammei haka take idan tayi Sallah kafin ta tashi a gurin sai ta dau lokaci mai tsayi. Zama yayi harta idda addu'ar kana ta tashi ta zauna a kujerar da yake, ƙasa ya zamo ya zauna dabas akan lallausan cafet ɗin dake shimfide a ɗakin kana ya ɗauki ƙafarta ya daura akan cinyarsa yana mata tausa. Murmushi kwance a fuskar ta a hankali ta ɗaura hannun ta akan lallausar sumar kansa me kama data larabawa kasan cewar tun shigowar sa ya cire naɗin dake kansa. Jin hannun nasa sanyi kanshi kuma zafi yasa ta tabbatar har yanzu da sauran ciwon, shiru suyi na wani lokaci ba me magana a cikin su. "Abdulmajeed" Ammei ta kira sunan sa cikin nutsuwa, jin yadda mahaifiyar tasa ta kira full name ɗin sa dan zai iya rantsewa tunda ya girma bai taɓa jin ta kira full name ɗin sa ba. Tashi ɗaya ya dena mata tausar kana ya juya gaba ɗaya yana fuskantar mahaifiyar tasa tare da maida Hankalin sa gaba ɗaya kanta. Kana ya amsa da "Na'am" yana zuba mata rikitattun idanun sa dasu kade su koma jajur. Saida ta sauke ajiyar zuciya kana. tace. "Meke damunka ne haka har wannan ciwon ke ƙoƙarin kama ka Majeed?". Saida ya sauke ajiyar zuciya kana ya ɗauke idanun sa akan ta, shidai harga Allah bai iya karya ba sam dan baima san yadda ake yin ta ba dan haka ya zaɓi yayi shiru. Jin yayi shiru alamun baida ta cewa kenan yasa ta sake cewa. "Majeed dakai fah nake". Kai ya langabe kana cikin silent voice din sa yace "Ammeiii". Ya idda maganar yana langab'e kai alamun baya son maganar, dama tasan da wuya ya faɗa yasa ta sake cewa. " Answer me Majeed". Fuska ya bata kana yace "Please Ammei tell me meya ce miki?". Shiru tayi tana kallon sa ba tare da tace komai ba hakan ya bashi tabbacin ba zata ce wani abuba kenan, shiru shima ya sake yi na wani lokaci yana tunani kana yace, "I swear to God, but I don't know what's wrong with me." Ajiyar zuciya kawai ta sauke tare da ce komai ba "Okay bari Dadyn ku ya dawo dan ɗazu yake cemin zasu taso yanzu na kirasa wayan sa bata shiga. "Tom Allah ya sauke sa lafiya". Da "ameen" ta amsa kana ta bashi maganin sa daga nan kuma downstairs su sakko domin yin lunch. Bayan gama lunch din ya wuce part d'in sa Youseef kuma ya fice. Ammei ce zaune ita da Auta suna tattaunawa akan batin ciwon Majeed, cike da damuwa Ammei ke cewa. "Wllh sam na rasa meke damun Yayan naku har wannan ciwon ke ƙoƙarin kama shi". Ajiyar zuciya Auta ta sauke kana itama cikin damuwa tace, "Ammei abinne abun tunani amma fah kinsan me nagani ɗazu kuwa a ɗakin sa?" Kallon ta Ammei tayi kana ta girgiza kai alamun a'a, "Humm Ammei kinsan hoton wa na gani akan screen ɗin system ɗin shi?" kai Ammei ta girgiza tana kallon Auta kana tace "Hoton wa ki gani?" Saida Auta ta sauke ajiyar zuciya kana tace, "Wallahi Azim Ammei hoton Safiyyah na gani a jiki sanye da hijjab da facemark da eyeglasses". Shiru Ammei tayi tana tunanin wacce Safiyyah kuma dan ita harga Allah bata gano Safiyyahn da Auta ke nufi ba. Kafin itama cikin sauke ajiyar zuciya tace, "Wai Auta wacece kuma Safiyyah kin sani a duhu?". Fuskar Auta cike da damuwa tace, "Ammei Safiyyah fah ta Haske TV wacce ake bikin ta yau". Shiru Ammei tayi kamar mutum mutumi tana kallon Auta cike da mamaki a zuciyar ta koh tunani take, meye haɗin sa kuma da Safiyyahn batin tasan shi sam mata basa gaban sa?. Taɓa ta da Auta tayi ne yasa ta kauda kanta a kallon ta kafin tace, "kin tabbata Auta?" "Wallahi Ammei kafin nazo kiran kune ma na kashe ta kinsan matan gidan nan da yan sa ido". Kai kawai ta gyaɗa ma Auta ba tare da ta sake cewa komai ba a zuciyar ta tace ai aikin gama ya riga daya gama tunda ta zama matar wani. Daga nan shiru ta biyo baya Ringing din wayar tane ma ya katse mata tunanin data tafi. *ASADI* sunan dake rubuce akan screen ɗin wayar a lokacin da Auta ta miko mata dan tasan Dady ne, ita wancan tunanin ta ture kana ta maye fuskar ta da murmushi kana ta ɗaga. Sanar da ita cewa gashi a gida yasa tunkan ta mike Auta ta fice da gudu kamar wata ƙaramar yarinya. Murmushi kawai tayi kana ta aje wayar itama ta nufi downstairs. Dai-dai isarta cikin parlourn shi kuma yake shigowa yayin da dagudu Auta taje ta ɗafe shi. Cike da farin cikin da ya kasa ɓoyuwa a fuskar Dady yake shafa kan Auta yayin da su Basma ma suzo su rungume shi, cikin parlourn ya ƙaraso kasan cewar yau ba wasu mutane a mai parlourn sai ɗai ɗai kun yan matan gidan ne a ciki sai kuma Hajja Mummy da dama ita ta fison zaman Main parlour kodan tayi sa idonta yadda take so. Kasan cewar duk wanda zai shiga ɗaya daga cikin part d'in gidan saiyabi ta nan parlourn. Cike da farin cikin ganin ɗan uwan nata ta dan dama dakon jiran dawowarsa take yi ganin tuni tama Yayan nata magana akan haɗa auren Majeed da Zaituna amma shiru takeji kamar ma Yayan nata ya manta da maganar, shiyasa yanzu jira take zuwa anjima taje ta sake samun sa da maganar dan taga alamun inba da zafi-zafi tayi ba sai abun ya gagare ta dan yaron nan sam baida mutunci. Kuma tunda tama 'yar ta alqawarin auren sa dole ne saiya aure ta, dan baida matar data wuce Zaituna. Ajiyar zuciya ta sauke bayan ta dawo daga duniyar tunanin data tafi tamishi sannu da zuwa, yayin da shi kuma ya haura sama domin watsa ruwa. Bayan gama kintsawar Dady dan yace shifa baya jin yunwa a koshe yake. Ya shirya Meeting a babban parlourn dake part d'in sa. Jin batun meeting d'in da Dadyn ya shirya kuma bama a part d'in granny ba a nashi parlourn yasa kowa hallara da wuri dan dagaji magana ce mai mahimmanci kuma gashinan yace dukan su harma da yaran. Granny ma tuni ta kintsa ta nufi part d'in Dadyn kasan cewar suma mazan gidan na nan wato su uncle Abdallah Dan tun Around 4 suke dawowo daga gurin aiki ranar FRIDAY. Gaba ɗaya parlourn na Dady a cike yake dan fa kowa ya hallara harda Youseef inka cire masu aiki kawai sai kuma Majeed da dama shi sai yayi African time. Dan har uncle Kabeer dake Saudiyya saida a kira ta video call a babbar system ɗin dady dake parlourn. Saida Dady ya gama bin kowa da kallo yaga ba Majeed kana ya ɗaga wayar sa yayi kiransa, ba'a wani dau lokaci mai yawa ba ya iso sanye cikin t-shirt fara tas sai Black Jen's, sumar Nan tasha gyara danko ta kwanta luf a bayan sa, babu abinda yake sai kamshi turaren nasa mai saka nutsuwa. Gurin zama ya nema ya zauna ɗan nesa da Dady kana ya gaida iyayen nasa cikin girmamawa, suma su amsa mishi da kulawa tare da masa ya jiki, dama tuni Dady yasan Majeed ɗin bashi da lafiya kasan cewar Dr Fadil ya kirasa ya sanar mishi. Bayan buɗe taro da addu'a Dady ya fara magana. "Abdulmajeed!" Kowa jin yadda dadyn ya kira sunan Majeed ɗin yasa wasu da yawa ɗago wa suna kallon dady dan abune dabai saba faɗa ba. A ɓangaren Majeed ma haka take dan shi zai iya rantsewa da Allah tunda yake bai taɓa jin mahaifin nasa ya kira wannan sunan ba sai yau, dan haka ya tabbatar da maganar mai mahimmanci ce, a hankali ya ɗago kansa dake masa ciwo ƙasa-ƙasa ya zuba ma dady idanun sa tare da amsa wa da, "Na'am dady" saida Dady ya sauke ajiyar zuciya kana ya cigaba da magana yayin da gaba ɗaya parlourn ya sake ɗaukar shiru. "Menene matsayina a gurin ka?" Yadda dady yayi magana fuskar sa sam ba alamun wasa gashi ya kafe Majeed da ido, yayin da cikin tsananin mamaki kowa ke kallon Dady bare Majeed daya d'ago yana kallon dady, cikin sauke ajiyar zuciya yace. "Dady kai mahaifinane wanda bani da kamar sa aduk faɗin duniyar nan". Dady ya jinjina kai tare da sakin murmushin gefen baki kana yace, "Masha Allah Toh a matsayina na mahaifin ka na zartar da umarni akanka yanzun nan". Zuciyar Majeed na luguden daka cikin sanyin murya da a yanzu ta sake komawa ƙasa-ƙasa yace, "Toh dady wani umarni?". Kai Dady ya jinjina kana ya cigaba da magana. "A matsayina na mahaifin ka na tabbatar ko wanne irin hukunci na yanke a kanka yayi, dan na tabbatar kome na kawo maka na baka zaka riƙemin shi amana, ka kula dashi kuma ka tattale shi saboda abun daga gareni yake, Toh a yau aka ɗaura maka Aure". Gaba ɗaya parlourn ɗago wa suyi cikin tsananin kiɗima suna kallon dady, musamman Majeed da kirjin sa yayi tsawar hadarin gabas na tsakiyar ogosta😂 Atsorace Majeed yake kallon dady yayinda zufa keta ambaliya adukkan sassan jikinsa, ya daure cikin rawar murya ya ce, "dady aurefa kace?" Dady ya ce, "kwarai aure nace Majeed, kuma ina fata amatsayina na mahaifinka zaka yimini biyaya, zaka kuma karb'i k'yautar da ubangiji yay maka da hannu biyu, natsuwarka nake buk'ata da farin cikinka". Shiru Majeed yayi girjin sa na ciga ba duka. Amma ya kasa magana. Yayin da Mummy ta kafe dady da Kallon kiɗima. Cikin kakkausar murya tace. "Aure kuma Yaya". Ta idda maganar cikin zaro ido tana kafe dady da kallo. Murmushin gefen baki ya saki tare da lumshe ido ya buɗe kana yace. "Kwarai kuwa Zakiyya Aure" ruf zancen na dady ya rufema Mummy baki Dan fah ta gagara cewa komai. Ammei madai kallon dadyn kawai take amma bazaka iya tantance halin data shigaba na farin ciki ne ko akasin haka, haka zalika batai magana ba illah "Alhamdulilah alah kulli halin" data faɗa ƙasa-ƙasa. A zuciyar ta kuwa tana ai yawa shiyasa taga dadyn cikin farin ciki kenan. Wata guɗa da granny ta ranɗa da saida yasa Majeed toshe kunnen sa tare da ɗago wa yana wasa mata harara, daga nan bata sake cewa komai ba sai alhamdulilah da take ta faman jerawa. Youseef madai kur yama dady da ido dan abune yazo musu na bazata. Wai yau Boss amma auren dolle eh lallai akwai kallo🤭 Zaituna kam da Fennat da wasu daga cikin yan Matana a tare girjin su ya buga, yayinda daka kalli Zaituna data koma kamar wata mara hankali dan yadda take bin dady da kallo.😂 Danko wata zabura tayi tare da dafe girji. Finnat kam tama kasa ƙwaƙwaran motsi saboda yadda maganar dadyn ta dake ta. Addah ma shiru tayi kanta a ƙasa ba tare da tace komai ba. Mama kam murmushi kwance a fuskar ta take kallon dadyn dan itama kanta zaman Majeed ɗin haka yana damun ta kwarai da gaske. Anty Amarya kam wani makirin murmushi tayi tana kallon Addah, dan itafa da da dama tashi zatai ta rangad'a buɗa harma da taka rawa saboda murna..........✍️ Toh nima nace ba'a barmu a baya ba dole ne muma mu taka💃💃 Hummm☹️ inji mai ciwon hakori Readers yaufa ake yin ta🤭🤗 toh amma bari dai nayi shiru muje page 46 danjin yadda zatakaya masoya masu hanjin ligidi😂 *ONE LOVE GUYS ❤️* *Typing📲* _Follow my WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _Follow my WhatsApp group_👇 https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 *✨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION ✨* *T.M.W.A✍️* *Amanar taurarin marubuta writer's.......✍️* *TEAM HAZIKAI BAKWAI 💪✨* Page. 4️⃣6️⃣➡️4️⃣7️⃣ .................. Dady yacigaba da maganarsa yana nazarin kowannensu, dariya taso kubce masa lokacin da idonsa ya sauka kan yah Majeed d'in, amma saiya danne ya kauda kai yana murmushi. "Zaman Majeed ya isheni hakanan, Dan haka Na yanke hukuncin masa aure da mace tagari, wadda Na yarda da ingancin tarbiyyarta, irin macce da kowane namiji ko Iyaye keso ɗan so ta zama matar sa, ban hanaka anangaba idan kasami wadda kakesoba ka k'ara. Bawata bace dan koh itad'in ba kaman komai bace amma sai dai itad'in mai tarbiyya ce hankali nutsuwa gami kamun kai, kuma itad'in mace ta gari ce, dan haka saiku fara shirye-shiryen tarbar amarya". Gaba ɗaya parlourn ya dau shiru kace wanda mutuwa ta ratsa na wani lokaci yayin da Yah Majeed yayi ƙasa da kansa kai tsaye inka kalle shi zaka gane tsantsar tsagoron tashin hankalin daya shiga. Amma kansa a kasa amma dolene ka fahimci yana cikin tashin hankali da wannan sabon al'amarin. Mumy ko gaba ɗaya hankali yayi kaura daga jikin ta babbar tambayar ta anan wacece wacce aka Aura ma Majeed ɗin? kuma taya? Waɗan nan tambayoyin sune cike a cikin zuciyar ta kuma take neman mai amsa mata. Zaituna kam kai tsaye da ka kalleta zaka gane hankali yayi kaura daga gare ta, wai ace Yah Majeed d'in nata Wanda take mafarki da muradin ya zama mijinta, nata ita kadai dan batajin zata iya share nashi da kowacce irin mace, shine yau ake sanar da ita cewa ya zama na wata, watan da batasan ko wacece itaba. Wai wacece ma wannan? wacece ke ƙoƙarin rabata da RAYUWARTA? Wacece ke ƙoƙarin rabata da MURADINTA? Waye uban ta a ƙasar nan? harda take ƙoƙarin mallakar abu mafi muhimmanci a cikin RAYUWARTA?. Ammei dai shiru tayi dan bata da tacewa amma itama aranta tunani take wacece kuma dadyn ya Aura ma Majeed ɗin, tayi farin ciki sosai yanda taji mijin nata na yabon yarinyar hakan na nufin ta dace da ɗan nasu kenan, Allah ya bashi irin macen da take addu'a akan Allah yaba ɗan nata, duk da Safiyyah tayi masa sha'awa toh ita yanzu ta riga da ta zama amarya. Finnat dai baka isa gane ainihin yadda nata tashin hankalin ya tafi ba amma kai tsaye daka kalle ta kasan maganar ta taɓa ta ainun. Amma a baɗini zuciyar ta zafi take mata, haka kai tsaye tunanin ta irin na Zaituna ne akan shin wacece wacce aka Aura ma abun son nata? a kuma ina take? Waye uban ta a ƙasar? Wannan tunanin da amsar take jira ta samu, toh amma a ina zata samu kuma waye zai warware mata. Toh suma dai matan gidan kowa da abinda yake sakawa a zuciya yayin da tun gama maganar dady bayan granny da su uncle Abdallah sunyi magana tare da addu'ar Allah yasa alkairi. Su mama dasu Addah suma suyi addu'ar Allah yasa alkairi. Amma har suka gama Mummy da gaba ɗaya kamar ma bata a ɗakin batace komai ba, yayin da Majeed ke zaune a inda yake dan koh ƙwaƙwaran motsi bayi yake ba, ya zaune kamar mutum mutimin da aka dasa, kanshi a kasa. Auta ma dai suma sunji mutukar mamakin wannan magana kuma sun shiga tunani yayin da kowa a cikin su da irin tunanin da yake a zuciyar sa. Youseef madai saida dady ya gama magana kana ya ɗauke idanun sa akan sa ya maida kan Yah Majeed ɗin gaba ɗaya kana kallon sa kasan yana cikin tashin hankali. Dady daya gama nazarin kowa daga ciki ya ɗaura da cewa. "Yan uwana ina mai neman afuwar ku akan shishigin da na muku akan ɗan ku, duk da kune keda alhakin hakan. Amma ku sani bawai nayi hakan bane dan na nuna muku baku isa ba, a'a nayi hakan ne sai dan bani da yadda zanyi, abun ne yazomin a mutukar bazata kamar yadda kuma yazo muku, toh amma bani da yadda zanyi kunsan ance dama sau ɗaya take zuwa ma mutum, shiyasa nayi amfani da damata kafin ta kufce min, duk da dai ance matar mutum kabarin sa kuma wani baya auran matar wani. Toh bani da yadda zanyi face kawai a ɗaura kasan cewar bazan iya bari mace mai tarbiyya irinta ta kufce wa Majeed ba sbd samun irin su a yanzu sai an tona. Alhaji Ahmad amini gareni shine wakilin Majeed kasan cewar baku kusa dani a lokacin. Ina fatan zaku fahimce Ni kuma zakumin uzuri, Sannan insha Allahu amarya zuwa gobe za'a kawota, ku kuma a matsayin ki na iyaye mata saiku fara shirye-shiryen tarbar Amarya, Allah Ubangiji ya bamu ikon rike amanar da Allah ya bamu Allah kuma yasa alkairi acikin wannan Aure. Sai kuma kai Youseef, a matsayin ka na aboki gare shi kuma ɗan uwa saiku fara duk wani shirye-shirye da kusan ya kamata akan auren da kuma abun da zakuyi sannan duk wasu kudi ko wani abu da ake bukata kamin Magana dan ban lamunce ayi komai ba inbada kuɗi naba, sannan inaso ayi bikin irin wanda kowa zai sheda auran na *Abdulmajeed Abubakar Saraki*". Gaba ɗaya da ameen aka amsa har uncle Kabeer dake sauraren su ta video call da'a kirasa, kana su uncle Sulaiman suka ce, "Ai Yaya duk abinda kayi yayi dai-dai kuma shima Alhaji Ahmad ai tamkar mune dan ko auran waye daga cikin familyn nan yana da ikon amsa dan shidin ya zama kamar dan uwa. Dan haka komai ku yanke yayi muma kuma munji daɗi sosai Allah kuma ubangiji yasa alkairi yasa abokiyar arziki ce". Nan ma ameen aka amsa sai granny d tayi magana na irin farin cikin da Dadyn yasa ta a yau tare da saka masa albarka kana ta juya gun Majeed tana mishi tsiya. Dashi a yanzu gaba ɗaya ya dena fahimtar komai da suke cewa dan nutsuwa ma tayi ƙaura daga gangar jikin sa. Youseef ne daya gama lura da abokin nasa ya matsa kusa dashi dan kamasa ya tashi dan tuni dady ya sallami kowa shima shirin shiga ciki yake. Yayin da wasu harma sun fice cike da tashin hankalin da suke ƙoƙarin boye wa wasu kuma nasu ya gaza boyuwa, wasu kuma suna zaune darshan sun kasa tashi irin su Zaituna kenan da suyi sumar zaune. Da kyar Youseef ya taimaka ma Majeed su fice a part din dadyn su nufi nashi kasan cewar ma da kofar da zata kaika har part din Majeed ɗin daga na dady haka na Ammei ma haka, kuma wannan ɗin duk tsarin Majeed ɗin ne. Suna shiga part din nashi ya zame hannun sa daga na Youseef ya wuce sama, da kallo kawai Youseef ya bishi a zuciyar sa yace, "duk da irin tashin hankalin daka kalle sa zakasan yana ciki amma ba abinda ya sauya daga cikin yanayin tafiyar sa, dan inba farin sani kayi masa ba baka isa gane yanayin nasa ba, saboda shi ko yaushe dama mai tsare gida ne ga kwarjinin da yake dashi." Dawowa yayi daga tunanin daya tafi kana yace, "Allah sarki ko wacece ke shirin shigowa gidan nan, harna tausaya miki". Ya idda maganar shima yana ficewa daga part din Dan bashi lokaci ya huta. Ko zai samu nutsuwa. A ɓangaren Majeed kuwa koda ya shiga bedroom d'in sa kai tsaye bathroom ya shiga inda ya shige ƙarƙashin shower yana sakarma kansa ruwan sanyi, duk da yamma ce kuma da ɗan sanyi-sanyi a garin haka ruwan ke sauka tun daga kansa zuwa ƙafarsa. Ya daɗe a bayin kana ya ɗaura alwala ya fito, yafad'a saman gado yana dafeda kansa dake masifar sara masa🤦‍♀, jiyake tamkar zai rabe biyu Dan ciwo. ___________🖤🤍 *Kaduna ✨* A hankali kana nun maganganu suka fara tashi a gidan, saboda shiru har gurin karfe 8:30 na dare ba'azo ɗaukar amarya ba. Nikaina shirun na Suraj ya fara damuna saboda gaba ɗaya kunin yau bai kirani ba duk wasu alƙawaruruka damuka daɗe muna shirya wa akan wannan ranar amma ba wanda Suraj ya cika. A hankali wasu hawaye su gan garomin na fargabar wannan halin da Suraj ya ɗauka, duk da ta wani fannin na zuciya ta na masa uzuri wani kuma ya kasa masa sam. Hannu nasa na share hawayen kafin wani daga cikin su Buhaisa ya lura na sake gyara kwanciya ta ina sauke ajiyar zuciya. ★★Luba ce ta haɗamin ruwa mai zafi da kayan turaren ƙamshi a ciki nayi, koda na fito da taimakon Ummi na kimtsa jikina. Ta kuma tsareni sai da naci abinci da wani nama na musamman mai romo a cikin kula. Naman yayi daɗi dan haka na saki jiki naci sosai, koda tace sai na cinyesa ma ban musaba na dage na cinye nasha romon. Hakan yasa cin abincin bai armashi ba garan sosai. Tun ina kallon agogo harna daina. Sai dai a raina inata mamaki, dan tara dai-dai ya kamata ace muna a wajen dinner. Amma gashi anan har taran yama wuce ba'a kaini gidan su Suraj ba balle ai batun zuwa dinner. Kayan da Ummi ta banine tare damin umarni dana sa yasa ni kallon ta, ganin yadda fuskar ta take a sani amsar kayan kafin nace komai tace, "Amshi kisa Safiyyah ba yau za'a kaiki gidan kiba sai Allah ya kaimu gobe". Daga haka ta raɓani ta wuce ba tare da ta bani damar tambayar taba. Da kallo kawai na bita harta fice a bedroom din kafin na dawo daga tunanin dana tafi, Buhaisa tazo tana min irin wasan damu saba tana kara tonona, "Kaga amaryar tamu wato ke dan ance zaki ƙara kwana ɗaya damu kafin a kaiki shine kike wani jin haushi koh? Toh bari inje in faɗa ma Ummi ko Yah Ansar ince kefa kin kosa alfarma ma da amiki bakiso, kinfi so kiji ki cikin jikin Angonk......". Dukan dana kai mata ne yasa ta kasa ƙarasa maganar ta fice da gudu tana dariya, binta nayi nima har parlourn inda su Ummi ke zaune suna hira. Bayan Ummi taje ta labe tana min gwalo. Cikin shagwaɓa nace, "Ummi kin ganta koh". Hannu na Ummi ta kamo ta zaunar kusa da ita tana faɗin, "zonan baby inji meke faruwa meya haɗa ki da bestien taki". Labari naba ma Ummi yadda mukai da Buhaisa itako Ummi cikin kunshe dariyar ta tace, "Kinji baby rabu da Buhaisa so take kiyi kuka maza jeki ƙarasa shirin ki kizo muyi hira". Cikin jin daɗi na daga mata kai kana natashi na shige ciki ina hararar Buhaisa data koma kusa da Mamy, Isha kuwa na gefa tana mana dariya, anty Hajara kuwa cewa tayi, "Dama ku ako ina saikun raba hali kwa karanta" baki itama na murguda mata na shige, na barta itada Buhaisadan nasan dama ba kyaleta zatai ba. Koda na shiga gaba ɗaya yan matan ko wacce da abinda da take masu chatting nayi masu waya da babyn su nayi. Ni gaba ɗaya mamaki ma nake ganin duk cikin su ba wacce tamin zancen rashin tafiyar mu yaudin a zuciya ta nace maybe sun sani ne, zancen na ture gefe na wuce na karasa shirya wa cikin doguwar rigar da Ummi ta bani. Bata da nauyi dan irin mai bin jikin nan ce, tsaf na gama shirya wa bayan nasa turaruka na masu shegen kamshi na fito parlourn inda na same su ana hira, toh nima zama nayi anayi dani cike da Nishaɗi. Bamu farga ba hirar ta ɗauke mu lokaci mai tsawo dan sai kusan ɗaya da wani abu Ummi tace mu shiga ciki mu kwanta, haka mu tashi mu shige ciki kamar kar a dena danni yanzu kwata-kwata banson ma goben tayi dan haka kawai dana tuna da goben za'a kaini gidan su Suraj sai naji gabana ya faɗi na rasa dalili. Koda mu shiga cikin tuni wasu daga cikin su Yasmeen sunyi bacci ƙalilan ne masu chat, toh nan ma maimakon mu kwanta sai a dasa da wata hirar irin ta ƙawaye da yan uwa. Mun daɗe muna hira daga baya kowa yayi bacci yayin da nidai kawai na kwanta ne amma baccin ya daɗe bai ɗauke niba dan bayi ma nashiga na ɗauro alwala nazo na tada sallah, sai gab da asuba wani bacci mai cike da mafarkai kala-kala yazo ya ɗauke ni. _____________🖤🤍 *Abuja 🤍* .................Tsaye yake a cikin garden daga can gurin wasu irin flowers masu kallar green da white gaba ɗaya sun ma gurin ƙawanya dan komai girmanka kaje gurin la zauna ba wanda ya isa ya ganka koda kuwa ace da rana ne balle kuma ace da dare ne. Gurin kwayar yake da hasken wuta wanda itama ta kasance green mai dan duhu-duhu, ba abinda yake sai kaida komowa acikin garden din alamu sun nuna da wanda yake jira. Kusan 5 mintues saiga wani nan yana shigowa ta kofar baya, yadda take tafiya ne da yanayin suffar jikin ta yasa na gane cewar ashe macece. Sanye take cikin shigar bakaken kaya sai wani uban hijjab data sa shi tun daga sama har ƙasa ya rufe nata sai bakin facemark shima data rufe fuska, ga wani uban glass da komai sa idon ka baka isa gane wacece ba, dan komai na jikin ta baka iya gani har tafukan hannun ta a sakaye suke cikin safar hannu. Tunkan ta ƙaraso gurin ya zuɓe ta da kallo harta iso, shiru suyi na wani lokaci alamun kowa da abinda yake sakawa a zuciyar sa kana ya fara magana cikin tsananin ɓacin rai haɗe da fushi. "Haka mukai dake ya kike so komai da mu shirya yake ƙoƙarin kubuce mana batare dana shirya hakan ba? Ko kinsan wannan auran shine plant ɗinmu mafi mahimmanci daya kamata ace munyi amma yana ƙoƙarin kubuce mana?" Saida taja numfashi kana cikin dake muryar ta Hadi da sakaya ta tace. "Musalta maka irin tashin hankalin da ɓacin ran dana shiga bata lokacine a wannan bakar ranar da naji cewa wancan makirin uban nasa ya aura mishi yarinyar da sam bamu san ma daga ina take ba. Ya ruguza mana gaba ɗaya shirin mu shiyasa nayi gaggawar kiran ka dan sanin mai ya kamata muyi kafin su ƙarasa ruguza mu". Kafeta yayi da ido harta kai arahe kana shima cikin fushi yace. "kinga duk matsalar kice wannan inda ace tun wuri kin sanar dani meke faruwa a wannan gidan naku da tuni munsan me zamuyi. Kinga yanzu munyi plant A yayi kyau plan B ya ɓaci plan C ma haka toh kinga dole mu tafi plant D mutukar muna so mu cinma burinmu". "Wannan haka yake Yash toh amma yanzu meye shirin namu na gaba?". Wata dariya yayi kana yace, "Matso kiji dan wannan sam bana wasa bane dan yanzu ne za'a fara wasan wancan duk wasan yara ne hhhhh". Ya idda maganar yana sakin wata dariya, dariyar itama ta taya shi. Toh daga nan ban sake jin mai kuma suke cewa ba dan duk Yadda zanyi naji na kasa, haka na tattaro alkalami na nayo waje🤭😂.........................✍️ *Typing📲* _Follow my WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _Follow my WhatsApp group_👇 https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 *✨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION ✨* *T.M.W.A✍️* *Amanar taurarin marubuta writer's.......✍️* *TEAM HAZIKAI BAKWAI 💪✨* Page. 4️⃣8️⃣➡️4️⃣9️⃣ ~AMMEII~ ..............Zaune take a makeken bedroom din na dady a wata kujerar da ke cikin ɗakin wanda ajesu dan hutawa kawai, yadda ta zuɓe dady da kallo dake kire-kiren waya yana sanar musu da bikin Majeed ɗin gobe ne yasata a mamaki. Duk abinda take hankalin sa na kanta kuma yana kallon ta, saida ya gama ya dawo da hankalin sa gaba ɗaya zuwa kanta, hannun ta ya kama kana cikin sayin murya da kwantar da hankali yace. "BILKISU!" A hankali ta ɗago da idanun ta tana kallon sa fuskar ta ta ƙawata da murmushi kana cikin sayin murya ta amsa da, "Na'am ASADI" Saida ya sauke ajiyar zuciya kana ya cigaba da cewa. "Please inason ki kwantar da hankalin ki akan batin auren nan nasan ki Bilkisu nasan ki da hakuri gami da kawaici Please Bilkisu ki daura a yadda na sanki, Auren nan anyi shine bisa wasu dalilai nawa da Ni kadai nasan su kuma insha Allah bazata bamu kunya ba. Dan haka Inaso ki kwantar da hankalin ki Ni nasan tunanin ki akan wacece wacce na aura ma ɗan ki ya take? wannan tambayar nasan itace a cikin zuciyar ki toh ki ajeta zuwa gobe insha Allah zaki sani, kuma nasan zaki mutukar farin ciki haɗi da jin daɗi dan haka ki kwantar min da hankalin ki kinji Bilkisu nah". Dady ya idda maganar murmushi kwance a fuskar shi yana kallon Ammei, itama da murmushin a fuskar ta tace, "Tabbas hakane tambayar dake a cikin zuciya ta kenan kuma Ni nasan bazaka zaba mishi wacce bata dace da shiba sai dai ina tsoran halin Majeed Dadyn su kasan shi, kasan yadda ya tsani mata sai naga kamar bazai amince ba". Saida dady ya nisa kana fuska ɗauke da murmushi yace "Bilkisu kenan amincewa kuma ta nawa kinsa Majeed da biyayya balle kuma wannan umarni na ne wanda tun yana ƙaramin shima baya tsallake wa balle yanzu daya girma na tabbata koda ace Youseef nama auran nan zai amsa da hannu bibbiyu balle Majeed". "kayi hak'uri Alhaji bahaka nake nufiba wlhy, ina farin ciki da umarninka, ALLAH kuma yasanya alkairi, wlhy tun kafin naga yarinyar ma tashiga raina, kuma naji k'aunarta. Allah Ubangiji ya shige mana gaba Allah kuma yasa alkairi bari na kira su Ammah na sanar musu, dan su fara shirin tahowa zuwa gobe domin tarbar amarya". "A'a ai tuni na kirasu tun bayan ɗaurin auren na sanar musu ƙalilan ne wanda ban sanar musu ba yanzu kuma nake kiran su, hatta yan Kano yau da shirin su zasu kwana gobe da safe zasu sauka insha Allah". Murmushi kwance a fuskar Ammei tace . "Lallai Dadyn su da shirin ka kake tafe kace Ammah tama rigamu ji kenan?" Yar dariya dady yayi kana yace, "Toh ai kinsan ance da zafi-zafi ake dukan karfe balle bikin Majeed guda, Jika Namiji ɗaya a familyn AA SARAKI a dolene bikin shi kowa yasan dashi, koya kikace? Sannan abinda yasa Ammah bata kiraki ba Ni nace ta kyaleki saikin kirata da kanki tukun na". Dariya itama Ammei tayi kana cikin farin cikin da idan ka kalli fuskar ta zaka sheda hakan tace, "Kwarai kuwa amma mu ai yan kallo ne sai dai mu zuba ido". "Ba wani zuba ido dan Allah tashi ki ɗauki wayar ki duk wanda ya dace ki kira ki kira ki sanar musu, duk da nasan wannan aikin su Ammah ne kuma yan Kaduna nasan duk zata sanar musu duk da Ni na kira wanda naga zan iya, sauran saita ƙara sa, toh amma kema ai aikwai wanda zaki kira, sannan kuma batun abokansa tun a ɗazu wasu daga cikin su su sani, Sannan kuma nasan wannan aikin Youseef zai ƙara sa shi ai, zuwa gobe duk wani abu da aga ya kamata sai ayi dan maybe sai yamma yan kawo amarya zasu ƙara so". Sosai Ammei ke mamakin mijin nata inda su zauna suyi shawara sosai akan yadda bikin zai kasance gobe dan shirin zuwa gurin granny ma take bayan magrib. ~ZAITUNA~ Sosai daka kalli Zaituna a daren nan zaka sheda tana cikin tsantsar tsagoron tashin hankali wanda ya kasa boyuwa a fuskar ta, dan tun ɗazu ta tasa mahaifiyar ta tana kuka akan alƙawarin datai mata na auran Majeed kuma ita kadai ce zata Aure shi dan ita kaɗai zai zauna. Sai gashi ɗazu Dady ke sanar da yama Majeed ɗin aure da wata ba itaba, wannan wacce irin masifa ce. Ita kanta Mummy Hankalin ta bashi a jikin ta tunda Dady ya gama maganar sai dai wayar datai da ƙawarta ce tasa ta ɗan ji daɗi, akan koma wacece aka aurama Majeed ɗin zuwa safiya zata sani dan zatasa a mata bincike ne akanta. Yaron da bata da wani buri daya wuce ya auri yarta dan koda ace Zaituna bata son sa toh fa dolene ta aure shi saboda wani dalilin ta, sai gashi wata can zata rusa mata shirin data dau shekaru gana yi. Meyasa ma Yayan nata ya mata haka? Meyasa ya aura masa wata bayan ta sanar dashi 'yarta tana son shi? Wacce ma wacce a aura ma Majeed ɗin? Waɗan nan tambayoyin sune cike da zuciyar ta wanda batada mai amsa mata. Ganin yadda Zaituna ta tasata a gaba sai uban tambayoyi take mata da kuku yasata kora ta waje dan ita kaɗai tasan meke damun ta. Tanaji duk tashin hankalin da Zaituna ta shiga na rashin Majeed baikai rabin wanda ita take ciki ba a yanzu, dan shirine data daɗe tana yi na tsawon shekaru su gashi cikin kuni ɗaya ana neman kaita ƙasa, "Impossible Wallahi". Ta faɗa da ƙarfi kamar wata zararriya. Koda Zaituna ta fito a ɗakin Mummy ɗakin ta tashiga inda ta tarar da Azima zaune ta zabga uban ta gumi alamun itama ta faɗa duniyar tunani. Jikinta ta faɗa tana sakin wani sabon kukan kana cikin kuka take cewa. "Shikenan na rasa shi Azima wallahi bazan juri rashin Yah Majeed ba a cikin RAYUWARTA bazan iya juraba Azima, duk son da nake mishi kuma yasan da inason shi amma harya bari Dady ya aura masa wata bani ba?". Kuka ya sarke ta inda Azima tayi shiru tana sauraren ta kana cikin kwantar da murya tace. "Zaituna dan Allah kiyi hakuri kisama zuciyar ki salama kwarai nasan da ciwo kuma da mamaki danni kai a cikin mamakin nake, kuma Yah Majeed ai baki rasa shina Zaituna dan yayi aure bashi ke nufin kin rasashi a RAYUWAR kiba Zaituna ki kwantar da hankalin ki mana". "Na kwantar da hankali kafae kice Azima kinsan me kike faɗa kuwa, wallahi hankali na bazai taɓa kwanciya ba saina san wacce a aura mishi wacce ke shirin rabani da RAYUWARTA, sannan naga na fitar da ita Ni kuma na shiga shine hankali na zai kwanta Azima". Mamakin Zaituna ne ya kama Azima sosai dan ita har dariya take idan taji ta nace saita auri Yah Majeed d'in. Cikin ƙasa-ƙasa da murya tace da Zaituna. "Humm Zaituna kenan toh ke taya zaki san wacce dady ya aurama Yah Majeed d'in? Ke nifa tunda naji batun auren nan nace maybe wacce ya aura masa ba 'yar ƙasar nan bace, nifa badin yaran Uncle Kabeer ba 'yan mata bane da sainace a cikin sune tunda kinga su a Saudiya suke, dan nifa a ganina Yah Majeed ya wucce a Aura masa 'yar Nigeria kuma a masa irin wannan auran inba ZAƁIN saba bace, kinga fa Dady daga ƙasar waje ya dawo kila acan ya samu 'yar abokinsa ya aura mas...". Tsawar da Zaituna ta dakama Azima ce tasa tayi shiru tana kallon ta, "Ya isa haka dan Allah Azima ya nazo miki da kukana kuma kina min wata maganar banza, wato nufin ki harni ma Yah Majeed ya wuce ajina bankai ya aureni ba kome ne"? "A'a kwantar sis ba haka nake nufi ba ina nufin ita wacce a aura mishi sai dai ba yar Kasar nan ba amma in yar ƙasar nan ce nace ya wuce ajinta. Keko wazai ce baki mishi ba kina da komai na matar manya gashi kin fito daga babban family ga class a kinkai Yah Majeed ya aure ki". Shiru dai Zaituna tayi bata sake cewa komai ba sai tashi da tayi ta koma ƙarshen gado ta kife kai ta cigaba da rera kukan ta, yayin da Azima ta taɓe baki murmushi kwance a fuskar ta ta tashi ta fice a ɗakin. ~FINNAT~ Kwance take a gado sai raira kuka take Basma dake gefen ta sai aikin rarrashi take, "Dan Allah anty Finnat ki kwantar da hankalin ki akan auran nan na Yah Majeed duk kin wani daga hankalin ki, auran na fa da yayi bashi ke nufi kin rasa Shiba, aa indai Allah ya hukunta zaki aure sa ai saikin aure sa dan haka Please ki kwantar da hankalin ki. Kuma mafa ni abinda yake bani haushi daku yadda ku mace akansa batin shi sam baya nuna alamun yasan kuna yi, sautari a gaban ku yasha sanar damu cewa yadda ba aure a tsakanin sa da Auta haka ya ɗauke mu ba aure a tsakanin mu dashi, Amma ku dukun mace akansa bamai iya danne sonda yake masa a cikin ku why?". Finnat na shirin magana Addah ta shigo hakan yasa ta fasa maganar da tayi niyar yima Basma. "Barka da dare Addah". Basma ta faɗa kai kawai Addah ta jinjina ma Basma kana tace. "Tashi ki zauna Finnat". Ba musu Finnat ta tashi ta zauna tana share hawayen dake fita a idanun ta, cikin daure fuska Addah ta fara magana. "Meyasa kike son maida kanki shashasha ne akan wanda sam baisan kina yiba idan ma yasani bai ɗauki abun serious ba?" Shiru Finnat tayi b tare da tace ma Addah komai ba sai ajiyar zuciya da take sauke wa. Addah ce ta cigaba da magana cikin taushin murya. "Toh inaso ki kwantar da hankalin ki indai mijin kine zaki Aure shi dan yayi aure bashi ke nufin bazai Aure kiba, a'a Aure nufin Allah ne, sannan kuma bazan ce ki cigaba da son shiba ba kuma zance ki dena son shiba Saboda dan uwan kine. Amma fah ki sani duk sanda son shi ya miki wata illar ke kijama kanki. My son ya ɗauke kune a matsayin kannen sa wanda su fito ciki ɗaya amma wai ke son shi kike wannan wanda irin abune haka Finnat? Toh Daga yau karkice ban gaya miki ba ba ruwana, kuma duk wacce ta kawomin wata matsala a sha'anin bikin nan wallahi zan mugun saɓa mata, koba alaƙar dake tare dani da Majeed aishi yaron Aminiyata ne, dan haka wllh ku kiyaye nasan ki Finnat nasan halin ki a haka kina a sanyi-sanyi amma bakida ragi ko kaɗan dan haka wannan kashedine". Daga haka ta mike ta fice rai a bace yayin da Basma ta bita da kallo, shiyasa Addahn tasu ke birgeta sam batada son zuciya akan wani komai nata tanayi ne iya gaskiyar ta gashi tana mutukar son Aminiyar tata. Yayin da Finnat ta koma t kwanta ta cigaba da kukan ta daga Yadda ta tsaya, baki Basma ta taɓe ta fice a ɗakin itama inda kai tsaye part d'in Ammei ta nufa dan tana son su gana da Auta kasan cewar duk yaran gidan ɗakunan su a part d'in iyayen su yake. ___________________ A wannan daren duk wanda ya kamata yaji bikin Majeed kam yaji harma da wanda bai kamata ba, wasu tuni sunji dan tun bayan ɗaurin aure dama dady ya kikira mutane da yawa ya sanar musu sai Alhaji Ahmed daya tayashi, dan familyn sane kawai bai sanar musu tun a waya ba saboda surprise d'in dayaso musu, kuma tabbas ya musu yaga masu so dama wanda basa so. Yan Kano kuwa tun a yammar su so tahowa sai dai yace su bari sa iso gobe tunda, su sai gobe za suyi nasu taron zuwa jibi amaryar ma sai zuwa goben zata iso. Ba musu suka barshi a sai goben yayin da duk wani shirin su sunyi zuwa gobe sai tahowa. Haka ɓangaren yaran gidan da suyi aure, su anty Hauwa dake a Legos a lokacin da Mama ta kirata ta sanar mata ba ƙaramin murna tayi ba, a kuma lokacin ta kira Majeed ɗin dan da kyar ya samu tabarshi dan saida ma ya kashe wayar. Ita kadai ce ke masa wasa harya biye ta kasan cewar ta sakuwar sa. Youseef kuwa tun barin sa part d'in Dady ya fara kiran friends din nasu yana sanar dasu bikin Majeed ɗin, inda suyi mutukar mamaki tare da jinjina wannan lamari akuma daren su fara kiran Majeed suna masa murna masu shakiyanci na masa, Yayin ji yake kamar ya kodesu saboda takaici. A ranar fah yasha amsa waya dan daga bayama kashe wayoyin nasa yayi ya kwanta zuciyar sa cike da alwashi iri-iri akan yarinyar da'a aura masa. Lokacin da Youseef yake sanar mada yaran Majeed ɗin su muktar ba ƙaramin mamaki su shigaba tare da jin daɗi, inda a lokacin Joseph ke cewa. " Haba no wonder naga Boss yau yayi wani kyau Allah na rage karya har wani haske ya ƙara duk kasan cewar sa fari". Dariya muktar yayi yace, "Humm nima da naga har wani kyalli yake ashe kyallin angoci ne". Dariya suka sa gaba ɗayan su harda Youseef dake sauraren su dan shima kanshi yaga Boss d'in ya Kara kyu yau ashe ango yake. Yayin da su cigaba dama Majeed ɗin shakiyanci tare da godema dady dan sun kosa suma suna matar Boss d'in haɗi d yaransa dan su nuna musu gata kamar yadda mahaifinsu ya nuna musu dan Boss d'in nasu fa na musamman ne. Anan ne Youseef ke cewa, "Nima maza-maza zanyi na samo matar aure kafin Dady ko Abba ya dawo kaina, dama shi Boss d'in muke jiran yayi toh yanzu ko dole muma mu shigo layi". Dariya sosai su Jabeer suke yi inda Jabeer yace, "Toh ai kai saidai ka zaba badai ka nemo ba kaida kake King of love". Duka Youseef ya kaima Jabeer ya kauce yana dariya, yayin shima Youseef dariyar yayi ba tare daya sake cewa komai ba. Daga nan kuma hira su cigaba da shirye-shiryen su. Toh a ɓangaren yaran gidan kowa sai murna dokin bikin Yah Majeed d'in suke, dan Auta ma ita kadai tasan farin cikin d take ciki dan a duniya bata da burin daya wuce ace taga Yayan nata yayi aure, kamar yadda sauran kawayen ta nasu suyi, sai dai kaji ana ina gidan anty ko munje anguwa da anty, amma ita shiru kasan cewar shi kaɗai ne namiji a familyn nasu, gashi tun bikin su anty Hafsah da ayi ba'a sake yin biki a gidan ba, kuma wasu daga cikin duk basu da wayo shiyasa suke mutukar son ayi biki a gidan nasu. Toh yau ga bikin Yah Majeed dan itafa tun barowar ta part din dady ta fara kiran friends dinta tana sanar dasu haka Basma tazo ta sameta su ɗaura daga yadda ta tsaya. Daga nan su fara shirye-shiryen yadda goben zata kasance. *WASHEGARI 🤍* A washe garin ranar FRIDAY wato asabar, gidajen rediyo dana television suka tashi dama mutane Albishir da auran na AA SARAKI wanda kowa yafi sani da *Abdulmajeed Abubakar Saraki* sosai sanar wa taba mutane mutukar mamaki dan jin abin suyi kamar a mafarki babban abun mamakin ma shine wacce aka faɗa cewa itace Amaryar. Sosai mutane su tayashi murna yayin da gaba ɗaya ƙasar ta ɗauka kasancewar sa Babban mutum da Nigeria keji mutukar ji dashi, dan yayi gadone daga Uban har kakan ana damawa dasu a Nigeria kasancewar su sannan nu a duniya dan ko a ina akace SARAKI FAMILY toh fa ansan da zaman su a ƙasar. Yayin da garin na Abuja harma da Kaduna yayi mutukar amsa kuwa da labarin bikin Majeed ɗin da amaryar tasa wacce itama ta zama sannaniya a tsakanin garuruwan saboda ba yadda prograns dinta baya zagawa. Mutane da yawa sunji mutukar mamaki na canjin Auran da aka samu a maimakon wanda akan tun farko shi zata aura, koya zancen yake? Wannan tambaya itace cike a bakin mutanen harma da 'yan uwanta 'yan jarida da suke son sanin wannan amsar. ____________🖤🤍 * AA SARAKI HOUSE* Misalin 12:00am na rana gidan a mugun cike yake da yan uwa da abokan arziki na kusa dana nesa. Duk da bikin jiya sukaji wasu ma sai dare bai hana su sauka yaudin ba, kunsan abu na jirgi awa ɗaya ne zuwa biyu ya kawo ka. Musamman 'yan Kano da tun 10 suka iso sosai duk parts ɗin gidan ke ɗauke da baki haka zalika ko wacce mata itama da tata tawagar, dan sosai part din granny ke cike da baki haka na Ammei dan tuni Ammah ta iso. Tuni fah gida ya cika da baki alabarshi SARAKI FAMILY wanda daka gansu kasan sune dan fa suna mutukar kama da juna ga auran zumunci da yawancin su shi sukeyi. Gaba ɗaya Majeed mamakin ganin bikin da suka shirya yake yi, dan Ammei kanta da su Ammah su Addah da komai da ita ake ko lokacin kansu basu da. Shi sai abun ya fara bashi mamaki bikin da kwata-kwata sai jiya bayan ɗaurin aure su san dashi amma shine har an mishi wannan shirin. Granny kam ai ba'a ganin ta sam, dan tana can cikin yan'uwa da ya'ya da jiko dan can na hango ta cikin wani fitinannen les da amishi ɗinkin bubu ga wani uban ɗauri daa coka mata kace itace Amaryar, Dan fah ita baki har kunne Dan musulta muku irin farin cikin da take ciki bata lokaci ne, kasan cewar yau ne zata aurar da Jikan nata ɗa ɗaya tilo Namiji dake gare su da duk duniya bata da burin daya wuce taga wannan ranar, ai ita ko iya auran sa ta gani ta mutu taji daɗi. Al'amarin Ammei ɗin tashi bai gama girmar kansa ba sai da Youseef ya kaisa masaukin da suka tanadarma abokan nasu, yaje ya samesu harma da wanda baiyi zaton gani ba. Aifa nan suka tasashi gaba da mitar rashin sanar musu auren nasa, dan sai da suka iso suke jin ai an rigada an ɗaura aure tun jiya, Bashi da bakin bayani sai kawai ya bar Youseef da musu sharhi. Yayinda shi yake jinsa wani iri dan shifa sam ya kasa gane kan wannan lamari na Auran dolen da aka mishi, shifa bai taɓa tunanin rashin Auran nasa ya dami Dady ba da har zai masa Aure da wacce bai sani ba. Shi a yadda ya tsara sam ba Aure a ra'ayin sa yanzu dan har yanzu baiga wacce tamishi ba. amma kwatsam sai gashi Dady ya rusa mishi wannan shirin nasa ya nasa auren dolen da ba yadda ya iya dole ya amsa, amma fah shi amsar da yake jira itace shin wa Dadyn ya aura masa? wacece ita? a ina take?. Waɗan amsar yake jira toh amma koyasha kwaya bai isa yaje ya tambayi Dady ba. Shakiyancin da Abokan nasa suke masa ne yasa shi jin kamar ya tashi ya basu guri dan harda Youseef, dama tun ɗazu ya isheshi sai da ya masa jan ido kana ya samu yabar shi amma yanzu tunda yagan sa da sauran friends d'in nasu shine ya daura a inda ya tsaya. Kasan cewar kusan duk abokan nasu sunada mata wasu ma ba ɗaya ba, dama shi suka tasa a gaba garashi Youseef yana shan love da yan matan sa amma shi ko yan matan ma baya kallo balle ya kula wannan dalilin yasa suyi mutukar samasa ido da son ganin matar dazai aura. Ji yake kamar ya tashi ya basu guri toh amma ba dama, dan tun farar safiya Dady ya turo masu gyaran dan har yanzu suna can suna gyaran part din shi abun mamakin ma wai badai a part din sa za'a sataba. Wata zuciyar tace "Toh inba nan ba part din Ammei za'a kaita?". Hannu yakai yaɗan shafa gashinsa dake kwance luf a gadon bayan sa tare da lumshe ido kana ya buɗe a lokaci guda. Dariya sosai Youseef su saki inda Khalid yace, "Wooo my friend anan can ana tunanin amaryar tamu ne?". Harara daya wulla masa ce tasa shi sakin dariya inda Taheer ya amshe da faɗin, "Ganemin hanya mutumina sai wani shafa kai yake da Lumshe ido". Dariya suka kuma saki a tare inda Faruq yace, "waini yaushe ma mutumin nan ya fara soyayya ne?". Abdul ne ya amsa da, "Abinda na gani kenan kaga yana wani sanfewa shiba ruwan sa da mata". A tare suka kuma sakin dariya irin ta shakiyancin inda Sadeeq ya amshe da cewa, "Kaga yana wani muzurai shi har yanzu baiga wacce tai mishiba". Dariya sosai suke yayinda Sameer yace, "Ai yanzu gashi yaga wacce ta mishi a Kaduna koh". Dariya suke keyi iya iyawar su dan yadda gogan ya wani haɗe fuska zai baka tabbacin a kusa yake, su kuma sanin hali yasa basu barshi ba su cigaba da yanda su tsaya. Tun yana jinsu har abun ya fara isarshi ya fara maida musu martani. Toh a ɓangaren 'yan matan gidan kowa da irin nata shirin da take yayin da irinsu Auta, Basma, Ihsan, Salma, sai sauran yaran SARAKI FAMILY dasu iso ɗazu Sa'a ninsu kansu ke a haɗe danfa yan matan family kashi-kashi ne. Su sai masu mugun jiji dakai wato su Zaituna da Azima, Asfad, bathool, saina su Finnat da Aynah, Sarah, Ashfa. Sai nasu Auta dake ƙasa dan su yan ba ruwan sune. Gaba ɗaya 'yan matan sun haɗe kowa ya kama nashi ɓangaren dan ma yaran uncle Kabeer basu zoba kuma Dady ne ya hana yace bayan bikin idan sun samu hutu saiya taho tare da iyalen nasa idan kafin nan ma shi Majeed ɗin yazo masa da tasa iyalin toh, wannan dalili ya hana zuwan ahalin uncle Kabeer din. Sosai ko wacce taci wankan ta Dan fah wanna bikin ba ƙaramin tanaji da dakon jiran sa suke ba sai gashi Allah ya kawoshi. Yayinda ta fanni Zaituna fah ko alamun tashi ta fara shiri batayi ba dan tana kwance shambar a gado kuka ma ta gama yi. Mummy ce ta shigo dakin inda ta samu kusa da Zaituna ta zauna, tashi tayi ta faɗa jikin ta tana sake sakin kuka. Cikin dacin murya tace. "Ya isa haka mana baby ki kwantar da hankalin ki wallahi wallahi wallahi indai Abdulmajeed ne kisa a ranki ki same shi dan kota halin ƙa-ƙa saikin auri Majeed ni na miki alƙawari dan wallahi yanzu za'a fara wasan. Dan haka maza tashi ki fara shiri kamar yadda sauran yan uwanki keyi, dan kema nan gaba kaɗan naki taron bikin za'a dawo tare Abdulmajeed wannan alƙawari nane Zaituna dan sam bazan yadda akaini ƙasa ba". Ina ita Zaituna yanzu tama dena fahimtar Mummy dan farin cikin alƙawarin data mata, shiyasa bata wani damu da zance baza'a kaita ƙasa ba dan ita burinta kawai shine mallakar RAYUWARTA wato Majeed. Kuma tunda Mummy ta mata alƙawari tasan bata da haufi akan mahaifiyar Tata, dan haka cikin kankanin lokaci ta fara shiri. Yayin da su Azima su shigo cikin nasu shirin da tabbas ka kallesu dole ka ƙara dan fa sun dau na agwagwa kowacce ta baza capacity yadda ya kamata. sun sameta tana shiri, mamaki sosai ne ya kama Azima ganin wacce su bari tana aikin kuka ce zaune tana shirin shagalin bikin abun son nata fuska ɗauke da murmushi toh meya sata farin ciki haka kamar wacce ace itace Amaryar? Koma dai itace Amaryar? Kai inna abinda bazai ma yiwuba kenan.🤔 A ɓangaren Finnat kuwa tuni tashi tayi shirin ta dan tun faɗan datasha jiya agun Addah haka yauma tasha, shiyasa ta dake ta shirya inda tasa aranta tunda taga Addah bata goyon bayan ta da Majeed ɗin toh fah ba hakan ke nufin zata hakura ba, dan dolene itama ta fara nata shirin basai ta jira wani ba. Shiyasa ta kuduri fara nata shirin dan daka kalleta baka isa gano akwai damuwa a zuciyar taba, dan tsaf fa ta zauna ta dau wanka da itada yan Team ɗin nata wato su Ayna dan anko suyi sun baza cafacity iya cafacity fah ba karya 💃😂. Huu huu huu😂🤣 yaufa akeyin ta bikin Big Bro watoh Yah Majeed koya zata kaya wacece amarya shin kodai Zaitunan ce🤔, toh fah nima ban sani ba 🤷 Readers ku biyo alƙalamin BILLY PINKY ✍️ Dan jin yadda zata kaya.💃😂 Nidai nayi nan 🏃🏃🏃🏃🏃 *Typing📲* _Follow my WhatsApp channel_ 👇 https://whatsapp.com/channel/0029VauF15RLNSZvrEQHsL0 _Follow my WhatsApp group_👇 https://chat.whatsapp.com/EKFnHpoI54t1MvodB5HgYB *🌹 RAYUWATA 🌹* _CREATED AND WRITING BY_ *Bilkeesu Sa'eed Aliyu* 💞*Billy pinky*💞 ✨*TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION* ✨ *T.M.W.A✍️* *Amanar taurarin marubuta writer's.......✍️* *TEAM HAZIKAI BAKWAI 💪✨* *END OF BOOK ONE* Page. 5️⃣0️⃣ .............Kamar yadda a gidan jiya FRIDAY ayi yinin biki yau Saturday ta kama cikar biki, sosai Yau ma nasha kyau Kamar ka sace ka gudu. Sosai yau tunda na tashi nake jin gabana na faɗuwa na rasa dalili yayin da kuma haka kwai naji sam bana son yau ɗin akaini gidan su Suraj ɗin kamar yadda ace sai yau. ___________★ Bayan gama walimar da Ummi ta sake shiryawa anan gidan Abba da safe inda a tashi gurin sha biyu. Sosai walimar ta kayatar dan ba karya. Sosai Mom taji mutukar bakin ciki na walimar da Ummin tayi a gidan dan fa duk wani abu da ayi a gurin kamu ba wanda 'Yan uwanta su boye mata, acewar suma gani ya kori ji dan dakko mata suyi a waya su nuna mata, aiko bata iya ta ƙarasa kallaba tace a kashe dan ita anty Waleeda ma tashi tayi ta shige ɗakin Mom d'in tana kuka, wai Safiyyah ta gama kwace mata Suraj d'in. Toh yanzu mafa shine ganin wannan walimar da Ummin ta shirya yasa bakin ciki ya cika Mom ɗin itada maƙaraban ta. _______★ *Around 4*★______ Bayan nayi sallar La'asar kamar yanda Ummie ta faɗa aka haɗamin ruwa mai zafi da kayan turaren ƙamshi a ciki nayi, koda na fito sai uban kamshi nake, dan da alama wannan ɗin yafi sauran da ake min amfani dasu. ace a fara shirin shiryani Sai kawai na sakin musu kuka anty Hajara tace "ƴar shagwaɓa". Dan wlhy jinake tamkar kar a kaini. Haka dai aka gama shiryani cikin atamfa datai matuƙar ƙyau ta kuma samu ɗinki na nutsuwa. Kawu Bala, Abban su Buhaisa da ya zo ɗazu, da sauran uncle's d'in nawa sai Abba nah su Yah Ansar, Yah Saif, Yah Safwan, sai su Mama Hadiza, su Ummie ne sukai min faɗa da nasiha mai matuƙar ratsa jiki da ɓargo. Daga ƙarshe suka sanya min albarka da fatan alkairi a rayuwar aurena. Sosai nake kuka mai tsuma zuciya dan zuwa yanzu nikam na fara karyewa. Duk da jiyama sun min nasihar hadi da faɗa amma nayau ɗin sai naji yafi najiyan. Karfe biyar saura mintuna saiga haddadun motoci masu matukar kyau da ƙyalli bakaken Prado da G-Wagon suka shiga unguwar cikin natsuwa da tsari. Unguwa ta tsaya cak. Kowa na kallon jerin motocin kamar faretin gwamnati. Ya subahannallah tsarin ya matuƙar haɗuwa, motar amarya a tsakkiya tasha flowers. Wasu na ɗaga waya suna ɗaukar bidiyo. Shigowar Anty Fatima tana cewa ga motoci sun zo. Sai a lokacin kuma naji duk na rikice. Nanfa na saki musu kuka, haka dai aka ƙara shiryani tare da chanja min atamfar zuwa wani fitinannen les ne komeye dai ban saniba sai wata irin alkyaba mai mutukar kyau, tsaf kuwa kayan suka tsayamin ga wani uban kyau dasu min duk da ba make-up ko ɗaya a fuska ta. Duk yanda akaso na miƙe naƙi nai hakan har sai da Kawu Bala da kansa ya shigo yana faɗa sannan. Kuka nake sosai har numfashina na shiɗewa. Amma babu wanda ya saurareni, sai ma gaban Mom da aka kaini na roƙi yafiyarta. Cikin taɓe baki tana wani fisge-fisge ta ce, "ALLAH ya yafe mana baki ɗaya sai aje aita haƙuri, dama ita rayuwa ai haka take babu tabbas..." ganin tana neman sakin layi Mama Hadiza ta kamani muka fito dan Ummie sam bata biyomu gurin Mom ba. Abba ma an sake kaini na masa sallama. Yah Ansar kam ya rufe kansa a ɗaki yaƙi yarda. Nasan kuka yake, dan haka nima na ƙara ƙarfin nawa kukan ina tutturjewa, sosai Ummie ta riƙeni kasan cewar tace saita kaini har ɗakina yayin dani sam bamga su Buhaisa da Isha ba. A rikicen da nake yasa bamma san kala ko adadin motocin da suka zo ɗaukata ba. Ni dai kawai Ummie ta sakani a motar da take ɗauke da wani irin ƙamshin. Mama Hadiza da Ummie ne tare da ni, sai gaba da ban san waye agun ba danni fa, tunda La'asar tayi gaba na ya tsananta faɗuwa ji nake kamar wani abune zai sameni. Sosai gurin yaɗau buɗe-buɗe yayin da masu ɗaukar video da hotuna sai faman ɗauka suke. Yah Saif kam tun bayan gama min faɗa ban sake sashi a idona ba harmu tafi. Mamaki kwance akan fuskata ganin mu a tashar jirgin ƙasa sosai gaba na ya cigaba da faɗuwa yayin da nakai kallona ga Ummie da niyar tambayar ta. Hannu tasa abakinta alamun karnace komai daga haka ta kama hannu na itada Mamy su nufi cikin jirgin dani, sosai nake son magana da Buhaisa akan sanin ina kuma za'a kaini, bayan nasan Suraj a Kaduna zai zauna amma ana shirin barin garin dani, zuciya tace ta tsinke tuno Suraj da nayi, Yayinda su Buhaisa suma su take mana baya su biyo mu cikin jirgin. Jirgin ya fara motsawa da ƙaramar ƙara. Gwaninta da kyau ya bayyana a tsarin komai – daga lafazin ma’aikata, zuwa ƙamshin sabbin kujeru. Amma a zuciya ta ba komai sai shiru mai nauyi, da tunanin da ke kewaya kamar hayakin jirgi. Ina zauna a wajen taga dan anan Ummie ta zaunar dani, ina kallon fitilun titi da ke wucewa da sauri. Ina jin kamar duniya ce ke kaucewa daga gareni, ina barinta da tambayoyi da ba su da amsa. Wani murmushi mai rauni ya leko a fuskata ba don farin ciki ba, sai don ƙoƙarin ƙarfafa kai. Ina tunanin “inane inda za'a kaini kuma? Me yasa suke boyemin bazasu faɗa min ba? Kuma me yasa Suraj sam bai nemeni ba?" Wadannan tambayoyin sune narke acikin zuciya ta da sam banda me amsa min su saboda tun jiya na fahimci akwai abinda ake boyemin, ga Ummie taƙi bani damar yimata tambaya, gashi ba wayana a hannu na, gashi basu Buhaisa a kusa dani, A hankali na sauke ajiyar zuciya tare da kwantar da kaina a kafadar Ummie ina lumshe ido. ___________★ *Abuja 🤍* Jirgin ya iso tashar Idu da ƙarfe Bakwai 7:00pm na dare. Fitilun tashar suna haskakawa cikin daɗin gani, amma a idanuna, duhu ne kawai da sabuwar rayuwar da ke gabana. A wajen fitowar fasinjoji, manyan motoci ne na alfarma jere masu mutukar kyau da ɗaukar ido. Wata fitinanniyar mota ce ƙirar Mercedes Maybach mai sheƙi. Fara tas tasha flowers. Kamar a Kaduna yanzu ma motar ɗaukar Amarya ce a tsakiya datai mugun haɗu wa. fuskata dake rufe cikin alkyabar datake shara-shara tanan nake ganin komai yayin da tuni zuciya ta ta sake tsinkewa gabana ya cigaba da faɗuwa a kuma dai-dai lokacin su Ummie da wata mata da bansan taba suka sakani a cikin wannan farar motar Mercedes Maybach cikin nutsuwa. Yayinda sauran motocin kowa ya debi iya adadin mutanen da zai iya, a jere manyan motocin suka bar tashar Idu motar amarya a tsakiya gaba da baya jami'an tsaro ne. Inda kai tsaye a bakin wani irin gida gidan daya amasa sunan shi gida, haka kuma gidan da kyawunsa yadarama dukka gidajen, duk dacewa gidajen naka mancece niya da juna, amah duk yafisu tsaruwa, Idanu nasake warewa tabbatar da cewar, glass din danaga yana budewa get ne ko akasin haka, Batare da nagama tinanin ba, Motocin suka kutsa kansu ciki, Wanda hakan ya tabbatar min da cewa get ne. *WELL COME TO THE AA SARAKI HOUSE* Shine ke rubuce asaman makeken gidan "Dammm" gabana ya bada sautin dan wllh Billy ji nayi kaina yana neman kwance wa dan gaba ɗaya duk wata nutsuwa da kuzarin dana dan samu sun gudu, ba abinda zuciya keyi sai gudu acikin girjina. Wai meke shirin faruwa dani ne Ni Safiyyah?" Wannan kalma dana furta a hankali da sam banma san ta fito fili bace ta dawo da Ummie da Mama Hadiza daga sumar wuccin gadin dasu tafi na ganin wannan fitinannen gidan. A hankali ummie ta sake damke hannu na cikin nata tare da furta "Ki nutsu Safiyyah". Shiru nayi ba tare dana ce komai ba sai bin komai dana keyi da ido. Ajere motocin duk suka shiga makeken compound din da Sam bai da iyaka ga Mai kallo, kowace ta tsaya a muhalin da akeson ganinta, *AA SARAKI HOUSE* A tsaye AA SARAKI FAMILY suke suna jiran isowar amarya wacce tunda ta ƙaraso cikin garin Abujan suka sani, Inda duk da ɗunbin mutanen nan dake cike da SARAKI house da wanda sukayo ma amarya rakiya hakan bai hana Granny da ke fama da tsufanta ba fitowa tarbar amarya ita da su Mahmah. An fara kaita sashen Ammei, Ammei ta rungume abarta tana share hawayen farin ciki, wai yau itace rungume da matar ɗan ta guda ɗaya tilo ALLAH ya cika mata burinta. Yayin da Ammah ta rungume Safiyyah daga baya kuma ta koma kan Ummie mamaki kwance akan fuskar ta. Bayan addu'oi aka fito da ita aka nufi sashen Granny da ita Anan kam dai cike da bariki Mummy ta tarbesu, addu'oi duk da basu kai ciki ba. Yayinda Granny ta rungume Safiyyah tsam tana samata albarka, Daga nan aka dawo da Safiyyah sashenta. Bayan an sakata tayi alwala aka shiga da ita ciki bakinta da addu'a. Anan bedroom ɗin ƙasa suka ajiyeta bisa umarnin Ummie        Gaba ɗaya dangin Mom sun gama sumewa a tsaye. Karo na farko na rayuwarsu suka fahimci ashe inda Safiyyah ta shigo ba ƙaramin guri bans, dan wlhy a dukiya irin ta wannan gidan da ginin kawai suka gani Suraj d'in da suke hauka akan su bakomai bane. Dan wutsiyar raƙumi tai nesa da ƙasa. Su Buhaisa kam sumar wuccin gadi suyi daga baya kuma su cigaba da kallon gidan tare da yabawa. Buhaisa mayyar hoto itada su Yasmeen ai tuni su fara aikin nasu.          Sosai ahalin Safiyyah sunji daɗin tarbar da akai musu. Tun daga kan shimfiɗar fuska har zuwa ta wajen zama da abinci dana sha komai Alhmdllhi. Mafi yawancinsu kuma ba ƙaramin rikicewa sukai da ƙaton mansion ɗin na SARAKI FAMILY ba. Har takai wasunsu ma sun gagara bakin magana. Su Buhaisa, Yasmeen, Bahijja,Isha, da sauran 'yan matan suka shiga cikin alhini da mamaki yayin da tuni masu hoto suka fara. Yayinda a fannin 'yan matan gidan su Zaituna dama kowa burin su shine ganin matar Yayan nasu dan a iya jikin ta kawai dasu kalla kai kasan bata wasa bace........✍️ *Alhamdullah 🙏. Anan zamu dakata a book one na wannan littafi mai suna RAYUWATA 🌹 sai kuma ALLAH yasa muna da rabon kaiwa wani lokacin dan banjin zan ɗaura da sakin sa maybe saina kammala rubuta NIDA YAH HAISAM tukun nan sai mu daura da Book 2 ɗin. Amma idan har naga yanayin yadda ku damu dashi maybe kafin na gama rubuta NIDA YAH HAISAM d'in na ɗaura da RAYUWATA tawa sai dai naga yanayin yadda ku damu dashi tukun na.* ★Tofa masu karatu yaya take ne?. ★Mike shirin faruwa?. ★Ina Suraj ango?. ★Meyasa Auran Safiyyah ya koma kan Majeed a maimakon Suraj? ★Wai Taya ma hakan ta kasance?. ★Shin Safiyyah zata amshi Majeed a matsayin miji kuma ta manta da Suraj? ★Shin Majeed Son Safiyyah yake ko me, meya kawo hoton ta kan screen ɗin system ɗin shi? ★Ya batun aikin Safiyyah shin Majeed zaibarta ta cigaba da zuwa aikin ta anan Abuja ko kuma zai hana? ★Shin Mummy zata janye kudurin ta na dole sai Majeed ya Auri Zaituna kunsan dai Mummy Bata wasa bace😂? ★Ya zaman Safiyyah zai kasance a cikin gidan AA SARAKI HOUSE ga manyan basawan dake zagaye da ita? ★Kunsan dai Safiyyah miskilace ga hakuri shin zata barsu ne suci lagonta ko zata chanja ne ta koma masifaffiya? ★Ɓangaren Mom kun dai san alƙalamin BILLY PINKY baya yafiya, dole kowa ya girbi abinda ya shuka? ★Ina anty Waleeda masoyiyar Suraj shinya soyayar tasu zata kasance shin Suraj zai sota? ★Shin ya su kansu matan cikin gidan su kansu akwai Zazzafan wasa a tsakanin su? ★Wai shin su waye waɗan nan su biyun mace da namijin nan? ★Shin waye ma yasama Majeed poison acikin madara? ★Ya soyayyar Isha data Yah Ansar zata kasance? ★Meye haɗin Ummie da Ammah? ★Wai shin ya zamuyi ma da Buhaisa ne? ★Shin Finnat ta hakura da Majeed ne ko kuwa tana nan akan bakarta? ★Wai shin ya batun gidan su Suraj (MD)? ★Anata magana an manta Ummahn su Safiyyah da Mom ta mata kurciya🤭 Shin tana rayane kota mutu idan tana raye shin zasu haɗu dasu Safiyyah? ★Magana fa ake ta an kawo amarya gidan mijinta amma ango ya rikiɗa zuwa wani daban.🤭😂🤔 ★Hhhhh masu karatu akwaifa gurmi. Gurmi gagarumi ma kuwa na musamman. Dan littafin nan ɗauke yake da nasa salon shima. Hargitsi da cakwakiyar dake cikinsa kuwa. Hhhhumm ba'a magana, dan bama mu fara komai ba sai a book 2 da zai zo duk sanda ku shirya, kuma komai da kuke buƙata yana a cikinsa ne. ★Dan shi kansa Majeed bakusan waye shiba har yanzu dan bakusan cikekken Tarihin saba suwaye SARAKI FAMILY? ★Kai kar dai na cikaku da surutu, kudai saikun shirya domin samun duka wannan amsoshin a RAYUWATA BOOK 2 har ma da wanda baku sani ba. ★Ya rabbi ka shiryar damu bisa tafarkin gaskiya, ka gafarta mana ka yafe mana kurakuran mu. Ƴar uwa! Ɗan uwa! Duk wanda naima ba dai-daiba ya gafarceni. Nima na yafema kowa. Fatana kumin addu'ar fatan alkairi nima na muku tare da iyayenmu baki ɗaya. Taku har kullum🤝 *BILKISU SA'EED ALIYU (DR)* *(BILLY PINKY✍️)* *San so, ƙaunar ƙauna Zafafa nake muku baki ɗayanku masoyah ❤️ kamar yanda kuke mana🤍💋* Muje zuwa BOOK 2 🏃🏃🏃 20, July 2025✍️