[09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 09033181070 1 BismillahirRahmanirRaheem. Fadi da tsawon nisan da dajin yake dashi ya zubawa manyan idanuwansa yana kallan shuka da ganyen hakukuwan da suka cike gurin Wanda babu hanyar wuce a gurin idan ma kace wucewa zakai to sedai Kabi hanyar da adda ko wuqar ringa sare ganye dan Ka ringa ganin gabanka Wanda su hakan ba komai bane a garesu sbd sun saba haka suke rayuwa a cikin ganye da shukoki hakama yawo da wuqa me tsananin kaifi da dafi a jikinsu kaman dole ne kokuma ace al’ada ce me karfin gaske sbd yanayin karni da ake ciki na safarar mutane Ana saidawa a matsayin bayi, Rayuwa ce ta koina zaka iya haduwa Wanda sukafi Ka karfi su raunana rayuwarka suyi safararka zuwa inda zasu siyar a matsayin bawa, Ba iya dan Adam daya ko biyu ko uku koma da yawa ake nuna karfin hakan ba hadda gari sukutum masu safarar basu Bari ba suna cinye gari da karfi su tattara suyi safararsu. ANJOM GHAZ Garin ANJOM GHAZ gari ne dayake zagaye da ruwa masu ya wan gaske gabas dinsa yamma,kudu da arewansa kafin manyan hakukuwa da bishiyoyi masu tsayi da hadarin gaske da suka rufesa a zagaye duk kuwa girmansa, Idan Ka shigo daji ne me girma da nisan gaske dayake dauke da macizai masu yawa wanda hakan ya samu ne sbd tamkar suna kiwonsu ne sbd yanda suke baza abincinsu da abubuwan da sukasan macizai na so dan zama a guri, Daga inda dajin ya qare kafi ne da tsaro suka kafa masu tsananin karfin da babu Wanda zai iya karyasu sai jinin shugaban garin wanda shine yayi kafin sbd zaman lafiya da tsaron jamaar garinsa dan haka wannan kafin baya barin Miciji ko daya shigo wa garin iyaka cinsu dajin Wanda duk baqon Daba gayyatarsa akai ba shigo wa garin kokuma Wanda bai saniba ya nufo garin baya kaiwa yake haduwa da ajalinsa sbd tsananin hadarin dayake garin, A duk girma da tsananin yawan garin ANJOM babu Wanda baida yanci da kwanciyan hankali a garin, Babu Wanda babu tsari a jikinsa na al’adarsu, Allah ya rufa musu asiri sosai a garin sbd arzikin qasa da Allah ya bas, Basu da talauci sbd kusan kowa nada tarin arziki kalan nasa, Babu bare kusan kowa dan uwan kowane sbd samun jajirtaccen shugaba Wanda babu kamarsa a jajircewa,Zarrah da karfi tareda rashin tsoro, Asalin sunan garin ANJOM GHAZ ya samo asaline ne daga asalin kakannin shugabansu na yanzu wato GHAZ ALI Wanda asalin sunan na ahalinsu ne wato ANJOM kakansu na farko kuma ANJOM Wanda shine ya kafa garin Shiyasa garin yake da sunansa. A yanzu GHAZ ALI shine shugabansu Wanda yake na uku a tarihin shugabancin ANJOM kuma Wanda shine ya dauko kakansa ANJOM da karfi da Zarrah tareda taurin zuciya da rashin tsoro ba kaman mahaifinsa ba daya zama me sanyi sosai. Lokaci ya tafi sosai kusan duka kakakkani da iyaye sun rasu a yanzu daga ghaz Ali sai iyalansa da suke rayuwa cikin mulki da kwanciyan hankali da Shaquwa tareda aminci. Matarsa daya Amma sai ‘ya’ya Hudu mace uku namiji daya, Namijin ne qaraminsu gaba daya ‘yayan, Shine namiji kuma shine me rauni da tsananin tausayi, AYANAH itace babba Wadda tayi gadon Mahaifinta a gurin tsananin so da kaunar Yan uwanta fiyeda kanta da komai, Bata hada kaunar kannenta data kowa, Bata iya karban abinda basu samu ba, A ko Yaushe sune a gabanta ba buqatarta ba Wanda hakan duka koyarwa ce da raayin hakan da mahaifinta ya saka a ranta tin tana Qarama sosai sbd kasancewanta babba dan duk ranar da babu shi itace a dolen dole zatai shugabancin garin sbd shine gadonta na farko da garin zasu Bari ta fara hawa sai idan bata da lafiya ko rashin hankali kokuma idan tanada ‘dan data Haifa Wanda ze hau a maimakonta shi kuma idan ya sauka a lokacin ne shugabancin ze dawo hannun Wanda ke Binta a kannenta. NURAT itace me bin AYANAH itama kaunar iyaye da Yan uwanta a jininta yake sedai ita tanada fada, sai ZUHRAH wadda mahaifiyarsu take tsananin Ji da ita dan haka ita gata yasa lalaci yai mata yawa amma itama tana tsananin son Yan uwanta Wanda duka a jinin su abin yake, ABAAS GHAZ Wanda asalin sunansa ABBAAS shine qaraminsu Wanda yakeda tsananin rauni fiyeda Yan uwansa da suke mata hakan ya saka ya kasance Wanda ake tsananin tausayi a cikinsu, Tsananin tausayi da kaunarsa suke fiyeda kowa, Rauninsa da yayi yasa baya iya ko shiga mutane baya sakewa a koina bare iya shiga koina saida Yan uwansa musamman Ayanah da itace tamkar kariya da kuzarinsa sai kuma mahaifinsa. Magani da kowane irin kokari anyi na kawar masa da hakan amma Sam babu nasara dan haka suka hakura suka barshi Akan lokaci kila zai iya sauyasa wata ran zuwa jarumin namijin da suke fata. Ghaz Ali ya bawa yayansa gata da dukkanin tar biyan da suke buqata tareda shaquwa me tsanani da sakewa a tsakaninsu, Dashi da yayansa babu boyo sai sakewa da kauna me karfin gaske, A duka fadin ANJOM GHAZ babu inda zasu gifta baa basu girma me tsanani ba, Girmamasu ake yi tamkar mahaifinsu ghaz Ali wasu guraren ma idan anje tamkar zaa bauta musu ake yi kasancewan zamani ne da musulmai da masu addini daban daban suke zaune kalau cikin aminci da kwanciyan hankali tamkar Yan uwa. Rayuwa a ANJOM GHAZ rayuwa ce da kowane dan Adam ya samu zaiwa Allah godia da samunta, Rayuwa ce da mutane daga duniya daban daban suke fatan samu sedai tayi musu nisan da baza su samu ba, Rayuwa ce ta kwanciyan hankali da nutsuwan da manyan Masarautu da dama basu samu ba sbd babu fitina babu tashin hankali, Gari ne da wasu garuruwan da dama suke kiransa da gidan kwanciyan hankali, Gari ne da basa karban bakon da basu San komai akansa ba bare Yan gudun hijira ko yan ci rani hakama gari ne da baya Aminta da kowane irin gari ko Masarauta ko wace iri sbd ikonsu suma dasuke Jin sunada shi. ************* Gyara tsayuwa Ghaz Ali yayi yana sake zubawa fadin dajin dabai iyaka idanuwansa yayi zuciyarsa na sosuwa da tsananin radadin masifar datafi kowace fara fadowa garinsa da zai iya bada rayuwansa dan basa kariya sbd garin anjom ghaz shine gata da rayuwar ‘yayansa da duk Ranar da suka tsallaka wajen garin suka barsa zuwa wata duniyar daga ranar kaddararsu zata sauyane zuwa wadda baisan ya rayuwa zatai dasu ba, ‘Yayansa sune rayuwarsa dayake tsaye cak akansu, Yayansa sune ginshikin rayuwan daya tsayu ya ginawa anjom ghaz, Yayansa sune bazai taba iya barin wannan masifar ta fadawa ba sai idan babu ransa a duniya, Mutuwansa fitar ransa a kirjinsa itace kadai zata Bari yayansa su fuskanci wannan masifar dayake Jin tamkar kirjinsa zai qone sbd Zafin baqin cikin dayake cikinsa, A taurin zuciya da Zafinta da Allah ya basa yasa ya zabi akawo masa gawar ‘yayansa kaf a jere a gabansa cewan sun mutu yafi masa Akan Ayi farautarsu zuwa a siyar a bayin wata qasar suyi qasqantacciyar rayuwar Bautar bayin da har kwanciya sarakuna ko yayan sarakuna zasu riqa yi dasu. Wannan zazzafan kakkarfan raayin na GHAZ Ali yasa duk Wanda yake ANJOM hakan ya kafu a ransa sun zabi mutuwa Akan a kamasu a tafi dasu bauta qasar da kaddararsu zata sauya har mutuwa. Matansu ma kusan hakan suka zaba mutuwa Akan barin a tafi dasu a maidasu dabbobin kwanciya da biyan buqata. Numfashi me zafi Ghaz ya sauke yana rintse idanuwansa kafin ya juyo ya kalli tarin mutanen da suka zo farkon garin dan gane wa ido da kuma tsoro daya fara shigar kowa na abinda yake tinkarosu sbd kaf a tarihi an sani duk garin da KUSRA( masu karfin safarar bayi da ikon siyar dasu qasashe qasashe na sarauta me karfin gaske) suka sakawa lamba to tabbas komai karfinsu to sai sun tashi garin sun tabbatarda duk wani me Sauran rai da numfashi a garin sun mallakesa sun tafi dashi sbd siyar da bayi ga manyan Masarautu. Mutanen ANJOM tinda suka fara samun Alaman Kusra garinsu suke hari take kwanciyan hankali ya fara qauracewa a anjom duk da shugaban gari bai nuna hakan ba amma sunsan wannan masifaffiyar kaddara ce da baza su iya kaucewaba idan ba ikon Allah ba hakama a garin baa tafiya gudun hijira idan ba shugabansu ne ya bada damar yin hakan ba. Abinda yake dan kwantar musu da hankali shine sanin baa iya shiga garin Kai tsaye sbd karfin nasu tsari da kafin da sukai duk da sunsan kusra nada karfin gaske suma amma kuma sanin su ne baa iya karya kafin saida jinin ahalin GHAZ dan haka tsananin karfin tsaron ahalin GHAZ ya tsananta baa Barinsu fita koina saida tsaron askarawa masu karfin gaske shi kuma Abaas kwata kwata ya Dena fita koina sbd ko wuqar jikinsa baa iya amfani da ita dan bama Kansa kariya. ****Gawar mutane sama da ashirin ne na mutanen ANJOM din da kusra suka kashe a Daren jiyan a wajen dajin Darin jere a qasa gaban ghaz Wanda yake sake kallan girman dajin yana tunanin yanda kusra suka samu damar isowa har gap da shigowa dajin garin Wanda sai an tsallako ruwa me karfi da yawan gaske duk da su kusra daman a ruwa suke rabin rayuwansu dan sunfi zuwa qasashe a jirginsu na ruwa me kamar gari dasuke tsallakawa da bayi Wanda yake dauke da dakunansu na bacci da komai na buqatan gudanar da rayuwansu dan bayinsu na kansu masu musu bauta da girke girke duk a ciki suke da nasa dakunan daban daban suna rayuwa hakama a inda suke zuba bayin da zasu siyar wa yana iya daukan sama da bayi daruruwa dan haka su babu Wanda ya taba sanin inda suke saidai idan Ka gansu kawai dan haka babu mai ikon daya taba kamasu sbd rashin sanin duniyoyin dasuke. Basu taba sanin akwai gari a tsallaken ruwan dasuke bi su wuce ba saida tsautsayi yasa suka bi wasu bayi da zasu Kama ba suka gudu har cikin dogayen itatuwan da suka rufe dajin hanyar garin daga Bakin ruwa dan haka Mutum ashirin da suka bi bayin suna ganin sun ratsa itatuwan binsu sukai suka ratsa ciki Wanda suna shiga tin anan mamakinsu ya fara dan haka suka bazu a dajin suka bisu. #MAMUH #SLAVERY #BEST MALE CHARACTER #LION OF BOYEM #BEST LOVE STORY #ROYALTY #BRAVERY #HISTORICAL #LOVE/HATE STORY HAYATEEM 700 0022419171 AccessBank maryam sani gummi 09033181070 [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 09033181070 2 Shugaban kusra subawa hanyar da sukabi idanuwa yayi sosai yana kalla yana Jin wani iri a jikinsa sbd duk inda aka samu hanya akabi to tabbas idan an kuwa ankai karshe komai nisa bazaa rasa inda zaaje ba a gurin. Gudun cetan rai bayin sukeyi sosai suna Waiwaye sbd mashin da ake harbo musu masu tsananin kaifi da dafin da take zai karya duka garkuwan jikinsu matiqar ya tabasu ko kadan ne. Basusan ina suke jefa kafafunsu ba bare inda suka dosa gudu kawai sukeyi na tashin hankali da tsananin tsoron da zuciya bazata iya dauka ba. Nisa suke Qarama suna kusantar hanyar ANJOM wadda take cike da hadari batareda sun sani ba. Cikin tsananin rashin Imani da babu ko Kadan a ran wainda suke biye dasu Wanda yake kaman shugaban Sauran ya bude baki yana tsaya wa daga gudun dayake ya Fiddo harshensa dayake da duhu sosai ya lashi fatar bakinsa dayake baqi qirin ya daga Kai sama yayi wani irin Ihu me karfi kafin ya sake dariya kaman me ciwon aljanu ya bude murya sosai yace ‘Dayan zuciyarsa nakeso a hannuna kafin ta Dena bugawa daga fitowa kirjinsa, Dayan kuma idanuwansa nakeso zanyi wa dass sarka dasu a wuya’ Sauran na Jin hakan suka qara gudu suna sake Harba musu arrows masu tsananin tsini. Na farko ganin ya kusa fita bishiyoyin zuwa filin dajin dayake hango hanyar da yasan zai iya samun gurin tsira da sauri ya sake tsananta gudu kafafunsa na fidda wani irin Jini na fashewan kafafunsa da tarin qayar da suke cike da tafi harma da saman kafarsa. Na bayansa kasawa ya fara yi sbd zuciyarsa dake kasa dauka fara rage gudu yayi kafafunsa na jinin dayafi na gabansa hancinsa ma jini ne yake fita dan haka hannunsa ya daga ahankali ya Zare jakar fatar jikinsa Qarama ta kudin da suke tare dasu ya daga zai jefawa dan uwansa ya bude baki daqyar zai Ambaci sunansa wani irin jini me karfi ya feso ta kirjinsa,. Cak ya tsaya hannuwansa na dawo wa qasa ahankali idanuwansa na yin jajir kaman zasu fidda hawayen jini sbd tsananin azabar dasuke bayyanarwa, Ahankali ya saukar da Kansa zuwa kirjinsa ya kalli tsinin mashin daya shigo ta bayansa ya bullo ta kirjinsa. Sarewa kafafunsa sukai cikin tsananin azabar da bata da Kama a lokacin. Kafin ya qarasa kaiwa qasa wani mashin ya sake ratsa wuyansa ya bullo ta gaba take wani jinin me yawan gaske ya feso ta bakinsa da wuyan yake ya zube a gurin ba rai a jikinsa. Suna isowa gurin Sauran basu tsaya ba tsananta gudu sukai dan cimma daya sbd a tarihin kusra basa rasa duk Wanda suke bi. Mutum biyu ne suka tsaya Akansa ba wata wata suka fidda wata kakkaifar wuqar da ko ice zaa yanka da ita bazaiyi Kyan gani ba take suka fara huda kirjinsa dan cika umarnin shugabansu. Jemo daya waiwayo yaga dan uwansa rayuwarsa ta riga ta fita take yaji zuciyarsa da jikinsa na sarewa wani irin Ihun kuka ya fasa yana cigaba da gudun da yasan ba tsira zaiyiba Kuka yake yi sosai sbd dan uwansa jininsa dashi kadai yake dashi a duniya baisan yaya zai yi rayuwa babu dan uwansa Juyowa ya sakeyi koina na jikinsa na wata irin rawa gudunsa na tsananta Juyowansa da shigar mashi a goshinsa lokaci dayan hakan ta faru take ya tsaya cak yana zubewa gefe ahankali jini ya gangarowa zuwa idanuwansa take ransa shima ya fita a gurin. Cikin rashin imanin fa basuda shi suka qaraso suna durqusawa gabansa Sauran kuma hanyar da suke hange suka zubawa ido wadda ganyen Shuke shuke suka rufe amma sunada tabbacin indai akwai shuke shuke a gurin to tabbas akwai mutane kokuma gari sbd shuke shuke ne da qaramin gari sosai bazai iya ba sai garin daya tara mutane da dama hakama kuma indai har akwai gari a cikin gurin to tabbas irin hakan suke so garin dayake a boye Wanda har zasu Kai hari su gama su tafi baa sani ba. Mutum hudu ne a cikinsu suka tinkari hanyar zuwa shuke shuken da suke hankowa daga nesa sosai suna dake zubawa hanyar ido sosai daga nesa suna kasa yadda da akwai gari a cikin wannan Jejin me tsananin hadari. Tafiya suke suna sake Sauri sbd wannan abune na farin cikinsu, Cak suka ga na gabansu ya tsaya tareda kallan qasansa da sauri sakamakon abinda yaji sai kuwa ga maciji baqi qirin yana wani irin qyalli cikin rana. Wuqar hannunsa ya saka ya fizgo macijin da ita ya rabasa biyu ya jefar suna cigaba da tafiya cikin zalamar son kaiwa inda suke son, Taku goma suka qara dafin macijin ya fara aiki a jikinsa duk da ya yanka gurin daya cijesa da wuqa dafin ya biyo jini yana fita. Wani irin zufa da zafi jikinsa ya fara dauka take bugun zuciyarsa ya fara sauyawa ya tsaya cak tareda durqusawa ya sake yanka fatar jikinsa da wuqa yana turo jini waje da hannunsa. Daga bayansa wani macijin yaji ya kuma sararsa take ya juyo yana kokarin Kai masa hannu ya kashe wani ma ya sake sararsa take ya fara kokarin mine wa amma ba damar hakan sbd sankarewa da jijiyoyin jikinsa suka fara suna Dena aika jini koina. Ganin hakan Sauran yan uwan nasa basu tsayaba suka cigaba da tafiya sedai ko ina basu kaiba dukkaninsu suka zube a gurin kowannesu kumfar tsananin dafi na fita jikinsu na dafin macizai. Sauran na ganin hakan suka fahimci me yake faruwa a gurin Wanda hakan ya gama basu tabbacin da suke nema na cewan akwai gari a karshen dajin. Jiya wa sukai suka koma Bayan sunyi doguwar tafiya me tsayi kafin suka bullo bakin gabar mahaukatan ruwan. Suna isowa suka sanar da Sarkinsu gabaki daya bayanin komai. Shiru yayi idanuwansa a rufe wani irin rashin Imani da bushewan zuciya na ratsashi batareda yace komaiba. Shiru na mintina a hakan kafin ya bude jajayen idanuwansa da basuda haske ko Kadan ya sauke Akan zuciyar da suka kawo masa tana jini ya dauka batareda ta juyaba ya jefawa mahaukacin karensa me tsananin girma da munin kallo tareda tsoron kalla Wanda yaci ya ginu da cin zuciyoyin mutane ko wani idanuwansu. Gashashen maman Dabbar ruwa da aka kawo masa ya miqa hannunsa ya fara ci batareda ya wanke ko goge hannu ba. Yaransa ya sake dagowa ya kalla wainda adadin yawansu baisan iyaka ba dan tsananin yawansu ya bude baki muryansa me tsananin kauri da rashin dadin saurara yace ‘Idan gari ne a dajin nan kaman nisansa daga yanzu ya zama na kusra, Dukkanin me rai tin daga kan dan Adam har dabbar datake da rai sun zama a cikin lissafin kusra, Wannan Karan bayin na musamman ne sbd lokacin da kusra zata gina Masarautarta da qasa me sunan kusra yayi dan kuwa bayin da masarautar BOYEM take buqata daga gareni zasu fito dan kuwa acan ne kadai zan Kai bayi na mallaki cikar Burina da aka haifan dashi, Babban burin iyaye da kakanni na Akan kusra takai matakin mallakar qasar kanta da mulkin kanta Akan siyar da bayi shine kai Bayi a BOYEM, Buri ne da kakana bai cika ba,babana bai cika ba dan haka nine zan cika wannan burin kota halin yaya, Bayin BOYEM na musamman ne sbd farashin d ake zubewa a siya Wanda yake sauya rayuwan duk me siyar da bayi, A guri daya BOYEM ke siyan bayinta bata taba sauyawa ba sbd tsaro da izzarsu dan hakan ne kusra basu taba samun wannan babbar damar ba duk kuwa qwarewansu a harkar bayi a tarihi dan hakanne duk wani kusra dayake duniya yasan burinsu da macimmarsu daya ne wato shiga BOYEM Kai bayi Wanda daga ranar da BOYEM ta siya bayi daga gurinsu sun samu yancin kafa daularsu yawo ya qare musu sedai azo daularsu a siya bayi koda zasu Kai sama da bayi rai dubu dari. Hadiye Naman bakinsa yayi yana sake bawa Kansa tabbacin wannan garin shine garin nasararsa sbd zai dauki bayi daga garin harya haura qasar baa saniba sbd a boye suke labarin harin da suka kaiwa garin bazai fita ba bare ya samu tangardar tafiya duk da baa taba kamasu ba amma bibiyan da ake musu idan ya kaiwa gari hari ya kwashe mutane yana basa Tangardar mutuwa bayinsa sosai sbd basa tsaya wa duk tsananin rashin Kyan ruwa haka suke tafiya a cikinsu batareda sun tsaya kowace qasa ba dan hakanne bayin da sukayo safara suke mutuwa sosai sbd rashin sabo amma a yanzu idan baa saniba tafiyar kwanciyan hankali zasu yi ba jigata bayi har zuwa BOYEM Wanda tsafa da Kyan bayinsa zaisa wannan Karan su samu shiga BOYEM din. Tutar bada izinin farauta ya miqa hannu ya fizgo ya daga sama cewa ‘Cikar burin kusra’ Cikin tsananin Murna da sauti me karfi na mutane masu yawan gaske ya ringa tashi suna amsa wa da ‘Cikar burin kusra’ Dajin gabaki dayansa da ruwan haka maganar ta ringa amsa wa dan haka take aka juya kan Jirgi zuwa baya inda suka baro zaa tsaya. Da Asuba suka isa inda Jirgin ke tsayawa kuma a cikin asubar suka hawo qananun Jirguna suka koma kusan su sama da dari biyu suka yada zango a cikin dajin inda zasu zauna kafin fadawa garin. #MAMUH #ROYALTY #WEALTH #LOVE #BEST MALE CHARACTER #NUAB ALMAZ BOYEM #GHAZ #KUSRAH #BEST LOVE/ROMANCE HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 09033181070 3 Daga wannan ranar burin kusra gabaki dayanta ya koma Akan ANJOM, Sun yada zango a duhun dajin kauyen ba shakka ba tsoro ba fargaba sbd babu abinda yake basu tsoro kuma daman su daji da cikin ruwa ne gurin rayuwansu, Idan suka saka Buri Akan gari to tabbas sai sun cika wannan burin ta hakanne sukai suna sukai karfi suka zama abin tsoro da shakka ga garuruwan daba manya ba, Abu na farko da suka fara fuskanta shine dajin na dauke da tarin macizai da babu Wanda zai iya tsallakewa ya wuce dajin gaba ya isa cikin hanyar garin dan sun fara rasa mutanensu sosai da dafi dan haka suka sauya mataki ta hanyar fara farautarsu amma kaman dai dajin babu abinda yake cikinsa sai tarinsu dan haka suka fara Neman hanyar shiga. Khams shugaba kuma me sarautar kusra shi kadai ne yake iya keta dajin ya shiga harya fita babu abinda ya samesa sbd tsananin abubuwan dake jikinsa na tsari da kariya daga kakanninsa, Dan haka shi kadai da Kansa ya shiga yayi tafiya me Nisan data daukesa kusan wani daya sai gashi a farkon garin ANJOM Wanda ya sakasa tsayawa cikin tsananin farin ciki yana Jin wani irin Mazarin ganin hasken samun cikar burinsa Wanda samun wannan garin zai cika masa, Jajayen idanuwansa ya rintse da karfi ya bude su ahankali yana shakar iskar garin me tsananin dadi da nutsuwa tareda kwanciyan hankalin da zai juya musu zuwa tabbataccen baqin cikin da baza su taba mantawa ba a tsawon tarihi, Juya wa yayi ya fara kallan koina dake nuna arziki a garin, Mutane daddaiku dake hidimar gabansu a farkon garin ya ringa bi da kallo wainda kowannensu yake harkar gabansa cikin farin ciki da annashuwa batareda sun Lura dashi ba sbd sanin baqon da baida shedan shigowa baqunta daga GHAZ baya taba shigowa garin. Wani iskan farin ciki da tsananin Jin dadi khams ya sake yana daga kafafunsa yaci gaba da takowa zuwa cikin garin yana Jin kaman ya kamasu a lokacin ya bude ido yagansa a bakin ruwan shiga qasar BOYEM. Tafiya yake yi yana sake Jin zalamarsa da tsananin rashin imaninsa yana fadada sbd yana qara shiga yana ganin tsananin mutanen da garin zai yi Wanda zasu cike dukkanin abinda yake nema. Ahankali daidaikun mutane suka fara kallansa suna shiga tsananin mama ki da fargaba sbd yanayin baqinsa da yayi yawa da muninsa tareda kalar kayan jikinsa da komai yake baqi babu abu ko daya dayake jikinsa dayake da wata kalar Bayan baqi. Lura da hakan ya zame ya dawo wajen gari ya fara dakun damar shiga garin har dare yayi sosai tukuna ya sulalo cikin garin yana zagaye wa ya gama Karance yanda rayuwan darensu take sedai abinda ya fahimta babu yanda zaa yi ya isa ko kusa da hanyar gidan shugaban garin Wanda a cikin Daren ya sake tabbatarda kafi ne a garin ta yanda yana buqatan karyasa kafin su samu daman shigowa su samu abinda suke so dan haka ya dawo farkon gari. Bakin wani qaramin gidan dake farkon garin ya tsaya yana zubawa gidan idanuwansa da babu komai a cikinsu sai rufe wan ido na rashin tausayi ko kadan. Kallan gidan yayi sosai kafin ya saka hannunsa jikinsa ya zaro wata wuqa baqa qirin me tsananin kaifi da dafi ya tinkari kofar shiga gidan yana isa kofar shiga wadda take ta itace kafarsa ya saka ya turata da karfin gaske Wanda take ta fadi sedai batai wani qara ba sbd kasancewanta ice ba karfe ko katako ba. Shigowa yayi Kai tsaye ya nufi dakin farko dayake gidan yana shiga dakin ya fizge labulen dake dake take hasken farin wata ya ratso cikin dakin, Yara ne su hudu a kwance jere suna bacci cikin nutsuwa Wuqar hannunsa ya daga bai tsaya komaiba ya qaddamar musu ya fito dakin hannuwansa da fuskansa duka jini ya fada Dayan dakin acan iyayen suke take ya take kan Baban da kafarsa ya soka masa wuqar hannunsa da karfi a gefen hannunsa yana fizgo maman itama ya doke wuyanta da karfi take ta yanke jiki ta some a gurin. Fizgo Baban yayi cikin tsananin karfi ya sake soka masa wuqa a gurin daya soka masa farko ya miqar dashi cikin rashin tausayi ko kadan ya dauresa ya durkusa ya dauki Matar yajasa da igaya ya fice dasu. A cikin duhun Daren ya biyo daji dasu ya Baro garin Tafiya me tsanani sukai har gari yayi haske tukuna suka samu tsallake rabin dajin zuwa me hadarin ga mamakinsa suma babu abinda ya samesu harya tsallake dasu suka sake nusawa Matar na farfadowa ya sauke ya daureta tareda mijin yaci gaba da jansu cikin Axaba da rashin tausayi ko kadan. Sai dare ya sosai ya iso wajen dajin dasu inda mutanensa suka taso suka tarbesa tareda karban masa. Azaba suke tsananin cikin musamman Baban da jininsa ke fita a hankali daga yankar da yayi masa, Maman kuma bakinta da dukkanin yawun jikinta sun gama bushewa daqyar dukkaninsu suke numfashin azaba da kafafunsu da duka sun fashe daga tafiyan. Kusrawa basu tsaya komaiba suka hau gana musu sabuwan azabar data saka kowannensu some wa amma a hakan suka cigaba da basu azabar data saka mijin mutuwa sbd jininsa daya qare qaf daga jikinsa. Duk wani sirrin ANJOM sun samesa a bakin Matar wadda azaba take daf da dauke ranta, Sun samu sanin komai da sanin asalin mene ze karya musu garin su samu shiga a bakinta batareda tasan mijinta ya mutu ba sbd ta tsiratar dasu ta fada musu abinda suke son ji. Azabarta bata qare ba sun saida suka tirsasata ta samo musu jinin GHAZ, Sbd Neman kubutar dasu mijinta ta dawo ANJOM inda ta fadi duk abinda ya faru Banda cewa mijinta na raye zata samo musu jinin GHAZ dan tseratar dashi, Da farko jinyarta akai a cikin iyalinsa sbd yanayinta da tausayin mummunan halin data shiga na rashin ‘yayanta duka da mijinta datace ya rasu batareda tasan da hasken ya rasu ba, Adalci da tsananin tausayin GHAZ Ali ya saka ya dawo da ita cikin iyalansa da qarin shakkar zasu iya dawowa su dauketa ko kasheta tinda taga inda suke. Raunika na fili da boye ne a jikinta da suke kokarin zama baraza ga rayuwarta duk da hakan tayi alkawarin tseratar da mijinta dan haka zamanta a cikin asalin GHAZ shine isharar datake ganin kaman Allah yayi mata Akan ta kubutar da mijinta sbd a farko tasan bazata taba iyawaba dan babu ta inda zata samu kusanci da ahalin GHAZ bare samun jininsu koda diqo daya ne sai gashi batareda tsammani ba Allah Kai tsaye ya shigar ita cikinsu. GHAZ Ali ya shigo da itane cikinsu shi kuma sbd ya sakata tsaro sosai ta yanda ko akwai wani abin bazata samu damar yi ba ko fita gari. ********Da wannan dalilin Asamah ta zama cikin iyalin GHAZ tareda jinya me kyau ta warke sosai ta zama tamkar amintacciyar ahalin sbd lokaci daya ja sosai hakama kusrawa suna bangaren sun kafa garin kansu sbd burinsu Wanda suke jiran ranar cikarsa. Lokaci ya tafi sosai kauna da shaquwa me tsafta ce a tsakanin dukkanin GHAZ da Asamah wadda kulawa da gabaki daya yaran gidan ta dawo hannunta duk da sun zama yan mata amma itace ke kulawa da komai nasu musamman Abaas Wanda yayi wata irin shaquwa da ita, Duk tsawon shekarun datai a cikinsu burinta Akan kubuto da mijinta bai taba fita a ranta ba duk da lokuta da dama tana Jin kaman ta hakura da hakan sbd tsoron illar da kusra zasu iya shigowa gari suyi Wanda a yanzu cikin garin ANJOM iyalan GHAZ ne kadai take dasu sbd tausayinta daya zamo kauna me karfi a gareta. A yanzu da shekaru suka ja kusra hakurinsu ya fara qare wa dan haka ahankali suka fara farautar duk Wanda zai fito daga garin dama hanyar makusanta hanyar dajin garin ta yanda gabaki daya nahiyar ta zama ta gagari kowane dan Adam bi a tahiri sbd duk Wanda ko hanya ta biyo dashi ta nahiyar ko gawarsa baa samu dan haka duniya da dukkanin nahiyar tarihi bin nahiyar ya zama tamkar tarihi sbd gabaki daya zagaye suke da dajin ANJOM Wanda ya koma babu shiga dajin babu fita dan haka rayuwar ANJOM ta fara shiga wani irin halin tsanani da rashin kwanciyan hankali da fargaban ko Yaushe komai ze iya faruwa garesu. Tin masifar na waje dajin nasu harta fara shigowa sbd kisan yayi yawan da a bakin gari suke samun gawarwakin mutanensu. Wannan tashin hankalin ne ya saka GHAZ fara tinanin iyalinsa da bazai iya barin wannan masifar dake kokarin afkowa ANJOM ta shafesu dan haka yasa aka fara Ramin fita garin ANJOM ta baya ta inda yake saka ran babu kusrawan zuwa ruwan dazai iya kaika nahiyoyi da dama dan tsira. ************ Zaune suke a wata irin lafiyayyan rumfar hutawarsu kowannensu na Zaune gurin cike da yayan marmari masu kyau sai qatuwar kwaryar dabino da shima yake da daukan ido. Ayanah ce kadai bata gurin sbd shirinta dayake daukan lokaci dan haka tana fito wa tareda baiwarta daya Sakeena dake biye da ita. Rumfar ta tinkaro a natse cikin takun dayake bayyanarda tsananin nutsuwarta da mulki yake ciki, Qarar sarkar hannunta data kafarta me fidda dan sautin daukan hankali ce ta saka Asamah dake sake jere Kayan marmari fara dagowa ahankali ta sauke idanwanta Akan hanyar tana zubawa halittar Ayanah dake daukan idanuwa duk Wanda zai kalleta ido Tana ambatar Masha Allah Masha Allah cikin zuciyar. Abaas ne ya juya ahankali shima yana kallan Ayanah din yana zubawa kyakkyawan fuskanta ido yana Godiyan Allah ako Yaushe da Ayanah ta kasance jininsa wadda yakejin kaman jinin da suka hada bai ishesa ba yana tsananin son ace ya sake hada wani abu da ita Wanda zaisa ace yafi duka Sauran yan uwansu kusanci da hada jini ita. Ganin idanuwansa akanta kaman koyaushe yana kallanta cike da kauna me tsanani ta jini bude bakinta tayi wani kyakkawan murmushi ya mamaye fuskanta har saida hakoranta suka dan bayyana ta qaraso gurin tana miqa masa hannunta dayake sanye da fararen azurfa masu kyau da rashin sirki. Kama hannunta Abaas din yayi cikin kulawa yana sake nasa murmushin me kyau daya qawata tasa fuskar dasuke tsananin Kama dan shi Kansa kyakkyawa ne da ake fadarsa a garin ANJOM Wanda lokuta da dama iyayensa ke tinanin bakin mutane ne ya saka ya kasance me rauni. #MAMUH #ANJOM GHAZ #AYANAH GHAZ #ABAAS GHAZ #BOYEM #BEST ROYALTY/BEST LOVE/BEST ROMANCE HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 09033181070 4 Zaunawa Ayanah tayi gefen dan uwanta tana kallansa Fuska cike da murmushi da sakewa tace ‘Godia nake GHAZ Abaas’ Dariya yayi yana sake hannunta yana cewa ‘Ayanaah…. Katsesa Zuhrah tayi batareda ta Bari ya fara fadar maganarsa da ako Yaushe take ta yanda yake Jin bazai iya rayuwa ba Ayanah bane wadda koyaushe damuwansa wani lokacin ta yanda zatai sure wata ran ta tafi tabarsu. Dariya dukkaninsu sukai ganin yanda ya juya ya harari zuhrah cikeda kauna itama sbd yanda ta katsesa da cewan sun gaji da maganarsa daya kullum. Fararen idanuwan Ayanah ta juyo ta sauke Akan fuskan mahaifiyarsu dake Zaune Nurat na kwance jikinta ta bude baki tace ‘Amma Barka da hutawa,kin tashi Lfy?’ Hannu Amman ta miqa ta Shafa fuskan Ayanah din tana Jin tsananin son yarta tace ‘Barka Ayanah ghaz,kin tashi Lfy kema’ Murmushi tayi tana dan Dora tafin hannunta Akan hannun Amman dake kan Fuskanta tana Jin kaman ta hadiye tace ‘Lafiya kalau Amma’ Juya wa tayi tana kallan zuhrah tace ‘Ki Dena damar mun da GHAZ Abaas sbd baya buqatan gorinki tareda dashi zan tafi duk inda zani kokuma na zabi zama a cikin ahalina har karshen rayuwata’ Nurat Baro jikin Amma tayi ta dawo gefen Ayanah ta lafe jikinta tana Jin kaman ma hakan ya kasance a rayuwar su kada suyi aure su rabu su tabbata a tare har abada Bude baki tayi tana kallan Ayanah data kalleta cikin sanyi tace ‘Ayanah inason na tabbata tareda ku duka mu tsufa mu mutu tare banason ko aure ya rabamu, Zan cewa Abaa(mahaifinsu) koda zamuyi aure abarmu da mazajenmu muyi rayuwa a cikin GHAZ batareda munje kowane gida aure ba’ Wani iri Ayanah taji a zuciyarta na Ina ma hakan zata kasance datafi kowa farin ciki sbd yan uwanta sune rayuwarta amma kuma kaman hakan bazai yiyu ba, Numfashi ta sauke tareda Kai bakinta cikin kauna ta sumbaci tsakiyar kan Nurat din tana Shafa gefen fuskanta tace ‘Nurat babu abinda zai raba mu a duniyar nan Bayan mutuwa sbd kune rayuwata’ Amma datake Jin kaman kada ta taba aurar ‘yayan nata sbd ganin baza su iya kowace rayuwa batareda junansu ba wani irin sanyi jikinta yayi ta Kama hannun Ayanah takai bakinta ta sumbata tana kallanta tace ‘Kece rayuwansu suma musamman a lokacinda zaku samu Kanku ba iyaye idan tsufa ko mutuwa tazo dan haka Ayanah kici gaba da zama uwa kaman yanda kike kaman mahaifiyarsu a yanzu’ Qurawa Amman idanuwa Ayanah tai tana Jin zuciyarta na sake cika da tsananin kaunar mahaifiyata, Gyada Kai tayi tana kwantawa jikin Amman batareda ta iya cewa komaiba. Abaas ne dayake Jin a jikinsa shikam da Ayanah baza su taba rabewa ba koda basa a raye sai yana Jin kaman baza su rabu ba dan kuwa tsananin so da kaunar dayake wa Ayanah da aure ya Halasta a tsakanin yan uwa to da bazai taba barin kowa ya dauke masa Yar uwa ba zata zauna a karkashinsa koda ba aure zai killaceta ya Hana kowa koda ganinta sbd kada kowane ido yayi mata illa, Duk da ba aure tsakaninsu yanada Alkawari da fatar duka yayan dazai haifa a rayuwarsa su hada jini Ayanarsa, idan kuma mace Allah zai basa to adduarsa koyaushe a cikin ibadarsa shine ta kasance tamkar Ayanarsa koda hakan shine burinsa na karshe yana fatar Allah ya cika masa shi koda a ranar mutuwarsa ce. Asamah da dukkanin jikinta yayi tsananin sanyi da kaunar ahalin GHAZ din da baka gane wane yafi wani kaunar dan uwansa Jin takeyi Inama nata ahalin sunanan da yayanta zasu yi girman su zuhrah da Abaas sbd itama ‘yaya mata biyu ne da ita sai namiji daya kaman Abaas, Hawayene masu tsananin zafi da radadi suka ciko idanuwanta ‘dacin rashinsu na taso mata Wanda daman a tsawon shekarun nan bata taba manta radadin ba koda na qanqanin lokaci ba, Hadiye hawayenta tayi sbd kada su bayyana a gabansu. Juya wa tayi Bayan ta gama jere komai ta kalli kakkaifar qaramar wuqar dake kan Kayan da zata bar gurin dasu ta yanka Kayan marmarin taga yanda take daukan ido, Zuciyarta ce tahau Kai kawo cikin tsananin qunci da baqin cikin daya taso mata na rashin yayanta da tsananin buqatar son dawowan mijinta gareta Wanda zuwa yanzu tasan azaba ta dade da sauyasa zuwa wata mummunan halittar amma tanason abinda a hakan. Shedan da zuciyarta dake rufewa idan abin ya taso mata Wanda yake tamkar tabin kwakwalwa batareda sanin kowaba suka saka zuciyarta rufewa tafara taku daya na biyun ta saki gabaki daya Kayan hannunta a jikin Abaas Wanda wuqar ta yanki gefen qafarsa take jini ya fara fito wa Wanda ya saka dukkaninsu miqewa cikin tsananin tashin hankali da damuwa Asamah ma cikin tashin hankalin da tsoro me tsanani ta zube gabansa tareda rigan kowa saka hannunta a kafarsa tana wani irin rawar jiki da kukan dayake fito wa daga qasan ranta tana basa hakuri cikin kulawa sbd a qasan ranta tasan kofar wata rayuwar ce zata bude wa duk Wanda yake garin ANJOM wadda bata San wace iri bace dan kuwa a gefen rigar jikinta ta goga jinin me yawa daga qafar Abaas batareda lurar kowa ba. Cikin sauri sakon fitar jini a jikin GHAZ Abaas ya isarwa Abaa dinsu wanda ba bata lokaci ya iso gurin Wanda ya saka duk Sauran bayin dake zagaye da gurin na kowannensu dake rumfar ja baya sosai cikin girmamawa. Wuqar da jininsa ya taba ya fara bada umarnin a karba hakama take aka kawo ruwa masu yawa a babbar tasa me kyau aka saka Asamah wanke duka hannuwanta da jinin Abaas ya taba kafin take GHAZ Ali din da Kansa yasa aka kawo magani ya karba yana kallan Abaas din Wanda hankalinsa yake son tashi sbd fitar jininsu tamkar hadari ne ga dukkanin ANJOM gabaki daya sbd da jininsu ne kadai ake iya karya komai dake ANJOM dan haka Sam baa taba yadda da kowa ba game da duk wani digon jinin GHAZ. Amma ganin Asamah ce ta raunanasa bada ganganba kuma tamkar ahali take sai hakan na hana zuciyarsa shiga tashin hankali da tsoro sosai. Kukan da Asamah ke yi ya saka Ayanah rarrashinta tareda Zuhrah Nurat da Amma kuwa suna jikin Abaas din cikeda damuwa suna kallan yanda GHAZ ya saka masa garin maganin da take jininsa ya tsaya ya Dena zuba. Ajiyan zuciya GHAZ ya sauke yana dagowa ya kalli Abaas din cikeda kulawa da qara tabbatar masa da tsananin mahimmancin jinin dayake yawo a jikinsu. Cikin nutsuwar mulkin dayake yawo jikinsa da kulawa tareda tabbatarda kiyayewa GHAZ ya bude baki yace ‘GHAZ Abaas ya koma dakinsa a tabbatarda an kiyaye danyen yankan kafarsa ta warke da kyau batareda ya sake fitowa ba’ Gyada Kai kowa yayi suna amsa wa da cewa ‘Angama’ Juya wa yayi ya bar gurin kowa yayi tsit cikeda damuwa da alhini har saida ya fice kwata kwata kafin Abaas din ya dago ya kalli Asamah kaman zai yi magana sai bai ce komaiba ya maida idanuwansa Akan Ammansa dake miqewa tabar gurin tana bin Bayan GHAZ Ayanah kuma hannu ta miqa masa ya Kama ya miqe suka nufi hanyar dakinsa tana cewa ‘Yankan qaramar wuqar cin tufa bazata girgiza jarumin anjom ba GHAZ din anjom me zuwa’ Yar dariya yayi yana kallan kafar tasa tareda cewa ‘Shekarun nawa basu Kai ba ai tukuna amma insha Allah idan nakai shekaru ashirin a duniya zan fara fita a matsayin jarumin na anjom wata ran harma na zama Garkuwa ga dukkaninku’ Har cikin ranta taji dadin abinda ya fada tana fatan hakan koda kuwa a mafarki ne. Rakasa tayi dakinsa Wanda acan suka zauna ta tayasa fira sai ga su Zuhrah da Nurat sun taho suma sbd sunsan saiya kwana biyu kafin ya fito koina sbd tsaro da dokar GHAZ din tin asali duk Wanda yake jinin GHAZ yaji rauni har jininsa ya fita to saiya kwana biyu a killace batareda fito wa koina ba sai Raunin ya qame, Hakan ne ya saka yan uwansa zuwa dan tayasa fira da debe kewa, Kayan ciye ciye da dafaffiyar madarar raqumi me dumi aka kawo aka ajiya musu sunata firarsu da hutawarsu cikin kwanciyan hankali da nishadin farin cikin kansacewa da juna, Anan suka wuni dan hatta ibadarsu anan sukayita, Da yamma ma mahaifinsu shigowa yayi cikinsu cikeda Shakuwa da kaunar juna suka cigaba da farin cikinsu anan cikinsu yayi sallah tareda iyalansa har cikin dare tukuna dukkaninsu suka watse kowa ya nufi makwancinsa. Ayanah na isa dakinta zare Kayan jikinta tayi ahankali tana rufe jikinta duka ruf da wata kakkaurar doguwar rigar wanka me Kama da alkyabba amma ita ta yadin saka me kyau. Baiwarta Sakina ce take biye da ita dauke da wutar haskawa. Gurin wankansu ta Nufa Wanda yake cike da ruwa masu tsafta da kullum ake sauyawa ta zare rigar tana zaunawa gaban ruwan tafara wanka a natse. Sakina ajiye mata hasken tayi ta koma kofa ta tsaya daga waje tana jiran fitowarta. Gama wankan tayi ta fito tana qamshin madarar flower me dadi. Dakinta ta shiga ta zauna Sakina tana tayata goge jikknta harta gama ta shirya ta nufi lafiyayyan gadonta na sarauta ta haye. Washe gari ma haka suka wuni gurin Abaas tareda iyayensu Wanda kwata kwata GHAZ ayau din bai fita koina ba yana cikin yayansa tausayin Abaas haka kawai yake shige masa zuciya sbd ganin kaman zuciyarsa tayi sanyin da bazai iya mulki ba idan ma yayi wahala zaisha sosai, Akan ‘yayansa mata ya maida idanuwansa yana kallan yanda suke dariya suna Wasagu da juna sautin dariyarsu na shiga kunnuwansa zuciyarsa na na cikewa da tsananin kaunarsu yanajin kaman ya maidasu cikin Mahaifiyarsu sbd basu tsaro da kariya daga dukkanin wata cutar duniya da wahala. Akan Ayanah ya tsayar da idanuwansa dariyarta na a bayyanarda asalin zallan Kyan da Allah yayi mata Wanda yasa Sam baa barinta fita daga GHAZ din itama, Ayanah nada zuciya me sanyi da hakuri tareda juriya tareda jajircewa Akan ‘yan uwanta Wanda yasa yakejin kannenta sun dace dan kuwa tamkar uwarsu haka take kulawa dasu, Akan Zuhrah ya maida idanuwansa yana kallan gashinta dayake sake zube a bayanta Wanda babu namijin da zai kalleta bata fizgi hankalinsa ba dan haka yake killace dukkanin wata al’aurarsu sam baya barin ko yatsar hannuwansu wani na waje na gani sbd a sujjarsa gabaki daya adduar ‘yayansa ne. Ahankali jikinsa na mutuwa ya daga hannunsa ya miqa akan Zuhrah ya fara tattare gashinta cikin kulawa ya daure mata yana janye mayafinta me ado dayake gefenta ajiye ya rufe gashin nata. #MAMUH #GHAZ #KUSRAH #BOYEM #ROYALTY #BEST LOVE HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 09033181070 5 Dago Kai Zuhrah tayi ta kalli Abaa din tana Dora hannunta akanta ta taba mayafin daya rufe kanta dashi tana zubawa mahaifinta ido ta bude baki zatai magana ya Dora hannunsa daya akan bakinta ya girgiza mata Kai ya bude baki yace ‘Kanki ya kasance koda Yaushe a rufe Zuhrah ghaz’ Gyada kanta tayi batareda ta dauke idanuwanta daga Kansa ba sbd ganin wani irin kallan tsananin kaunar dayake mata. Tsakiyar kanta ya sumbata yace ‘Albarkar Allah ta tabbata a rayuwanki Zuhrah koda yan uwanki duka’ ‘Amin Abaa’ ta fada tana matsowa sosai jikinsa ta zauna. Nurat ya maida idanuwansa ya kalla wadda take jikinta yayi sanyi sbd itace tafi kowa saurin kamuwa da yanayin da duk ya sauya, Ta fisu saurin hawaye da zama emotional sbd tanada qawazuci sosai na iyayensu dan haka hannunsa ya miqa mata ta taso daga gefen Abaas ta dawo gefensa ta kallesa idanuwanta na raurau haka kawai. Wani murmushi me sanyi da kyau ya dake yana Shafa fuskanta ya girgiza mata Kai yace ‘Jarumar ‘yata Nurat bata barin jikinta yayi sanyi a kowane yanayi’ Murmushi ta sake tana Kama hannunsa qamqam tace ‘Abaa ina fatan na kasance hakan daka fada koba yanzu ba’ ‘Insha Allah Nurat zaki zama jajirtacciya dakakkiya bazaki taba gazawaba insha Allah’ Maganarsa ta saka Ammansu kallansa tana dan murmushi batareda tace komaiba. Qarasa fitar da wunin sukai cikin tsananin kaunar dasuke Jin tafi ta koyaushe musamman da mahaifinsu yaketa yabonsu yana kasa dauke kallansa akansu cikeda kauna hakama Amma Jin takeyi tana sake kaunar mijinta sbd yanda ya tarbiyantar da ita da yayansu. Da daddare Bayan sunyi sallah ishai Abinci da Kayan marmari aka kawo aka Jere musu tareda fitilun wutar ishen flower masu sanyin kamshi da aka kewaye gurin dasu suna basu haske tareda kamshi. Dagowa GHAZ yayi ya kalli sakina baiwar Ayanah dake gefensa ya bude baki yace ‘Ina Asamah gabaki daya yau ban ganta ba’ Sunkuyar da Kai sakina tayi cikin girmamawa ta bude baki tace ‘Tin jiya bata fito ba babu Wanda ya ganta a yau sbd damuwan abinda ya faru da GHAZ Abaas’ Kallan Amma GHAZ yayi yana Neman qarin bayanin hakan Kallansa tayi itama cikin kwantar masa da hankali tace ‘Tashiga damuwa sosai ne har dare jiya tana gurina tana kukan Neman Gafara da Afuwan abinda ya faru dan hakanne yau Kowa ya kyaleta ta dawo daidai’ Shiru yayi sbd bayason nuna damuwa ko fada a cikin iyalansa dan haka baice komaiba sbd duk tsawon shekarun nan bai taba dauke saka Idonsa da saka taka tsantsan sosai akan Asamah ba dan haka tin jiyan da jinin Abaas ya fita yake Jin rashin nutsuwa amma baya iya nunawa sbd yanzu suna cikin wani hali ne na kusrawa dake Neman kawo musu hari kowane lokaci suka samu damar hakan. Abinci suka ci suna fira da nishadinsu har suka gama nanma suka ci gaba da firarsu har dare sosai kafin Abaa da Kansa ya raka kowacensu dakinta da Kansa kafin ya dawo ya tafi da Amma dakinsu itama tukuna ya fito ya dawo dakin Abaas sosai kafin ya fito ya shige shima. Tsakiyar dare sosai Nurat dake kwance taba bacci cikin kwanciyan hankali da nutsuwa ta farka da karfi cikin mummunan faduwan gaba sbd mummunan mafarkin datai. Bude idanuwanta tayi ahankali tana sauke ajiyan zuciya a sanyaye kafin ta tashi Zaune tana Jin rashin nutsuwa, Shiru tayi tana Dora hannunta kan kirjinta dake bugawa sosai cikin rashin Jin dadi, Koma wa tayi ahankali tana kokarin kwanciya taji motsi me karfi daga waje dan haka gabanta ya sake faduwa ta zuro kafafunta qasa da sauri tana saukowa gadon tareda daukan mayafi tana Daurawa akanta ta nufo kofa tana bude kofar ta fito Kai tsaye batareda tsoron duhun Daren ba. Takawa tayi Kai tsaye ta nufi dakin Ayanah sedai kafin ta isa dakin wani irin jan haske taga yana gauraye saman garin na alamar wuta. Saman ta ringa kalla tana nufar dakin sai kuma hayaniyar tashin qara daga nesa Wanda ya sakata qarasawa dakin da sauri tanajin tsoro na shigarta. Tura dakin tayi ta shiga da sauri ta qarasa gadon Ayanah ta haye gadon tana shigewa jikinta ta qanqameta. Cikin bacci Ayanah taji Nurat cikin jikinta wadda tasan itace Kai tsaye sbd itace Kai tsaye take zuwa lokuta da dama cikin dare gurinta idan ta kasa bacci. Numfashi da ajiyan zuciya Ayanah ta sauke tana Shafa kan Nurat din sedai kafin ta bude baki tayi magana aka sake turo dakin cikin wani irin sauri da karfi. A tare suka miqe Zaune cikin faduwan gaba da mamaki, ‘Abaa’ Ayanah ta Ambaci sunan mahaifinsu dake shigowa da qaramin hasken wuta a hannunsa. Nurat ma cikin fargaba tace ‘Abaa’ Qarasowa yayi da sauri batareda ya amsa su ba Amma na gefensa da hasken itama jikinta na tsananin rawan mummunan tashin hankalin da basu taba samun kansu a ciki ba tsawon tarihin GHAZ. Riga me tsananin kauri ya janyo a cikin Kayan Ayanah ya miqa mata cikin kokarin hana mummunan tashin hankalinsa fita sbd kada su firgita yace ‘Saka wannan Ayanah’ Karba tayi hannuwanta na dan rawa tana sakawa akan kayanta tace ‘Abaa meya faru ne?’ Bai amsata ba ya janyo wata rigar ya saka a hannun Nurat dake sake shiga rikici idanuwanta na raurau Amma ce ta taimakawa Nurat din gurin saka rigar Abaa ya Kama hannunsu su biyun ya nufo kofa dasu wannan Karan Amma ce riqe da hasken gaba daya. Dakin Zuhrah suka isa wadda take bacci sosai hankali kwance Cak Abaa ya tadata Zaune Wanda ya sakata bude ido tana sake lumshewa zata zame ta sake komawa kwance ya miqar da ita gabaki daya yana cewa ‘Ayanah samo mata Riga me nauyi sbd sanyi’ Da sauri Ayanah ta nufi Kayan Zuhrah din ta dauko Riga da sauri ta kawo tana miqa masa Da Kansa ya sakawa Zuhrah din yana Kama hannunta itama suka fito. Dakin Abaas suke kokarin nufa wani irin kuka da Ihun mutane mara dadin saurare ya sake tsananta yana gauraye garin tareda qaruwar hasken wutar dake cin garin sosai. Sai a lokacin bacci gabaki daya ya sake su Ayanah suka shiga tsoro da faduwan gaba me tsanani suna kasa ma tambayan meya ke faruwa. Abaas ma baccin yake Ayanah ce tayi saurin isa gurinsa ta tadashi da sauri dukkanin jikinta na rawa. Fitowa sukai Abaa yaja su zuwa kofar baya ta fita gidan ya tura su wani daki tareda dukkanin bayin gidan mata ya kalli Amma batareda yace komaiba ya qanqame hannunta ya kalli Ayanah itama yace ‘Ku kula karku fito saina dawo Idan kuma kunji shiru ban dawoba ku fita ta baya akwai hanyar dana tanadar muku ta barin gari ku bi karku tsaya sai kun fita ruwa gabaki daya kun fada nahiyar yom acan zaku samu rayuwan kwanciyan hankali idan har kuka fadawa sarkin garin ku GHAZ ne. Shiru sukai dukkaninsu Banda Ayanah da Amma da suka riqe hannunsa suna girgiza kai, Nurat da Zuhrah tareda Abaas kuwa cikin tsananin tashin hankali da wani irin firgici suka ce ‘Abaa ina zaka? Karka fita dan Allah kazo mu tafi din bama sai mun jira ba dan Allah Abaa’ Girgiza kai yayi yana kallansu da jajayen idanuwansa da suke rine da tsananin ‘daci da baqin ciki yace ‘Ni shugaba ne ta yaya zan tafi nabar mutane na batareda nasan meya ke faruwa a garin ba…….. Katsesa Amma tayi cikin wani irin mugun tashin hankali muryanta na rawa zufa na tsiyayo mata da cewa ‘Koma menene ba alkhairi bane sbd Ihu da kukan da garin gabaki daya ya dauka ya tabbatarda hakan, Masifa ce da balai a garin yau karka tafi dan Allah ka tsaya’ Zare hannunsa yayi cikin nata idanuwansa na sake kada wa jajir. Cafke hannunsa Ayanah tayi tana fadawa jikinsa ta qanqamesa wasu hawayen tashin hankali me tsanani suna kufce mata a rikice tace ‘Abaa dan Allah karka tafi mu tafi mubar garin tare bazamu iya tafiya koina babu kai ba’ Nurat ma qanqamesa tayi Zuhrah ta fada jikin Amma tana qanqameta Abaas ma Abaan ya riqe yana wani irin rawar jikin tashin hankali da tsoro take ya fasa kukan daya saka Abaan kallansa yanajin tsananin tausayinsa. Banbare Ayanah da Nurat yake a jikinsa suna qanqamesa Ayanah tayi fashewa da wani irin kukan da bata taba sakewaba a rayuwarta tana ambatar sunan Abaan. Fincikesu yayi da qarfi yana hana zuciyarsa karyewa ya turasu jikin Amma ya fice da sauri yana janyo marufin dakin. Rawa da kuka sukeyi sosai Wanda gabaki daya gurin yayi tsit sai sautin kukansu dake tashi ahankali cikin mummunan tsoro,fargaba da tashin hankali. Masifa,balai da kaddara ne suka saukarwa garin ANJOM a cikin Daren dayake na farko a tarihinsu da wannan masifar ta fadowa garin, Wuta ce take ci tako ina zagaye da garin Wanda saida kusrawa suka gama cinnawa zagayen garin wuta sosai koina ya Kama sannan suka shigo cikin silalowa suka sakawa koina wuta a cikin garin kafin suka afkawa garin da wata irin mummunan kisan da take jini yafara fesuwa koina na mutane. Ihun da kukan Neman agaji da ceto mutane suka fara Wanda ya saka gabaki daya garin daukan hayaniyan Data saka kowa fitowa Ana gudun Neman ceto sedai yawa da karfin da kusrawan ke dashi ya saka munin lamarin yayi yawan da komai ya lalace. Kukan kananun yara dana mata da dabbobi ma dake gudun cetan rayuwansu ne yake gauraye gari da dajin ANJOM dayake amsa wa cikin sauti mara dadi da karya zuciya tareda tsananin tausayi. Wuta kuwa haka take cin wasu mutane harma da dabbobi sbd gobara sosai garin ya dauka kowane gida sakawa wuta sukeyi sbd kada ma mutane su samu gurin boye dan haka komai ya zama tashin hankali mara misali lokaci daya. GHAZ da fadawansa da askarawansa koda suka fito dan bada ceto ga jamaar gari lamarin ya gama munanar da babu abinda zasu iya sbd Angama cinye garin ANJOM da wuta da jinin mutane dan haka take suka fara cetan wainda zasu iya cikin azabar wuta da tashin hankalin munin gawawwakin mutane da suke tsallakewa da takawa. #MAMUH #ROYALTY #SLAVERY #BEST LOVE HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 09033181070 6 *_PRIME SCENT_* 08103155915 Shin Kina neman duniyar kamshi ta turarukan wutan da in kin kunna zaki ji ki kamar a Royal palace din larabawa? Ko kuma kina neman wanda zaki kunna ya kaiki garden full of vibrant, mind & soul soothing fresh scents? Ko kuwa wanda zai baki rich and luxurious scent na elites? Ko kuwa kina neman qamshi mai sauke fushi da gajiyar da oga ya kwaso ne? Are you looking for qamshin da duk inda kika shiga sai kin janyo attention din mutane, ko kuwa wanda in an matso kusa dake sai an lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya na jin dadi da kwanciyar hankali tare da samun nutsuwa? Hajiya ta albishirinki! Ga PRIME SCENT Duniyar kamshin da babu kamarsa, Duniyar kamshin da ko kin bada kayanki ko curtains naki wanki baza su Dena bada kamshi me nutsuwa da dadin shaqa ba, PRIME SCENT sune kankat ba na biyunsu. 08103155915 ******** ********** Wani irin zufane yake jiqa Dukkaninsu zuciyoyinsu kaman zasu fado sbd munin tashin hankalin dasuke ciki, Cikin duhun hasken wutar daya kusa cinyewa Ammah ta dago Idanuwanta da sukai jajir da hawaye masu karya zuciya ta kalli Ayanah kafin ta maida kallanta kan Sauran ‘yayan daya bayan tana hana hawayenta saukowa fuskanta sbd zuciyoyinsu duka a karya suke batason qarasa karyasu gabaki daya. Juya kanta tayi ta kalli kofar dakin zuciyarta na kasa jurewa ta juyo ta sake kallan Ayanah wadda tayi saurin riqeta cikin mummunan tashin hankali ta bude baki da wata irin murya mara karfi cikin yarensu tace ‘Aāyi Amma, ātadirigi Amma, dan Allah Amma karkiyi hakan, āyi Amma.’ Hawayen da Amman ke riqewa ne suka gangaro cikin tsananin karyewan zuciya ta kalli Ayanah din tace ‘Ayanah dole zan dubosa sbd da hakan zamu tsira gabaki dayanmu’ Wani irin rikitaccen kukan tashin hankali me tsanani Ayanah ta sake tana rintse idanuwanta tareda sake qanqame hannun Amman tana girgiza akai ko magana ta kasa, Nurat datake qame tin Bayan biyar Abaansu riqe hannun Amman daya tayi Tana girgiza kai itama hawaye masu tsananin zafi na gangarowa daga idanuwanta. Abaas dake rungume dashi da Zuhrah saurin fadawa jikin Amman yayi ya rungumeta shima dukkanin jikinsa na rawa yace ‘Amma babu inda zaki tafi’ A rufe murya na rawa Zuhrah tace ‘Abaa ya tafi zai dawo Amma mu jirasa dan Allah karki tafi, Idan kin tafi zan biki mu dubosa tare’ Turesu tayi daga jikinta tana kasa kallan kowannesu tace ‘Ku jira zan dawo, Ayanah ki kula dasu karki Bari kowa ya biyo koda ban gansa ba zan dawo’ Sake riqeta Ayanah tayi Tana girgiza kai hannunta na rawa sosai muryanta na sake mutuwa kukanta na bayyana tace ‘Amma bazan iya ba dan Allah karki fita, Amma bazan iya ba, Āyi Amma dan Allah’ Zare hannu Amman tayi tace ‘Ayanah zaki iya yanzu fa zan dawo, Nima idan na dade ku tafi kawai zamu taho daga baya ni dashi mu sameku acan Kawai ki tabbatarda kin kula dasu sbd kece uwa a cikinsu kinji?’ Kasa cewa komai Ayanah din tayi kukanta na qaruwa tana girgiza kai jikinta na rawa sosai, Su Zuhrah ma kuka sukeyi sosai suna qanqame Amman hankalinsu a tsananin tashe tsoronsu na sake bayyana. Sake daukan Ihun tashin hankali da tsananin tsoro garin ke dauka hakama wuta tako ina Wanda ya saka Amman kasa riqe kanta sbd tana buqatan janyo GHAZ subar garin dan kuwa ba lallai su tsira ba hakan kawai ya hakura su tafi kawai dan tseratar da ahalinsu. Tsoronta cirewa yayi tana Jin tsananin buqatan dawowansa su bar garin ta qwace daga riqon da yayanta sukai mata ta fice tareda janyo kofar da sauri ta rufe tana cewa bayin dake ciki tareda su suriqe su karsu Bari kowa ya fito. Kai tsaye Amman na fitowa gidan taga masifar fata saka kafafunta daukan wata irin rawar tsoro da firgici zuciyarta na Neman bugawa da sauri ta dafa bango sbd jirin daya debeta na ganin wuta koina da jini kaman bana mutane ba. Bangon dafa jini ne taji a tafin hannunta da sauri ta janye hannunta jikinta na sake daukan rawa. Juyawa tafara yi kafafunta na Neman kasa daukanta tafara baza ido Tana kwada kiran GHAZ Wanda bazai taba jinta ba koda yana kusa sbd karfi da qarar wuta da Ihun mutane da gurnanin rayukan da basu gama fita kirjin mutane ba, Taku kadan tayi Tana kutsa hanyar da mutane ke fitowa suna gudu baa hayyacinsu ba Ana ture juna, Bata ganin komai sai hayaqi da tsananin hasken wuta dake Kama mutane Tana kashe idanuwanta ga wani irin Zafin azabar da basu taba Ji ba dan haka ja da baya ta fara Tana wani irin Ihun kiran GHAZ. Gadan gadan kusrawa sukayo bangaren suna sarar mutane tako ina Ana gudu da Ihun mafi munin tashin hankali. Bude baki tayi Tana sake yin baya da sauri Tana kokarin ambatar GHAZ data hango yana fitowa gurin da gudun shima dauke da wasu yara qananu guda biyu duka mata Bude bakinta batareda maganarta takai ga fita ba wani irin mashi mai tsinin gaske ya keta wuyanta ya shiga makoshinta ya fita ta baya. Cak GHAZ daya kawo daf da ita ya tsaya yana cin wani irin birki idanuwansa a kafe sbd mummunan tashin hankali da firgici mafi munin rayuwansa. Sakin yaran hannunsa yayi yana tarota da sauri ta fado jikinsa babu rai idanuwanta a bude….. Jininta ne ya fara gangarowa daga wuyanta zuwa tafukan hannunsa dake tallafe da ita, Mummunan rawa dukkanin jikinsa keyi daya kasa riqeta din ta zame daga jikinsa. Rufewa idanuwansa sukai baya gani amma a hakan ya miqe ya sunkuceta ya Dora a kafadarsa ya Kama hannuwan yaran da hannunsa daya suka bar gurin da wani irin mummunan tashin hankali sbd gari kam an gama cinyesa wutar ta kawo gurin su sosai dan haka yake tsananta gudu. Gida ya nufa da tsananin tashin hankali sabo sbd dai dole yabar garin da yayansa sbd kowane lokaci zaa iya kashe su ko kamawa sbd wutar harta fara shigowa gidan nasa sosai. Yana shigowa ajiye gawar Amma yayi daga gefen dakin ya fizge rigarsa ta sama me dan kaurin saqi ya rufeta da ita. Ihun shigowan mutane dake Neman hanyar tsira ne da Ihun wainda wuta ke ci ne ta cike gidan nasa dan haka da gaggawa idanuwansa jajir fuskansa duk jinin Amma daya dauko koina ya bata fuskansa hakama hannuwansa da jikinsa koina jini ne. Tura kofar dakin yayi da karfi Wanda ya saka dukkaninsu miqewa tsaye cikin tsananin firgici da tsoro, Nurat ce ta fara cewa ‘ABAA’ cikin mummunan tashin hankali Tana nufosa da gudun gaske ta fada jikinsa. Abaas ya miqawa hannu ya Kama ya janyosa hakama Zuhrah koina jikinta wani irin mazari ya dauka ta fara ja da baya tana fita hayyacinta, Ayanah ma jinin jikinsa da fuskansa take kallo Tana kasa hawaye ma sai rawan jiki da jajayen ido, Fizgo Zuhrah Abaa din yayi yana cewa Ayanah ‘Muje,ku fita da sauri,Kuyi sauri ba lokaci’ Daqyar Ayanah ta iya bude bakinta daya bushe qayau sbd masifar tashin hankali tace ‘Abaa Amma bata nan,taje nemanka, Ina zamu ba tareda ta dawo ba? Qin kallanta Abaan yayi ya Kamo hannunta itama da karfi ya fito dasu Sauran mutanen da zasu samu kubuta tareda su suna biye dasu. Nurat dake da kokarin wucewa kaman ance ta juya idanuwanta suka sauka akan gawar Amma dake shimfide fuskanta kawai ne a rufe abin hannunta ta gane take ta tsaya cak tareda cewa ‘AMMA’ cikin wani irin sanyi da mutuwan jikin kasa yadda. Ayanah ce ta kalli gurin da sauri itama Tana Jin jininta na Neman kafewa, Abaas ne ya kwace daga riqon mahaifinsa ya nufi gurin da gudun gaske yana isa ya yaye rufar take ya some a gurin, Nurat ma silalewa tayi a gurin some sbd kasa dauka da zuciyar su tayi Ayanah ma salalewa qasa tayi zuciyarta na Neman bugawa ganinta yana disashewa Abaa yayi saurin dagota da karfin gaske shima zuciyarsa radadin gaske take kaman zata Dena bugawa amma sbd su bazai iya karyewa a lokacin ba sbd kubutar da rayuwarsu daga garin, Girgizata yayi da karfi tareda ambatar sunanta yana danne abinda yake Ji a kirjinsa na bugawan zuciyan dayake kokarin samu yace ‘Ayanah karki karye ke uwa ce a yanxu da babu Amma, Kece zaki zama garkuwan yan uwanki, Kece Amma yanzu, Kece madubi fitilar da zata haske hanyar da rayuwanku zatabi, Karki karye kiyi jarumta ba yanzune lokacin kukan rashin Amma ba, Ki dake zuciyarki ki kubutar da yan uwanki daga nan Allah ya Riga ya karbi Amma karki Bari burinta na kubutar da rayuwanku ya tashi a banza.’ Wata irin jijjiga jikin Ayanah keyi taba girgiza kai kuka me tsananin gaske na zuwar mata tace ‘Abaa bazan iya ba, Abaa ina buqatan kai da Amma a gurin zamtowa uwa garesu, Abaa kune hasken rayuwanmu,kune garkuwanmu, Abaa kune rayuwarmu tayaya zan iya babu dayanku?’ Rungumeta yayi jikinsa da karfin gaske yana rintse idanuwansa da a Karan farko rayuwansa suka zubewa hawaye ya kasa cewa komai yana sake qanqameta a jikinsa Tana wani irin kuka me tsananin karfin gaske hannuwanta na kakkarwa. Sakinta Abaan yayi ya janyo Zuhrah datai mutuwan tsaye bata ko motsawa jikinsa itama ya qanqameta yana hanasu ganin hawayensa. Sakinta yayi sbd da alama an shigo gidan nasa dan haka Abaas da Nurat ya zubawa ruwan dake gurin da suka fara daukan dumin wuta suna bude ido ya fizgesu tsaye Da gudu Ayanah tazo gaban gawar Amma ta saka hannu ta shafe idanuwanta suka rufe hannuwanta na tsananta kakkarwa ta saka hannunta cikin na Amman ta zare abin hannunta na zallan azurfa Wanda yake dauke da sunan Amma din tayi mata addua hakama Sauran adduar sukai mata a tsaye Abaa ya fizgesu suna kuka me tsananin gaske na tashin hankali. Turasu wata qaramar hanya dake baya yayi cikin sauri yana waiwaye sbd yana jiyowa sun shigo gidan da yawansu. Kirjinsa wani irin radadi da ciwo yake masa Wanda yakejin bazai iya Nisaba amma ko yayane zai tabbatarda ‘yayansu sun tsira, A bayansu yafara Jin takunsu me karfi da tsanani dan haka cikin sauri ya juya ya kalli hanyar kafin ya kalli gabansu da akwai Sauran tafiya kafin su bulla daji harma su isa bakin ruwa gashi sunada yawa fa qananun yara. Tsayawa yayi tareda kamo hannun Ayanah ya kalleta taje dukkaninsu suka tsaya cak kowa ya zuba masa ido, Ganin irin kallan dayake mata ya saka Ayanah fizge hannunta tareda ja baya Tana rintse idanuwanta Tana girgiza kai da karfi Tana fita hayyacinta gabaki daya. #MAMUH #SLAVERY #ROYALTY #BEST LOVE #GHAZ #BOYEM HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 09033181070 7 *_PRIME SCENT_* 08103155915 Shin Kina neman duniyar kamshi ta turarukan wutan da in kin kunna zaki ji ki kamar a Royal palace din larabawa? Ko kuma kina neman wanda zaki kunna ya kaiki garden full of vibrant, mind & soul soothing fresh scents? Ko kuwa wanda zai baki rich and luxurious scent na elites? Ko kuwa kina neman qamshi mai sauke fushi da gajiyar da oga ya kwaso ne? Are you looking for qamshin da duk inda kika shiga sai kin janyo attention din mutane, ko kuwa wanda in an matso kusa dake sai an lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya na jin dadi da kwanciyar hankali tare da samun nutsuwa? Hajiya ta albishirinki! Ga PRIME SCENT Duniyar kamshin da babu kamarsa, Duniyar kamshin da ko kin bada kayanki ko curtains naki wanki baza su Dena bada kamshi me nutsuwa da dadin shaqa ba, PRIME SCENT sune kankat ba na biyunsu. 08103155915 ******** ************* Matsota Abaa yayi tayi saurin sake yin baya da karfi tana fasa kuka me karfin gaske numfashinta na sarkewa. Abaas da Zuhrah da Nurat kuwa gabaki daya riqe Abaan sukai kowannesu jikinsa na rawa suna tsananin rokonsa akan ya biyo su su tafi karya sauya hakan. Zafafan hawayensa ne masu tsananin zafi suka Riga akan fuskan Abaas dake jikinsa ya sauke Kansa yana banbaresu daga jikinsa yace suyi sauri subar gurin shi zai rufe hanyar kafin kusrawa su qaraso sunyi nisa zai biyo su daga baya. Girgiza kai dukkaninsu suka hau Ayanah kuma tsananta kukanta yayi tana Jin kirjinta na wani irin radadi me tsananin gaske. Harbin mashi suka fara Ji tako ina ba tsammani take suka fara gudu dukkaninsu wasu kuma kibiyar na samun su dan haka suka shiga firgici me firgitarwa suna Neman rarrabewa amma Abaa ya kasa barin hakan ya taresu ta baya suna gudu me tsanani batareda sunsan inda suke jefa kafafunsu ba. Biyosu kusrawa sama da arbain sukai suna harbosu da kibiya tako ina suna wani irin ihu dake girgiza duk wani me sauraro. Duhun dajin suke bi suna gudu sosai Wanda kusan da yawan wainda suke tareda su suna Jin yanda suke mutuwa amma babu daman tsayawa wa hakama Abaa cikin tsananin tashin hankali ya hanasu juyawa su waiwaiya baya yace suyita gudu karsu tsaya. Cikin gudu da tsananin ciwon dayakeji a kirjinsa na tsananta yace ‘Ayanah duk tsanani kada ku tsaye kuyita gudu harsai kun tsira’ Sanyi jikinta yayi zata juyo cikin karfin hali da daga murya yace karki juyo Kuyita gudu Ayanah. Muryansa da bataji daidai ba ya sakata juyowa da sauri idanuwanta suka akan kibiyar data bullo gefen kirjinsa ta bayansa da aka harbo Tsayawa zatai Ya fizgeta da karfi yana turata yace ‘Ku tafi karku tsaya, Ku tafi Ayanah, Ki tafi dasu karki Bari kowa ya juyo bare tsayawa’ Kasa wa tayi ta juyo tareda riqe hannunsa suna gudu tare yana turata daga jikinsa zuwa gaba yana cewa ta tafi ta kula da yan uwanta ta tabbatarda sun tsira sun kubuta sun Gina rayuwa me kyau. Fara gazawa yayi dan haka turata da karfin gaske tana kokarin dawowa ya dago idanuwansa jajir yace ‘Ban Aminta ki tsaya ba bare dawowa gareni ki tafi Allah zai zama gatanku insha Allah, Burina burin Ammanku shine ku tsira dan haka Ayanah ku tafi ku cika mana wannan burin ku rayu, Duk rintsi ku hada kai karku rabu da juna’ Sake turata yayi sa karfi tana qara riqosa amma ina jini sosai yake fita a kirjinsa harma da bakin sa take kafafunsa suka kasa daukansa ya durqushe a gurin ta kira sunansa da karfi tana kokarin durqusawa Kaman daga sama taji bayanta an riqeta. Cikin tsananin azaba ya dago idanuwansa ya kalli Asamah wadda bata hayyacinta sbd kukan baqin ciki da danasanin datake ciki tareda fatan tayi mummunan mutuwan data jawa rayukan dake ANJOM. Daqyar ya bude baki jini na fita sosai yana kallan Asamah yace ‘Ki tseratar dasu, Karki bari kowannesu ya tsaya bare dawowa ANJOM ‘ Janta Asamah tayi tana Hana su Zuhrah dawowa suka fara ihu ganin halinda Abaansu ya shiga ransa na kokarin barin kirjinsa sbd wani irin jinin dake fita bakinsa. Kaman daga sama sai ganin Mutum biyu sukai akansa ba Imani a tare suka soka wuqa biyu a wuyansa idanuwansa na kan yayansa dake Ihun gaske suna Neman zarewa sbd mummunan tashin hankalin sheda mutuwan mahaifinsu akan idonsu. Asamah cigaba da turasu tayi suka kutsa dajin suna tsananta gudu hannun Ayanah yana cikin na Abaas hakama Nurat da zuhrah suma hannuwansu na riqe dana juna. Biyo su akai wannan Karan an Dena harbin da alama da rai ake sonsu. Kuka sosai sukeyi suna tsananta gudunsu Banda Ayanah datake Jin zuciyarta na kokarin nema bugawa hakama idanuwanta basa ganin komai jefa kafa kawai takeyi. Dukkaninsu sun kasa yadda a awannin da basu wuce uku ba sun rasa iyayensu duka cikin dare daya a Masifa da mummunan kaddara daya, Neman sarewa sukeyi amma Sam Asamah ta kasa Bari saima hanya data sauya musu sbd an kusa kamosu dan haka cikin wani irin qazantaccen rami ta turasu suka shige suka boye tareda sakina wadda take riqe da Zuhrah a yanzu. Suna shigewa Asamah ce ta saka hannuwanta ta toshe bakin Nurat da Abaas ita kuma sakina ta rufe na Zuhrah sbd yanda suke kuka suna wata irin jijjiga. Ayanah ta kasa komai ta koma tamkar marasa hankali da kwakwalwa kwata kwata dan haka batace komai bare kukan Wanda ya kasa fitowa tsabar muni da girman tashin hankalin datake ciki. Suna Ji kusrawan na wucewa da gudu da karfi suna ihu me ban tsoro amma basu motsa ba har saida suka Ji sun gama wuce kafin Asamah ta zare hannunta a Bakinsu Sai a lokacin Nurat ta fasa wani irin kukan daya saka Idon sakina fara zubar hawaye Asamah kuwa kukan itama ta fasa me tsananin ciwo tana rungume Zuhrah dake jijjiga kaman me wani ciwo. Rintse idanuwa Ayanah tayi tareda sunkuyar da kai tana fasa kuka mai tsima zuciya da girgiza kowa. Babu Wanda yace komai a cikinsu dukkaninsu kuka ne sukeyi mara dadin Ji bame rarrashin wani sbd kaddarar tayi musu nauyin da zuciyarsu take kasa dauka, Ayanah hannu ta Dora Akan kirjinta tana duka kukanta na sake tsananta sbd kirjinta ya toshe Jin takeyi kaman ta mutu tabi iyayenta. Har asuba tayi gari ya fara haske suna cikin ramin idanuwansu sunyi wani irin kumbura da ja babu me iya dogon motsi sbd mutuwa da jikinsu yayi rayuwan gabaki daya ta fice musu arai sbd basu San ta ina zasu fara rayuwa babu daya daga cikin iyayensu ba, Basu San koinaba,basu taba fita ANJOM ba tinda aka haifesu, Basu saba da kowa ba Bayan junansu fa iyayensu, Basu taba jagorantar lamarin su ba da kansu komai iyayesu ne ke tafiyar musu dashi, Abinci ma basu taba Cinsa batareda iyayensu ba, Ayau dare daya sun tsinci kansu a mummunan kaddarar da basuma San ina zasu ba, Gurin wa zasu? Tayaya zasu fara rayuwa? Yaya rayuwa zatai dasu bare Wanda zai tsaya ga lamarinsu dan haka Ayanah kukanta ke karuwa sbd batasan ta ina zata fara zamowa uwa da iyayenta suke fada Akan kannanta kawai dai abu daya ta sani a yanzu zata iya rasa rayuwarta akan wani abu ya samesu sbd sune rayuwanta. Sakina ce takeda dan Sauran kuzari a jikinta sbd itama Asamah a cikin mummunan yanayi take samun tabbacin mutuwan mijinta tin shekarun baya hakama a Daren itama daqyar Tasha sbd umarnin a kasheta da shugaban kusra ya bayar. Fitowa sukai daga ramin babu me gani sosai sbd kumburin ido. Sakina ce ta Kama hannuwansu daya bayan daya suka gama fitowa suna kallan filin dajin da hayaqi yake tashi sbd wutar garin da har lokacin ci takeyi sosai hakama koina yayi tsit ko kukan dabbobi babu. Hanya suka jijjuyawa suna Neman gurin bi sbd sun riga sun sauka daga kan hanyar da Abaa ya dorasu da zata kaisu inda yace kuma bazasu maida kansu hanyar komawaba bare su sake hawa hanyar daga can. Hawaye ne masu tsananin zafi suka gangaro daga idanuwan Ayanah ta sake riqe hannun Abaas dake cikin nata gefe daya kuma Nurat na riqe da ita Zuhrah na riqe da Asamah suka Kama hanya ba tareda sunsan inda zasu ba suka cigaba da nutsuwa cikin dajin. Tafiya sukeyi bame cewa komai ba kuma me kuzari dan haka har rana ta fara ketowa zafi na ratsa su ga babu me takarma a kafa dan haka wahala ta faro sako kai amma duk da hakan babu Wanda yace komai har lokacin. Wuni guda sukai suna tafiya sai gab da magrib suka fara hango ruwa daga nesa dan haka suka dan sauke ajiyan zuciya kadan Sai a lokacin Ayanah ta kalli kafafun yan uwanta taga kowa kafarsa ya fashe sosai jini sukeyi dan haka tace su zauna su huta. Guri suka nema suka zauna babu me kuzari a jiki, Nurat da Zuhrah ne suka kwantar da kansu a kafadunta suna rufe idanuwansu hawaye masu dumi suna gangarowa daga ciki, Abaas kuwa gefe ya zauna tareda sunkuyar da Kansa yana kafawa qasa jajayen idanuwansa da sukai nauyi da kumburi. Har duhun dare yayi suna Zaune gurin salla ma a haka sukai da taimama ba ruwa, Nurat ce me tsoron cikinsu dan haka duhu na qarawa hankalinsa yana sake tashi dan haka dole suka miqe a hakan suka sake bin hanya cikin hudun dare babu motsin komai koda kuwa na dabba ne daman hakan dajin yake shiru babu motsin komai gwanin tsoro da firgita. Tafiya sosai sukai har dare ya sake tsalawa sosai karfinsu gabaki daya ya qare ga yunwa da azaba Zuhrah Amanta uku a hanya. Duk wannan tafiyar da sukeyi suna maqale da juna sun kasa sake juna, Fitsari Nurat tace zatai dan haka suka tsaya ta dan matsa gefe kadan ta durqusa tayi ta gama kenan tana miqewa taji Mutum ya cafkota gabaki dayanta batasan lokacinda ta fasa wani irin mummunan ihu me karfin gaske ba daya saka Sauran kusrawan dake gurin tahowa gurin da sauri suna ihun daya saka fitsari kufcewa Sakina. Cikin mummunan tashin hankali da tsananin tsoro Su Ayanah sukayo gurin sedai Asamah da sakinah riqe su sukai da karfi suna hanasu tafiya sbd kada Ayi biyu, Sama kusrawan su shida sukai da Nurat suna dariyar farin ciki suna tsalle tana ihu da wani irin kukan mafi tashin hankalin rayuwanta. Kwacewa Ayanah ta fara yi tareda bude baki zata kwala kiran Nurat Asamah suka rufe musu baki take suka fara kokawan kwacewa sbd ganin zaa tafi da Nurat batareda an gansu ba dan haka Abaas ya bude baki ya kira sunan Nurat din karfi sbd sunfi son a tafi dasu dukansu koma inane da a dauke dayansu abar saura su rabu. Cikin rashin Imani kuwa kusrawan suka juyo tareda biyo su Ayanah din wainda da kansu suka fito suna nufar Nurat da gudu suka rungume junansu su hudun suna fashewa da kuka. #MAMUH #ROYALTY #BEST LOVE #BOYEM #BOYEM PALACE HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 09033181070 8 *_PRIME SCENT_* 08103155915 Shin Kina neman duniyar kamshi ta turarukan wutan da in kin kunna zaki ji ki kamar a Royal palace din larabawa? Ko kuma kina neman wanda zaki kunna ya kaiki garden full of vibrant, mind & soul soothing fresh scents? Ko kuwa wanda zai baki rich and luxurious scent na elites? Ko kuwa kina neman qamshi mai sauke fushi da gajiyar da oga ya kwaso ne? Are you looking for qamshin da duk inda kika shiga sai kin janyo attention din mutane, ko kuwa wanda in an matso kusa dake sai an lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya na jin dadi da kwanciyar hankali tare da samun nutsuwa? Hajiya ta albishirinki! Ga PRIME SCENT Duniyar kamshin da babu kamarsa, Duniyar kamshin da ko kin bada kayanki ko curtains naki wanki baza su Dena bada kamshi me nutsuwa da dadin shaqa ba, PRIME SCENT sune kankat ba na biyunsu. 08103155915 ******** ************ Wani irin kuka mai tsananin ratsa kunnuwa Ayanah ta fasa itada Nurat a lokaci daya suna rungume juna da tsananin karfin gaske jikinsu na wata irin rawa mummunan tsoron da basu taba shiga ba, Abaas da Zuhrah ma dukansu kukan sukeyi suna rungume junansu gabaki dayansu kowannensu jikinsa kakkarwa yakeyi musamman Nurat datafi shiga matsanancin tsoron dayake Neman juyar da kanta ita data shiga hannun kusrawan, Asamah da sakina ma qarasowa sukai da gudu suna kasa barinsu suka rungumesu kowannensu kuka yakeyi sosai sbd sanin rayuwa kuma ta tsaya musu daga wannan daqiqar. Magana Nurat ke son yi amma yanda jikinta ke fizga bakinta na kasa budewa sbd bata hayyacinta gabaki daya yasa Ayanah dake wani irin kuka mai tsanani itama jikin na rawa sake qanqameta jikinta tana kasa maganar itama, Hannunta daya ta saka ta sake qanqamo su Abaas da Zuhrah tana ambatar sunan Abaansu da karfi tareda Neman dauki daga ubangiji sbd bazasu iya rayuwan nan me cikeda tsoro ba basuda kowa a duniyar. Wata irin dariyar Jin dadi me karfi da ban tsoro tareda firgitarwa kusrawan sukeyi suna zagaye su tareda wani irin tsalle kaman sunga nama. Duk dan Adam din dazai sauke idanuwansa Akan kusrawa saiya shiga tsoro me tsananin gaske sbd kamanninsu da yanayinsu da rahamar Allah ta gama fice wa a rayuwansu sbd girma da yawan rayukan da suka raba da duniya babu tausayi ko Imani ko kadan, Ganinsu ko mafarki mummunan tashin hankali da tsoro ne sbd Al’adarsu ma da kadai yanayin shigarsu da wasu irin hudan kunnuwa dana hanci dake tattare dasu ga gashinsu da basa Daurewa a sake yake ga wainda basada gashina kuwa wani irin kitso ne me tsoro ga zane a jikinsu da shima alama ce ta kusrawa ga kowace kusra. Asamah ce ta bude hannuwanta tana karesu dan basu kariya itama jikinta koina rawa yakeyi tana jin wani iri kaman haukacewa zatai sbd yanda zuciyarta da kirjinta ke tsananin nutso a cikin qunci da tabarbarewan rayuwa data samu kanta na halin data saka rayukan da basu adadi tareda maida yara sama da daruruwa marayu, Tareda saka mata sama da daruruwa rasa mazajensu zasu zamo bayi, Yaya da iyaye sama da daruruwa sun rabu babu ranar haduwa har abada sbd kowa da inda ya gudu da kuma inda zaa siyar dashi. Juyawa kanta yaci gaba da yi zuciyarta da kwakwalwanta na sake kasa dauka idanuwanta na rage gani sbd haqqin ran daruruwan mutanen dake kanta, Rintse idanuwanta tayi tana sake ganin duhu kanta na Juyawa sosai amma har lokacin karesu takeyi da hannuwanta, Jin kaman zuciyarta na Neman bugawa ta juyo tsoronta da tsananin tausayinta akansu na qaruwa sbd sun riga sun rasa yanci da gata harma da asalinsu tareda rayuwansu batareda sun San yaya duniyar take ba a wajen gidansu,a kuma wajen garinsu,a Bayan ran iyayensu, Basusan yaya zasu gudanar da rayuwarda babu iyayensu a cikinta ba koda iyayensu na raye bare yanxu da basa duniyar, Ko a darasin ilimin rayuwa da iyayensu ke musu tareda tarihi da labarun rayuwar dake gudana a duniya wadda baa cikin ANJOM ba baa taba fada musu menene asalin zamowa bawa ba da ukubar dake cikin bauta wadda bakasan karshentaba ko Ka samu yanci wata rana kokuma Ka mutu a cikinta. Wani irin Jan rikitarwa idanuwanta suka tana saka hannunta daya a kirjinta tana dafewa Ahankali ta kalli Ayanah tareda bude bakinta ahankali ta Ambaci sunanta kafin ta maida idanuwanta Akan Abaas datafi shaquwa dashi tareda tsananin kauna a tsakaninsu me karfin gaske ta qura masa ido wasu irin hawaye masu tsananin ciwo na gangaro mata ta sunkuyar da kanta qasa tana jin rayuwarta kwata kwata bata da sauran amfani. Dagowa tayi ta kalli kusrawan da sukayo kansu kowannesu na zaro mummunar wuqar da zata yanka Mutum a qanqanin daqiqu fit ta rabaka da ranka. Lumshe idanuwa Ayanah tayi suna sake rungume junansu dukkaninsu suna samun nutsuwa da saukin a rabasu da ransu su bi iyayensu yafi musu saukin rayuwan da basusan yaya ake gudanar da itaba, Rayuwar da babu tabbacin ko zasu take ko wahala da gagari zasu yi karshe su mutu a cikin garari dan haka gwara tin a qasar garinsu batareda sun bar garin da gawar iyayensu take ba subar duniyar. Abaas dayansu ya fizgo da karfin gaske yana Dora wuqa mai tsananin kaifi da wani mummunan fadi a wuyansa zai fizge jijiyar wuyansa da wuqar Asamah ce da idanuwanta ke cikowa da hawaye masu radadin gaske ta bude baki jikinta na saki tace ‘Inada damar alfarma guda daya tak da khams ya bani a matsayin abinda zaa biyani dashi kuma dukkaninku kun San da hakan’ Cikin rashin Imani Wanda yake riqe da wuqar a wuyan Abaas yace ‘Damarki guda daya ce tak kina fadarta shikenan kin rasa kowace irin dama…… Katsesa tayi muryanta na sake raunana da cewa ‘Kar a kashe ko dayansu shine abu daya tak danake so…… Dukkanin kusra dariya me karfi suna kece da ita kafin babban cikinsu ya kalleta cikin tinatar da ita babban gangancin da zatai wa rayuwarta sbd Ana cika mata wannan buqatar ita rasa nata ran zatai yace ‘Kina sane a dama daya tak da aka baki zaki iya zabar abarki da rayuwarki kitafi duk inda zaki ki Gina sabuwar rayuwa? Kina sane da hakan? Sannan Kina sane da idan kika zabi rayuwarsu ke bazaki rayu ba??? Gangarowa hawayen cikin idanuwanta da sukai jajir sukai ta juya sake kallansu babu Wanda jikinsa baya kakkarwa cikin wani irin mummunan halin daya saka zuciyarta sake nauyi, Abaas ta zubawa idanuwanta idanuwansa na rufe yana jiran barin duniyar kafin ta dawo da idanuwanta Akan Ayanah dake kallanta cikin yanayin da suka fi buqatan mutuwan Akan rayuwar Zuhrah ce ta iya bude baki da tsananin kuka me ratsa zuciya tace ‘Asamah mun zabi bin iyayenmu dan Allah karki zabi barin mu kema sbd kece wadda a yanzu muke kallan zaki zame mana ido a wannan rayuwar da muke makafi bamusan komaiba dan haka munfi tsananin buqatan komawa ga mahaliccinmu kaman iyayenmu…… Ayanah data kasa magana sbd tsananin shidewan datake sbd tsananin tashin hankali da kukan da hawaye basa fita a cikin dare daya da wuni hawayenta sun kafe kallan Asaman takeyi tana girgiza kai dukkanin jikinta na rawar da bata hayyaci bace. Rintse idanuwa Asamah tayi ahankali tana bude su Akan su duka tace ‘Allah zai zama gatanku, Allah zai Baku kariya, Allah zai kawo ido da haske a rayuwarku kudai ku jajirce karku rabu duk tsanani ku kasance bangon juna’ Maida kallanta tayi kan kusran ta basa amsarsa da cewa ‘Na zabi rayuwansu Akan tawa a cika mun damar da aka ban ta hanyar barinsu da rayuwansu harsai lokacin da ubangijin daya halitta musu ita zai karba da kansa… Ayanah ce tayi saurin yunqurowa da rarrafe mai sauri ga Asaman tana miqa hannu zata riqeta sbd suna tsananin buqatanta a yanzu…….. Jinin daya fesu a fuskanta da hannunta data miqa ne yawa na Asamah ya sakata sanqamewa a gurin tana dauke wuta hannunata na kakkarwa me tsanani. Wuqar da kawai aka fizge fatar wuyan tareda jijiyan Asamah kaman wucewan iska Wanda ya saka jinin bartsi sosai ta kalla a hannun Wanda yayi aikin batareda bata lokacin su ba sbd zabinta ne. Wurgar da Abaas sukai a gaban yan uwansa da gawar Asamah dake gangaro da jini, Mutuwan Zaune dukkaninsu sukai tareda dauke wuta sbd babu Wanda a jikinsu jinin bai bartsanwa ba, Abaas daya kasa matsawa yana kwance a inda suka jehosa kaman mataciyar dabba rufe idanuwansa yayi hawaye na zubowa idanuwansa yana kasa motsawa. Babu Wanda yace musu komai haka suka juya suka bar gurin shugaban cikinsu ma dago murya yace ‘Kusra bata tada Alkawari idan tayi dan haka ku tafi an cika mata burinta ko bata raye amma wannan damar itace ta cika Alkawari idan mun sake haduwa daku kun zamo namu’ Har suka bace wa gurin babu Wanda ya motsa a cikinsu Ayanah sbd babu wanda ya dawo hayyacinsa, Sakinah dake Bayan Ayanah motsawa tayi ahankali tareda qarasowa gaban gawar Asamah ta saka hannunta yana rawa sosai ta shafe idanuwanta suka rufe tana fasa kuka mai tsima zuciya itama. A lokacinne Zuhrah ta fasa kukan itama me karfin gaske tana fadawa jikin Ayanah. Nurat da bata hayyacinta miqewa tayi da sauri a zare tana bin hanyar daji kafafunta na hardewa tana qwala kiran sunan Abaansu. Ganin tana Neman nisa ne ya saka Abaas miqewa da gudu yana kamota ya rungume yana kiran sunanta da karfi da fashewa da sabon kuka. A lokacin ne Ayanah da Zuhrah suka taso suma suna riqeta tana kwacewa cikin wani irin ihu na gushewan hankali Wanda ya saka yan uwanta suna fasa sabon kuka me taba zuciya dukkaninsu suna qara riqeta sbd zaucewa takeyi. Sakinah ma kukan take fasawa itama tana rungume dukansu. Ihun Nurat ke fasawa tana fizge fizge tana yakushin kanta da karfi tana kwala kiran Abaa dajin na amsawa sosai. Qin Sakinta sukai suna sake saka karfinsu su duka suna riqeta sosai kukansu na qaruwa. Sun jima a cikin wannan sabon tashin hankalin kafin Nurat din ta zube qasa suma suka zube gabaki dayansu har lokacin basu iya Sakinta ba sbd kada ta gudu. Shiru sukai sai ajiyan zuciyar kukansu dake sauka akai akai na tsawon lokaci shima kafin suka miqe hannun Zuhrah na riqe dana Nurat din suka bar gurin. Gabas suka kalla suka sake miqa suna kutsawa hanya batareda sunsan inda suka dosa ba. Yunwa da azaba ce kawai a cike da rayuwarsu a lokacin tareda mafi girman baqin ciki da qunci, Wuni suka sake shudewa suna zagayen dajin sun rasa hanyar fita bare komawa ANJOM duk da sunsan garin ya zama na kusra yanzu. Cikin dare sosai suka sake samun wani guri suka zauna tareda maqale da junansu suka dunqule guri daya dukkaninsu suna cikin jikin Ayanah wadda ita kuma sakinah ce ta bata kariya ta bayanta ta hanyar zauna wa ta jingina da bayanta. Shiru sukai ko dogon numfashin basa yi sbd tsoro da fargaba tareda damuwa. Darensu na jiya ta tina Wanda suke tareda Asamah ta basu kariya da kulawa a lokacinda suka yanke rahama daga duk wata samun kulawa koman kankantarta, Maganar Asamah datai musu Daren jiyan ta tina a lokacinda ta Shafa fuskan Abaas. ‘Ayanah akwai rayuwa me tsauri da qalubale a gabanmu dan haka idan matiqar muna son kada a rabamu da Abaas daga cikinmu to tabbas muna buqatan maidasa mace sbd qalubalen da zamu fuskanta zaa iya kaiwa matakin da zaa rabamu sbd shi namiji ne mu kuma mata dan haka sbd Kaucewa hakan muna buqatan boye jinsinsa sbd tseratar da rayuwarsa tareda tabbacin zamansa a tareda ku kada komai ya rabaku’ #MAMUH #SLAVERY #HISTORICAL #ROYALTY #BEST LOVE #BEST SISTERS #BOYEM #NUAB ALMAZ BOYEM HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 9 *_PRIME SCENT_* 08103155915 Shin Kina neman duniyar kamshi ta turarukan wutan da in kin kunna zaki ji ki kamar a Royal palace din larabawa? Ko kuma kina neman wanda zaki kunna ya kaiki garden full of vibrant, mind & soul soothing fresh scents? Ko kuwa wanda zai baki rich and luxurious scent na elites? Ko kuwa kina neman qamshi mai sauke fushi da gajiyar da oga ya kwaso ne? Are you looking for qamshin da duk inda kika shiga sai kin janyo attention din mutane, ko kuwa wanda in an matso kusa dake sai an lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya na jin dadi da kwanciyar hankali tare da samun nutsuwa? Hajiya ta albishirinki! Ga PRIME SCENT Duniyar kamshin da babu kamarsa, Duniyar kamshin da ko kin bada kayanki ko curtains naki wanki baza su Dena bada kamshi me nutsuwa da dadin shaqa ba, PRIME SCENT sune kankat ba na biyunsu. 08103155915 ******** Rintse idanuwanta Ayanah tayi ahankali tana sake rungumesa jikinta tareda Sauran kannan nata sbd boye jinsinsa da tabbas zatai a yanzu har zuwa lokacinda bata sani ba nakasta rayuwansa ne nakasa me munin da babu ranar gyara, Jin takeyi kaman bazata iya hakan ba amma kuma bazata iya barin a rabasu ba har abada sbd suna rabuwa babu Wanda zai iya rayuwa a cikinsu batareda juna ba, Sake qanqamesu tayi a matiqar sanyaye tana jin da gaske yanzu kam ta zama uwa, Ta zama uwar da batasan komaiba sai yayanta,su kadai ne rayuwarta da duniyarta. Suna gurin a maqale guri daya kaman ba mutane ba har suka ga duhu ya fara dan ragewa alaman asuba tayi harta gota, Basu saki juna ba saida gari ya qara haske sosai suna iya ganin koina da komai tukuna suka warware juna, Ayanah ce ta umarce suyi sallah a yanda suke sbd basuda gurin tsafta ce jikinsu dan babu ruwa babu komai qasar ba babu sosai hakukuwane suka fi yawa sun cike koina. Shiru sukai tsawon lokaci babu magana Bare motsawa Bayan sunyi sallolin dake kansu. Shiru tsit babu ko kukan kowace irin dabba a dajin Wanda hakan alama ce ta dajin baida kyau sbd kukan dabbobi ko tsuntsaye yana rage tsoron daji. Rana ce ta fara ketowa me tsananin zafi suna Zaune a gurin har lokacin dan haka Ayanah ta juyo ahankali ta fara kallan Nurat dake kwance jikin Zuhrah tana maganganu kadan kadan har lokacin na zautuwa tana ambatar sunan Amma da Abaa. Lumshe jajayen idanuwanta da suka bushe qayau tayi suna mata wani irin radadi tana dan Hadiye wani Numfashi me cikeda radadi shima kafin ta sunkuyar da kanta tana kasa kallan Abaas Wanda shi da Zuhrah harma da sakinah ita suke kalla sbd fahimtar akwai abinda takeson fada amma ta kasa. Hanyar da zasu bi ta dago ta kalla idanuwanta na cikowa da hawaye sbd batasan rayuwar da zasu Tatar ba a hanyar idan suka qarasa Binta Wanda tasan duk inda suke basa nesa da ruwa ko lambum wani gari sbd sanyin da suka kwana yana fesowa na alaman hakan Shiyasa koda garin ya waye kaman zasu sanqare sbd sanyi. Dawo da fuskanta tayi amma ta kasa kallan Abaas Wanda ya tsareta da ido jikinsa na tsananin sanyi hannunsa na rawa ya riqe gwiwowinsa da hannuwansa dake rawar sbd take ya gane abinda yake ranta amma zuciyarta na tareda sbd shima da abin ya kwana a ransa tsoro da fargaba me tsananin yanda zaa iya rabasa da yan uwansa amma kuma duk da baida shekaru amma kasancewansa namijin GHAZ daya bayan mahaifinsa sauyasa zuwa mace shine mafi girman qasqanci da zuriar GHAZ suka samu ko Bayan ransu duka tin daga kakanni, Shi rayuwarsa ta mutu ne daga lokacinda zai koma mace, Ya rasa darajarsa,ya rasa sunansa,ya rasa yancinsa da damarsa ta zama GHAZ na har abada sbd yana cikin tsatsauran al’adarsu matiqar namiji ya zama tamkar mace kokuma zamowa mace ko shigar danganci mace to har abada bazai taba karban gadon matsayin shugabancin Ahalin GHAZ ba bare ANJOM. Rawa jikinsa yafara cikeda wani irin radadi da ciwon daya saka idanuwansa cikowa da hawaye masu Zafin gaske yana qanqame kafafunsa, Zuhrah data fahimci hakan kallan Ayanah dake sauke kai itama hawaye na gangaro mata da tsananin tsoro da faraba tace ‘Ayanah saimunyi hakan zamu rayu tareda shi, Bazan iya rayuwa ba idan aka rabamu dashi, Ayanah koma menene zamuyi masa shi dan rayuwa tareda shi koda hakan na nufin komawansa mace har ranar da Allah zai dauki rayuwarsa ko tamu… Kuka ta fasa mai sanyi tana cewa ‘AMMA kada kice bazaki iya ba’ Wani irin kuka me karfi Ayanah da Abaas din suka fashe dashi a lokaci daya kowannesu na saka kansa cikin kafafunsa sbd AMMAN data Ambaci Ayanah dashi Wanda daga lokacin ta tabbatarda ita ta gama karban Ayanah a matsayin Uwa duk da ba shekaru masu tsayi tsakaninsu amma dai ta Riga ta maye musu gurbin Ammah kaman yanda su Abaa ke cewa ita uwarsu sbd tsanani son da uwa kewa ‘da take musu suma suna mata tsananin son fa ‘da kewa uwa. Sakinah ma kuka takeyi sosai sbd rayuwarsa me suna da Abaas zai rasa daga yau shikenan. Kuka sukeyi sosai a tsakaninsu harda Nurat da bata cikakken hayyacinta kukan takeyi sosai cikeda tausayi me karya zuciya. Tsananin Zafin rana ke dukansu ga kuka da suka kasa Denawa sai hakan ya fara raunana lafiyansu dan haka daqyar sukai shiru Ayanah sai a lokacin ta dago ta kalli Abaas Wanda kansa ke qasa har qasa lokacin burinsa na zamowa namiji,dan uwa kuma uba dayake fatan wata rana zuriarsa data Ayanah ko daya daga cikin yan uwansa yana narkewa tareda bin iska a yau,zai mutu batareda samun wannan cikar burinba. Sakina ce cikin tsananin kukan da tasan illa da nakasun da rayuwarsa zata samu daga yau ta saka hannu tana zare ‘yan kunnan azurfan dasuke kunnenta duka guda biyu ta kamo hannun Ayanah dake kuka sosai ta saka mata su ahankali tana Juyawa baya jikinta a sanyaye sbd ita har yanzu baiwar su ce bazata kalla yanda zaa yaga qimar uwayen gidanta ba. Qanqame abin kunnayen Ayanah tayi a hannunta tana dauke kanta daga kallansu su duka kukanta na Neman tsananta amma dole zata aikatawa dan uwanta hakan. Zuhrah ce da itama kukan takeyi ta miqe tsaye tareda Kama hannun Ayanah ta kasa maganar da zatai sbd kukan dake zuwar mata sabo mai ciwo dan haka juyawa tayi itama tana Dora hannunta a kirjinta dake ciwo da nauyi. Rarrafowa Ayanah tayi cikin mummunan gaban Abaas din tareda daga hannuwanta dake rawa sosai takai tafukan hannayenta fuskansa ta tallafo ta kallesa ya Lumshe idanuwansa yana kasa barin taga tsananin rauni da baqin ciki tareda quncin dayake cikinsu sbd kada ya qarasa karya zuciyarta da gangar jikinta. Bakinta takai kan gefen fuskansa ta sumbacesa hawaye na gangaro mata kafin ta sake dorawa kan goshinsa ta sumbacesa hawayenta na diga kan goshin nasa. Zuhrah ma cikin karfin Hali tana danne zuciyarta ta juyo ta durqusa gabansa ta Kama hannuwansa biyu ta sumbacesu duka kafin ta sumbaci tsakiyar kansa da gashinsa me tsayi kaman mace yake daure har lokacin. Tafin hannu Ayanah ta bude ta kalli yan kunnayen kafin ta daga ahankali tareda Kama kunnansa, Bude idanuwansa yayi ya sauke Akan fuskan Ayanah din wadda cikin idanuwansa take kallo tana masa kallan tsananin kaunar dake nuni da har abada idan kowa zai gujesa su suna tareda dashi har mutuwa sbd su a gurinsu rasa kowace darajarsa ba ta ‘da namiji. Baice komaiba Bayan rufe idanuwansa da yayi ahankali sbd su kadai yake buqata a rayuwarsa daman kuma idan yana tareda su shikenan zai iya jure komai. Hannunta ta Dora a kunnansa cikin radadin zuciya ta huda kunnan nasa da karfin da na karfin hali ne, Zuhrah kaman a zuciyarta haka taji hujin kunnan shi kuwa ko motsawa beyiba sai wasu hawayen da bana radadi bane suka gangaro masa. Haka Ayanah ta huda Dayan kunnan tana bar masa yan kunnayen a kunnuwansa. Tallafe fuskansa ta sake yi da hannuwanta tana kallan idanuwansa dake rufe yana riqe kukansa me tsanani dake zuwar masa. Itama kokarin riqe nata takeyi har saida Zuhrah ta saka hannunta cikin riqe nata kukan itama ta zare daurin gashinsa take gashin ya sauka har kafadarsa, Wani irin kuka me karfi da gunji suka sake a tareda dukkaninsu suna rungumesa. Har lokacin Sakinah bata juyoba itama kuka takeyi sosai a yanda take, Nurat ma kukan ta fasa tana fadawa cikinsu tareda ambatar Ayanah da AMMA itama. Rigar Zuhrah me dan adon Kayan mata suka zare aka saka masa tasa kuma Zuhrah din ta saka. Sakinah ce ta matsa kadan gaba ta Debo wani ganye shar ta kawo Ayanah ce ta murza ganyen da hannuwanta biyu ta goga a fuskan Abaas din Wanda bazai bazai taba barin gashi ya fito a fuskansa ba. Sake rungumesa Ayanah tayi suka sake samun Yar nutsuwa da dangana kafin suka miqe suna kama hannuwan juna suka bi hanya ahankali cikin galabaita Wanda babu ta yanda zaka zan akwai namiji a cikinsu.. Koda rana ta fadi babu me iya tsayuwa sosai a cikinsu sbd tafiya da azaba, Kafafunsu dukansu babu Wanda bai fashe ba, Kaman a mafarki suka fara hango ruwa me yawan gaske yake dukkaninsu suka Ji sun samu dan kuzarin daya qare musu. Ruwan suka nufa suna jin maqoshi da jininsu na sake qafewa. Ana magrib suka isa ruwan Wanda da rarrafe dukkaninsu suka qaraso sbd qarewar karfi gabaki daya, Nurat bata iya qarasowa ba sbd ranta dake gap da fita dan haka Abaas ne yayi saurin diban ruwan da hannuwansa biyu yana kawo wa inda take yana bata a baki batareda damuwa sa qazantar dake ruwan ba. Daqyar yake takawa yana kai mata ruwa yana zuba mata a baki har shima ya gaza ya fadi yana zubewa a gurin. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 10 *_PRIME SCENT_* 08103155915 Shin Kina neman duniyar kamshi ta turarukan wutan da in kin kunna zaki ji ki kamar a Royal palace din larabawa? Ko kuma kina neman wanda zaki kunna ya kaiki garden full of vibrant, mind & soul soothing fresh scents? Ko kuwa wanda zai baki rich and luxurious scent na elites? Ko kuwa kina neman qamshi mai sauke fushi da gajiyar da oga ya kwaso ne? Are you looking for qamshin da duk inda kika shiga sai kin janyo attention din mutane, ko kuwa wanda in an matso kusa dake sai an lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya na jin dadi da kwanciyar hankali tare da samun nutsuwa? Hajiya ta albishirinki! Ga PRIME SCENT Duniyar kamshin da babu kamarsa, Duniyar kamshin da ko kin bada kayanki ko curtains naki wanki baza su Dena bada kamshi me nutsuwa da dadin shaqa ba, PRIME SCENT sune kankat ba na biyunsu. 08103155915 ******** Ayanah datai tsananin laushi itama ce ta qaraso gurinsa da rarrafe cikin sauri tana kokarin kamo sa amma hannuwanta rawa sukeyi sosai gashi bata da kuzari sai kuma ta kasa iya Dena kokarin rungumosa jikinta idanuwanta da sukai surfi sosai suna kasa ko hawaye. Sakinah ce da itama taje Numfashi daqyar ta matso ta fara Debo ruwan itama a hannunta tana tahowa tana zubewa a bakinsa suka samu yasha sosai numfashin sa ya fara daidaita ya rufe idanuwa yana lashe lips dinsa da suka bushe qayau harsun fara tsagewa. Ayanah ma Sakinar ce ta kawo ruwan ta ringa bata ta dan samu karfi da kuzari itama tana lashe bakinta daya bushe ya tsatsage. Acan bakin ruwan sakinah tasha ruwan sosai itama kafin ta zube a gurin a kwanta tana sauke Numfashi bakinta itama yana samun sassaucin azabar yankewan bushewa. Zuhrah kuwa daman tana bakin ruwan tin dazi a kife Jin takeyi kaman ta fada ruwan ta sanyaye jikinta da bakinta da suka bushe har sun yayyanke musamman kafafunsu da basuda kyalla sun fashe kace kaca sunyi wata irin Dauda da munin kalla. Ba iya kafafunsu ne da munin kallo ba sbd Dauda me yawa hadda su sbd dauda ce sosai a jikinsu tareda jinin da sukayo gwagwarmaya dashi daya bushe a jikinsu tin daga kan na Ammansu dama Abaansu da Ayanah ta taba saina Asamah dama Sauran wainda aka kakkashe tin farkon barowansu babu me Kyan gani a cikinsu sbd sun koma wata halittar sbd dauda da kyama. Dukkaninsu kwance suke a gurin babu Wanda ya motsa Numfashi suke sauke wa a hankali ba kuzari kuma ma idan sun miqe basu San tayaya zasu tsallaka ruwan ba bare dan haka magana ce ta sake zagayawa dajin zasu yi Neman hanyar da zata fiddasu inda ba ruwa su fice daga nahiyar gabaki daya su fada inda garururwa da Jamaa suke. Shiru sukai kowa idanuwansa na kasa qaqaro hawayen tashin hankalin inda zasu sake komawa dan Neman hanya. Kasa tashi kowannensu yayi a gurin anan suka kwana kwance gaban ruwan kowa a inda yake zube anan ya kwana sai asuba suka dan iya tashi suka hade guri daya suka dunqule sbd tsananin sanyin ruwan dayake ratsa su. Daqyar suka iya sallah Bayan gari yayi haske suka sake Zaunawa guri daya a hade kaman kashin awaki, Shiru sukai suna tinanin yanda zasu sake komawa su kutsa cikin dajin Wanda basu San ranar fitar sa ba, Tsananin tsoronsu haduwa da Kusra da suke cikinsa dan haka suke Jin kaman suyita zama bakin ruwan har ransu yabar jikinsu. Zuhrah da har jikinta ya fara rawa sbd tsananin tsoro da tashin hankali tareda tina azababbiyar tafiyar kallan Ayanah tayi da idanuwanta da sukai ja sosai ta bude baki cikin tsananin tsoro da sallamawa tace ‘Ayanah wannan itace karshen kaddararmu, Mu karbeta kada mu koma dajin nan, Mu fada ruwan nan rayuwarmu tazo Karshe mu huta dan Allah, Bazan iya ba Ayanah, Mutuwar tafi mana biyu Hutu da sauki dan Allah Ayanah mu fada ruwan nan mu tafi mubar duniyar nan wlh bazamu iya ba, Koina bazamu kai ba zamu rasa kanmu dan haka dan Allah mu yankewa kanmu wahala….. Abaas na Jin hakan yaji zuciyarsa na Aminta da yadda da hakan dan haka Ayanah yake kalla idanuwansa cikeda hawayen rauni da ‘qunci yana Jiran jin tace ta amince da hakan, Kallansu Ayanah tayi tana jin zuciyarta na yadda da hakan itama sbd tabbas din bazasu iyaba dan haka gwara su mutu anan tin kafin azabar da ukubar tayi yawan da babu iyaka. Ganin yanayin Ayanah din na itama tana ganin hakan shine zai fi musu yasa Zuhrah Jin dan dadi dan har zuciyarsu gabaki daya sun zabi mutuwar sbd itace hutun karshe da zasu samu a wannan duniyar dan haka miqewa tayi tana Juyawa ta kalli ruwan tana Lumshe idanuwanta zuciyarta cikeda samun nutsuwa ta juya gurin Nurat dake Zaune quri babu alaman tasan komai dayake gudana a rayuwanta yanzu ta durqusa gabanta ta kamo fuskanta da tafukan hannuwanta biyu takai bakinta ta sumbaci gefen fuskanta da gashinta kafin ta hade goshinsu tana cewa ‘Nurat inda su Abaa da Amma suka tafi zamu tafi zamu bar nan bazamu iyaba,ke kin rasa hankalinki bazaki taba gane azabar da zamu shiga ba amma kuma zaki kasance cikin hadari dan haka mu tafi…. Kama hannun Nurat tayi ta miqar da ita ta kalli Abaas ta miqa masa hannu shima ya Kama ya miqe tsaye, Ayanah suka tsaya akanta suna kallan da jiranta, Abaas da Zuhrah din tare suka miqa hannu ta kallesu tana miqa hannunta ta Kama nasu zata miqe Sakinah tayi saurin riqeta tana girgiza mata kai tace ‘Idan kun zabi mutuwa Akan rayuwa zan biku Nima na zabi mutuwar sedai idan kukai hakan sadaukarwar iyayenku dan kawai ku rayu ta zama ta banza, Sadaukarwar Asamah ta zama ta banza itama, Ayanah ki tina su Abaa basu da burin daya wuce ku rayu kota yayane, Ku tsira kota yaya ne, Duka duniyar kowa dake gwagwarmaya yana yi dan cika burin magadansa da magabatansa amma ko kwanaki masu yawa baa yiba zaku kashe kanku sbd kasa rungumar jarabawa., Idan har jinin iyayenku ne jinin GHAZ yake yawo a jinin jijiyoyin jikinku to tabbas zakuyi kowace irin gwagwarmaya ku jure ku rayu dan tabbatarda burin iyayenku ya cika kun tsira sun rayu kun samu rayuwa da zaku tina baya ya zama tarihi, Wannan shine ya kamata ya zama sabon Alkwarin jini da duk wani jinin GHAZ zai taso a cikinsa na duk zuriar GHAZ da zasu zo a gaba wato juriya ga dukkanin tsananin rayuwa kowane iri ne ka tsira ka rayu, Karku manta kune jinin GHAZ na karshe Wanda kuna barin duniya dukkaninku to shikenan jinin GHAZ Yazo Yazo karshe kun shafe a duniya sedai a tarihi idan an ambaceku dan haka Kuyi hakuri Kuyi juriya Kuyi gwagwarmaya kuci gaba da jagorantar GHAZ ku yada zuriar da zata ci gaba da jan sunan GHAZ a duniya.’ Kuka Zuhrah keyi sosai da maganganun da suka shige su amma ita har lokacin tana jin tafi son mutuwar sbd bazata iya rayuwar da dabbobi ma sunfi su yanci da gata da rufin asiri tareda kwanciyan hankaliba, Kallan Ayanah dake kuka sosai kaman ranta zai fita cikeda da gajiwa take kukan idanuwanta sunyi kumburanda kaman zasu fado su tsiyaye. Maida kallanta kan Abaas tayi Wanda shima kukan yakeyi sosai hannuwansa na kakkarwa, Nurat ta juyo itama ta kalla wadda ta koma abar tausayi yanzu sbd bata iya cewa komai zuru tayi da idanuwanta dake bayyanarda tsananin qunci da Neman Hutu na barin duniyar sedai batada tinani na kanta yanzu sai yanda akai da ita. Itama Zuhrah jin tayi kaman kanta da zuciyarta bazasu dauka ba dan haka ta fara ja da baya tana hawaye. Miqewa Ayanah tayi batareda tasan tanada Sauran karfinba tayi kan Zuhrah din da sauri sedai Juyawa zuhran tayi tana nufar ruwan da gudu zata fada, Abaas ne shima yayi kanta da gudu hakama sakinah Ayanah Sakinah kuwa Nurat ta riqe sbd kada itama ta juye ta bisu ta fada ruwan. Har Zuhrah ta fada ruwan Abaas ya Riga Ayanah isa gareta ya riqota tana fizge wa tana kuka me karfi tana rokonsu su tafi. Rungumeta Abaas tayi sosai jikinsa yana bude baki cikin karfin Halin dake zuciyarsa data fara bushewa yace ‘Zuhrah zamu jure,zamu jajirce,zamu tsira,zamu rayu insha Allah zaku ma mu sake amsa sunanmu GHAZ wata ran…. Girgiza kai takeyi tana cewa ‘Aa Aa Abaas bazamu sake amsa sunanmu ba har abada gwara mu tafi dan Allah’ Girgiza mata kai yakeyi shima yana sake daurewa kukan dayake zuwar masa Ayanah ma rungumesu tayi dukansu tana maimaita abinda Abaas ya fada Akan sun rungumi hukuncin ubangiji duk tsananin tsanani zasu jure zasu jajirce zasu rayu a cikin kowane Hali dadi ko wuya. Kuka Zuhrah keyi sosai tana girgiza kai a hakan haka har suka fito ruwan suna samun guri suka zauna suna yin shiru tsawon lokaci kafin suka kalli juna suka sake daukanwa kansu alkwarin jurewa da rungumar kaddara tareda kasancewa da juna sbd duk masifa da munin rayuwan da zasu fuskanta idan suna tare da juna zasu jure dan rabu wa da junansu shine mafi muni da girman kaddarar da suke tinanin zai samesu Wanda gwara musu mutuwa Akan hakan. Fitowa rana ya saka suka miqe suna sake cika cikinsu da ruwan sosai suka bar gurin Bayan sun jiqa kayansu sosai da ruwa har suna tsiyaya ta yanda zasu yi tafiya me tsayi basu azabtu da tsananin Zafin rana da kishirwa ba. Komawa sukai cikin dajin suna kallan hanyar gabas suka miqa suna riqe hannun juna Nurat kuma tana hannun Abaas ya riqe hannunta gam cikin nasa. Wuni sukai suna tafiya har rana ta fadi duhu yayi suka nema guri suka zauna babu me iya numfashin arziki sbd wahalar yunwa da kishirwa. Dukkaninsu sunyi galabaitar da baa magana dan haka tinda suka zube a gurin babu Wanda ya sake motsi kaman matacci har gari ya kuma wayewa yayi haske. Numfashinsu fara Neman gagararsu yakeyi amma a hakan suka tashi suka sake bin hanya suna kasa ko riqe juna wannan Karan, Wuni suka sake yi suna yawo a dajin batareda ma sun San inda suke jefa kafafunsu ba gashi kaman dajin dayake da wani sirri dan baka iya gane gurin fita.. Kwanaki suka dauka suna ragaita a mummunan dajin Wanda zuwa lokacin tini suka fara cin ganyen duk icen da suka samu Wanda yafara maidasu kaman wasu dabbobi, Kamanninsu sun sauya daga mutane zuwa wasu kalar, Fatar su ta koma kaman busashiyar dabinon daya fito cikin qasar sahara, Bakinsu ya bushe ya far fashe jinin dayake fitarwa shi Kansa ya bushe, Wata irin dauda da qasa tareda qazanta ce kala kala a jikinsu Wanda bushewan da sukai qayau yake rage warin dake tashi a jikinsu, Zuwa lokacin dukkaninsu sun gama cire rai daga rayuwa harda Sakina kanta me basu kwarin gwiwa wannan Karan mutuwar take fata da son ta dauke su sbd rayuwa dai ta qare musu a inda ko gawarsu basuda me kalla yayi musu fatan rahama sedai tsutsa su cinye namansu iska ya busar da saura sbd ko dabbar da zata cinye namansu a dajin babu. #MAMUH #BEST STORY #ROYALTY #SLAVERY #BEST LOVE #BOYEM HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 11 *_PRIME SCENT_* 08103155915 Shin Kina neman duniyar kamshi ta turarukan wutan da in kin kunna zaki ji ki kamar a Royal palace din larabawa? Ko kuma kina neman wanda zaki kunna ya kaiki garden full of vibrant, mind & soul soothing fresh scents? Ko kuwa wanda zai baki rich and luxurious scent na elites? Ko kuwa kina neman qamshi mai sauke fushi da gajiyar da oga ya kwaso ne? Are you looking for qamshin da duk inda kika shiga sai kin janyo attention din mutane, ko kuwa wanda in an matso kusa dake sai an lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya na jin dadi da kwanciyar hankali tare da samun nutsuwa? Hajiya ta albishirinki! Ga PRIME SCENT Duniyar kamshin da babu kamarsa, Duniyar kamshin da ko kin bada kayanki ko curtains naki wanki baza su Dena bada kamshi me nutsuwa da dadin shaqa ba, PRIME SCENT sune kankat ba na biyunsu. 08103155915 ******** Idanuwan Ayanah da suka koma manya sbd gabaki daya naman fuskanta daya tafi babu shi sai qashi zalla Wanda Kana kallanta zaka dauke idonka akanta sbd gabaki dayansu haka suka koma babu Kyan gani sbd babban cin kamannninsu da wanda qwarangwal fata ne da dan abinda baa rasa ba sai Sauran rai dayake jikinsu, Kallan kannenta dake kwance gefenta dukansu kaman gawar dataqi rami takeson yi amma ganinta yayi Raunin da bata iya gane wa sosai dan haka bushashen hannunta ta motsa daqyar yakai kan fuskan Abaas wanda wasu haqoran wahala kawai ta iya Ji a fuskan tasa wainda sune kadai a tsaye sbd babu komai a fuskan tasa idanuwansa sunyi zurfin data kasa iya tantance ramin ido ne ko kuwa ramin bakinsa dan haka ta sauke wani wahalallen Numfashi daqyar tana taba Zuhrah wadda cikinta ya hade da bayanta ta koma halittar da zata iya firgita qananun yaran gata. Hawayen da babu su ne a jikinsu Ayanah ke kokarin hada wa amma babu yanda zasu taho sbd basu da Sauran ruwan komai a jikinsu sbd fitsarinsu ya dade da komawa baqi qirin sukeyinsa alaman babu Sauran ruwan komai a jikinsu. Nurat wadda kowane lokaci ranta zai iya fita jikinta ta sauke hannunta akanta tana Jin kanta ba komai sbd gashin kanta data ringa figewa a kwanakin sbd azaba da rashin cikakken hankali. Rufe idanuwanta tayi tana Rokan Allah ya kawo musu daukin da shine ya kamacesu. Sakina ta dan kalla daqyar bata gane kamanninta tana fatar ko a Aljannah Allah ya hada su guri daya da Sakina sbd ta zama jininsu koda basu hada jinin gaske ba. Zafi garin ya sake dauka sosai da tsananin azaba har rana ta fadi suna kwance har duhun dare yayi, Tsakiyar dare ruwan sama ya sauko wanda da ruwan saman ne daman suke samun sauki a wasu lokutan. Yanzunma ruwan saman ne dayake sauka kansu sosai ya dan saka wasu daga cikinsu motsawa amma ba wanda ya iya tashi har saida ruwan ya dauke da safe tukuna dukkaninsu suka bude idanuwansu amma babu me iya tashi. Zuhrah ce kunnuwanta suka fara jiyo mata takun mutane me dan karfi kadan kadan sai ta Lumshe ido tana fatar abinda take Jin da gaske ne dan kuwa suna buqatan koma masu kashe su ne a yanzu suzo su kashe su tinda a yanzu basuda ma karfin yi da kansu. Hanyar ta qurawa ido daga kwancen datake duk da bata gani sosai gabaki dayansu dishi dishi suke gani ganinsu ya samu matsala wanda kaman illar ganyan da suke ci ne kaman dabbobi. Ayanah ma ahankali ta fara jiyo takun amma bazata iya Juyawa ba bangaren ta kalla sedai Lumshe idanuwan datai na jiran tsammanin koma menene sbd su yanzu kusan tsoro ya cire daga rayukansu. Sauran ma dukansu suna jiyo takun da sautin sa ke amsawa a dajin ta nan bangaren da suke, Sakina ce tafara daga hannu Daqyar tana fatar a hangosu su samu koma wane irin dauki ne. Shiru shiru baa nufo ta bangaren da suke ba har yamma basu Dena jin hayaniya sama sama ba, Duhu ya fara harsun cire rai da tsammani ita Zuhrah da Nurat harma da Abaas duka sun some babu me Sauran numfashi a jikinsu. Sakina da Ayanah ne keda Sauran numfashi amma suma idanuwansu a rufe koma sun bude basa ganin komai se duhu ga kuma dare. Tsakiyar dare sosai Ayanah itama ta some gabaki daya bata numfashi sakina data rage sama sama taji magana akansu Ana cewa ‘Muna buqatan hada wa dasu tinda sunada Sauran rai idan anje can zasu farfado tinda kams yace duk wani dan Adam koma dabba ce idan har tanada rai a tattaro a kawo masa sbd yaune ranar mu tanada qarshe a wannan nahiyar Bayan tsawon shekaru idan muka tafi yau har abada munbar nan tinda a yanzu babu gari anan sedai a tarihi kuma., Daukansu sukai dukansu tsaf suka bar gurin dasu suna dorawa Akan dokuna masu karfi bakyan gani suma sbd abubuwan da duk suka Shafa musu da adon ban tsoro. Suna barin gurin itama sakinah ahankali numfashinta ya tsaya bata sake sanin inda take ba. Mutane sosai suka tattaro a dajin duk sun galabaita wasu kuma sun mutu harsun bushe wasu kuma suna gap da mutuwar wasu kuma macijai sun kashesu wasu kuma sun zare sbd gane ganen Masifa hadda jinnu. Fiyeda Rabin tarin yawan rayukan garin ANJOM sun kashesu dan haka wainda suka mutu sunfi wainda suka Kama sosai dan haka basu wani samu yanda suke so ba Shiyasa ya bada umarnin a sake shiga dajin da zagayensa a kamo wainda suka tsira sbd ya samu tarin bayin da zai siyar wannan Karan su haura daruruwa dan yanada wasu tarin bayin dasuka safaro daga nahiya daban daban a cikin jirginsa me kamar gari guda. Bayan gari ya waye har rana ta keto tukuna suka samu gama hada bayinsu a cikin bangarensu daban can qasan jirgin wanda kowace bawa kafafunsa a daure suke da kaca hannuwansu ne kadai a sake, Su Ayanah da ire irensu da suka gama lalacewa mutuwa kawai suke jira daban aka ware su Ana zuba musu ruwa duk bayan dan lokaci. Yamma sosai kusrawa suka daga daga nahiyar gabaki dayanta har abada sbd basa maimaicin zuwa gari komai nasarar da suka samu akansa, Sun dauki shekaru a nahiyar ANJOM din wanda daga karshe sun samu abinda suke samu dan haka kai tsaye daga nan nasararsu da cikar burinsu zai cika sbd wainnan bayin na kaiwa MASARAUTAR BOYEM ne, Masarautar da duk suka samu ta karbi bayinsu to tabbas burinsu ya gama cika na duniya. Masarautar da babu kamarta a iko da tarin mulki da arzikin dayafi na kowace Masarauta tarihi, Idan har BOYEM ta karbi bayinsu to tabbas zasu shiga cikin littafin tarihi da ko Bayan shudewansu zaa San kusra. Jirginsu ahakali ya daga daga nan yana keta wa tareda Kama hanyar ruwan da zasu tsallake sama da nahiya hamsin kafin su isa nahiyar BOYEM. ********* tafiya me nisa akai ta kwana da wuni baa gama fita nahiyar dajin ANJOM ba wadda a qalla sai sunyi kusan sati kafin su fita dajin. A wannan kwana da wunin babu wanda ya farfado a cikinsu Ayanah saida aka kuka wuni tukuna suka fara farfadowa shima sbd ruwan da aketa zuba musu ne masu tsananin sanyi. Suna bude idanuwansu cikin Ayanah ce ta fara bude ido taga inda take cikin wani irin rikitaccen karfin da baifi ma jaririn rago ba ta yunkura tana tashi amma bata iyawa sosai, Sunan Abaas tafara ambata cikin dan karfin datake dashi tana dudduba gefenta dataga mutane barkatai sama da Dari duk wasu a kwance. ‘Zuhrahhh,Abaas,Nurat,Sakinah…….. Haka ta ringa jerosu tana kiransu jikinta na Wani irin mummunan rawar tashin hankali. Zuhrah ce ta fara jiyo Ayanah din da sauri itama t bude idanuwanta tana kwala sunan Ayanah din da dan karfi hankalinta a tashe ko gani batayi ta miqe tana kokarin takawa ta kife sbd kacar dake kafarta. Bude ido tayi a inda ta fadi sai idanuwanta suka sauka Akan Abaas cikin sauri ta cakumosa tana kwala kiran Ayanah. Ayanah gurin ta rarrafo ta iso suka rungume juna da karfin gaske suna jin sassauci. Nurat suka fara kira itama tareda sakina sai kuwa gasu sun gani a guri daya take suka rungume juma kaman Ana partyn ‘yayan aljanu sbd yanda suke hada qasusuwan jikinsu suna rungumewa. Can Kurya suka rakube inda baida haske sbd basason Abaas na bayyana sosai kada tsautsayi yasa a gane duk da bazaka taba kallansa kai tsaye kace ga ba macen bane suka maqale juna a zazzaune kowannesu da kaca a kafansa. Tsoro ne zuciya da gangar jikinsu sbd sun gama tabbatarda sun Riga sun zama bayi, Sun zama bayinda har abada basu yancin rayuwarsu sai yanda akai dasu, Sun rasa sunansu,sun rasa asalinsu rayuwa kuma yanzu sedai wadda aka zaba ko hukuntar musu. Bude kofar qaton dakin da suke akai daga sama kofar take. Kallo wanda ya bude kofar yayi musu tsaf kafin ya fara Jeho musu daurin gayar tuwon alkama da akai da nono. Masu dan karfin cikinsu take suka fara ruguwan Abinci suna tura Bakinsu cikin tsananin yunwa da ficewa hayyaci. Sakinah ma cikin karfin Hali ta yunqura tana wawaso abincin tana jefo musu take jikinsu na rawa suka fara sararsa suna Turawa Bakinsu hannuwansu na rawa. Zuhrah dataji kaman bazata iya tsayawaba yake itama ta rarrafa ta fada cikin wawason tana Turawa bakinta a haukace. Abaas ma fadawa yayi hakama Ayanah da Nurat Take suka zama kaman mahaukata kowa wawa yakeyi yana Turawa bakinsa a haukace. #MAMUH #BEST STORY #BEST LOVE #ROMANCE #ROYALTY HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 12 A cikin Hali na wawason suka ringa Turawa Bakinsu ko taunawa basa yi hadewa kawai sukeyi yana wucewa maqoshinsu da wani irin karfin gaske, Wani irin kuka hanjinsu keyi na samun abinda suka dade basu samuba wato abinci, Danne juna ake yi sosai Ana yiwa juna rauni da hakan suka samu suka cika cikinsu sedai kusan dukkaninsu sun samu rauni dan haka suka rarrafa gefe suka rabe suna dunqulewa sbd tsananin ciwon ciki daya taso musu. A kwance suka wuni ba lafiya sosai sbd ciwon ciki da lafiyarsu da daman babuta yanzu, Tsakiyar dare haka aka sake zuwa aka kawo abincin Ana jeho musu suna wawaso sedai wannan karan ba kowane ya iya tasowa ga abincin ba sbd kusan duka dakin basa da lafiya dan kuwa duka kusan ciwon su daya ne ciwon ciki sbd dade wa me tsayi ba abinci, Zubewa suke son yi kwance su jujjuya ko azabar ciwon cikin zai rage amma dakin babu gurin da kowa zai samu ya kwanta sedai suyi rayuwar zama a cikinsa ko bacci sedai kayi daga Zaune. Dan haka su Ayanah babu Wanda ya iya zuwa cin abincin tsakar Daren se Nurat data fada cikin masu wawan tayita ci da hauka itama sbd rashin cikakken hankali ne kuma duk anji mata ciwo sosai hada bakinta aka fasa yana jini suna kallo babu me iya motsawa saida ta koshi dan kanta ta dawo cikinsu. Kwantar da kansu sukai a kafadun juna suna sake lafewa jikin juna da babu wani sauran taushi na tsoka sai qashi amma su a gurinsu hakan shine mafi nutsuwa da kwanciyan hankali Jinsu a jikin juna, Amai wasunsu suka fara wanda ya hargitsa numfashin dasuke shaqa a gurin, Amai sosai kowa yakeyi haddasu Ayanah din saida dukansu suka galabaita amma a hakan baa bude su ba saida safe gari ya waye sosai aka bude su haka aka ringa zubo musu ruwa masu yawan gaske daga sama Ana wankesu kaman dabbobi, Bakinsu suke budewa ruwan na shiga har sukasha sosai kafin ruka zauna ruwan na dukansu da ake zubowa har jikinsu ya wanke tas. Kowa saida jikinsa ya wanke kafin aka fara Fiddosu daya bayan daya daga dakin ana Jere su a fili. Babu me iya miqewa tsaye sosai sbd yunwa da wahalar data gama cinyesu, Hasken sararin samaniya suke kalla yana kashe musu idanuwa sbd duhun da suka fito cikinsa, Kirgasu aka fara yi Ana daya bayan daya Ana raba maza daban mata daban Wanda anan hankalinsu ya tashi tsoro da fargaba suka shigesu Ayanah ta miqa hannu cikin na Abaas da dukkanin jikinsa yake rawa sbd fargaban kada a ganesa, Su duka rawa jikinsu keyi dan Ana gane Abaas mutuwa ce tahau kansa, Qanqame hannunsa Ayanah tayi shima qanqame nata tayi Zuhrah kuwa mannewa tayi a jikinsa itama tana riqe sa suna kokarin hana bayyanar tsoronsu da fargabansu. Shi Kansa Abaas zuciyarsa cikin wani mummunan Hali take na halin da zasu shiga idan asirin hakan ya tonu. Duk Wanda aka Kirga sai an masa sheda a gefen hannunsa da wani karfen wuta. Ana zuwa kansu Nurat aka fara fizgo wa aka kirqa baa tsaya komaiba aka manna mata karfen wuta a gefen hannu Wanda ya sakata qwalla wata gigitacciyar qara tana zubewa a gurin. Cikin firgita Ayanah tayi kanta zata tarota tayi mummunan kife wa kanta na buguwa da katon drum din ruwan dake gurin Wanda ake watsawa duk Wanda ya sume gurin ruwa sbd azaba. Wani Juyawa kanta ya ringa yi sbd bugawan da yayi bata dawo hayyacinta ba taji saukar azababbiyar azaba Akan gefen hannunta Wanda ya sakata somewa a gurin itama. Motsawa Abaas yayi da sauri yana yin kanta itama shima ya kife sbd sarkan dake kafarsa hakama Zuhrah. Anan aka mannawa kowa tasa Shedan cikin azaba suka dunqule suna fidda Wani irin zufa Zuhrah saida ta yanka Wani irin Ihun azabar da bata taba jiba, Abaas duk tsananin azabar dayaji rana ratsa jini,tsokar jiki,qashi da kwakwalwansa kasa ihu yayi sbd Alkwarin da sukaiwa juna na har abada idan basu fita wannan ukubarba bazai taba magana aji sautinsa ba na namiji dan haka daga lokacinda ya aka saiya jinsa zuwa na mace ya koma kurman da baya magana sedai nuni. Wasu irin hawaye masu Zafin radadi a ido da zuci ne suka gangaro masa na tsananin azabar dake ratsashi gashi shi ya kasa somewan. Bulala aka daga me kaurin gaske ta fatar dabba aka zabga masa yayi daurin rintse ido numfashinsa na sarkewa akace ya tashi. Da rarrafe ya koma gefen wainda akaiwa Shedan numfashinsa har lokacin na kokarin yankewa hakama yanason fasa kukan azabar dake ratsashi amma fitan sautin kukansa zai bayyana sautin muryansa datake da dan kauri ta maza dan haka haka yaci gaba da danne azabar yana hadiyewa jikinsa na wata irin muguwan rawa. Zuhrah ma dake Ihun gigitacciyar azaba har lokacin bulala me Zafin datakai azabar wutar aka sakar mata wadda ta sakata sakin qara me rikitarwa Tana rarrafawa gurin Abaas nenam dauki. Ruwa aka watasawa su Ayanah da Sauran bayin da suka some Ana dukansu da Bulala a haukace suke rarrafawa gefe suka fadawa kan yan uwansu. Sakinah ma bata some ba amma tashiga kidima da fitar hayyaci azaba, Nurat duk rashin hankalinta kuka takeyi sosai na azaba Tana nunawa Ayanah hannunta dake tsananin radadi. Hawaye Ayanah ke fitarwa Tana rungumesu cikin azaba da wahala me tsanani suna dauriya da karban wannan sabuwar masifar da suka samu kansu kuma a ciki. Ana gama kirgasu aka fara raba musu Abinci suna karba Ana wucewa dasu dayan dakin da Sauran bayin duka suka ciki sama da daruruwa masu shegen yawa. A yunwace suna jin azaba suka hau cin abincinsu Bayan sun Nemi guri sun rakube a cikin dakin, Ana gama shigo da kowa aka rufe kofofin dakin dake sama take dakin yayi duhu nan take kuma aka fara ihu da kuruwa tareda hayaniyar kokuwan masu karfi da marasa karfi gurin qwacen abinci. Cikin tsananin sabon tsoro su Ayanah suka qanqame juna suna hadewa guri daya take sakinah ta tura Abincinta duka a baki tana hadiyewa tace suka Suyi hakan. Tura abincin sukai gabaki daya a baki suna hadewa cikin azaba da wahala yana yankar maqoshi amma haka suka Hadiye. Kafin kace me gurin anji wa sama da Mutum Hamsin rauni wasu ma a qonuwarsu aka raunatasu. Su kansu Ayanah sunsha duka da shuri na mutane kafin dakin yayi tsit Angama kokawar. Wani Daren ne ya tsala sosai koina yayi tsit duk da basa gane dare bare rana sbd duhun inda suke dan amma shirun ya tabbatar da Daren yayi. Babu Wanda ya samu bacci a cikinsu shiru sukai zuru a jikin juna har lokacin suna maqale, Zafin zazzabi me karfi ne ya fara saukarwa Nurat har tana dan fizga Hakan yasa Ayanah rungumeta a jikinta Tana Shafa bayanta Ahankali, Itama zazzabin take fama dashi sosai amma bata kwantaba sedai jikinta da yayi Wani irin zafi sosai. Zuhrah ma zazzabin ne ya sakata zame wa ahankali ta kwanta da jingina, Abaas ma karfinsa lamarin yaci ya bangare a gurin idanuwansa na rufewa jikinsa na rawar zazzabin. Sakinah duk abinda suke Ji tana jinsa amma haka ta daure ta taya Ayanah kulawa dasu duk da babu abinda zasu iya ko suke musu Bayan Shafa bayansu dan basu sassauci koma yayane. Gari na wayewa tinda Sauran duhu aka bude kofa aka diba Mutum hamsin aka fice dasu zuwa aiki. Dayan dakin suka wanke me tsananin girma tareda aikin tsafta ce duka Sauran koina dake jirgin, Suna aikin suna Shan Wani irin dukan azaba a haka suka gama aka dawo dasu kafin aka fara jeho musu abincin safe Bayan rana ta dade da yi kenan. Haka suka wuni cikin duhu da azaba har wani Daren kafin aka sake basu abinci Wanda kullum so biyu ko daya ake basu abinci. Fitsari da kashinsu kuwa anan suke yinsa a cikinsu cikin wata qatuwar durum wadda aka ajiye a karshen dakin cikinsu sai da safe ake sakasu kwasarshi suna zubarwa a iska dan haka a cikin mugun wari da qarni da Zarni suke kwana suna wuni. *******ahankali ahankali su Ayanah suka fara fuskanta da yadda da wannan rayuwar fa itace yanzu zasu yi har karshen rayuwarsu dan haka duk muninta haka zasu karbi kaddarar rungumarta su koyi yinta, Hakan ne ya saka suka fara sabawa Bayan sunyi ciwon,sunyi ciwon amma gangar jiki tafara sabawa da duka da wahala, Hakama hanci da hanjin cikinsu sun fara sabawa da wari tareda manta akwai kamshi a rayuwa, Idanuwansu da zuciyoyinsu sun saba da duhu da qunci sbd a cikinsa suke rayuwa dip Baka ganin ko dan uwanka dayake kusa dakai Shiyasa su Ayanah basu taba yadda sun matsa ko inci dayaba daga junansu, Ko lalurar zagayawa Fitsari ko abinda ya fisa ya kamasu tare suke zuwa da sarka a qafafunsu su jira Wanda zeyi su gama su dawo tare, Sunayin hakan ne na zuwa gabaki daya dan bawa Abaas kariya daga tsautsayin wani ya gansa. Rayuwar bauta sun Riga sun samu kansu a cikinta dan haka yanzu basuda Sauran Buri Bayan Allah yabar su tare suyita bautar a tare da junansu. Ahankali yunwa ta fara barin jikinsu duk da ci daya ko biyu suke samu a rana amma sbd suna samu din dai dakuma Zaune da suke guri daya ba rana sai suka fara rage mummunar kamar aljanu da suke cikinta amma ita datti da wahala a jikinsu har lokacin qaruwa ma takeyi ba raguwaba. Duk wannan rayuwar da suke Abaas ya zama Kurman da gaske bai taba magana ba koda tsautsayi komai wuya kuma baya fidda sauti haka yake hadiyewa musamman idan Ana dukansu bai taba fidda sauti ba ko su yan uwan nasa yanzu da hannu yake musu magana duk da magana ba basu cika yiba sbd baqin ciki da qunci rayuwa daya gama cike zukata da bakinsu babu abin fada sedai ido. Tafiyar Sati hudu sukai a cikin ruwan kafin jirginsu ya sauka a wata babbar qasar da zasu tsaya su siyar da wasu qalilan daga bayinsu dan siyan Kayan abinci su zuba a jirginsu tukuna su wuce dan haka zasu yada zango anan na kwanaki kafin su wuce. #MAMUH #SLAVERY #ROYALTY #BOYEM #AYANAH #YANAH #BEST LOVE #BEST STORY HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 09033181070 13 *JEWELRY JUNCTION* 08039440312 Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma, Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne?? To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan, Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana, ✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌 ✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌 ✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌 ✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍 🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah. WhatsApp 08039440312 Tiktok :@sokoto jewelry seller Instagram: jewelryjunction23 ************** Koda suka iso qasar Boshan tsakiyar dare ne amma bakin bodar ruwan tamkar rana tsaka,tamkar Ana gagarumar cin kasuwa sbd mutane sosai da hasken wuta fitilun itace da kyandir koina fes anata cin kasuwar komai da komai a lokacin harma da kasuwar bayi ake ci wadda itace ma tafi komai karfi a gurin wato cin kasuwar mutane a matsayin bayi, Kaman yanda ake kasa kifi a Jere Ana cinikinsa haka aka baza bayi gasunan kashi kashi daban daban Ana siyar wa, Kason masu karfi lafiyayyu daban hakama kudin su daban, Kason masu Yar dama dama daban suma kudin su daban, Kason gajiyayyi daban da kudinsu suma daban Hakama akwai Kason yan yara yara daban. A daure suke da sarka hannuwansu da kafafunsu kowa ya Kebe nasa sai cinikayya ake yi ta siya da siyarwar, Garuruwan dake qasar boshan din kusan dukansu kaf anan suke zuwa cin kasuwan bayi Ana kaiwa masarautun cikin qasar dan haka wakilan Masarautu ne da dama suke zuwa cin kasuwar hakama Ba Masarautu kadai ba duk wani me arziki ko dan rufin asiri idan yanada kudin sa yana siyan bawa dan hidimarsa da raayinsa Shiyasa ake siyan bayin a duniyar wannan qarnin sosai sbd duk me rufin asiri baya rasa bawa daya ko bayi fiyeda daya a gidansa dan hakan ne sosai kasuwancin bayi yake tafiya a duniyar. Bude kofar inda tarin bayin suke akai na babban jirgin kusrah dayafi kowanne jirgin girma a nahiyar take dukkanin yawancin bayin dake cikin gurin suna Numfashi ahankali cikin wani yanayi dagowa suna saukewa tareda fidda Numfashi me dan nauyi sbd a yanda suke din numfashinsu ya cike dakin koina duk girma sbd tsananin yawansu sai numfashin gurin yayi dum babu inda iskan gaske yake shigo musu dan haka wasunsu da yawa sun Laushi sun galabaita sosai da numfashin wasuma sun fita hayyacinsu wasu kuwa harsun some. Hakan suke rayuwar ta bayi wadda numfashinda zaka shaqa ma kusan kaman Ana qayyade musu me kyau da mara kyau ne sbd su da samun Numfashi me nutsuwa da iska sai an bude su kuka Ana gamawa ake sake rufe su. Isowarsu ya saka kasuwar dake daukan shelar isowan kusrawa da tarin bayi masu kyau da lafiya da karfi dan haka kowa ya dakata yana rage siye siye dan Adana kudinsa na siyan bayin kusrah din. Saida suka dauki lokaci mai tsayi suna fidda bayinsu da kowa ke fatar a nan zaa siyar dashi wahalarsa ta ragu, Su Ayanah ma da suka fahimci rage bayi zaayi anan din a siyar taje dukkaninsu suka fara fatan suna cikin wainda zaa siyar anan su kubuta daga hannun kusrawan ko zasu samu Numfashi kadai ma ya ishesu. Cikin rashin saa Ana zuwa kansu adadin wainda ake son diba ya kare dan haka aka turasu da karfi Ana dukansu da bulalar data sakasu rarrafawa zuwa baya aka rufe kofar. Koina jikinsu radadi yakeyi amma a hakan kallan jikin juna sukeyi kafin duka tsayar da hannuwansu jikin Nurat dayafi na kowa fashewa suna Shafawa cikin duhu suna hura mata tana kasa kuka sai qanqame Abaas datai sbd ita rashin hankali ya saka bata ma iya kowane kuka sedai ihu idan taji azaba. Bayi arbain suka diba aka fito dasu kowanne da tambarinsa na bayin kusrah a hannu Wanda akai musu da wuta, Ruwa suka zuba musu sosai Wanda ya wanke daudar da suke cikinta kafin suka fito dasu daga jirgin Wanda aka bude kusrawan na saukowa sama da su tamanin suka fito dan shaqatawa da cin kasuwar dan ko shigabansu baya fitowa duk qasar da zasu idan ba babbar qasa ba dan haka duk kwanakin da zasu yi shi bai cika fitowa ba sedai manyan yaransa su ciye musu kasuwar su siyo Kayan abincin da zaa zuba jirgin dazai dauke su satittika kafin a isa wata qasar idan har ya fito to sun isa inda zasu zube bayinsu gabaki daya su siyar dan hakanne wannan Karan idan ba sun isa manyan qasashe ba ya fito ya dan sha iska ya koma to tabbas sai sun isa BOYEM zai sauko gabaki daya sai kuma sun gama sun bar qasar. Kaman dabbobi haka aka janyo bayin Bayan an hade sarkar dake daure dasu guri daya gabaki dayansu dan haka a Jere suke kansu a qasa sanyi me tsanani yana ratsasu. Tambarinsu na kusrah da asalinta yake ma kasuwacin bayi suka nuna tareda rubutun dake cikin busashiyar fatar raqumi suka nuna tukuna aka bude musu bodar shigowa garin qasar dan haka suka shigo Kai tsaye dan daman duk qasar da zakaci kasuwar siyar da bayin Ka sai kanada Shedan kasuwancin wanda shi zai Baka izinin shiga qasar. Kai tsaye cikin kasuwar suka ratsa da bayinsu inda tini aka fara ganin wainda akeso a cikinsu sbd bayinsu duk wuya da munin halinda suke ciki basada yunwa kamar Sauran sbd hakanne suke kokarin basu abinci so biyu dan kada yunwa ta hanasu daraja Shiyasa akeson bayinsu basa bushewa sosai kaman na sauran. Tsakiyar kasuwar suka bajesu a gefen wata rumfar me siyar da agwagi da kaji harma da manyan dabbobi. Daure su sukai a tirke Dayan Bayan Dayan kafin suka ajiye me tsaresu suka baza ma cikin garin bakin bodar da gabaki dayansu kasuwa da gidan karuwai da hutawa ne dan su huta sai gobe zasu ci kasuwar bayin. Kai tsaye gidajen karuwai suka rarrabu sai wasu kuka mashaya dan samun jin dadi, Wanda yake shugaban tafiyar Kai tsaye gurin hutawar dayafi na koina a bakin bodar ya isa take aka Kama masa daki tareda lafiyayyun tsala tsalan matan da suka Ji ado daidai misali na azurfa taka yana zare makaman jikinsa yana jefarwa yana nufar lafiyayyan gadon dakin yana isa ya zare Kayan jikinsa yayi Zigidir yana wani irin zama tareda baje koina jikinsa ya dago yana binsu da mayen fitinanniyar kallo kafin suka fara tako wa ahankali suna zare nasa Kayan jikin suma suna masa Wani irin girgizan dake sake tada dukkanin wata kakkarfar shaawansa. Hannu ya saka da karfi yana fizgo daya daga cikinsu sbd hakurinsa daya qare gabaki daya Tura kanta yayi tsakiyar kafafunsa yana Lumshe idanuwansa da karfi tareda dake ihu me karfi yana kwantar da Kansa baya sbd halinda yafara jin Kansa ciki. Ihun dayake sakewa yake tabbatarda nishadin dayake ciki tareda biyan buqatan dayake saukewa sbd kaman Wanda ake yanka naman jikinsa haka yake ihu yana qarawa duk sbd jin dadi. Suma sauran kusran kowannensu na nasa gurin daban yana jin dadinsa har gari ya waye suna abu daya dan haka saida safiya tayi suka kwanta bacci kamar matacci Bayan sun biya karuwan azurfa me yawa. Rana ta keto sosai amma har lokacin basu fito ba suna can suna hutawa. Bayin da aka ajiye tsakiyar kasuwar rana ta fito da tsananin zafinta akansu azaba suke Ji me karfin gaske ta zafi, Jikinsu yayi Wani irin daukan Zafin da kaman namansu da fatar su zasu gasu a ranar, Zufa sukeyi sosai Wanda ya jiqa kayansu duka gashi ita kanta qasar da suke Zaune Jere akanta ta dauki wani irin Zafin da suke jinsa har cikin kwakwalwansu dan haka suka galabaitu basa ko iya dago Kai ga kishirwa amma har lokacin baayi ta kansu ba, Sai guraren yamma tukuna suka iso aka bude kasuwarsu tareda saka musu kudi take aka fara siyansu cikin kudi me daraja Ana zare duk Wanda aka siya Ana cire masa sarka a miqa sa. Har cikin dare sosai Ana cin kasuwar wadda ta sake dauka zafi da hada hada sbd wasu ma manyan masu kawo bayin da suka iso bodar suma a cikin Daren. Ana gamawa sake komawa sukai hutawa abinsu hankali kwance suna cigaba da huldodi su. Acan cikin jirgi ma kusan duka kusrawan hutawa sukeyi tareda jin dadi sosai da bayi dan kusan kullum sai sun fasa budurcin matan dake ciki hakama musamman shugaba khams da baya kwanciya da mace sai wadda shine zai fara fasata Idan kuwa ya kwana da mace yaji ba shine na farko ba a bakin rayuwarta kenan sbd a Daren zaa yankata a jefar cikin ruwa, Idan kuwa ya kwana dake baiji wata gamsuwa ba yaransa ne zasu qarasa lalata rayuwarki sbd kusan namijin dazai dandana yaji baida adadi. A hakan da yawa bayinsu mata ke mutuwa Wainda basu mutu ba kuma da yawa ta hakan suke tara yayan dake girma su zama kusrawa Shiyasa suke da mugun yawa. Akwai wainda kuma a cikinsu da mazan suke amfani Akwai wainda suke amfani da matan kuma suyi da mazan. Wannan Sabon mummunan tashin hankalin daya qarasa tabbatar musu da su din basuda banbanci da dabbobi a gurin uwayen gidan nasu ya saka hankalin mummunan tashi tareda shiga firgici mai tsanani tareda rashin nutsuwar zuciya burinsa ya duqufa ga fatar a siyar dasu koma ina ne su fita cikin kusrawa. Tinda suka tsaya bosham baa taba fiddaso su ba sedai a bude su a basu abinci a sake rufe su tsananin ma qaruwa yayi sbd yanzu a tsaye jirgin yake. Kwana shida suka shafe a bosham kafin suka daga zuwa ci gaba da tafiyarsu. Tafiya ce take tafiya suna qara shiga tsanani da munin rayuwa sbd sun tashi daga halittarsu zuwa wata halittar daban, Basa da yunwa sosai sbd Ana samun ci amma kuma tsanani da azabar dasuke ciki tayi yawan da hankalinsu yake Neman fara gushewa, Tashin farko Kana kallansu zaka dauka tarin mahaukata ne aka Kama, Kana doso su wari da qarni ne yake daibaiye da rayuwarsu Wanda hanci da zuciyarka bazasu iya dauka ba, Gashin kansu Ayanzu Nurat tafi su jin dadin rayuwa ta wannan bangaren sbd a yanzu ita batada gashin da yawa sbd duk ta cire sai Wanda ya fito mata a yanzu sabanin su da datti da cututtuka suke cikinsu nasu suna damunsu. Tsoron dayafi na mutuwar dake cike da ransu da kowace gaba da jinin dake yawo cikin jijiyoyin jikinsu shine yanda ake kwanciya da bayin sosai, Ba kullum ake zuwa zaba ba amma akai akai Ana zabar dan haka tsoro ya gama toshe kwakwalwa su da suke fatar mutuwa kafin hakan ta kasance da dayansu, Abaas ma addua da fatan dayake Allah ya dauki ransa dayaga ranar da zaa keta haddin daya daga cikin yan uwansa sbd zuciyarsa bazata iya dauka ba, Dukansu fatar su daya ce Allah ya hanasu dandana wannan baqin cikin da kaddarar dan haka suka qara fita hayyacinsu sosai. #MAMUH #ROYALTY #BOYEM #NUAB BOYEM #SULTAN BOYEM #JEALOUSY #PROMISES HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 09033181070 14 *JEWELRY JUNCTION* 08039440312 Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma, Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne?? To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan, Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana, ✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌 ✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌 ✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌 ✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍 🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah. WhatsApp 08039440312 Tiktok :@sokoto jewelry seller Instagram: jewelryjunction23 *************** Tafiyar sati shida ta kawo su qasar baskar inda suka share sati guda a garin suna cin kasuwa kafin suka tattara suka bar qasar suka sake Kama hanya Bayan nanma an siyar da wasu bayin, Tafiyar sati biyu sukai suka tsaya wani garin daya raba tsakanin wasu qasashe guda biyu suka sake tarwatsa wani garin suka kwashe mutanen ciki gabaki daya masu tsananin yawa suka bar qasar. Qaruwar yawansu ya saka tsoro da fargaban su Ayanah raguwa kadan sbd warin yawansu zai saka su samu tsira daga mummunan rayuwar da suke tsoro hakama wainda aka kamo din yanzu sunfi su Kyan gani sbd basa tareda wahala fes suke dan haka sune masu daukan hankali. Su kuma wainda aka kamo din tsoron su Ayanah sukeyi da sauran bayin sbd babu me Kyan gani a cikinsu sun koma baqi qirin kamar gumakan bautar qabilu hakama wani wari da tsami me tsanani sukeyi. Ranar farko da aka fara raba abinci ta hanyar jefowa a ranar sabbin bayin suka fara gane rayuwar inda ta dosa amma duk da hakan basu Saba ba a tsorace suke, Kwana biyu da kawo sabbin bayi komai ya lafa an gama rabe matansu da mazansu ankai maza inda maza suke ankawo matan inda matan suke Angama musu tambarin shedar kusrah da numbar kowa a hannunsu dan haka komai ya lafa sedai su jiyo hayaniyarsu daga sama idan suna shagalinsu musamman da daddare da kaman kullum sai sunyi shagalin dare sbd rashin addini kawai. Yauma baa basu abincin dare ba suna rufe har tsakar dare yayi sunaji suna hayaniyarsu har suka gama aka bude kofar su ta sama Wanda take hasken farin wata me sanyi da wata sanyayar Niima suka ratso cikin gurin amma tsoron sanin me bude kofa a lokacin yake nufi ya saka babu Wanda iskar da hasken ya ratsa zuciyarsa saima tsamo tsamo da sukai kamar dabbobin da suka sha ruwan sama. Ahankali koina na jikin Ayanah na rawa tayi baya kadan tana qanqame hannuwan qannenta dake hannunta tareda sakina. Suma cikin rawar jikin da wani irin sanyin jiki sukai Bayan suna dan shigewa duhun lungun da suke tareda sunkuyar da Kai qashi Bayan wuyansu zuwa qugunsu yana bayyana har kana ganin shatin yanda Allah ya haliccesa sbd munin halinda rayuwarsu ta koma. A cikin sabbin bayin da basu gama munana ba take aka tsince Mutum bakwai aka fice dasu hadda wata qaramar budurwan da bata wuce shekaru goma sha uku ba aka fice dasu suna kuka da ihu nai karfi Ana dukansu duka mai tsanani sbd duk Wanda yayi kuka ko ihu duka sosai ake masa kuma a tafi dashi a hakan, Wainda suka San babu ceto a harkar basa kuka haka zaa tafi dasu zuciyoyinsu cike da tsantsar baqin ciki mara misaltuwa. Yarinyar wadda Ana fizgota cikin rikitaccen yanayi ta Kama hannuwan Ayanah duka biyu Tana fasa Ihun kuka a cikin mummunan tsoron daya saka hawaye gangarowa idanuwan Ayanah harma da Abaas lokaci daya Tana jin ciwo na yankar kirjinta na tausayin yarinyar duk da basusan yaya tasu kaddarar zata qare ba a wannan tafiyar amma dai suna fatar mutuwa ce ma kawai ba wannan mummunan aikin ba. Ficewa aka gama yi dasu aka sake rufe Sauran bayin take daddaikun su suka dan sauke ajiyan zuciya suna rintse Idanuwanu. Ajiyan zuciya suka sauke suma Zuhrah da Zarah fa suka toshe bakin Nurat suka Sakinta sbd duk lokacinda wani zaiyi ihu itama Ihun takeyi Wanda suke tsoron hakan ya saka wata rana mummunan kadarrar da basa fata ta hau kanta Wanda basa fatar gani. Tinda aka fice dasu bayin ranar dan sauke buqata akansu jikin Ayanah ke rawa ta rintse idanuwanta sbd Ihun yarinyar datake Ji har lokacin a kunnuwanta wadda da alaman dakin dayake saman inda suke aka shiga da ita dan haka kusan kunnuwansu na jiyo musu komai. Hannuwanta biyu ta saka ahankali hawayenta na tsananta saukowa ta rufe kunnuwan Nurat shima Abaas Tana cewa ya rufe kunnuwansa Zuhrah ma dake wata irin jijjiga sbd tsoro sedai sakina ta rufe mata kunnuwa. Ihun yarinyar da gurnanin Wanda yake ketata kunuwan Ayanah da sakina yake tareda sauran bayin suna jin yanda yagata yana fadar abinda yakeji na budurcinta dayake keta wa, Wasu irin hawaye da kuka mara sauti Ayanah sakewa tana tsananta rufe kunnuwan Nurat dan hanata jin wannan masifa. Kamar sakina ma kuka takeyi sosai tana sake rufe kunnuwan Zuhrah itama. Tsawon lokaci wannan masifar na saukar musu a kunnuwa har saida yarinyar takai bata iya kuka ko ihu sbd azaba da yanda yake shigarta tako ina gaba da bayanta yana ihunsa da maganganunsa tsawon lokaci me tsayi tukuna ya gansu yana sauka kanta ya fito zigidir yana sauke Numfashi da shakar iska me dadi yana jin Kansa wasai hakama ya samu gamsuwa sosai da ita duk da bata tsaya ba. Yaransa biyu dake gadin kofar dakinsa ne suka fada dakin suka daukota tareda fitowa da ita suka fice zuwa maida ita. Wasu bayin ne guda biyu suka fada dakin suka gyara masa tareda hada masa ruwan zafi a qaton bahon dayake shiga ya kwanta ciki yayi wanka suka fice. Komawa dakin khams yayi yana jin bacci sosai a idanuwansa ya fada ruwan ya wanke jikinsa kawai ya fito ya fada gadon ba komai a jikinsa ya bige da bacci. A kofar dakin kafin a maidata suka ajiyeta aka kawo ruwa masu sanyi aka zuba mata a jikinta jinin dake fitowa gabanta yafara bin ruwa yana wankewa batareda ta San meya ke faruwa a rayuwarta ba suka bude kofar tareda jefata suka rufe suna barin gurin. Kasa motsawa kowa yayi bare dogon numfashi a dakin hakama babu Wanda ya iya ko Juyawa ya kalleta duk da duhu ne bare tabata ko bata taimako. Ayanah data rintse idanuwanta da karfi Tana dauke Numfashi sbd tsoro da bugawan zuciyar gabansu data fado har hannunta na sauka kan kafafun ayanar batareda ta farfado ba. Tsawon Daren a wannan mummunan halin suke haka aka ringa dawo dasu Dayan bayan daya sedai Mutum biyar kadai suka dawo sauran biyun an kashe an jefar. Asuba tayi har gari ya waye sosai su Ayanah sunyi tsit baccin wahala da ake yi daga Zaune a dan sauke su Ayanah taji an Kama kafarta a razane jikin na daukan rawa ta bude ido Tana firgita sedai kafin tayi baya yarinyar ta sake riqe kafarta tana son bude baki tayi magana amma bazata iyaba sai hawaye masu radadin dake bin fuskanta. A sanyaye Ayanah ta Dora hannunta akai nata din Tana kasa cewa komai. Daqyar cikin azabar yarinyar tafara kokarin miqewa amma take jini ya balle mata Wanda ya sakata Lumshe ido Tana sake qanqame hannun Ayanah ranta na fita take. Ayanah batasan ta rasu ba ta sake riqe hannunta dan bata sassauci sbd duhu ne. Baa basu abincin safe ba haka suka wuni a rufe har saida Ayanah taji jikin yarinyar yayi sanyi sosai ya sanqare ta gane mutuwa tayi dan haka ahankali ta zare hannunta daga nata tana kuka mara sauti jikinta na qarasa mutuwa sosai. Sai dare aka zo basu abinci akaga gawar yarinyar aka dauketa tareda fiddata daga cikinsu aka jefar a ruwa. Abincin da aka basu ranar cikin damuwa da sanyin jiki suka cisa sbd zuwa lokacin dai sun sake tabbatarda rayuwar ba sauki a tsakanin wahalar ko mutuwar. ******** Nisa rayuwarsu da tafiyar keyi a cikin kusrawa dan zuwa lokacin sunkai watanni biyar a cikinsu batareda sunkai inda Allah zai yanke tasu wahalar ba, Qasashe sosai daban daban ake tsayawa anata rage bayi Ana kuma tsayawa wasu garuruwan Ana qara wasu. Tsawon wannan rayuwar da sukai ko so daya Nurat bata taba dawowa hayyacinta ba, Abaas bai taba bude bakinsa ba maganarsa ta jima da qarewa, Zuhrah bata taba fita tsoro da firgici ba, Ayanah bata taba Dena kuka na fili dana boye ba,.zuciyarta bata taba samun Hutu da sassaucin baqin ciki da qunci ba koma daqiqa ne, Sakinah kuwa bata taba Dena adduarta akansu ba da zubda hawayen tausayin su da kanta ba, Dan hakanne rayuwar take tsananta tsanani a garesu, Nurat yanayinta a kwanakin rikice wa yakeyi Wanda hakan ya karya dukkanin kuzari da juriyarsu, Wata irin rama takeyi Tana yin fayau dan haka suka Dena cin abincinsu suna tattarawa suna bata saisu ci na Mutum biyu su kuma su taru suci sauran. Babu wani sauyi dan haka jikinsu ke sake yin sanyi da shiga sabuwan damuwa, Daren da zasu isa qasar Gaku baccin wahala da damuwa ya dauke su daqyar sai aka bude kofar wannan Karan ba hasken farin watan dan haka cikin duhun kawai aka fara damkosu kawai Ana jeho wa waje saida aka dauki mace tara tukuna aka rifesu. Ana rufe su gurin yayi tsit Zuhrah dake maqe da jikinta Tana rawar jiki sosai sbd yau duk har gurinsu aka taho saura dakan a damqota Allah ya kubutar da ita dan haka jikinta ke rawa sosai tana kakkarwa. Motsawa tayi Tana fidda hannunta daya dan sake kamo Nurat datake riqe da ita tashin hankalin ya raba hannuwansu sai taji babu Nurat din a gefenta. Zuro hannuwanta tayi duka biyun taba lalubar gefenta da sauri hannuwanta na tsananta rawa taji babu Nurat da karfi ta Ambaci sunanta saida gurin ya amsa gabaki daya da hakan. Ayanah da zuciyarta ta tsaya cak da bugawa hannuwanta na muguwar rawa ta miqa tana lalubar Zuhrah Tana cewa ‘Meya faru? Ina Nurat din?? Girgiza Kai Zuhrah tayi Tana Neman zarewa tace ‘Nurat banjitaba,bata nan,banji ta ba’ Abaas ma cak kirjinsa ya Dena bugawa ya Kama hannun Ayanah da karfin gaske yana son magana amma ba dama sbd alkawarin dayake kansu dan haka cizon harshensa yafara yana jijjiga Ayanah da karfin gaske. Ayanah da karfi itama ta kwala kiran Nurat din wadda kaman daga sama suka Ji saukan muryanta a tsakiyar kunnuwansu Ta kwalla qara me karfi tareda kiran sunan AMMA saida kunnuwansu suka amsa Amo zuwa kirjinsu musamman Ayanah datasan ita Nurat din take kira da Ammah. Saman dakin suka kalla da wani irin mafi girman firgici sbd jin baa cikin dakin take ba dakin dake samansu ne na shugaba khams… #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 09033181070 15 *JEWELRY JUNCTION* 08039440312 Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma, Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne?? To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan, Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana, ✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌 ✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌 ✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌 ✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍 🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah. WhatsApp 08039440312 Tiktok :@sokoto jewelry seller Instagram: jewelryjunction23 ************ Miqewa tsaye dukkaninsu sukai kafafunsu na kasa daukansu sosai sbd zaman dayake cinye lafiyar kafafun, Jijjiga da fizga jikin Ayanah yakeyi bama rawa ba ta bude Baki da karfin gaske Tana kwala kiran Nurat wadda take Ihun itama sosai. Abaas harshensa yake cizo yana wani irin gurnanin kiran Yar uwarsa a zuciya jini na fitowa bakinsa sbd mummunan tashin hankali da yanda yake cizan harshensa. Zuhrah Neman zarewa takeyi itama kaman Nurat Tana qwala kiran Nurat qafafunta na kasa daukanta. Sakinah ma kuka takeyi sosai zuciyarta na bugawa kaman zata fado, Miqewa tsaye Ayanah tayi cikin tsananin duhun tana kokarin taka mutane ta isa kofar ta kife sbd sarkar kafarta amma bata tsaya komaiba jikinta na tsananta rawa ta sake miqewa kwala kiran Nurat da karfin daye amsa dakin dukansa har sama inda Nurat din take Tana sake faduwa taba sake tashi tana taka mutane hankalinta gabaki daya ya gushe daga jikinta Ihun kiran Nurat takeyi Tana jin kaman mutuwa zatai a lokacin, Ihun Nurat dinne yafara ratsosu itama cikin tsantsar azaba tana kiran Ayanah da sunan Ammah muryanta ba dadin sauraro. Isowa setin kofa Ayanah tayi tafara bugawa da hannuwanta tana wani matsanancin kukan da ihu, Yanda take bugawa hannuwanta duga biyun da karfi batareda damuwa da yankewan da hannun keyi ba ga qusa dake jikin gurin Tana fasa hannuwanta jini na fita jin kawai takeyi tamkar ranta ne zai fita idan rayuwan Nurat dinta ta lalace. Kukan datake yi Sam bata hayyacinta sbd da a gabansu ne ake kokarin hakan da yau duka zasu bar duniya sbd bazasu tsaya kallo ba zasu qwaceta koda hakan na nufin rabasu da ransu. Jini sosai taje fiddawa a hannuwanta amma ta kasa denawa sbd bata ma Jin Zafin komai kukanta na qaruwa sosai har maqoshinta na kasa fidda sauti. Abaas da Zuhrah harma da sakina da suma kowa ke cikin mummunan Hali suka rarrafo basa gani zuwa inda sautin muryan Ayanah din yake fita Zuhrah ce tayi saurin riqeta Tana rungumeta sbd jinin dataji hannuwanta nayi data lalabo ta tareda fasa sabon kuka itama jikinta na fizga, Abaas ma Kansa yake bugawa a kofar yana wani irin kuka zuciyarsa na yagewa tako ina da radadi me yawa ga bakinsa bazai budu ba dai harshensa yake taunawa yana jini yana cigaba da buga Kansa a kofar, A daidai lokacin da Nurat ta qwalla wata mummunan qara wadda take tabbatarda azaba ce ta keta ta da akai da wasu irin surutai da khams ke sakewa a cikin kunnuwansu suna ratsa zuciya da kwakwalwansu take kowannensu ya silale qasa suna yin tsit sedai sakinah ce ta saki wani irin kuka a lokacin Tana riqe hannuwansu su duka ukun a cikin nata duka biyu sbd yanda suke jijjiga batareda sun iya sake kowane irin yunquri ba alaman zuciyarsu bugawa zatai ko ta dauke wuta, A cikin kunnuwansu sautin duk abinda khams keyi yake sauka tareda kukan Nurat dake fita har tayi tsit babu kowane irin sautinta sai nasa Wanda duk abinda yayi da ita kunnuwansu sunji musu Wanda kuma sauti ne da zai zauna a kunnuwansu da zuciyoyinsu har abada har ranar da jinsu zai dauke Bayan rai ya fita a jikinsu, Zuhrah juyewa kanta yake yi itama sbd dukan da zuciyarta ta samu mummunan dayake Neman buga zuciyarta. Sakinah rungumesu tayi da hannuwanta Tana qanqamesu kukanta na tsananta sbd yanda dakin yayi tsit kowane bawan dake jirgin ranar duk da halin da suke ciki kukansu Ayanah din ya sanyaya jikinsu tareda hawayen tausayin qaddadarsu su duka da basusan ya zata qare ba. Ayanah zubewa tayi jikin sakinah gabaki daya jikinta na saki idanuwanta na kasa Juyawa ta koma kamar wadda aka zarewa komai aka Barta da rai kawai. Jin hakan sakinah ta sake rungumeta jikinta kukanta na tsananta Tana Jin inama a ranar da suka so kashe kansu ta barsu sun mutu sun bar duniyar da sun huta da ganin wannan balain da daace iyayensu na raye mutuwa zasu yi idan suka Ji wannan mummunan ranar. Tsit babu Wanda ya iya ko dogon motsi a dakin kwata kwata kaman yanda babu Wanda ya sake Jin ko kukan su Ayanah ne dukansu sun mutu a inda suke babu abinda ke motsi a jikinsu Bayan zuciya dake bugawa. Gap da asuba aka bude dakin Wanda ya saka su Ayanah daga Kai ahankali suna kallo aka turo Nurat wadda Kayan jikinta gabaki daya suke a yage harma kusan Rabin jikinta duka a bayyane. Abaas ne ya Tara hannuwansu biyu ya tareda ta fado jikinsa ya rungume ahankali yana rufe jikinsa ta inda jikinta yake bayyane yana sake rungumeta tsamtsam. Wasu hawaye ne masu dumi suka gangaro daga idanuwanta Wanda ya sauka tafin hannuwan Zuhrah data motsa zata tabata, Saukar hawayen nata ta saka Zuhrah kallan fuskanta cikin duhun bakinta na budewa da tsananin sanyi tace ‘Nurat,Yene(my/tawa) Nurat,Yene fikir(love/masoyiya) Nurat Rabin Raina.’ Wasu sabbin hawayen ne suka gangarowa Nurat din Tana son Dora hannunta Akan na zuhrah din ta kasa dan haka ta rufe idanuwanta bakinta daqyar ya iya budewa tace ‘Ammah’ Kalmar yanka zuciyar Ayanah da dukkaninsu tayi Ayanah ta rufe idanuwa hawaye masu tsananin zafi suka gangaro mata ta motsa hannuwanta dake rawa ta Kai fuskar Nurat din taji wani abu yana gangarowa ta hancinta Wanda ta tabbatarda jini ne yake fitowa ta fasa wani irin wahalallen kuka Mara sauti tareda Kai fuskanta ta hade data Nurat din tayi sumbaci goshinta ta sumbaci hancinta tareda sarqe hannunta da nata Tana kasa furta komai sai sumbatar hannunta taje yi tana wahalallen kuka Mara sauti jikinta a mace gabaki daya ba karfi ko daya. Zuhrah hannuwanta ta kasa janye wa daga hawayen Nurat din dake zuba suna zuba a hannunta itama kukan takeyi sosai kaman ranta zai fita mara sauti, Nurat data dawo hayyacinta Tana jinsu amma babu inda take iya motsawa a jikinta sbd jininta dayake qarewa yana qarasa zubewa sbd tin acan take zubar da jini sosai haryanzu sosai yake fita a jikinta batareda yan uwanta sun saniba duk da ko sun sani basuda abinda zasu yi sedai zubawa sarautar Allah ido. A haka suke Zaune kowannensu kuka ne na fitar hankali sukeyi mara sauti har lokacin Abaas yana rungume da ita cikin jikinsa hakama Ayanah na riqe da hannunta tana sumbata Tana kukan da shi Kansa kukan ya gaji sai Zuhrah dake tare hawayenta da hannuwanta duka biyu kowace diga yanka zuciyarta yakeyi,sakinah ma Tana Bayan Ayanah kuka takeyi kawai tana kusan abinda dukansu suke Ji, Gari ne yi yi haske sbd safiyar datai dan haka duhun dakin ya ragu sosai suna iya kallan fuskanta kuma har lokacin babu Wanda yayi hayaniya ko doguwar motsi a dakin sbd duk da suna qangin bauta suna sheda tsananin kauna da son da yan uwan kewa juna kaman rai, Ahankali Nurat din ta sake bude ido ta zubawa Abaas Wanda ya kasa kuka sedai jinin dake fitowa daga bakinsa idanuwansa sunyi jan da gap suke da fara fidda jini, Hannunta ta daga daqyar yana rawa sosai ta share masa jinin bakinsa Tana kallan cikin qwayar idanuwansa hawaye suka sake gangaro mata ta kasa iya cewa komai kafin ta dauke idanuwanta a galabaice tanason kallan Zuhrah da Ayanah amma Allah bai bata ikoba jikinta ya sake ahankali ranta na fita. Dukansu babu Wanda ya motsa sbd tashin hankalin daya wuce Kai tsaye cikin kansu ya sanqarar da komai nasu, Sakinah ma mutuwar Zaune tayi dukansu suka dauki mintina a hakan kafin Ahankali Ayanah ta motsa tana tallafo fuskan Nurat din datai haske sosai tareda duka jikinta sbd jininta daya gama tsiyayewa tas ta hade fuskanta da tata muryanta na rawa tace ‘Nurat rayuwata, Nurat hasken rayuwata,yene Nurat,Nurat kece kuzarina, Nurat kune haske da kuzarin rayuwata da ruhina da bazan iya rayuwa babu ku ba, Nurat kune karfin daya saka zuciyata take bugawa haryanxu batareda ta tsaya ba, Nurat ke suka keta amma mu rayuwar ce aka keta sbd kece rayuwarmu, Nurat ki bude idanuwanki ki kalli halinda muke ciki Bazamu taba dawowa daidai ba har abada idan babu ke koda kuwa mun samu sauyin rayuwa, Nurat,Nurat…….wani irin kuka me tsananin jijjiga duk me saurare da ratsa zuciyar kowane dan Adam dazai jisa ta sake Tana sumbatar tsakiyar kan Nurat din da goshinta kafin ta rungume kanta a kirjinta tana rufe idonta kukanta naci gaba da fita. Zuhrah ma hannunta Nurat din ta riqe ta sumbata Tana rungumewa kukanta na fita da tsananin kashe jiki, Abaas a kirjin Nurat din shima ya kife Kansa a Karan farko da sautinsa ya fita Bayan tsawon watanni yana fasa wani irin kuka mai tsananin taba zuciya da narkarwa. Basu taba tunanin samun kansu a cikin wannnan mummunar halin ba da zasu rungume gawar daya daga cikinsu ba a Hali mafi muni irin wannan, Koda iyayensu suka bar duniyar sun mutu a hanyar Neman tsira da sauran mutuncinsu, Amma ayau Nurat ta rasu tabar duniyar da ciwon baqin cikin abinda ya faru da ita, Bata rasu ba saida tashin hankalin data fuskanta ya dawo da hankalinta jikinta dan hakanne baqin cikin abinda y sameta dashi ta rasu a ranta dole. Kaman yanda Baqin cikin rashinta bazai taba barinsu ba hakama harsu mutu sautin kukanta a lokacinda ake keta haddinta bazai taba fita daga kunnuwansu da zuciyarsu ba shikenan ya musu rauni a zuci. Har rana ta keto suna rungume da gawar Nurat sun kasa sakewa saida aka bude su dan basu abinci, Jeho abinci akeyi masu karba na wawason karba amma babu Wanda ya motsa a cikinsu suna rungume da ita har lokacin babu Wanda idanuwansu ke Dubuwa sbd kumburi da ja. Saida aka gama Rabon abincin a daidai lokacin suka iso qasar hidua jirginsu ya tsaya a bodar qasar zaayi abinda aka Saba tukuna aka shigo dan diban bayi Sai a lokacin akasan da akwai gawa a cikin gurin. Zabar bayinsu suka fara yi wainda zasu siyar suka fitar dasu kafin suka dawo suka dauki gawar wadda aka cire daqyar a hannunsu Ayanah da suka riqeta gamgam dukkaninsu ganin bazasu sake ba aka dauko Bulala aka fara dukansu da karfi jikinsu na fashewa amma har lokacin kasa sake gawar sukai. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 16 *JEWELRY JUNCTION* 08039440312 Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma, Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne?? To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan, Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana, ✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌 ✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌 ✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌 ✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍 🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah. WhatsApp 08039440312 Tiktok :@sokoto jewelry seller Instagram: jewelryjunction23 *************** Wani irin mummunan dukan Bulala aka ringa saukarwa hannuwansu Ayanah Wanda ya saka hannuwan nasu fara fashewa harma dukan yana sauka kan gawar Nurat wadda tayi haske sosai fuskanta tayi Wani irin fayau idanuwanta dake rufe sun boye mummunan ramar dasuke ciki kafin rasuwarta, Ayanah Akan gawar ta zuba ido tana kallan dukan dake sauka akanta Wanda zuciyarta ta sake gabaki daya taji tana hakura da dangana tinda Nurat ta rasu hakan shine saukin data samu da hutawa daga wannan duniyar da babu komai cikinta sai qunci da azaba hakama babu abinda gawar Nurat ke buqata Bayan Hutu koda kuwa ba binneta zaayi ba taba buqatar abarta ta fita hannun kusra dan haka ahankali ta sake hannuwanta suna saki idanuwanta na tsananta ja jikinta gabaki daya na sanyi hawaye takeson yi amma sun kafe Idon ya gaji da kuka. Zuhrah ma azabar dukan dayake fasa hannunta y saka hannuwanta saki tana sunkuyar da kanta kasa hawaye na diga babu sautin kuka sbd karfinta daya qare tas. Abaas ne ya kasa sakin Nurat din dan haka suka taru akansa suna masa wani dukan dayake fasa fatar jikinsa har jini na fita ya kasa Sakinta kuma y kasa kuka dan haka suka tsananta dukan har saida Ayanah da bata hayyacinta sakinah ta girgizata da karfi ta tana cewa ‘Abaas zai rasa ransa’ Dagowa Ayanah din tayi tana kallan dukan da ake masa jikinsa duka yana jini da dan sauran karfin datake dashi ta fada Kansa ta rungumesa tareda Kama hannuwansa tana banbarewa daga Nurat jikinta na wata irin rawa sbd itama Jin takeyi kaman bazata iya barin a tafi da Nurat din ba. Girgiza Kai Abaas keyi da karfi yana kasa Sakinta yana kallan Ayanah wadda ta kasa dagowa sbd yanda jikinta ke rawa ta zare hannuwansa tareda rungumesa tana basa kariya daga dukan da ake masa har lokacin aka hada su tare akai musu mummunan dukan daya saka Zuhrah bata kariya itama dukan na sauka kanta. Saida suka gaji dan kansu sukabar dukansu suka dauki gawar Nurat suka fice da ita. Babban arzikin da Nurat ta samu Bayan rasuwarta shine suna bakin bodar wata qasar dan haka ba damar yar da gawa sbd cikin mutane ne dan haka rami akai kaman kowace gawa aka rufeta a qasar. Kwanansu biyar a qasar suka barta aka wuce sedai tamkar zuciyoyinsu Ayanah ne aka Bari a qasar haka suke Ji sbd tamkar sun rasa barin rayuwarsu a qasar da bazasu taba mantawa ba tinda Nurat dinsu na qasar. Rayuwarsu ta raunana daga lokacin dan haka ko abinci sun wani Dena ci sai sakinah ce take wawusowa ta kawo musu ta takura musu tareda roqo ta samu su ci amma gabaki daya rayuwar ta qarasa fita kansu barin duniyar shine kawai fatansu a yanzu, Quncin da suke ciki ne ya saka duk wahalar da suke ciki yanzu basa jinta dan kuwa a yanzu kusan babu abinda bazasu iya jurewaba a rayuwa illa rabuwa da juna. ******Tafiyar sati biyu sukai a ruwa suka isa qasar Nuggi wadda qasa biyu ce a gabanta kafin isa BOYEM, Tinda suka tinkaro qasar jikin dukkaninsu yayi sanyi duk da basusan suna tinkarar kowace qasaba a taqaice ma basusan ina suke ba kokuma ina suke dosa, Da asuba ne suka iso bakin bodar qasar dan haka baa bude su ba saida gari ya fara haske tukuna aka basu abinci. Yau Ayanah da kanta ta shiga karban abincin ta rarrafo gefensu ta zauna ta kallesu kowannensu ya zama wani halittar daban yunwa na yawo koina a jikinsu da wahala. Zaunawa tayi tsakiyar Zuhrah da Abaas din ta sauke ajiyan zuciya me sanyi da mutuwar jiki kafin ta dago ta kalli Abaas ta saka hannuwanta biyu ta Kamo fuskarsa ta sumbaci goshinsa ta sumbaci gefen fuskansa da tsananin sanyi murya tace ‘Bazan iya rayuwa babu Kai ba hasken idaniyata ka riqe hakan kada ka yadda ka sake laifin da zasu illatamun kai kaji???? Dago idanuwansa da sukai ja yayi take ya sauke Akan fuskanta da idanuwanta suka ciko da hawayen rauni da tsananin kaunarsa dake bayyane a fuskanta. Gangarowa hawayenta sukai tace ‘Kamun Alkawarin bazaka taba sake abinda zai saka rayuwanka a hadari ba koda bana raye tareda ku? Saurin kallanta yayi yana son rufe bakinta da hannunsa ta riqe hannun tana girgiza masa kai hawayenta na gangarowa da gudu tace ‘Kamun alkawarin hakan Abaas, Kamun alkawarin zaka kula tareda kiyayewa sbd mutuwa zanyi idan wani abu ya samu daya daga cikin ku biyun,dan Allah Kamun Alkwari…..’ Qarasa fada tayi muryanta na karyewa sosai tana sunkuyar dakai sbd gajiyayyan kukan dake taso mata. Kama hannuwanta yayi yana hawaye masu dumi shima ya sumbaci hannunta kafin ya kamo kanta ya sumbaci goshinta yana rungumeta cikin jikinsa yana share mata hawayenta. Tashi tayi ahankali daga jikinsa ta juyo ta kalli Zuhrah tareda zuba mata ido tana kallanta cikeda tausayi da kauna me karfi, Hannu takai ta shafi fuskanta ahankali kafin ta sumbaci gefen fuskarta tareda rungumeta ahankali ta bude baki tace ‘Zan tabbatarda na kashe kaina kafin wani ya lalamin rayuwarki sbd ke zuciyata ce,ke Rabin jikina ce,ke jinin jikina ce keda Abaas…’ Sake sumbatar goshinta tayi tana hada su itada Abaas ta rungume sukai shiru tsawon lokaci a hakan kafin ta janye su tana fara basu dambun alkamar da akai zalla babu komai a cikinsa tafara basu a baki da hannunta tana kallansu kaman zata cinyesu. Basu takeyi a baki suma suna diba suna bata hakama Abaas na bata yaba Zuhrah hakama Zuhrah tabawa Ayanah din ta bawa Abaas a haka suka ciyar da junansu babu Wanda baya hawayen qunci da radadi a cikinsu. Suna gamawa suka kwanta jikin juna sakinah na gefensu tana hawayen tausayinsu dana kanta da batada kowa a duniyar Bayan su. A haka suka wuni shiru jigum babu motsin komai sbd se dare kuma zaa sake basu abinci dan haka ko motsi babu keyi dakin tsit yake. Har dare suna jikin juna saida Daren yayi tukuna zaa fara cin kasuwar bayi ta garin dan haka aka zo aka bude kofar su dan diban bayi. Ana budewa take suka fara diban suna turasu waje, Bayi arbain zasu siyar dan haka Ana kirqa Talatin da Tara Wanda yake diban ya finciko Abaas kai tsaye ya jefa kofa yana cikewa arbain dashi, A tsananin haukace Ayanah ta miqe tana riqe hannun Abaas din da tsananin karfin gaske har tana kife wa qasa sbd sarkar kafarta amma bata sake hannun Abaas ba Wanda shima ya riqeta da tsananin karfin gaske duka jikinsa na daukan mummunan rawa, Zuhrah ma fadowa tayi kan Abaas din tana riqe sa da karfin gaske tana kiran sunansa da karfin gaske duka jikinta jijjiga tsabar rawa. Ayanah miqewa tayi tana fadawa jikinsa ta qanqamesa da karfin gaske tana cewa a siyar dasu tare dan Allah idan ba haka ba mutuwa zatai. Zuhrah ma hakan ta riqe sa tana kukan da ko maganarta bata fita. Ganin hakan y saka kai tsaye aka dauko buloli masu tsananin tsayi aka fara dukansu da ita amma Sam daga Ayanah har Zuhrah da Abaas din sun kasa sakin juna Neman zarewa sukeyi da tsananin tashin hankalin daya saka sakina ma fasa kuka tana fadawa kansu tana rufe su sbd tsananin dukan da ake musu jini na fita jikinsu. Azabar dukan da ake musu sun kasa sakin juna jininsu na fita ya saka gangar Zuhrah kasa dauka ta fara zame wa qasa idanuwanta na Neman rufewa zuciyarta na tsananin gajiya wa da komai ta zube a gurin a some. Ayanah data kasa sakinsa duk da komai nata musamman zuciyar sun gama gajiya da rayuwar gabaki daya sun gaza hannuwanta jini sukeyi amma ta kasa sakinsa daukanta ake cigaba da yi Sakinah na dan kare mata har itama sakinar ta some a gurin. Karfin gaske Mutum shida suka saka uku suka jata uku suka ja Abaas suka rabasu yana Ihu a Karan farko itama tana ihu moqashinta harya kasa Dena fidda sauti shima hakan bakinsa na fidda jinin harshensa dayake cixa tana fidda jini itama ta hancinta sbd munin halinda take ciki a haka aka rabasu suna jansa suka fice dashi gabaki daya suna Wani irin kukan daya saka gabaki daya bayin dake gurin hawaye sbd da gaske dai zata iya mutuwa idan aka rabata dashi kaman yanda suka Ji tana fada masa lokuta da dama. Ficewa akai dashi tareda rufe kofar Wanda yayi daidai da yankewan jikinta ta fadi a gurin ba Sauran numfashi ko motsin komai jikinta. Shi Karan Kansa saida suka sumar dashi suka fice dashi Wanda cikin saa take shi suka fara siyar wa aka tattara gurin aka Bari dashi sedai ya farfado ya samu Kansa wani gurin. Sbd ma yanda su Ayanah din suka kawo musu matsala ya saka basu kwana ba suka gama cin kasuwarsu sukai siyayya suka bar qasar a ranar. Suna barin qasar kai tsaye umarni khams ya bada bazaa sake tsayawa kowace qasar ba sai ta BOYEM dan haka tafiya Sambai aka dauka zuwa BOYEM wadda ta saka aka fara sauyawa bayin abinci zuwa wadatacce me kyau sbd suyi Kyan gani da masarautar zata karba. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 17 *JEWELRY JUNCTION* 08039440312 Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma, Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne?? To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan, Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana, ✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌 ✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌 ✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌 ✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍 🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah. WhatsApp 08039440312 Tiktok :@sokoto jewelry seller Instagram: jewelryjunction23 *********** Koda su Ayanah suka farfado sun Riga sun bar qasar da ruhinsu yake acan babu sauran abinda ya rage a tattare dasu Bayan gangar jikinda babu ruhi babu zuciya sbd Nurat da Abaas sune ruhi da zuciyar Ayanah Zuhrah kuma rayuwarta, Ita kanta Zuhrah yan uwanta sune rayuwarta da ita kanta dan haka tana farfadowa babu Abaas da gaske an rabasu rabuwar da har abada sun rabu bazasu sake haduwaba,bazasu sake sanin yana raye kokuma shi yasan sun raye ba hakama bazasu San halinda zai shiga ba ya rayu har zuwa mutuwar sa ba shima bazai San halinda zasu shiga ba na rayuwa ko mutuwa sai kawai ta sake sumewa batareda ta motsa daga inda take ba. Ayanah kuwa tana farfadowa ta tabbatarda an rabasu da Abaas saita rarrafa ta isa kofa tana bugawa Da dan karfin da baifi na yaron goye ba sbd batada Sauran karfi ko kuzari kokuma wani amfani dan baqin ciki da qunci tareda rabata wainda sune kuzari da rayuwarta yariga yayi mata illar da bazata taba moruwa ba ko dawowa daidai abada A karo na babu adadi take jin ta sake zabar mutuwa Akan rayuwa, Inama ace mutuwa Abaas yayi a gabanta tasan ya komawa ubangiji baya duniyar yafi mata samun sassauci da nutsuwa Akan rabasu da akai batareda sunsan Ina rayuwa zata kaisaba shima,wace duniya ko sabuwar kaddarar zai fada duk basu saniba. Kiran sunan Abaas takeyi duk lokacinda ta bugu kofar batareda akwai lakar komaiba a jikinta tamkar yar maye ko fita muryanta baya yi amma a hakan bata hakura ta Dena ba Abaas tsakanin buqata a kusa da ita kokuma a zubar dasu ko a ruwan qasar ne kafin a gama barin qasar. Tsananin wahala,qunci,nannauyan baqin ciki,tarin gajiya da ruhi gangar jiki da zuciya sukai harma da idanuwa ya sakata silalewa qasa kwance a gurin tana fidda Numfashi gajiyayye tareda rufe idanuwanta ahankali jikinta na saki batareda ta some ba kawai dai ba lallai ta sake moruwa ba ko taba dawowa daidai ba. Sakinah dake rungume da Zuhrah itama ta gama fita hayyacinta matsowa tayi gefen Ayanah din tareda dagota jikinta ta kwantar sukai shiru sbd yanzu kam babu wani qarshen qunci da baqin ciki dayayi saura Wanda basu gani ba dan haka koma me zasu tarar a gaba bazasu Ji komaiba. Haka suka kwana suka wuni tamkar gangar jikinsu babu rai a jikinta, Babu me iya kowane irin motsi idanuwansu ma a rufe suke ko abinci sun dena iya ci sedai sakina ce take karbowa ta rarrafo ta zauna tsakiyar su ta ringa basu a baki Akan dole sbd karfinsu dayake sake yin qasa sosai Wanda Sai a yanzu sakina ke sake tabbatarda kasancensu su duka hudun a tare da gaske shine rayuwa,ruhi,kuzari da karfin zuciyarsu sbd a yanzu Ayanah da zuhran gasunan sun zama tamkar marasa cikakken hankali. Idan dare yayi haka zata zauna tsakiyar su ta kwantar da kansu a jikinta tana Shafa bayansu da fuskar su sbd samar da nutsuwa ko yar qanqanuwa ce a zuciya da gangar jikinsu. Idan gari ya waye haka zata jawosu inda ake fiddosu Ana zuba musu ruwa sbd su wanke kullum kafin isarsu inda zaa kaisu, Haka zata janyo su kaman qananun yara Ana dukansu duk da yanzu an rage dukansu sosai sbd duk anason suyi dan yi Kyan kallo dan haka kullum Ana fiddosu a hade guri daya a ringa zuba musu ruwa masu tsananin yawa suna goge jikinsu Wanda baya goga jikinsa lokacin da ake zuba ruwan duka yake sha da Bulala dan haka sakinah ganin kullum sai an dake su amma tamkar jiran duka sukeyi sbd ya wahala ta kashesu subar daniya ya saka koyaushe idan Ana zuba ruwan itace me wanke jikinta ta wanke nasu su dukan. Ana gama wankesu haka zaa sake shanyasu a rana sai sun bushe a gargadasu a maidasu inda suke a rufe, ***********sake nutsawa tafiyarsu tayi Wanda a yanzu suna samun abinci sosai hakama wankan kullum ake musu dan haka yunwarsu ta ragu sosai sedai shi wanka kam ya saka duk fatar su ta bushe qayau sun koma wata sabuwar halittar daban kowannensu cikin bayin ka kalla tamkar an birkidasa cikin farin gari an ciro sbd kullum ruwan kawai ake zuba musu sannan a shanyasu a rana. Har lokacin babu abinda ya sauya a sabuwar kaddararriyar rayuwar data samu su Ayanah, A yanzu basa iya ko magana daga ido se ido sai kallo dan haka ne ita kuma sakinah nauyinsu ya dawo kanta gabaki daya fatarta dai suna isa qasar da zasu din a siyesu koda kashesu zaayi gwara a siyesu acan din da azo baa siyesu ba kusrawa su dawo dasu. **********Tafiyar sati bakwai sukai tukuna jirginsu ya fara shigowa qasar da kowane tarihin zamanin ke fadar iko,girma,mulki,arziki da tsananin da masarautar qasar take dashi sakamakon sarakunanta da suke aje tarihi me girman gaske kafin rasuwa subar karagarsu. Tsananin tsaro da tsari tareda dokokin dake zagaye da qasar daban yake da duka Sauran qasashen duniyar Wanda ya saka zuwa qasar yake tamkar samun babban rabone da saa a duniyar da suke rayuwar, Suna gap da isowa kusan iyakar bodar da zata shigo dasu farkon ruwan qasar saida aka sake tsafta ce kowane bawa kafin suma suka wanke kansu da dan gyara komai na tsarinsu dasu kansu din. Boda biyar ce tin daga farkon shigowa nahiyar qasar kafin isa cikin bodar ruwa ta cikin qasar wadda ita kanta bakin bodar cikin kasar daga nan bakin zuwa cikin qasar tafiya ce tsananin tafiya. A bodar farko saida suka share kwana daya a bakin wajen qasar batareda sun samu damar shiga ba saida aka gama binciken tabbacin kasuwan bayin sukeyi kafin aka barsu suka wuce. Wuni guda suka sake share wa Bayan barinsu Checking point na bodar farko kafin suka iso ta biyu. Anan ta biyu ba saida suka share kwana daya harda wuni kafin aka gama tareda basu damar wucewa. Shima tsakanin boda ta biyun zuwa ta uku tafiyar wuni guda ce sukutum sai tsakar dare suka isa dan haka baa duba kowane jirgin ba duka jiragen da suka taho a wajen bodar suka kwana sai washe gari aka fara aiki akansu. Tashin farko abinda suka fuskanta anan shine bazasu shiga da jirginsu can bodar karshe ta cikin asalin qasar ba dan haka duka yawansu anan bodar zasu tsaya da jirginsu sedai shugabansu da wasu daga cikin manyansu da bazasu wuce Mutum Ashirinba dan a qaida baa wuce hakan dan hakan komai yawan bayinsu koda bayinsu sunfi dubu daruruwa to su dai da zasuci kasuwarsu bazasu wuce Mutum ashirin ba kuma da jirgin bakin bodar zasu biya su dauka su isa can sai sun dawo su koma jirginsu su koma inda suka fito. Wannan dalilin ya saka kowace boda dake qasar girman bodar kawai yana fin girman qasashe da dama sbd irin tarin manyan mahaukatan jiragen ruwan dake tsayawa ko zama a gurin ba qaramar qasa ke iya daukansu ba, Kowace boda dake qasar tamkar wata qasar ce me zaman kanta sbd gari ne da mutane sosai sbd duk wani maaikacin bakin boda na qasar anan yake rayuwa da iyalansa da yan kasuwarsu harma da sauran manyan huldodon kasuwancin qasar da akeyi kuma anan ma Ana cin kasuwar bayi sedai acan babbar bodar ake cin asalin babbar kasuwar bayin datafi kowace a duniyarsu, Hakanne ya saka kowace bodar qasar gari ce guda mai zaman Kansa hidima sosai da cin kasuwanni akeyi tareda dubban Jamaa. A nan jirgin kusrawa ya tsaya suka gama karba da biyan komai na tsantsar dukiya me yawan gaske kafin suka fiddo bayinsu kaf aka Kirgasu tareda biyawa kowane bawa daya Lasisin shiga qasar. Saida suka kwana biyu a wannan bodar Ana harkar lasisin shiga qasar kafin aka kammala komai suka zuba bayinsu a sabon jirgi da zai kaisu suka wuce tareda barin dukannin Sauran kusrawa a garin bodar su samu shaqatawa da hutawa suma kafin su dawo Wanda a kalla basu San kwanakin da zasu shafe ba kafin dawowan tasu. Bodar gaba baa tsaya komaiba lasisin bayinsu aka bi daya bayan daya Ana duba wa tareda tabbacin sa tukuna aka barsu suka wuce. Suna wucewa khams ya sauke wata sanyayar ajiyar zuciyar samun nutsuwa da jin qamshin cikar Buri, Qamshi da iskar da kake shaqa a kasar kusan daban yake sbd nutsuwa da tarin arziki kawai kake Ji da gani tako ina, Su Karan kansu bayin nutsuwan ruhi da zuciya suka Ji suna samu ahankali cikin sanyi sbd koba komai sunsan yanzu kam sun iso qasar da zaa siyar dasu su fita hannu kusrawa, Dukkanin bayin a lokacin aka fara fitowa dasu daga jirgin kusra a wancan bodar da suka fito duk Wanda ya saka tafin kafarsa ya taka qasar da allah ya shimfida a duniya sai hawaye sun gangaro masa na godia ga Allah daya sauko jirgin ya fito batareda ya rasa rayuwarsa ba ko mutuncinsa kokuma dai Allah ya masa arzikin fitowa daga balai da masifar datafi komai a rayuwa wato jirgin kusra. Ita kanta Ayanah a lokacinda jirginsu ya isa asalin bodar cikin qasar dago idanuwanta tayi ahankali ta kalli ruwan qasar da suke shar iskar su na ratso musu sbd a wannan jirgin inda ake ajiye bayi ba a rufe yake ba cikin duhu a bude yake suna iya ganin koina sbd harda winduna wani sanyi na ratsa fuskarta zuwa gangar jikinta daya sakata rufe idanuwanta ahankali tana dan qanqame jikinta hawaye masu dumi na gangaro mata tinanin Nurat da Abaas na danne kirjinta da dayanzu dasu zasu shaqa wannan iskar da suka manta rabon da su shaqa sedai wari da zarni tareda tsami da karnin dakin bayin dasu ciki na jirgin kusrawa. A bakin bodar su khams suka fara tabbatarda sun iso qasar datafi kowace a duniyar da suka sani sbd wasu Hasken wutattakin Turawa dake haske gurare daban daban hakama maaikatan mahukunta qasar gasunan koina, Tsananin girma da fadin gari da kasuwannin bodar baa iya ganin iyakarsu sbd girman garin ya baci sbd akwai kasuwanni da gidajen da suka hau dubu Dari kuma a hakan ba baa shiga asalin cikin garuruwan dake qasar ba bare akai ga isa asalin babban birnin qasar da acan Masarautarsu take ba Wanda akwai ma tafiya me tsananin gaske. Sake tabbatarda lasisin su na shigowa kasar cin kasuwar bayi akai tareda tantance lasisin bayin daya bayan daya tukuna suka samu saukowa suna taka qasar masarautar BOYEM Wadda take sanyaya zukatan kusrawan da bayin sbd Allah ya yanke musu azabar kusra. #MAMUH #BOYEM #BOYEM #BOYEM HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 18 *JEWELRY JUNCTION* 08039440312 Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma, Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne?? To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan, Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana, ✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌 ✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌 ✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌 ✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍 🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah. WhatsApp 08039440312 Tiktok :@sokoto jewelry seller Instagram: jewelryjunction23 ********* Sabuwar duniyar da kamar ba wadda suke rayuwaba suka samu kansu cikeda farin ciki da mamakin abubuwan rayuwan da suke gani da dama Wanda suke tinanin idan nan bakin bodar ruwan qasar ne yake da daukan hankali da mamakin duniya haka to yaya cikin qasar zata kasance musamman masarautar da a tarihi da labari suke jin tsaruwarta wasuma cewa suke da kalar asalin zinari akai adonta koina nata zinariya ce ke haskata. Duk bawan da zai samu shiga masarautar BOYEM da sunan bauta ma a cikin tarihi sune masu saa da rabo ma dan haka ne da dama suke siyar da kansu a matsayin bayin BOYEM idan sunxo cin kasuwar sedai danginsu su dauka ya mutu sbd shikenan basa sake ganinsa. Gidan ma sauki suka kama a cikin babbar kasuwar da zata fara ci ta bayin nan da kwana biyu dan haka rumfar da zasu ci kasuwa suka fara kamawa me girman gaske suka biya komai kafin suka zube bayinsu a rumfar tareda maida musu sarkar kafafunsu da duka aka cire sai aka Jere su tareda barin masu tsaresu Bayan sun saka tambarinsu babba Akan rumfar su dake nuni da kasuwancinsu. Wucewa sukai zuwa masaukin da suka Kama dan hutawa a qasar BOYEM su kafar da tarihin hakan sbd hutawan gaske zasuyi da jin dadin da akace ana dashi a qasar. Tinda aka Jere su Ayanah da sauran bayin duka a rumfar babu Wanda ya iya dagowa kan kowannesu a qasa yake suna kallan qasa sbd basuda ikon dagowa su kalli koina sai Angama cin kasuwansu. Ayanah da batada sauran kuzari ko tinanin kanta bare iya kallan koina idanuwanta a rufe suke ta soka kanta a tsakiyar kafafunta zuciyarta na Wani irin yanka da radadi me zafi, Ta rasa wasu gurbi masu girma a rayuwarta da bazata taba cikesu ba har karshen rayuwarta, Rayuwarsu ta sauya ne a dare daya,kaddararsu tazo ne a daya dare,tashin hankali da baqin cikinsu duka Yazo ne a dare ya sauya rayuwarsu gabaki Dayan tamkar kyaftawar idanuwa. Basuda sauran rayuwar da zasu kira rayuwarsu kuma, Basuda komai da zasu kira nasu sbd gangar jikinsu da rayuwarsu gabaki daya ba tasu bace sbd basu da ikonta, Daga yanzu a inda suke daga lokacinda wani zai saka kudi ya siyesu ta tabbas sun qarasa rasa kansu har abada har sai ranar da Wanda ya siyesu ya iya yantasu idan ma ya mutu batareda yanta su ba suna cikin gadon iyalinsa kamar wasu kadara. Numfashi ta sauke me dumi tana sake rungume jikinta sbd sanyi dayake rata fatarta yana keta wa har cikin qashinta da yunwa ta gama rage masa kwari. Zuhrah idanuwanta a bude suke ita sedai kanta na qasa ta qurawa qasa ido tana kallan qasar dake gabanta zuciyarta na Wani irin mutuwa da sanyin dayake na tsagwaron baqin cikin da qunci, Motsa yatsun kafarta tayi ahankali suna shiga cikin qasa ta Lumshe ido ahankali wasu hawaye masu dumi suka gangaro mata a karo na farko Bayan rabuwansu da Abaas da zuciyarsu ta kafe ta kangare, Wannan itace qasar da a yanzu zasuyi rayuwa a cikinta babu ranar fita ko tafiya harsai rayuwarsu ta qare kenan, Sun rasa uwa da ubansu da gidansu da garinsu da rayuwarsu da yanci su da qasarsu duka sbd kaddarar zuwa nan, Anan Allah ya kaddaro zasu qarasa rayuwa Shiyasa duka wannan kaddarorin suka hau kansu, Numfashi me dumi ta sauke ahankali mara sauti tana gode wa Allah Akan wannan jarabawar me nauyi da munin daya kaddaro musu tareda fatan su cika fa Imani su samu Hutu Bayan mutuwarsu sbd a yanzu da dukkaninsu kowa ya rasa babban bangare na rayuwarsa babu komai da yayi saura kuma a kaddararriyar rayuwarsu Bayan jiran lokacin mutuwa kuma dan haka duk abinda zasu gani na azaba ko baqin ciki basajin zuciyarsu ma zata girgiza ko kasa dauka sbd rayuwarsu bata shigo qasar d sauran kowane irin taushi ba a zuciya ta gama bushewa. Sakinah dake kallan qasa itama lashe lips dinta da suka bushe tayi ahankali tana Hadiye wani busashen yawun daya wuce maqoshinta daqyar Tana jin itama wannan Karan takai karshen zamowa baiwa sbd acan baya datake baiwa a gidan GHAZ Ashe ba bauta takeyi ba cikin gata take Sai yanzu ne zatai asalin bauta Bayan zuciya da rayuwar gabaki daya ta bushe musu. Dukkanin sauran bayin kowa da tinani da quncin tareda radadin da zuciyarsa take ciki kansu a qasa gabaki daya basa ma iyawa ko ikon dagowa su kalli mutane masu yanci kokuma wainda zasu iya siyensu. A haka suka kwana gurin gari ya waye suka sake wuni a gurin sedai a basu ruwa so daya da dan abinci su ci kansu a qasa babu Wanda har lokacin ya dago bare yasan kalan duniyar da suka taho. Haka suka wuni suka sake kwana babu kowane irin alamar zaa fara siyar dasu sai ranar cin kasuwar zaa bude tasu hajar a kasar dasu. ****kwana hudu sukai a gurin a Shanye sunsha rana sun bugu da rana da sanyi da iska da sauro harma da qwari Kala Kala kafin ranar cin kasuwar ta iso. Tamkar ranar sallah ta duniya haka ake ta hada hadar kasuwar da zata ci sbd manyan mutane da wakilan Masarautu da suke zuwa cin kasuwar, Daga qasashe daban daban na nesa da kusa ake zuwa cin kasuwar wasu daga qasashen nesa wasu daga qasashen kusa wasuma daga wata duniyar daban da baa San inda suka fito ba, Dan haka wasu irin mutane ne tako ina ke cika koina wainda mutane da dama basu taba ganin yawan mutane irin hakan ba ciki kuwa harda kusan duka bayin da zaaci kasuwarsu basu taba ganin tari da taron mutane masu yawa irin hakan ba dan haka kusan harda tsoron tarin girma da yawan mutanen dake cike ne sha cika su. Khams da Yaransa tin da sauran duhun safiyar ranar suka Baro gurin hutawar da suka Kama suna holewa da mata suka iso rumfar su aka sake tsara komai tareda fara tantance bayinsu daya bayan daya. Kamar kwason dankali haka aka kasa su masu karfi da cikakkiyar lafiya daban, Masu yar dama dama daban hakama maza daban mata daban hakama yan yaran da basu qarasa zama mata ba ko maza suma daban. Yanda aka rabasu din a guri daya aka hade su Ayanah da Zuhrah da sakina basu samu an rabasu ba dan haka babu motsin ko wata kuzarin yin komai da su keda suna Zaune da sarqa a kafafunsu duka babu me iya ko doguwar motsi. Rana tsaka kasuwar take kokarin fara ci amma a al’adar cinta ko a kaidar cinta bata fara ci sai wakilin Sarkin bayin qasar ya iso ya fara bude kasuwar da siyan bayin masarautar qasar kafin kowa ya fara siya daga baya. Wannan Karan ma al’adu kala Kala aka ringa gabatarwa Ana siye da siyarwan Sauran abubuwan Banda bayi tareda dabbobin ruwa da tsiron ruwa daban daban duka gasunan anata siyarwa da siya. Isowan wakilin Sarkin bayi na BOYEM ne ya saka kasuwar ta fara kokarin yin tsit duk girmanta sbd askarawan da suka shigo kasuwar tareda wasu irin manyan motocin Masarauta masu kyau budaddi dake Kwasar bayi zuwa Masarauta hakama masu tsayu kusan guda biyar. Take dukkanin masu kasuwancin bayi suke mimmiqe daga Zaune dan nuna girmamawansu ga wakilin Sarkin bayi na Masarauta me alfarma. Babu bata lokaci kuwa ya fito tareda wasu daga cikin manyan askarawansu kafin mutane suka ringa gaidasa manyan yan kasuwa kuwa duk sun qaraso dan tarbansa dan haka a tareda Jamaa sosai manyan kasuwar ya kutso kasuwar yana amsa gaisuwar da tarin mutane da dama suke aiko masa. Rumfar farko ta bayi ya fara tsayawa ya karbi Shedan kasuwansu da lasisin su ya duba tukuna ya kalli bayin wainda ke a daddaure da sarka suma hadda hannuwansu duka a daure suke da sarka. A take ya diba guda dari ya siye aka zube musu danyar zinariya da azurfa sbd inda zasu koma basa buqatan kudin takarda sedai zinariya da azurfa, Tattara lasisin bayin akai Bayan an saka basu damar saka hannu daya bayan Dayan Ana wucewa dasu Ana zare sarkar su ana sakawa mota, Rumfa ta biyu turawan Rome ne dan haka bayinsu da tarin dalolin takarda aka siyesu Wanda suma take kowa ya sake saka hannu aka wuce dasu sbd saka hannun shine abinda yafi komai mahimmanci a zamowa bawan Masarautar BOYEM mai cikeda kaidoji daban daban. Rumfa ta hudu ce tasu kusrawa dan haka koda aka iso gurinsu suna a tsaye cikeda Wani irin farin cikin khams daya kasa boyuwa ya miqe tareda tsananin fatar yau burinsa ya cika sbd matiqar baa siye bayinsu duka ba to sun tabka babbar Asarar da kafin su farfado sai sun dauki shekaru dan kuwa duk abinda suke dashi da fiyeda rabin bayinsu sun siyar dan ciyar da kansu hanyar zuwa nan da kuma lasisin shigowa qasar dana kowane bawa da sukai ya cinye gabaki daya tattalin arzikinsu, Idan an siye bayinsu duka hakan ne zai basu cikakkiyar lasisin ringa kawo bayinsu BOYEM Wanda hakan ne burinsa daman Wanda arzikine zai bude musu kofa dan haka gabaki dayansu fatan sukeyi duka bayin a siyesu su samu wannan abinda suka jima suna buri. Tsayawa wakilin yayi daqyau Akan rumfar Bayan ya gama amsawa da gaisa wa dasu khams din wainda suka gabatar masa da wani lafiyayyan koshashen bawan dayake tamkar basa mude Akan koshi a matsayin kyauta ta musamman Wanda tinda suka dauko sa suka Kebe sa suna ciyar dashi da kyau da basa kulawa sbd hakan. Cikin Jinjinawa ya amsa da godia sedai ba shine abinda yake sakasa siyan bayin da matakan dasuke buqata basu kaiba. Matan dake cikin tarin bayinsu ya zubawa ido yana tantancewa daya bayan tsawon lokaci kafin ya juya gurin mazan suma ya fara tantance su yana duba abubuwan da sune ke saka su siya bawa. Tsananin yanda duka bayin suke nuna biyayya da tsoro ne matakin farko dayake saka Ka siya bawa, Sai jarumta da karfin Hali tareda jajircewa da bushewan zuciya da itace zata saka bawa yin bautarsa sai kuma Sauran abubuwan da sirrin masarautarsu ne da suke siyan bayi Akai. Hannu ya miqa a gefensa kan akwatin da ake biye dashi a bude ya saka hannu zai dauko lambar adadin bayin da zasu siya a rumfar taje kowa yayi tsit suna jiran ganin adadin, Kusrawa ma gabaki dayansu harbawa zuciyarsu keyi da tsallen fargaban adadin da wakilin zai dago Wanda basa tafar komawa da bawa ko daya dan haka idanuwansu kaman zasu feso waje haka suka zubawa hannunsa dazai fidda idanuwansu. #MAMUH #ROYALTY #BOYEM HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:46 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 19 *JEWELRY JUNCTION* 08039440312 Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma, Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne?? To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan, Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana, ✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌 ✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌 ✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌 ✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍 🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah. WhatsApp 08039440312 Tiktok :@sokoto jewelry seller Instagram: jewelryjunction23 ************** Ahankali hannunsa ya fito daga akwatin Wanda yake dauke da lambar data saka Wani irin Ihun murnan daya saka rumfar gabaki daya girgiza sbd Ihun samudawan Kusra dayake tashi yana ratsa kunnuwan bayinsu dake sake shiga Hali na Godiyan Allah suma daya rabasu da kusra daga karshe dai sunga karshen wata kaddarar tasu mara dadi zasu su tarar da wadda basusan yaya zata kaya ba. Sai a lokacin Ayanah ta bude idanuwanta ahankali tana zubawa qasar gabanta idanuwanta da sukai jajir tana ji a zuciyarta kaddararta bata qare ba dan kuwa sai ranar da ranta yabar jikinta kaddarar rayuwarta kila zata qare. Lumshe idanuwanta tayi tana sake jin Ihun kusrawa na ratsa kunnuwanta zuwa zuciyarta dake Wani irin quntatar da batada mafita ko samun sauki. Take aka fara Jere dunqulallen zinariyar da sai an auna nauyin kowace kafin a Jereta Ana Kirga bayin tareda auna nauyin kowane sbd nauyinsu ne yake zabar musu farashinsu, Daya bayan daya aka fara aunasu tareda rubutu wa a lasisin kowannensu farashin da aka siyesa da nauyinsa kafin a dangwala hannunsa a matsayin to a zama cikakken bawan BOYEM har qarshen rayuwarka. Ana zuwa kan Ayanah hakanan kowa ya tsayar da idanuwansa akanta Ana jin Wani irin yanayi na tausayi da Jin nauyi har aka gama da kanta ta daga hannunta a hankali ta dangwali ruwan saka shedar ta Dora akan lasisinta ta daga kafarta ta tsallaka zuwa inda rayuwarta ta koma a yanzu kwata kwata tana fita daga hannun kusra. Zuhrah Ana zuwa kanta tana dangwala hannunta kasa sakawa tayi a lasisin da zai tabbatarda fitar ta daga hannun kusrawa Hawaye masu tsananin zafi suna gangarowa daga a idanuwanta sbd daga yau shikenan sun yadda da kaddarar data rabasu da rayuwarsu ta baya da yan uwansu, Daga yau sun rabu da dukkanin abinda zai iya sake hadasu da Abaas ko wata ran, Daga yau sun zama abinda aka saka kudi aka siya sannan daga yau ne zasu fara amsa asalin sunan zama bayi sbd a baya da Allah zai kubutar dasu daga hannun kusrawa zasu iya gudu wa su Gina sabuwar rayuwa amma daga yanxu da aka biya kudin su sun zama cikakkun bayin da har abada shikenan. Rawa hannunta keyi sosai a lokacinda ta daga hannun ta saka a lasisin dayake dauke da sunanta a matsayin baiwa ta lambar dake hannunta wadda akai musu da wuta harta warke ta zama kamar Zanen tattoo. Wucewa tayi ahankali ta isa inda Ayanah take tsaye hawayen ita sun qare mata basa iya fitowa sedai Idon yayi jajir. Sakinah ma gurinsu din ta tsaya a gefe Bayan an tantance ta a hakan har aka kammala komai aka biya dukiya me tarin yawa gurin siyansu cinikayya ta gama tabbatuwa aka zuba su a motar da basusan mecece ba amma kuma basuji tsoro ba sbd babu Sauran tsoron komai ya fice musu. Sai tsakar dare sosai aka gama cin kasuwar wadda iya ta bayin aka gama ci daga nan ne Sauran kasuwancin yaci gaba da gudana Wanda zaaita ci har safe har a wuni sbd sai kasuwar tayi kwana biyar tana ci, Motocin masarautar BOYEM dai a Daren suka daga zuwa cikin qasar wadda tafiya ce me tsayi ta kwana biyu kafin ma an isa cikin qasar kafin isa babban birnin kasar inda asalin masarautar take. Motocin na daga wa aka fara bukukuwan cin kasuwa da kide kiden al’adarsu dana taya wainda suka ci kasuwar bayi Murna. Tinda suka fara tafiya hannun Zuhrah yana cikin na Ayanah sun riqe juna shiru babu me iya ko dogon motsi sbd rayuwar kowa data gama mutuwa. Sakina ma tana Dayan gefen Ayanah wadda Ayanah ta miqa wa hannunta daya itama ta Kama suka riqe hannuwan juna su ukun suna jin dumin tafukan hannun juna. Tafiya me tsayin gaske akai kafin aka tsaya aka fiddo bayin gaba daya sukabi kayi aka rarraba musu abinci da ruwa kafin kafin masu lalura suka sauke suka huta tukuna aka sake daukan hanya. Tafiya me tsayi gaske sukai kusan kwana uku suna shiga garuruwa masu girma da Kyan gaske da abinda basuma San duniya na da shi ba kafin suka fara shigowa asalin babban birnin daular BOYEM Wanda a garesu ganinsa tamkar Aljannar duniya ce da ko a labarai basu taba Jin akwai irin wannan duniyar ba, Dukkanin abinda idanuwansu ke gani kansu ya kasa dauka sbd tsoro ma suka ji ya fara kamasu mai tsananin gaske take suka Ji duniya ma suke son Bari gabaki daya dan bazasu iya rayuwa a cikin irin wannan daular ba. Kai tsaye suna shigowa babban birnin qasar Wanda yake da wani irin tsari da tsaro tareda wata irin rayuwar da ni’imar iskar ma da kake shaqa jinsa zaka yi daban, Koina a birnin Ihun tsantsar dukiya da arziki yakeyi sbd kusan duka garin yana cike da masu sarauta da mulkin kasar, Manyan daular qasar gabaki dayanta suna cikin birnin, Duk inda Ka daga kai Ka kalla tambarin masarautar BOYEM ne Wanda hakan yake nuni da karfin mulkin masarautar tafi na gwamnatin qasar da zagayenta gabaki daya, Tsananin karfin iko da tsananin dukiya da arziki tareda rashin tsoro da asalin jarumta da ahalin BOYEM suke dashi tin kakanni da kakannin shekaru daruruwa ya saka sune suke juya qasar da duka kasashen zagayenta Wanda sune suka kirkira tareda kafa qasar gabaki dayanta Shiyasa kasar take da sunansu kuma haryanzu generation Bayan generation sune suke juya qasar kuma har gobe babu me irin tarin arzikinsu a qasar sbd koyaushe gaba suke sake yi ba baya ba dan hakanne ma kasancewanka jinin BOYEM a duniyar tasu ba qaramar sallama mutanen duniyar suke ganin Allah ya maka ba a zaman rayuwar duniyar dai sbd koda duk wani asalin jinin BOYEM koda zai fado duniya cikin zanin goyansa yanada arziki da dukiyar da harya bar duniya bazai gama cinyewaba, Yanada power me karfin gaske sbd ko dan shekara biyu jinin BOYEM zai iya yanke maka hukuncin da zai iya rabaka da duniya kuma Ka tafi kenan matiqar kayi laifin daya sa yace bayason sake ganinka, Hakama yanada gata da suna sbd duniya zata sansa koina kuma Ayi shakkarsa. Abu daya ne yake qaranci a zuriar BOYEM tin asali Wanda suke ganin shine kadai abinda zai iya kawo rauni a wani bangaren duk da hakan sun tsaya cak akan hakan shima kuma Allah na dafa musu waton shine yawan ‘yaya maza Wanda tin daga kakannin kakanninsu ne, Kowane zamani kowane generation yanada wuya duk namijin dake zuriyar BOYEM ya wuce samun yaya maza biyu ko uku, Mutum hudu ne kaf suka taba haihuwan yaya maza biyar da shida sai me takawas a tarin zuriyar tasu datafi hada zuriar sama da dubban dububuwan da har abada baa iya kirqe zuriarsu sedai wainda sukai mulkinsu kuma suma Mutum hudun tin a farkon karnin dasuka dade da gabata ne dan duka zuriar kowa yayi mulkinsa ya gama yabar duniyar yayansu ma sun hau sunyi sun tafi hakama jikokinsu duka sunyi sun tafi harma da tattaba kunne haka haka sarautar take tafiya, Masarautar BOYEM sune suka kafata da karfinsu da jininsu da zufansu da dukiyarsu harta kafu ta zama masarautar da kowa ke shakka yake tsoro ba masu kudi ba,ba talakawa ba hakama ba Sauran masu mulki ba kowa yana shakkarta da tsoronta sbd tsaurin hukuncin da rashin shamakinta a komai kuma hakan ya saka babu Wanda ya taba mulkar BOYEM Wanda ba asalin jininta ba kuma har abada bazasu taba barin Wanda ba jininta ba ya hau mulkinta matiqar ba Allah ya kaddaro hakan ba dan hakanne duk wani Sarkin da yayi mulkin BOYEM yana ‘yaya masu tsananin yawa sbd sunada IMEBĒTI wainda suke kiransu ARKI wato kuyangin da ake kai musu suke kwana dasu suna hayayyafar musu zuriar da suke alfaharin sunada ita fiyeda kowane ahali. *******tin daga babban lafiyayyan titin dayake tsakiyar gari da zai dauki hanyar zuwa masarautar checking points masu tsananin karfi da tsaro na wasu irin kakin askarawa da bindigogin da kowace kalar babu da wasu irin sharp wuqaqe dake soke jikin kowane jami’i,weapons dai gasunan Kala Kala marasa Kyan gani Wanda kasan Ana Dora daya akan jikinka to sai maqabarta direct kabari. Bayan tsaro Wani irin tsari ne da kowane Taku daya yake nuni da ba qaramin guri ne Ka zo ba, Gine gine ne masu tsananin tsayi da kyau da daukan ido da gigitarwa kaman zasu fado a Kanka sbd har wani jiri suke sakawa suna haske ido kaman zinariyar ce da gaske a jikinsu kaman yanda tarihi yake fada akan masarautar. Duka duka checking points uku suka wuce suka isa daular bayin dake kafin isa asalin makekiyar kofar datake kaman gida guda ta shiga masarautar. Daular bayi ake kiran babbar bangaren da aka Gina me girman gaske na horar da bayi sama da dubban miliyoyi Wanda kuma a cikin daular bayin bangare guda lafiyayyan gidan Sarkin bayi ne Wanda masarauta ta tanadar masa estate guda a daular bayin inda gidansa a cikin estate din yafi kowanne girma da tsari da tarin dukiya kafin Sauran na dukanin Sauran ma’ikatan dasuka shafi kula da dukkanin harkar bayi kowa da iyalansa da yayansa da iyalan yayansa dan haka daular bayin duniya ce guda mai zaman kanta datake cike da tsaro da tsari tareda daula tamkar wani babban shugaban wata qasar ne a nan, Acan nesa da estate na gidajen babban bangaren kula da bayin yake Wanda shima a tsare yake a tsaftace tamkar wata lafiyayyan jamiar karatu sbd komai nasu a tsare yake, Uniform ne dasu masu kyau da qarko coffee brown Wanda kowane bawan a tashin farko Kala biyar biyar ake bawa kowa kafin kuma lokaci lokaci Ana sauya musu sabbi sbd tsantsar tsaftar da BOYEM take dashi Akan mulkinta. Akwai bangare daban kuma daga nesa Wanda yake da girman dayafi koina sbd tarin manyan dabbobin daji masu mahaukacin girma da koshi sbd zakunan su da da misos jinsu naman jikinsu har wata irin rawa yakeyi sbd qoshi tareda samun cikakkiyar kulawa, Mahaukatan wild animals ba kadan suke dasu ba wainda suka samu mahaukacin training da zama savage Wanda suma kansu sarautar suke bugawa sbd hatta dabbar masarautar BOYEM din Taku ne dasu sbd training, Tsananin tsaro da tsarin yanda aka killace su wani abu ne me girma na daban dan kusan kilometers ne a tsakaninsu da inda Sauran bangarotan suke. A dayan bangaren dayake kusa da dabbobin bangaren hora bayi ne masu laifi da basu azaba dan haka daular bayin take da bangarora manya manya daban daban. Isowan Sarkin bayi tareda sabbin bayin daya siyo din ya saka aka bude babbar kofar da bangaren bayin Ana jiran saukowansu daga mota daya bayan daya bayan anyi parking motocin kenan. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 20 *JEWELRY JUNCTION* 08039440312 Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma, Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne?? To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan, Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana, ✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌 ✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌 ✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌 ✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍 🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah. WhatsApp 08039440312 Tiktok :@sokoto jewelry seller Instagram: jewelryjunction23 ******** Ayanah na saukowa kanta a qasa yake sai data sauke ajiyan zuciya kafin ta dago ahankali tana bude idanuwanta da sukai Zurfi sosai ta kalli fadin harabar inda tarin motocin masu girma suke babu adadi masu yawan gaske, Akan wadda suka fito ta dawo da idanuwanta ta tsayar tana kalla jikinta na Wani irin sanyin da babu tinanin komai a cikin kwakwalwanta lokacin dan haka ta tsayar da idanuwanta Akan Zuhrah dake saukowa a sanyaye itama babu Sauran tinanin kanta ko ‘daya daya rage musu. Hannu Ayanah din ta daga zata miqawa Zuhrah sakina dake kusa da ita tayi saurin riqeta ahankali tareda dan girgiza mata kai batareda ta juyo ta kalleta ba sbd a dokar bauta baa yan uwantaka a nata sanin duk da kusan kowace nahiya da yanda suke nasu dokar. Gefen Ayanah din Zuhrah ta tsaya Sauran suka qarasa fitowa kafin aka Dora su a hanya Ana wucewa dasu kansu duk kaf a qasa sbd duniyar da suka samu kansu wata abace da Allah bai taba nuna musu ko a mafarki ba, Kaf dinsu kusan qalilan ne suka fito na gidajen alfarma ba da rufin asiri me girma, Sunga daula iri iri me daukan hankali da iyalinsa duniya me rikitarwa amma kuma a nan inda suke gani yanxu ya wanke tinani da kwakwalwansu tas babu Sauran abinda ya rage sbd sun gama tabbatarda sunzo inda babu kamarsa a duniyarsu da idanuwansu suka gani hakama babu ranar komawansu ga iyalai ko qasa ko kuma taba ganin Wanda ma idanuwanka suka taba gani har abada dan hakanne kowane bawa a cikinsu jikinsa yake a sake sun gama saddaqarwa su yanzu basu din bane tace bayin BOYEM kuma da wannan sunan zasu mutu subar duniya. Wata doguwar hanya aka wuce dasu me tsayin gaske wadda ta rabasu kwata kwata da harabar gurin inda bazasu sake ganinta ba zuwa babbar doguwar kofar shiga bangarensu me girman gaske. Daya bayan daya aka fara shiga dasu dakin da ake fara shiga kafin wucewa ciki, Daki ne babba Wanda yake tamkar office da cameras a ciki da tarin computers da wasu abubuwan da duka dai basu taba gani ba a rayuwarsu, Daya bayan daya ake shiga dasu Ana yiwa kowa hoto tareda Id card dayake dauke da sunan kowa da hotonsa tareda uniforms da Sauran abubuwan amfaninsa. Wuni akai Ana wannan aikin nasu har aka kwana anayi saida aka kwana biyu Ana wannan aikin nasu kafin aka gama yiwa kowa, Duk Wanda akaiwa shine kadai yake wucewa ciki Wanda baayiwa yana waje saida suka kwana a waje kuma kusan a tsaye, Su Ayanah ne kusan na karshe sunji jiki sun galabaita sosai har basa iya tsayuwa daidai a rankwafe suke tafiya, Suna shiga suma a kwai jakadiyar Sarkin bayi ta mata dake ciki itace kai tsaye ta basu nasu dakin, Cikin saar da basu zata ba aka basu daki daya su uku tareda wasu Mutum uku din sbd duk daki Mutum shida ne. Koda suka isa dakin akwai Mutum uku dake dakin daman wainda daman sun jima sosai a BOYEM din. Basa nan suna gurin aikinsu da aka raba musu dan haka kai tsaye umarnin da jakadiyar bayin ta basu kowa ke kokarin cika wa Banda Ayanah data jingina jikin bangon dakin nasu Bayan ta shigo ta silale qasa tana rufe idanuwanta dake tsananin radadi quncin dake soya jini da gangar jikinta tana jin zuciyarta na Wani irin zafi da ciwon baqin cikin rayuwa me girman gaske dan batasan tayaya zata fara sabuwan rayuwar data samesu ba ta har abada babu Iyayenta da Nurat da Abaas ba a cikinta, Batasan tayaya zata rayun bama sbd zuciyarta ta mutu gangar jikinta ne kawai ranta rage, Zuhrah ma dawowa tayi gefen Ayanah din ta zauna ahankali tana kwantar da kanta a gefen kafadar Ayanah din tareda saka hannunta cikin nata suka sarkafe ahankali bata ce komaiba ta rufe ido hawaye masu dumi suka gangaro mata suna sauka a kan hannuwansu dake sarqe. Bude idanuwa Ayanah tayi ahankali ta kalli hawayen yanda suke gangara a fatar Bayan hannunta ta Lumshe ido ta bude tareda Dora hannunta daya Akan fuskan zuhrah ta Shafa ahankali tareda juyowa kadan tayi sumbaci tsakiyar kanta da babu dankwali sun zama tamkar mahaukata ta sauke ajiyan zuciya tareda bude baki ahankali tace ‘Zuhrah hįyįwetēni bemulu,ye’īne aleem zuhrah(Zuhrah my whole life, zuhrah my world) Allah ya hanani dandana rabuwa dake, Ina rokon Allah ya dauki rayuwata kafin kaddarar da zata rabani dake tazo..’ Tsananta gudu hawayen Zuhrah sukai ta sake shigewa jikin Ayanah din tana fidda kuka Mara sauti tareda girgiza kai tana cewa ‘Ayanah idan babu ke wlh zan kashe kaina na biku duka bazan iya rayuwa a duniya ni kadai babu ku dukanku ba, Na Roki Allah kaman yanda yabarmu muka rayu a tare zuwa yanzu ya raya mu a tare mu mutu tare mubar duniyar tare.’ Girgiza Kai Ayanah tayi idanuwanta na qara yin jajir tace ‘Abaas…’ sai ta kasa cigaba da magana ta rufe idanuwanta tareda sauke Numfashi me zafi. Sun jima a hakan tsawon lokaci kafin sakinah da itama tana rabe a gefe ta taimaka musu suka miqe kafin suyi wani motsi aka fara buga wata qararrawa me karfi ta kiran kowa da anfada musu maanarta tin kafin a basu daki dan haka a sanyaye babu me iya miqewa tsaye daidai suka fito. Kusan su Dari harda qari ne bayi mata sababbi da aka kawo yau din dan haka iya su dinne a bangaren yanzu sbd tsofin bayin basa nan duka suna gurin aiki dan haka suna fitowa a wani babban guri me fadin gaske dayake shafe da tiles fari qal da hanyar wucewan ruwa da famfuna babu adadi da hanyar wucewan ruwa Wanda yake nuna alama da gurin wanki ne, A ciki gabaki daya aka turasu daya bayan daya aka saka kowace su ta tube Kayan jikinta aka sakar musu ruwa daga samansu batareda sunsan ta inda ruwan ke fitowa ba, Ruwa sosai ne yake sauka akansu inda wata irin dauda take jiqa a jikinsu me yawan gaske tana gangara qasa take tiles din gurin ya sauya Kala haka ganin farinsa ko kadan ruwan daudar jikinsu ne kawai ke kwarara a qasa, Wani irin qarni da tsami tareda wari ne sosai ya gauraye gurin take Wanda ya saka maaikatan mata sake ja baya suna nesa dasu dan duk bawan da aka kawo BOYEM sai an tsaftace sa sosai tin asali dan haka kowane bawa dake BOYEM ya samu Kansa a irin yanayin, Umarni daga cikin lasifikar dake hannun jakadiyar ne ya shiga kunnuwansu cewan kowa ya Shafa abinda aka basa su wanke jikinsu sosai sosai. Maaikatan da zasu tsaftace su ne suka fara shigowa daya bayan daya dauke da trays masu girma suna Jeruwa har suka gama shigowa kusan su goma sha biyar kafin jakadiyar ta shigo daga karshe. Layi aka fara jansu daya bayan daya, Ta farkon da aka fara da ita shaving cream aka shafe musu jikinsu dasu inda yake da gashi kafin aka dauki lafiyayyan almakashi aka Kama gashinta kai tsaye aka yankesa sosai aka bar Wanda tsayinsa bai wuce tsayin rabin biro ba. Haka aka fara yi musu daya bayan daya Ana fesa Musu wani abu a cikin gashin Wanda take yake kashe dukkanin qwari ko qwarqwata idan akwai a ciki. Haka aka ringa musu daya bayan har aka zo kansu Ayanah wainda idanuwansu suke a rufe zuciyar kowannensu na qarasa macewa tana barin gangar jikinsu. Kama gashin Ayanah akai me tsananin tsayi take aka yankesa duk da akwai wainda suka fita tsayin gashin da yawa tinda su kusan a qasashensu babu mara gashin daman suna rage tsayin gashi yayan sarautarsu ne kadai basa rage gashi sosai sbd cikon al’ada ne ga dukkanin jinin sarauta, Na Zuhrah ma dayake da tsayin dayafi na Ayanah haka aka yankesa Wanda ya sakata sauke ajiyan zuciya sbd shi Kansa gashin a yanzu tamkar azaba ce a garesu. Mintina qalilan aka sake sakar musu ruwa masu yawa sosai aka sake wankesu sosai a karo na biyu kafin aka sako musu ruwan sabulu me kumfa sosai shima anan wankan sosai aka sakasu sukai tareda wanke kansu Wanda wasu hadda jini yake fitarwa tsabar qwarin dake cikin gashin suna Shan jininsu a maqale, Sosai aka sake wankesu da ruwa me kyau kafin aka sake zuba musu kumfa sai da sukai wanka kusan so goma kafin aka sallamesu ana basu saqi na zanin Daurawa me kauri daya bayan daya suna wucewa. Koda suka koma daki kusan da yawansu zazzabi ya gama rufe su na wankan duk sun shaqa ruwa wasu kuma sanyin ya shigesu sosai dan haka magani aka sake rabawa kowa koda haka zazzabin ance kowa ya sha. Uniforms suka saka wainda bazasu iyaba kuwa zazzabi me karfi ya kwantar dasu Wanda ya saka da yawansu basu iya fitowa karban abinci ba harda su Ayanah wainda suke kwance sosai har jijjiga sukeyi. Sakinah ce ta iya fita tabi Layi ta karbo musu abinci ta dawo dakin ta taimakawa Ayanah taci kafin ta taimakawa Zuhrah itama taci kafin ita taci daga baya. Basu iya Shan maganin da aka basu ba sbd basusan tayaya zasu iya shansa ba, Shiru sukai a daki babu Wanda yake iya ko tashi zaune a cikinsu sbd itama sakinar daga baya zazzabin bugar da ita yayi. Sai dare kusan karfe daya tukuna suka Ji shigowan Sauran Mutum uku din dake dakin. Babu wadda ta iya tashi a cikinsu suna dunqule guri daya sunyi Laushi sosai, Dayar cikin wainda suka shigo dakin ce ta iya isowa inda suke taga yanda suke jijjiga sbd zazzabin dan haka tayi saurin daukan maganin da aka basu ta jiqasa da ruwa ta fara kamo kan Zuhrah ta bata a baki Tasha sosai sbd kishirwa take ji. Sakinta tayi ta Kama Ayanah itama ta bata tareda ruwa sosai kafin sakin daga qarshe. Amai sosai zuhrah tayi sosai Wanda ya saka Ayanah tattara karfin Hali ta miqe sbd kulawa da ita cikin wahalar nata ciwon. Sakina ma karfin halin miqewa daga ciwon tayi itama suka taru dan kulawa da Zuhrah wadda take jin jiki sosai harma hankalin Ayanah yayi mugun tashi tsoro me karfin gaske ya kamata. Daqyar suka samu gari ya waye jikin Zuhrah din ya dan samu sauki sosai tayi bacci wadda bata taba samuba a watannin. Itama Ayanah baccin ne ya dauketa na wahala har tsawon lokaci Wanda shine ya taimaka musu suka samu Wani irin sassauci me girma da qwari sosai. Guraren 10 na safe aka buga kararrawar kira wadda ta fiddo kowa suka bi Layi aka raba musu abinci suka dawo daki suka zauna suka Turawa cikinsu sbd basajin dadin rayuwar bare abinci #MAMUH #BEST LOVE STORY #BEST ROYALTY STORY #BOYEMS #GHAZ #NUAB BOYEM #LOVE #ROMANCE HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 21 *JEWELRY JUNCTION* 08039440312 Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma, Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne?? To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan, Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana, ✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌 ✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌 ✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌 ✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍 🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah. WhatsApp 08039440312 Tiktok :@sokoto jewelry seller Instagram: jewelryjunction23 ************ Wuni sukai a daki ba komai ba wani hayaniya ko doguwar motsi koina tsit sbd kowa ya fice sai su sabbin zuwa, Sai yamma aka sake kiransu wanka haka aka kuma wankesu tas suka dawo daki yau kusan kowa da Kansa yasha maganinsa sbd abinda ya hanasu Shan na farko rashin sanin yanda zasu sha amma ganin ya taimaka musu jiyan sai kowa yasha. Da dare ma haka aka kuma kiransu aka raba abinci sukaci suka kwanta Wanda take baccin wuya ya dauke dukansu kamar bugaggu Wanda basu saniba harda maganin bacci ake basu sbd anason su samu ishashen baccin da zai warware qwaqwalwarsu ta sake sbd gudanar da rayuwarsu a natse dan komai a BOYEM nutsuwa ce tsagwaranta yake buqata. Washe gari ma haka aka kuma basu ci da wanka tareda magani suka wuni suna bacci da hutawa, Duk yanda zuciya da kwakwalwan su Ayanah yake cikin wani irin qunci da damuwa me nauyi maganin da aka Dora su akai fin karfinsu yayi bacci suke yi sosai batareda sunsan ma tayaya kansu ya fara sakewa ba yana dan dawowa da tinaninsu Akan hanya daga fatan mutuwar da sukewa kansu kullum. *****kaman yanda doka da kaidar Masarautar BOYEM take sai anyi sati biyu cif Ana basu abinci fa Hutu sosai kafin Ayi wata daya Ana horar dasu komai na masarautar Bayan an gama tababbatarda sun yadda ce tarihinta da sanin kowane irin bayani Akan bautar da zasuyi dakyau Wanda idan Baka da qwaqwalwar haddace komai da riqe komai kan hidimar dake gabanka shine ake Tura Mutum bangaren wahala da azaba inda zaka gwammace rayuwa a wata qaramar masarautar daji da babu gabas bare yamma. Haka su Ayanah suka share sati biyu Ana basu Hutu duk da babu Wanda yake cikin dadin zuciya ko kadan a cikinsu amma jikinsu da fatar su ya samu lafiya sosai dan kuwa ko gurin Kwanciyansu a tsare yake da tsafta da dokoki, Sun sauya sosai gangar jikinsu ta samu nutsuwa dan haka aka fara koyar dasu mataki ma biyu Wanda kullum ne ake koyar dasu yanda ake aiki da komai a masarautar irin su wanke toilet da gyara tareda iya aikin koina da yanda zasu iya fuskantar rayuwarsu idan sun tsayu a gaban duk Wanda yake jinin BOYEM. Rayuwar bayin BOYEM hatta inda zasu iya dagowa su kalla a qayyade yake hakama yanda zaka iya bude baki ko fidda Numfashi me sauti a gaban jinin BOYEM Akan kaida da doka yake hatta dukkanin gangar jikin bawa da abinda yake gangar jikinsa Akan kaida da tsari tareda amarni yake. Wasu irin kaidoji da dokoki tareda tsari masu tsauri da karfi aka fara dorasu dan kuwa ko tafiyarka a tsari take aka dorasu, Lokutansu na bacci da fitowa fara aiki tareda wata irin tsaftar gaske duka Akan tsari suke da yanda ma zaka dago kai Ka iya kallan inda kake sbd kaida ne koyaushe Kanka ya zama a qasa, Duk jin dadi da nutsuwar da suka samu a BOYEM din tsari da dokokin tini suka daga hankalinsu tareda shiga tsoro me tsanani sbd laifuka da kurakuran da zasu iya rabaka da ranka a masarautar yawa ne dasu sbd mafi yawan hukuncin kasar cire kai ne kawai kokuma ciyar da dabbobi namanka dan haka babu Wanda yake yadda komai tsananin tsautsayi yayi laifi dan tsira da rayuwa, Mataki mataki ne na bayin masarautar sai Wanda yakeda matakin saar karshe ta rayuwa yake samun damar yin aiki a inda asalin jinin BOYEMs din suke. ***Ayanah da Zuhrah harma da sakina basuda Sauran kowane zabi Bayan mayarda hankali suna daukan karatun da ake musu tareda samun qarin nutsuwa sbd a yanzu damuwa da kuncinsu a natse ma yake cinsu, Sun sauya sosai kawai dai quncin dake kwance a zuciyarsu ne yake hanasu yin jiki ko mulmulewa suna nan basu wani qara kiban komai ba kawai dai yunwa tabar jikinsu. Kullum da safe a kaida da doka zasuyi wanka su shirya a cikin uniform dinsu tsaf tsaf su isa gurin karban abinci abi Layi su karba abinci su ci kafin masu wucewa aiki su wuce su kuma su isa inda ake karantar dasu acan suke wuni sai yamma suke dawowa. Sakinah data Saba da bauta zuwa yanzu ta sake ta karbi sabuwar rayuwarta da babu matsi hannu bibbiyu tareda samun nutsuwa da gode wa Allah daya rayar da ita ta fito daga hannun kusra batareda rasa komai nata ba dan haka a yanzu batada doguwar damuwa saita Ayanah wadda koda minti daya quncin dayake zuciyarta bai taba fita ba zuciyarta a qulle take tamau da wani irin qunci da damuwan da har abada kila bazasu fita ba dan rayuwarta ta Riga tayi rushewan da bazata taba gyaruwa ba, Tana komai Akan lokaci tareda komai da ake Dorasu akai a natse babu hayaniya babu rawan jiki komai nata yayi sanyi ya koma zallan nutsuwa bata sake bude baki ta Ambaci Abaas ko Nurat ba komai ta tattara ta ajiye sa a cikin zuciyarta yana cin lafiyanta da kwakwalwanta a hankali ahankali batareda sanin kowannensu ba, Sakinah datafi su wayo da shekaru sosai ta fahimci Ayanah ta kafe komai a tsakiyar zuciyarta Wanda illar da hakan zai mata tasan mai yawa ce sbd ta riqe baqin cikin da quncin gam a cikin rai ta kasa fitarwa amma ganin bata nuna ba tana komai na rayuwarta a natse ya saka bata ce komaiba sai itama ta sake sbd tinanin insha Allah lokaci na tafiya quncin kila zai ringa wankewa yana ficewa daga ranta. Zuhrah da farko mamakin Ayanah ta ringa yi ta yanda ta Dena maganar su Abaas kwata kwata da iyayensu ta nutsu duk da tayi sanyi sosai kaman ba ita dinba ko dagowan magana bata iya yi yanzu Wani irin miskilanci da son kadaici ya aureta, Zuwa yanzu kusan sunsan koina a bangaren nasu na bayi da yawan bayin da suka taho tare sun sake sun karbi wannan rayuwar dari bisa Dari farin cikinsu sukeyi da walwala tareda jin dadi, Suna Sauran sati daya a kwashe su zuwa cikin asalin masarautar subar daular bayin hankalin Zuhrah ya tashi sbd tsananin tsoro da fargaban shiga BOYEM palace take dan abu daya ne akace a cikin biyun matiqar Kafarka ta shiga gate din masarautar aka rufe to tabbas gawarka ce kadai idan lokaci yayi zata fito bauta ce zakai har tsawon ranka sai kuma idan Ka zamo daya daga cikin bayin da zaa riqa kwanciya dasu Ka zama abar kwanciya kenan a duk lokacinda aka ga dama har tsufanka shima kokuma idan an gama jin buqatar kusantar taka zaka koma tamkar fankon da baida Sauran amfani a duniya shikenan. Wannan tinanin ne yake saka zuciyar Zuhrah shiga mafi girman tsoro da tashin hankali harma firgita takeyi a cikin baccinta duk tabi ta firgice ta rasa nutsuwarta ga yawan mafarkin Abaas da Nurat datake suna zuwar mata cikin yanayi na tsananin tausayi. Yanayin ya saka ta fara kasa maida hankali Akan karatun da ake musu ta fara zama yanayi na kaman tana Neman fita hayyacinta, Yau ma cikin damuwa me tsananin yawa take zaune ta kasa saka Kayanta daya fito wanka ta qurawa guri daya ido hannuwanta qanqame da uniform dinta kanta bai ma San tinanin dayake ba. Ayanah ce ta fito wankan daure da abin wankanta me tsayi da kauri fatar jikinta ta samu lafiya sosai haskensu kusan duka ya kusa dawowa, Cikin sanyinta da rashin hayaniya ta dauko uniform dinta zata saka Zuhrah daya zuba mata idanuwanta da sukai jajir zuciyarta na Wani irin zafi da quncin dayake lullabe dasu ta bude baki idanuwanta na cikowa da hawaye tace, ‘Ayanah kin samu sabuwar rayuwar data mantar dake abaas na can wata duniyar yana gararin da zai iya rasa rayuwarsa koma ya rasa din? Ayanah kin manta komai ne kin zubar da komai? Sakinah data fito wanka ne ta iso gurin Zuhrah din da sauri tana riqe hannunta cikin tausasawa tace ‘Kar kice haka Zuhrah’ Fizge hannu Zuhrah tayi tana Miqewa tsaye idanuwanta na gangaro da hawaye tace iso gaban Ayanah din wadda bata iya juyowa ba ta kalleta cikin wani irin radadin zuciya tace ‘Maye a cikin wannan sabuwar rayuwar daya mantar dake yan uwanki da halinda muka shiga? Daman damuwarki Akan yan uwanki na dan lokaci ne? Daman akwai jin dadin da zai taho miki ki manta dan uwanki dake can duniya cikin garari da qunci?…. Riqota da karfi sakina tayi tana cewa ‘Ya isa haka Zuhrah,kinfi kowa sanin Ayanah ba haka take ba karki Bari Batan tinani yakaiki ga aikin dana sani’ Sake fizge wa tayi tana kallan Ayanah wadda ta dago ta zubawa Zuhrah idanuwanta da sukai wani irin jajir tsananin qunci da radadi me ciwon gaske yana cikesu amma bazata iya cewa komaiba Bayan kallan zuhran dake fada mata maganganu masu ciwo da radadin gaske. Zuhran ma cikin tsananin jin ciwo da radadin ganin idanuwan Ayanah din taci gaba da fada mata maganganun da itama suke sosa zuciyarta tace ‘Ayanah su Amma sai sunyi Allah wadai dake da zasu dawo duniya su ga yanda kika zabi jin dadin duniya kika manta amanar da suka bar miki a lokaci dan qanqani, Abaas zaiyi baqin cikin zabar sonki fiyeda Sauran yan uwansu idan yaga yanda kika zabi wata rayuwar akan tinaninsa, Ayanah inama ace Nurat ce aka bar mana dan ita bazata taba manta yan uwanta ba koda bata cikin hankalinta…..’ Wasu irin hawaye ne masu tsananin dumi suka gangaro daga cikin idanuwan Ayanah a karo na farko Bayan tsawon lokaci mai nisa, Silalewa qasa take kokarin yi sakina tayi saurin riqeta tana fasa kukan kalaman Zuhrah itama sbd tsananin tausayin Ayanah wadda har lokacin ta kasa furta komai sbd rabata da ranta ne kawai kalaman Zuhrah basuyi ba amma sun gama ratsa zuciyarta sun yayyankata, Kalaman sun qarasa karya duk wani kuzarin daya rage mata na rayuwa, Kalaman sun yanka mata sabon Raunin da shima har abada bazai warke ba……. Wasu irin hawayene ke gudu sosai a fuskanta ta kasa iya tsayuwa duk riqon da sakina tayi mata silalewa qasa tayi tana Dora tafin hannuwanta biyu a fuskanta ta rufe wani irin kuka mai qaramin sautin daya saka Zuhrah yin tsit yana zuwar mata jikinta na wata irin rawa sosai wadda ta saka sakina zubewa qasa tana rungumeta da sauri, Zuhrah ma sautin kukan ya ringa sosa zuciyarta ta durqushe itama a gurin tana fasa kuka sosai zuciyarta na dana sanin saka Ayanah kuka irin haka. Shiru dakin ya dauka babu sautin dayake tashi saina kukansu mara sauti sosai amma babu dadin Ji ko kadan. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 22 *JEWELRY JUNCTION* 08039440312 Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma, Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne?? To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan, Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana, ✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌 ✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌 ✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌 ✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍 🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah. WhatsApp 08039440312 Tiktok :@sokoto jewelry seller Instagram: jewelryjunction23 ********* Sun jima a wannan yanayin kafin Ayanah ta taqaita kukanta data jima bata samu yi ba sai yau ta miqe tareda sake komawa toilet. Acan ma wani irin sabon kuka ta durqushe tana yi Wanda dukkaninsu suna jiyota daga bandakin sai data jima tayi ta gama ta wanke fuskanta da ruwa ta fito ta goge fuskanta ta shirya cikin uniform dinta tana jin kirjinta da zuciyarta na Wani irin ciwo amma batada abin yi musu kawai qarasa shirinta tayi ta koma gefe ta zauna tareda kallan Zuhrah dake kuka har lokacin ta taso ta rankwafo kawai ta sumbaci tsakiyar kanta da gefen fuskanta ta bude baki da tsananin sanyin murya ta bude baki tace ‘Ya isa haka ki wanke Fuska ki shirya mu fice’ Ajiyan zuciya Zuhrah ta sake tareda dagowa ta kalli Ayanah din zata bude baki tayi magana Ayanah ta girgiza mata kai tana cewa ‘Ba komai ya wuce kije ki shirya din’ Miqewa Zuhrah tayi ta fada toilet duk ta zama kalar tausayi. Tana fitowa sakinah ma ta shiga suka gama shiryawa tsaf suka fito su ukun suka wuce zuwa hall din karatun. Wannan sabanin da suka samu ya sake ruguza Ayanah ta qarasa rasa walwala da kuzarinta sbd damuwan datai mata yawan gaske a cikin rai dan haka ta sake zama tamkar qanqara sbd sanyi da rashin magana sosai, Komai Zuhrah takeso shi kawai take mata bata iya hayaniya ko magana koyaushe indai suna daki Zuhrah na jikinta kwance zata rungumeta tana mata addua da shafata dan bata nutsuwa sbd tsoro da firgici na Neman taba kwakwalwan Zuhrah din tsoro mai tsanani kawai take samun kanta sbd ganin kaman suna shiga palace din sun rasa kansu kenan har abada kila ma harda junansu, Tsananin tsoron rabuwa da Ayanah take ji fiyeda komai ma daya faru a baya, Idan har zata rasa Ayanah so take Allah ya dauki ranta ta mutu, Koba komai mutuwar ma take tsananin so sbd rashin nutsuwan datake ji a zuciyarta. Ana gobe ne ranar tafiyarsu zuwa cikin palace a zaune suka kwana rungume da juna Sai a Daren Ayanah ta bude baki tayi doguwar magana da Zuhrah din tareda tinatar da ita babu abinda zasu iya yi a duniya yanzu su samu damar haduwa da Abaas wata rana irin su jajirce su rayu har zuwa lokacinda Allah zai sake kawo musu wani sauyin rayuwar, Babu abinda zasu sakawa kowane dan GHAZ dashi Bayan su rayu su kai labari dan haka matiqar tanason Allah ya kawo mata ranar haduwa da Abaas ko jin labarinsa to tabbas zata jajirce ta rayu zuwa lokacinda Allah zai dauki ranta. Zuhrah da Sai a lokacin ta fahimci karfin halin da Ayanah takeyi jin tayi jikinta ya sake mutuwa dan kuwa kaman ita bazata iya ba takeji amma ko bazata iya ba zatai kokarin bawa Ayanah karfin gwiwan rayuwa sbd itace kadai a raye wadda take saka zuciyar Ayanah bugawa daidai, Ita dai kam bazata iyaba da gasken gaske duniyar take son Allah ya dauketa daga cikinta ta tafi ta huta amma kuma idan babu ta Ayanah zata zama mara amfani a duniya sbd bazata taba moruwa ba. Koda asuba tayi suna tsaye sbd tin kafin asuba aka tadasu aka tarasu a babban guri, Anan aka sake rarraba musu uniform da abubuwan amfani a jaka aka bawa kowa nasa, Sallar asuba kawai suka koma daki sukai aka sake buga qararrawa kira suka ringa fitowa kowa dauke da jakarsa fes dasu, Jikin Ayanah dana Zuhrah a sanyaye sbd Sai yanzu ne Ayanah take sake fahimtar tsoron Zuhrah na zaa iya rabasu a gurin aiki ko gurin kwana dan haka itama jikinta ya tsananta sanyi. Motoci ne masu tsayi bus bus aka zuba su a ciki aka fice dasu zuwa cikin palace din. A mota ma hannuwansu na riqe dana juna qamqam sakina na gefensu, Ficewa akai dasu daga babbar gate din daular bayi aka miqa zuwa mahaukacin gate din shiga BOYEM palace wadda securities dinta suka mugun baci sbd tsananin tsaro, Shi Karan Kansa gate din shiga Masarauta kashe idanuwansu sukaga kaman yana yi sbd kyansa dayake tamkar na zinari, Scannin komai nasu dasu kansu akai daya bayan wuni guda Ana abu daya kafin Ana gap da kammala wa aka zo kan wasu su biyu wainda sunan mahaifinsu Yazo irin daya komai da komai. Dakatar dasu akai tareda zagaye su da wasu irin securities da suka sakasu saurin durqusawa kasa kansu a qasa jikinsu na wata irin rawa cikeda tsoron dake Neman rabasu da bugawan zuciyarsu. Chief security ne Yazo gurin da Kansa ya kallesu dakyau kafin ya kalli sunayen nasu Akan wadda tafi girma ya tsaida idanuwansa ya bude baki yace ‘Meye alaqarku da sunanku Yazo daya?? Wani yawu babbar ta Hadiye kafin cikin sanyi kanta na qasa tace ‘Alaqar jini ce…… Ko rufe baki bata gama yi ba akai sama da ita tamkar ba Mutum ba aka jefa cikin wata motar da batai Kama da mota ba sbd tsarinta dayafi Kama da motar yaqi. Wani ihu taje yi tana kokarin riqo qanwarta a lokacinda ake janta tana jin kaman ranta zai fita amma ko imanin kallanta babu take aka buga kanta da karfen motar ta zube a cikin motar jini na fitowa gefen fuskanta kadan. Qanwar tata ma Wani irin kuka me karfin gaske takeyi tana ambatar sunan yar uwarta kaman ranta zai bar jikinta take aka sumar da ita da wata shocker a gurin akace a dauketa a maidata daular bayi. Ganin hakan ya saka wainda ke bayinsu suma su uku fara rawar jiki sbd suma yan uwane uwa daya uba daya. Suma Ana duba sunayen su take aka rarrabu su ukun aka soke lasisin biyu aka bar daya Sauran zaa rabasu zuwa dauloli daban daban ga Wanda yayi rashin saa kuma ciyar da dabbobi namansu kawai akeyi sbd tin farkon shigowa qasar baa karban bayin da suke da alaqa da juna, Doka ce da kaida me tsananin karfin gaske baa barin masu alaqa a masarautar matsayin bayi duk lokacinda aka Kama masu alaqa kai tsaye hukuncinsu a kashe daya abar daya tin asalin asali wannan dollar take sbd a shekarun baya sosai da suka gabata akwai bayi uku da suke uwa daya uba daya da suka kulla shirin guduwan juyin mulkin daya haddasa fitina mai tsananin gaske a masarautar boyem wadda baa taba maimaita irinta ba dan haka tin kakannin kamanninsu aka tsauranta dokar tareda kafata mai karfin gaske kai tsaye duk bawan daya kasance yanada ahali to kai tsaye hukuncin Kisa ne ga ahalin gabaki dayansu sbd kawar da kowace irin barna, Bayi da yawa tin shekarun da suka gabata sun rasa ahalinsu akan hakan, Duk bawan dayake boyem Sai an tabbatarda baida kowa a duniya Bayan Kansa sbd Kaucewa fitar sirrin masarautar Shiyasa ko Ka samu yancin Ka baka taba barin qasar boyem sbd bakada kowa a duniyar sedai Ka Gina sabuwar rayuwa. Dan hakanne yasa duk wainda suke kawo bayi qasar sai sun tabbatarda bayinsu basuda kowa a duniya ko sunada Sai a tabbatarda basa duniya an kawar dasu sbd Ka zama na masarautar ita daya, Kusrawa tin a farkon shigowa qasar sun tabbatarda bayinsu basuda kowa a duniya dan hakanne kai tsaye a yanzu duk Wanda aka samu yana tareda wani nasa zaa kawar da daya a bar daya. Doka ce da tsananin karfinta babu Wanda zai taba wucewa kai tsaye ba tsayawa tinanin komai ake kawai da daya dan haka yanzu dinma hakanne zai faru akan wainnan sabbin bayin. Cikin masifaffiyar azaba suna tsananin fita hayyaci suke kasa rabuwa da juna inda daga karshe suka zabi a dauki ransu su duka ukun wainda suke Bayan na farkon dan hakan babu bata lokaci take aka jasu su ukun kai tsaye akai baya dasu sedai kawai yaji qarar bindigar cika musu burin abinda suka zaba amma babu Wanda yaga inda aka fito ko yi da gawarsu. Zuhrah da Ayanah dake kusan qarshe dagowa sukai a Wani irin slow suka kalli juna dukkaninsu jikinsu na qarasa sakewa gabaki daya da sabuwar mummunan kaddarar dake gabansu wadda basuda ma tinanin yi akanta. Jajir idanuwan Ayanah sukai Zuhrah kuwa gangarowa nata hawayen suka fara da idanuwanta da suka kasa daukewa daga kan Ayanah tanajin tin yanzu tamkar ruhinta na barin jikinta sbd rabuwa da Ayanah na nufin mutuwarta, Ita zata zabi a kasheta abar Ayanah sedai kuma basuda masaniyar waye zaa Bari a cikinsu kuma waye zaa bari, Ita tanason Ayanah ta rayu sbd tanada dauriya da tawakkali hakama zata rayu a cikin aminci anan din amma kuma tasan Ayanaah zata zabi a kashesu gabaki dayansu kaman yanda na gabansu suka zaba sbd bazata iya barin a rabasu ba. Wasu hawayen ne masu zafi suka gangaro mata tana sake kallan Ayanah tanason rungumarta taji dumin jikinta na bankwana amma daman hakan ta gama qare musu har abada dan haka zata zabi su rayu sbd Ayanaah kawai koda hakan na nufin raba jininsu har abada indai tana ganinta hakan ma ya isheta. Sakinah dake gabansu dan juyowa tayi ahankali ta shiga tsakiyar su itama idanuwanta na cikowa da hawayen tsananin tausayinsu musamman Ayanah dake girgiza kai ahankali idanuwanta na tsananta ja hannuwanta na fara rawa ahankali ta bude baki tana kallan Zuhrah dake kallanta tana hawaye masu tsananin rauni da ciwo tace ‘Zuhrah bazan iya rayuwa babu ke ba, Zuhrah na zabi barin duniya tareda dake mu tafi mu huta….. Girgiza kai Zuhrah tayi hawayenta na tsananta jikinta a sanyaye tace ‘Abaas fa?’ ‘Allah zai zama gatansa amma a yanzu da kike tare dani bazan iya rayuwar da babu ke ba Zuhrah’ Kuka Mara sauti Zuhrah ta sake tana kokarin zare hannunta daga na Ayanaah din tace ‘Sbd ki rayu tare dani din zan zabi hakan, Inason ki rayu Ayanah ki samu rayuwan da zai baki nutsuwa dan hakanne dole zamu zabi raba jini, Kina raye Ina raye muna Masarauta daya muna shakar Numfashi guri daya insha Allah zamu samu yancinmu wata rana mu tafi tare’ Girgiza kai Ayanah tayi da karfi tana sake riqe hannun Zuhrah tace ‘Zuhrah idan muka zabi hakan mun rabu kenan har abada,muna guri daya amma bazamu taba nuna mun san juna ba bare Hadin jini, Bazamu taba sake jin dumin juna ba, Bazamu taba kallan juna ba, Bazamu taba dawowa Ayanah da Zuhrah GHAZ ba shikenan mun rabu har abada sai kuma ranar da Allah ya bamu yanci Kinsan da hakan? Wannan shine doka da qaidar kuma taka hakan a bakin rayuwarka kenan,bazan iyaba Zuhrah.’ #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 23 FREE CLASS ALERT 07068433198 Kinason business dinki ya zama tamkar kamfani me zaman kansa, Kina da kaya ko sabis Amman tallanki baya Jan hankali? Mutane suna ganin tallanki Amman basa saye? Lokaci yayi da Zaki koyi yadda ake vedio advert mai daukar hankali da kawo kwastomomi🥳🎉 Shiga wannan FREE CLASS ki koyi yadda ake hada vedio da zai juya masu kallo zuwa kwastomomi🎉 ********** Sakinah data yadda da indai zasu rayu gwara su hakura din matiqar sunsan suna guri daya yafi a san sunada alaqa tin anan gurin a kashesu a banza kokuma a rabasu duniya daban daban gwara su tsaya guri daya koda babu abinda zai sake hadasu har abada dan haka hannuwansu ta Kama da hannuwanta biyu ta rabasu da karfi Zuhrah na Wani irin kuka Mara sauti zuciyarta na mutuwa a matakin karshe na shikenan. Ayanaah ma wani irin kuka takeyi mata sautin tana kasa dauke idanuwanta daga Zuhrah wadda itama ita take kalla sakinah ma hawayen takeyi tana sunkuyar da kanta qasa. Layi na zuwa kansu sunansu AYANAAH GHAZ da ZUHRAH GHAZ Ana tambayan alaqarsu Ayanah ta dago jajayen idanuwanta da suka rine gabaki daya ta zubawa Zuhrah wadda ta goge fuskanta tas ta bude baki tace ‘BABU ALAQAR JINI sunan ne iri daya’ Tana fadar haka take aka buga stamp a sunayensu tareda wata irin stamp ta daban wadda take bada tabbacin ko a toilet daya tsautsayi ya hadasu a kashe dayansu abar daya sbd kawar da zargi hakama duk ranar da dayansu ya kalli daya shima hukuncin daya ne. Miqa musu Id cards nasu akai tareda jansu zuwa ciki Wanda kowannensu babu abinda yake aiki a gangar jikinsu Bayan kafafunsu dake jansu kaman marasa lakka a jiki. Hawaye ne masu tsananin zafi suka gangarowa Ayanah tanajin kusan komai nata na Dena aiki tanason dagowa tayiwa Zuhrah kallan karshe amma damar ta qare hakama itama Zuhrah Ayanah takeson kallan ba damar ta qare sedai hawaye suka sauko mata ta rufe idanuwanta tana bin inda ake tafiya dasu hanya daban da wadda aka tura Ayanah da sakina. Duk Taku daya da Ayanah ke yi jin takeyi tana rabuwa da ruhinta sbd a yanzu kam takai matakin karshe na rasa komai nata batada Sauran hasken da idanuwanta zasu gani ko miskala zarratan, Rawa kafafunta keyi zuciyarta na kasa wa sbd bazata iya rabuwa da Zuhrah ba koda hakan zai rabata da rayuwanta ta yadda dan haka ta dakata ahankali daga tafiyan datake, Dagowa tayi ahankali zata juya ta kalli Zuhrah koda hakan zaiyi sanadin rayuwanta, Da sauri sakinah dake bayanta ta riqeta cikin nutsuwan da bazata bari a gane su ba ta hanata Juyawa sbd bazata iya barinta Juyawa ta rasa rayuwanta kokari da sadaukarwar Zuhrah ya tashi a banza, Wasu hawayen ne masu tsananin zafi suka cigaba da gangarowa Zuhrah wadda itama bata juyoba tana Jin ciwo da radadin halinda Ayanaah take a jikinta, Sakinah ce ta iya waiwayowa a hankali ta zubawa Bayan Zuhrah dake tafiya jikinta na bayyanarda gap take da samun bugawan zuciya, Tausayinta ne ya rufe zuciyar sakinar sbd ita zata rayu bateda duk Wanda rayuwarta ta taba sani ba dan gwara Ayanaah din ita tana tareda ita, Koma menene tasan wannan ma wata sabuwar jarabawar ce Allah zaici gaba da jarabtarsu da ita, Ahankali ahankali aka gama rabasu zuwa bangarori da dama Wanda sai da aka kuma daukansu cikin wasu motocin aka isa dasu can ciki inda duniyar boyem take, Tsari da yanayin gini da aljannar duniyar dake cikin Masarautar boyem ya wuce tinanin duk wani labarin daular duniya da ake bada labari da tarihin Masarautu, Tamkar suna tafiya baa cikin duniyar ba haka suke jin kansu sbd koina da ake giftawa dasu madubai ne suke ganin kansu a ciki suna daukan idanuwansu dan haka tsoro duka ya cika su suka sake saukar da kawunansu a qasa suna kama jikinsu dake rawa sbd tsoro suna tattaro nutsuwarsu sbd itace gaba a komai na aikinsu. Kai tsaye sabon bangaren bayin dake cikin masarautar aka kaisu aka basu daki shima kamar wancan da suka Baro daular bayi sedai wannan Mutum uku uku ne a daki. Duniyar da aka jefata daban data Zuhrah sbd tsakanin bangare da bangare akwai yar tazara da kuma tsaro sosai dan haka ita kai tsaye ita bangaren imebētiś aka kaita Wanda yake duniya ce guda mai zaman kanta wadda take dauke da part part sun kai hamsin duka na imebētiś ne maana mistresses na sarki, Duk macen da sarki ya kwana da ita indai ta samu ciki anan zaa bata flat dinta mai shegen kyau da wata irin daula a cikinsa tareda bayi sama da goma wainda sun zama nata zatai rainon cikinta anan ta haihu anan ta reni jini boyem cikin jin dadi da daular da hankali ma bazai daukaba kuma anan zataci gaba da rayuwanta da bayinta cikin jin dadi da yanci har sai jinin BOYEM data haifa ya girma ya kai shekaru goma sha biyar shikenan zaa ware masa nasa muhallin daya zarce tinani acan cikin asalin ginin da sultan yake a zuba masa bayin ya koma can sedai Yazo gaida mahaifiyarsa kokuma ita taje gurinsa. Duk macen da sarki ya kwana da ita kuma bata samu ciki ba bangarensu daban bautar suke komawa sedai Ana sauya musu guri a cire su cikin asalin bayi, To Ayanah a cikin bayin dake kulawa da sabuwar imebētin sultan aka kaita itada sakina ita kuma Zuhrah a can asalin bangaren uwargidan sultan aka kaita dan haka sukaiwa juna Nisan da babu ranar cike gurbin. Tinda suka iso dakinsu Neman somewa Ayanaah keyi sbd halinda tashiga na rabuwa da Zuhrah daqyar sakina ke kokarin bata taimakon daya hanata somewan sedai har tsakar dare tana fama da ita kafin Allah ya kawo mata dangana ta sakawa kanta karfin halin hakura. Washe gari tinda asubar fari suka shirya cikin uniform dinsu tsaf suka fito zuwa aikinsu, Kai tsaye bangaren sabuwar imebetin suka isa su shida ne dan haka suna isa suka bude suka shiga kai tsaye kowannensu ya fara hidimarta tin kafin ma ta tashi. Ayanah aikin gyara toilet tayi tareda wanke Kayan wankin da ime din tayi amfani dasu ta wanke su sosai da hannuwanta batareda ta saka washing machine ba duk da an koya musu komai da yanda zasuyi amfani da koman a gurin karatunsu, Tana gamawa sake gyara toilet tayi ta hada mata ruwan wanka masu dumi sosai da Kayan qamshi masu dadi na wanka Wanda duka shima an koya musu dan kusan babu abinda baa koyar musu ba komai kankantarsa, Tana gamawa ta koma bakin toilet din ta tsaya kanta a qasa tana jiran farkawanta, Tsayuwan mintina talatin tayi kafin ta fito daga cikin makeken lafiyayyan gadonta mai rumfar dataji ado da dukiya. Tana qarasowa ko amsa gaisuwan da Ayanah din tai mata bataiba ta zare rigar baccinta ta Sama ta Bari a gurin tareda shigewa toilet din daya gama tsaruwa, Sunkuyawa qasa Ayanaah tayi a natse ta dauke rigar data zare din tana barin gurin ta kai rigar inda Kayan wanki suke ta dawo ta isa inda towels suke sama da guda ashirin ta dauko guda uku harda na goge kai suna wani qamshi me sanyi ta dawo bakin kofar ta tsaya da towels din. Tsayi me tsanani tayi a gurin batareda ta motsa ba duk kuwa azabar datake ji ta tsayin hakan take a tsaye kanta a qasa har tsawon lokacin da batasan Yaushe ne ba tukuna ime din ta bude kofar toilet din Wanda Ayanaah tayi saurin miqa mata towel din farko ta amsa ta daura a jikinta kafin ta sake bata wani t rufo jikinta kafin na ukun ta Dora akai dan goge kanta. Tana wucewa gaban mirror Ayanah ta fada toilet din ta sake gyaresa tsaf ta qamar da ruwan toilet din tsaf duk kaman ba yanzu aka fito wanka cikinsa ba. Tana gamawa ta fito tana gyara dakin da gadon dakin sakina da wata baiwar daya suka shigo suna busar mata da gashinta tareda gyarasa tana zaune tana kallan kanta a madubi. Tsawon lokaci suka dauka suna hidimarta kafin suk kammala ta fito cin abincin da Sauran su suka dafa mata sama da Kala daya ta zauna suka zagayeta kowannesu da abinda yake mata. Har dare suna tsaye kan kafafunsu basu zauna ba Bayan sallah babu abinda sukeyi sai hidimarta wadda bata qarewa. Sai tsakar dare sosai suka koma daki Bayan tayi bacci, A tsananin gajiye suke dan haka komai babu Wanda suka iya yi bacci suka buge dashi mai karfin gaske, Asubar fari aka buga qararrawa tashi yake suka fito sukai ayyukan bangarensu na bayi har lokacin sallahn asuba yayi sukai sallah sukai wanka tareda shirya wa suka fice ayyukansu na iyayen gidansu. Kaman yanda sukai jiya yauma haka suka wuni suna aikin wahala da bauta babu sukuni abincin da sukeci ma a tsaye suke cinsa ba yancin zama. ****farkon wannan wahalar da suka samu kansu a cikinta na bautar da babu Hutu ko kadan dan Baka isa kayi bacci ba sai Wanda kake bauta wa yayi nisa sosai a nasa baccin, Farko farko kafin su Saba sosai suke jin jiki amma ahankali ahankali suka saba da wahalar wadda ta zama jiki har basa jin komai, Kaman computers haka suke da aiki ba mantawa ba kuskure a natse, Watanni hudu kenan yanzu a zamansu cikakkun bayin boyem da suka Riga suka saba da tsantsan na masarautar da dokokinta ba kuskure ko daya, Idan aka hada da watannin da sukai a daular bayi kusan wata bakwai kenan a BOYEM Wanda yayi daidai da shekara guda harda wata daya rabon su iyayensu, Tsawon watannin nan babu ranar da Ayanaah bata baqin ciki da quncin rashin Zuhrah, A kowane motsi da numfashinta babu abinda ya rage na rayuwar baqin ciki da quncin datai tareda rashin yan uwanta a tareda da ita, Sakinah ce kadai zata iya shedar da qunci ne zallansa a daddabe da zuciyar Ayanah amma a bayyane ta rungumi kaddarar datake cikinta. Ime dinsu da suke bautawa kwatsam Allah ya azurtata da samun cikin daya saka aka yayeta daga zuwa shimfidar sarki sai kuma idan ta haihu idan tanada rabon ya sake kwanciya da ita kenan. Yayeta da akai ya saka dukkanin bayi shiga fargaba da tsoron sabbin imebētin da zaa zabar wa sarki Wanda a yanzu baya qasar kafin dawowansa zaa kuma zabar sabbin imebētin da zai huta dasu dakyau idan ya dawo. #MAMUH #ROYALTY #AYANAH GHAZ #NUAB BOYEM HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 24 Duk damuwa da fargaba da duka kyawawan bayin dake BOYEM ke dan shiga da tsoron sabbin imebētin da zaa zaba Ayanah bata taba ma San da hakan ba sbd bama huriminsu ne na shiga ba dan kuwa tasan a cikin sama da mata bayi sama da dubu dake bauta a masarautar bama sa cikin wainda zaa iya gani bare sani tinda suna bangaren imebētis din sarki suna bauta basa can bangaren matansa biyu da bayansu bai taba qarawa ba. Dan haka bautarta kawai takeyi babu tinani kowane iri a zuciya da rayuwarta Bayan na ‘yar uwarta datake azabtuwa da rashinta a kowane daqiqa, Tinda ta rabu da Zuhrah bata taba jin sassauci na rashinta ba ko kadan a zuciyarta Wanda bama ita kadaiba kowace daqiqa tana wuce mata ne da tsananin ciwo da quncin rashin Nurat da Abaas da Zuhrah din, Suna tsananin so da kaunar iyayensu amma yanda suke tsananin son junansu da irin gwagwarmayan da suka shiga ya saka suke jin mummunan ciwon rashin junansu fiyeda Zafin rashin iyayensu, A nata zuciyarma gabaki dayansu a cikin jininta yake jinsu tamkar itace ta haifesu din da gaske sbd uwar data zama garesu musamman Nurat datake ambatarta da AMMAH kafin rasuwarta, Ciwon rashin ‘yan uwanta da sune rayuwanta bazai taba barin zuciya da ruhinta ba har abada,da wannan ciwon zata mutu idan ma ba ciwon rashinsu bane zai zama ajalinta sbd a yanda takeji babu wahala ko azabar da bazata iya dauka ba amma ciwon rashinsu abu ne da zuciya da gangar jikinta bazai taba dauka ba musamman irin rasuwar da Nurat tayi. Rayuwanta a Masarautar BOYEM bata taba sakewa ko sabawa da kowa ba Bayan sakinah wadda take tsananin kulawa da ita idan suna daki sbd tsoron bugawan zuciyarta datake riqe da abubuwa da dama ta kasa saki ta kuma kasa fada Bare nunawa, Cin zuciyarta damuwa da quncin sukeyi Wanda suke bawa zuciyarta illa ahankali batareda saninta ba dan haka sakinah batada damuwa itama a nata rayuwar yanzu Bayan ta Ayanah din, Itama sakinah ko a mafarki ma bata taba saka kanta a lissafin da wasu bayin keyi na shakka ko tsoro sbd ko zasuyi shekaru dari a BOYEM babu ranar ma da ko bawa irin su zai iya cewa yana shaawansu bare me qasar da kansa duk da bai taba zaben macen dazai kwanta da ita ba da kansa duka wannan aikin shugabar jakadan qasar BOYEM ce gabaki dayanta wadda take Zaune cikin masarautar itama da nata bayin sbd babu me matsayi dake Masarautar BOYEM fa baya cikin nasa jin dadin da daula me girma tareda tarin dukiya. Meleketen’ya wadda ake kira da Ten’ya wato jakadiya da yarensu itama matsayi ne da ake gadonsa sbd tin kakanni da shekarun da suka gabata jini daya ne suma suke riqe wannan matsayin dan haka shima matsayi ne me girma da iko dan kuwa duka bayin dake cikin asalin masarautar BOYEM a karkashin iko da umarninta suke yawo da aiki, Hakama tenya din itace me kulawa da dukkanin abinda ya shafi sirri da babbar buqatun matan sultan da ‘yayansa wainda suke jininsa, SULTAN YASAR ALMAZ BOYEM shine Sarkin Boyem da ikonsa yake zagaye da kusan fiyeda Rabin daulolin dake duniyarsu, SULTAN YASAR sarki ne da mulkinsa yakeda tsananin zafi da karfi tareda tsananin doka da ikon daya saka ko dabbar masarautar shakkar laifi takeyi sbd hukuncin dayane fa Mutum ga dabba wato cire kai kawai dan haka a cikin tarihi yana cikin sarakuna masu Zafin gaske da akai a BOYEM, Sultan YASAR yana daya daga cikin sarakunan jinin BOYEM da su keda abubuwa da dama da suka Zarrah na kowa a tarihi dan hakanne shima yayi Wani irin sunan da sunan BOYEM yake sake gauraye duniya, Sultan YASAR yana tarin dukiyar data qara Habbaka dukiyar Masarauta duk da asalin BOYEM sunada da wasu irin arziki wadda basa talauci Allah ya gama bude musu kofofin arzikinsa tin asalinsu babu talaka ko daya hakama su kansu basa sanin tarin arzikinsu sbd yawansa da yaduwarsa, Sultan YASAR yana daya daga cikin sarakunan BOYEM da sukai karatun ilimin boko sosai da Larabci sbd asalinsu balarabiya ce Matar farko ta BOYEM dan haka suke tamkar ruwa biyu amma sunfi maida hankali akan karatu da samun ilimi da yarensu na Amharic da arziv dan haka qalilan ne a cikinsu suke karatun ilimin boko da larabci sosai dan haka sultan YASAR yana daya daga cikin masu bokon hakama yana cikin masu zafi, Bayan duka wainnan sultan YASAR ya sakance cikin wainda Allah bai azurta da samun namiji ko daya ba a tarihin wainda suka mulki kujeran BOYEM, ‘Yayansa duka mata ne suma kusan duka imebētinsa ne suke haifar masa su, Matansa biyu rak suma aure ne da kaman Alkawari da ake wa kowane Sarkin daya hau mulkin dan kuwa su biyun jinin BOYEM ne suma auren gida ne duk da bama qasa daya suke Zaune ba sai da akai auren aka kawo masa su a rana daya a lokaci daya, Uwargidan itace HAILE wadda duniya take fadar kyauta da kaf BOYEM ba kamarta, Jinin BOYEM ne yake yawo a jikinta itama, A qasar Morocco take rayuwa itada iyayenta a cikin wata irin daula da ikon da mulkin da suke zubawa kafin auren daya kafa tarihi ya dawo da ita cikin BOYEM qasar da kowa ke kwadayi da maitar son zuwa yayi rayuwa a ciki dan haka ita a duniyar babu me saa irin tata samun kanta a matsayin Matar sultan YASAR ALMAZ BOYEM kuma uwargida dan hakanne duniya ke kiranta da HAILE(me power) kenan hakama kaf duniya Bayan bayinta babu Wanda yake da saa ko matsayi ko ikon ganin asalin fuskanta da ake cewa tafi kowace mace kyau sai shi sultan din da kansa Wanda take tsananin so fiyeda komai na duniya da ita kanta, Kishinsa take kaman zata kashe kanta sbd son da take masa yayi yawan daya fita hankali dan hakanne ta ringa haihuwa bata jira sbd son ta haifar masa namiji amma Allah bai bata ba tana Ji tana gani aka ringa wanke masa imebēti masu kyau da daukan hankali Ana kai masa yana kwana dasu, Da farko duk imebētin daya kwana da ita bada umarnin a kawar dasu takeyi sbd zuciyarta bata iya dauka Wanda hakan ya saka bayi da yawa shiga mummunan Hali daga lokacinda aka Zabesu zuwa shimfidar sultan sun San kwanansu ya qare ne a duniya, Abinda ya kawo sauki da sassaucin kishinta akan hakan shine fara samun ciki da sukai suna haihuwan yaya mata kuma babban me mata duba ya sanar da ita itace zata haifawa sultan YASAR ALMAZ BOYEM namiji. Wannan bayanin ya saka ta sassautowa ta kyalesu ta duqufa rokon Allah samun ‘da namiji koma yaya yake ko wane iri ne tanaso hakama tana hada wa da aikin bokayen malamanta masu tsananin karfin gaske. ‘yayanta uku mata wainda sune manyan yayan sultan YASAR wato ASLAM,NEESAT da MERYAM, Sun girma sun zama yan matan da sukafi kowace mace daraja a qasar BOYEM sbd sune arzikin sultan da BOYEM a yanzu tinda sune jinin sultan YASAR ALMAZ na farko a duniya, MARAKI itace Matar sultan YASAR ALMAZ BOYEM ta biyu wadda itama kyauta kusan daya dana HAILE sedai anfi zuzuta na HAILE cin sbd itace uwargida kuma wadda kaman sultan din yafi Ji da ita duk da bawai ya fada ko nunawa bane kawai macen da sarki yafi kwanciya da itace wadda yafi so kenan a cikin matansa ko imebētis dinsa dan hakan na nufin samun cikakkiyar gamsuwa yake da ita, MARAKI batai shekarun HAILE ba duk ba wani shekaru ta bata ba hakama ita MARAKI bata taba samun haihuwa ba kwata kwata Shiyasa batada wani power kaman HAILE amma itama kam duniya ce gida take Juyawa a bangarenta wanda yake dauke da bayin hidima sama da ashirin sbd girmansa da daular datake ciki, A cikin matan sultan da duk wata mace wadda take jinin BOYEM babu wani adon dayake jikinta Wanda ba asalin zinari bane yake motsi a jikinta, Sarkan wuyansu, ‘yan kunnen dake kunnuwansu Wanda a qalla zaa samu huji sama da uku a kowanne kunnen, da zoben hujin dogayen hancinsu na gadon asalin BOYEM, Zobunan hannuwansu da chains na hannu da bangles, Chains na kafafunsu da zobunan yatsar kafarsu da sarkar adon dogayen gashin kansu gabaki dayansu na zinari ne kawai suke amfani dashi sbd basusan kowane irin abin ado ba Bayan na zinari Wanda kaf idan ba a jini da masarautar BOYEM ba babu irin wannan dukiyar,hatta abinda suke rufe fuskan su me kyau adonsa akwai zinari a cikinsa dan hakanne ake zuba asalin mulki da sarauta a BOYEM. A cikin imebētin da suka haifawa sultan YASAR yaya basu fi goma ba dan kusan su kansu imebētin Wanda tenya taji bai mata ba a gurin haifawa sultan yaya tsarin hanasu daukan ciki takeyi, Rashin samun ‘da namiji a masarautar yanzu shine babban qalubale da tashin hankalin da ake ciki Wanda shi kansa sultan rashin samun LEUL BOYEM ne kadai abinda ya taba taba zuciyarsa dake tsaye babu sanyi ko kadan a cikinta, LEUL BOYEM shine kowane sultan daya mulki BOYEM baya da nutsuwa sai ya Haifa sbd shine ze qarasa kafa tarihin mulkinka, Rashin haihuwan LEUL BOYEM na nufin sarautar BOYEM Bayan kai zata koma wani dakin Wanda kai Baka cike tarihinka ba kenan, Babu qasar da bata tsoron yaqi ko tinkarar masarautar BOYEM, Babu sarki ko sultan din da baya shakkar sultan YASAR BOYEM, Babu bawa ko wani Mutum da baisan ransa baa bakin komai yake ba a masarautar BOYEM idan yayi kuskure ko laifi, Babu me mulki ko muqamin wasu qasashen da baya shakka da tsananin tsoron Masarautar BOYEM da sultan dinta YASAR ALMAZ, Babu matarsa ko imebētinsa da basa sunkuyar da kansu a qasa idan yana kusa Amma duka wannan babu babban Buri me tsananin gaske ga sultan YASAR irin samun LEUL, Ya batar da dukiyar da bata lissafuwa ko a gurin masu lissafi gurin sadaka da Malamai gurin adduar Neman haihuwan LEUL Wanda babu abinda bazai iyaba akan ya samu haihuwan Namijin. jamaar qasar BOYEM da masoyanta a tsaye suke gurin addua da biyan malamai wasu harma da Neman manyan bokayen qasashe duk akan Allah ya bawa sultan YASAR magajinsa wato LEUL BOYEM, Duk Wanda yasan BOYEM da Wanda yake cikinta koda bawa ne kuwa yasan da wannan tsantsan burin me girma da karfi na sultan YASAR ALMAZ BOYEM, Wannan shine babban dalilin daya saka ake zabar masa imebēti daban daban yana kwanciya dasu babu kakkautawa sbd Neman haihuwan LEUL BOYEM wato magaji zakin BOYEM. #MAMUH #BOYEM #BEST LOVE #BEST ROYALTY HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 25 Ayanah tana cikin masu kulawa da yanayi na laulayin faree wato imebētin sultan wadda kwata kwata batai farin ciki da samun cikinba sbd yanda taso taci gaba da samun damar datafi mata komai duniya ta zuwa shimfidar namijin dayafi kowane namiji daraja a qasar BOYEM dama zagayenta, A ranta tariga tasan kila itama macen zata Haifa tinda shine baya haihuwan namiji dan haka Sam bata wani doki da cikin gashi matiqar mace na laulayi baa kara kaita tirakarsa sbd baya iya mu’amalantar mace me laulayi sosai dan haka faree sai an yayeta sedai ta jira haihuwa idan tanada rabo zai sake buqatan kwanciya da ita, Wannan quncin da baqin cikin ne a zuciyar faree wadda laulayi takeyi sosai ga qarin baqin cikinta shikenan ta zama macen da har abada bazata sake samun Wanda zai aureta ko kwanciya da ita har sai ranar da sultan YASAR baya duniya dan babu Wanda ya isa yana raye ya kusanci Matar da shi ya kausanta indai ta haifar masa ‘yaya kenan. Baqin cikin dake cin zuciyarta da damuwan hakan ya saka laulayinta yake tsananta bata kaunar kowa ko komai Bayan hantara da kyara da rashin daraja ko kadan babu abinda take yiwa bayin dake mata hidima kaman zasu bata rayuwarsu. Ayanah ma kusan so biyu tana qonewa a hannu da ruwan zafi sbd hidimarta da fadanta, Duk wahalar da Ayanaah Tasha sosai ta rayuwar da suka fito ta qangin bautar kusrah ta wanke sosai lafiyar fatarta ta dawo haskenta ya dawo sosai amma ba duka ba sbd ba lallai ta koma asalin fararta qal ba har abada kila, Tsayin gashinsu ya dawo sosai duk da akai akai ana yanke musu tsayinsa sbd tsafta baa wani son tsayin gasu sosai a gurin bayi dan haka duk Bayan watanni kadan ake yanke musu tsayinsa bawai aski ba kawai dai zaa yankesa baa son ya wuce iya wuyansu ya sauka kafada zuwa bayansu. Gashinta ya dawo sosai da tsayinsa gashi lokacin yanke musu baiyiba dan haka take dunqulesa sosai a cikin hularta ta uniform, Faree dukkanin bayin dake mata hidima kyawawa ne sosai bama kaman ita Ayanah din wadda sanyinta da nutsuwanta ke qara mata kyau da burgewa, Faree jin tayi duk ta tsanesu bata ko kaunar ganinsu dan idan kaddararsu me kyau ce ko a cikinsu zaa iya zabar imebēti koma dukansu zaa iya zabarsu, A duk lokacin data gansu tafasa da ciwon rai zuciyarta keyi dan haka ta dauki hanyar illatasu a cikin dabarar da bazaa taba zabarsu ba, Hakanne ya saka so biyu tana kokarin koma Ayanaah da ruwan zafi sedai Allah bai saka ta taba samunta a Fuska ba sedai hannuwa kuma har so biyun babu inda fatar Ayanah tayi tabo sbd matiqar kanada tabon daya wuce numbernk ta Shedan bauta dake jikinka to Ka haramta ga zama imebēti. Ayau ma umarnin su hada mata ruwan wanke kafa tayi su dukan haka suka hada ruwan mai dumi daidai yanda zai mata daidai a fata suka kawo suna ajiye a gurin hutawanta dake dan madaidaicin American garden dinta dake nan cikin bangarenta, Tamkar wadda zatai wata gagarumar hidima haka aka tsara mata gurin suka shirya mata komai daidai yanda zata Ji dadin hutawan da wankin kafar da zaayi mata, Ayanah da sakina ne biye da ita kansu a qasa a lokacinda take fitowa tana isowa gurin Ayanah na dauke da wani lallausan showel din lullubawa mai tsananin taushi Wanda idan iskan gurin yayi mata yawa zaa rufa mata, Sakinah kuwa wasu towels din da zaa goge kafafun ne idan an gama a hannunta suma masu Laushi suka qaraso, Zaunawa tayi dukansu suka koma bayanta suka tsaya Sauran masu wankin kafar kuwa suna durqushe gabanta suna jiranta, Farawa sukai ta jingina bayanta jikin lallausan kujeran tana Lumshe idanuwanta, Tray din tea mai Zafin gaske aka kawo mata da snacks din da yanzu ne akai mata su da Zafin su aka kawo aka ajiye gabanta, Zuba mata tea din akai yana wani irin siracin daya sakata zubawa hannun wadda ke zuba mata din idanuwa tana kallan yanda zara zara yatsun hannunta farare tas ke daukan ido take taji wani irin abu ya taso ya danne zuciyarta batasan lokacinda ta dauko ruwan tea din gabaki daya ta watsa musu su hudu dake gabanta ba duka a Fuska tareda wurgi da Kayan gaban nata tana jin Wani irin Zafin zuciya kaman zai kasheta. Cikin tsananin azabar data ratsasu har cikin qwaqwalwa suka sauke kansu qasa batareda sun zabura ba ko magana bare nuna halinda suke ciki sedai idanuwansu sukai jajir suna sake sauke kansu qasa tareda bata hakuri akan abinda ya bata ranta. Ayanah ma qasa suka sake yi da kansu cikeda wani irin sanyin jiki batareda sun motsa ba, Cikin zafi da faree ta bude baki tace ‘Ina buqatar wani shayin ganye’ Miqewa sukai a natse suka bar gurin dan hado mata wani. Suna barin gurin sakinah ce ta zagayo gabanta ta durqusa itada Ayanah suka fara wanke mata kafafun cikin nutsuwa da tattali kaman kafar zinari. Suna cikin yi aka sake kawo mata sha yin ba Imani ta sake zubawa su Ayanah dake gabanta Wanda sakinah dake gefen Ayanah tafi samun ruwan sosai sbd dan karewa Ayanaah datai batareda lurar faree din ba dan haka suma take idanuwansu sukai jajir Wanda ya tabbatarwa da faree wannan Karan kam ta gama da bayin bangarenta babu wadda zaa iya zaba a cikinsu sbd duka konuwarsu a Fuska ne indai ta tashi to tabbas sun haramta har abada. Hakan data ga ta samu ya sakata samun sassauci da sakewa hankalinta ya dan kwanta ta koma yar walwalarta. Su kuwa gabaki dayansu su Ayanah kusan ruwan sun kona fatarsu sosai musamman sakinah wadda har wuyanta saida konuwar ta dan tashi dan haka kwana Ayanah tayi bawa sakinah kulawa sbd ita iya ruwan da suka sameta basu wani Konata ba ja kawai gurin yayi kuma koda gari ya waye jan ya rage kuma a kirjinta ne dan haka baa gani. Haka suka shirya suka taho aikinsu kowa gefen Fuska da wuya a kone ga zazzabin azabar wutar ga radadi haka suke aikin. Kwana biyu konuwar tayi ta dan caccabe haka dan haka faree ta sake samun nutsuwa suka ci gaba da hidimarsu, Sakinah da Ayanah take kulawa da ita sosai idan sun koma daki sai tata wutar ta Riga ta Sauran warke wa amma ba kwata kwata ba gashi kusan sati biyu kenan suma Sauran tasu ta warke sama sama, Tsoro biyu ne damuwa biyu take cinsu akan konuwar sbd idan ranar zabar imebēti tayi aka sameka da tabon dayake sabo ba tsoho ba to tabbas kanada hukunci me tsauri dan hakan yana nuni da sakacinka dan kuwa ko yancin raunana Kanka baka dashi sam tinda jikinka ma ba ikonka bane dan haka suke cikin tsananin tsoron hukuncin hakan. ********A daren ranar da zaa tara bayi mata kaf kwana Ayanah tayi Zaune itada sakina cikin wata irin damuwa da sanyin jikin hukuncin da sakinah zata iya karba na qaton tabon konuwarta, Dukansu damuwansu daya ne kada a sauyawa sakinah guri a cikin hukuncinta a rabasu, Ta Dayan bangaren kuma acan qasan zuciyar Ayanah dake sosuwa sosai da qunci shine inama itace ta kone din, Basu wani rintsa ba da damuwa me nauyi da sanyin jiki suka gama komai suka fito zuwa aikinsu. A kaidar zabar imebēti daki daki ake bi dan haka Layi bai iso bangaren imebēti faree ba Sai dare Wanda tenya ce da kanta tareda bayinta kusan su goma biye da ita cikin nutsuwa da taqama da wani irin kwarjininta ta iso take dukansu suka zube qasa hadda faree wadda itama kanta yake qasa sbd ten’ya kwarjininta nada nasaba da matsayin datake riqe dashi na ita kadai ce takeda power ta zabawa sultan macen dazai kwanta da ita,ita kadai ce takeda power ta zabar wadda zata iya daukan cikin sultan ta haifar masa ‘yaya kuma itama tanaji a jikinta insha Allah a cikin zabinta ne zaa samu macen da zata kafa tarihin haifar LEUL na wannan zamanin dan hakanne ma wannan Karan mata shida zata zabar masa lokaci daya yana dawowa saiyayi sati kullum yana Bare sabuwar mace. Kai tsaye idanuwanta ta sauke akan fuskokinsu zuwa daya bayan daya tana binsu da kallan nutsuwan da kyau ne zalla take gani a tattare dasu sedai kowacensu babban tabo ne a Fuska,wuya da hannuwansu, Batace komaiba ta zubawa faree ido tana karantar yanayinta kafin ta maida idanuwanta akan tabonsu dayake nuna wuta ce a jikin kowannensu, Kyansu ta sake kalla da kyau take ta fahimci komai ta tabbatarda meya faru dan haka kai tsaye akan Ayanah ta tsayar da idanuwanta wadda kanta ke qasa. Cikin bayinta ta kalli daya kai tsaye wadda ta fahimci me take nufi take ta matso gurin Ayanah ta saka hannu ta zare Hular kanta gashinta dayake dunqule take ya zubo ahankali yana sauka a bayanta. Faree da kanta ke qasa har lokacin wani mummunan yawu ta Hadiye zuciyarta na harbawa da karfe sedai kafin su dake jan Numfashi su fitar take ten’ya ta kalli Ayanah ta bude baki tace ‘Tashi ki bisu’ Ayanaah da bata gane me hakan ke nufi ba miqewa tayi ahankali tareda bin Bayan bayi biyu da akace ta bi tana adduar kada hukuncin da zaa yiwa su sakina daya saka akace ta tafi yayi tsauri. Tafi me dan tsayi kadan sukai suka isa wani babban guri nai shegen kyau da tsari Wanda a cikinsa zaa yiwa duk macen da aka zaba gyaran fitar hankali na ciki da waje na wata daya. Tana saka kafarta cikin gurin taga mata a jere tsaye gabanta yayi mummunan faduwa ta tsaya cak tana kallan gurin da idanuwanta Wanda ke fahimtar da ita menene yake shirin faruwa a gurin. Kasa daga kafarta tayi sbd toshewan da kanta ke Neman yi ta juyo ahankali ta kalli wainda suka kawota zatai magana numfashinta ya dauke cak bakinta ma kafewa yayi komai nata ya Dena aiki ya tsaya cak sbd idanuwanta da suka sauka akan Zuhrah da aka shigo da ita itama…… #MAMUH #BEST ROYALTY STORY #BEST LOVE #LOVE/ROMANCE HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 26 *_UMMU ASLAM COLLECTION_* 08035014107 -Ina mata yan kwalisa masu son burgewa? -Shin Kayan kitchen na zamani masu sauki da rahusa na kitchen din yan gayu dama na gargajiya kike so? -shin abayas na yayi da daukan ido da burgewa kike nema? -kokuwa original misk dahara kuke buqata dan asali? -kokuwa Kayan GHT na Neman lafiya da gyara kike so? -ke harma laces da atampopi na alfarma masu sauki kikeso? To duka kinzo gidansu indai sune abinda kike buqata ba bata lokaci kinzo kin gama samu kawai tintibi UMMU ASLAM COLLECTION 08035014107 duk inda kike zata aika miki. *********** Dauke wuta kafafunta suma sukai maqoshinta na wata irin bushewa qayau yawun bakinta suma suka dauke, Wani yaji yaji taji yana cike idanuwanta sbd tashin hankalin da baida ‘dan uwa a gareta, Zuciyarta kuwa harbawa take a kirjinta da mugun karfi da wani irin rauni dayake gauraye gangar jikinta na ganin Zuhrah Ayau cikin idanuwanta a Karan farko Bayan rabuwarsu kusan shekara guda, Ayau idanuwanta sun samu haske da rahamar da suka rasa, Ayau zuciyarta ta samu abinda ta rasa na haske da bugawa daidai Bayan shekara guda, Ayau dukkanin duhu da yanar dake zuciyarta sun haskaka da ganin gudan jininta ruhinta Zuhrah wadda itama Zuhrah dake cikin tsananin qunci da baqin ciki komai nata sakewa yayi da ganin Ayanaah dinta rayuwarta,kuzarinta,gangar jikinta,bugun zuciyarta harma ganinta sbd a tsawon wannan lokacin ita ko na minti daya bata taba walwala ko farin ciki ko misqala zarratan sbd da gaske Ayanah ce rayuwarta hakama bata tareda kowa da zai kaunace ta ko kulawa da ita ko Wanda zatai wa magana ko kalla taji sassaucin komai ita kadai take rayuwarta babu kowa a cikinta Wanda hakan ya taba rayuwarta da zuciyarta sosai harma da kanta sbd babu abinda take ako Yaushe koda da dare ne Bayan zubawa guri daya idanuwa tana ganin duka ahalinta a idanuwanta ba kamar Ayanaah ba datake tareda Sakinah, Ganin Ayanah a gabanta yau cikin idanuwanta ya gama cike dukkanin gurbin matacciyar zuciyarta da bugawa kadai takeyi babu abinda ya rage a cikinta, Ganin Ayanah Ayau ya farfado da rayuwarta dake gap da barin duniya sbd tana cikin tsananin qunci da azaba sbd a inda take babu sauki ko kadan ta rame sosai tayi Wani irin fayau alaman kowane lokaci ciwon dake zuciyarta zai buga zuciyarta ta tafiyarta itama, Kokarin gazawa kafafunta sukeyi dan mutuwan da duka jikinta keyi yana sanyi amma a hakan take daga kafafunta ahankali tana tako wa ahankali sbd wainda suke tareda ita, Qasa tayi ahankali da idanuwanta a daidai lokacinda suka iso gurin da su Ayanaah din suke tanajin zuciyarta na Wani irin yanka da radadin dayafi na kullum babu abinda ruhinta da gangar jikinta da zuciya ke tsananin so a lokacin Bayan jin jikinta dana Ayanaah ya hadu sun rungume juna sunji dumin juna sun Ambaci sunan juna sun Shafa fuskan juna sunji muryoyin juna, Da zata samu hakan tabbas da ciwon dayake cin zuciyarta zai warke koda kuwa warkewan tafiya ce to tabbas zata so hakan, Ayanaah ma da zuciyarta ke wata irin bugawa kaman zata faso kirjinta ta fado sbd tsananin so da kaunar yar uwarta daya taso mata ahankali ta sauke kanta tana Jin kowane sautin takun Zuhrah na sauka kunnuwanta yana dukan kirjinta a lokacinda suke kokarin wucewa ta gefensu sunaji suna gani kowannensu ya sauke kansa daga kallan junansu, Rintse idanuwa Ayanah tayi ahankali wani radadi na sake cikesu suna yin jajir duk abinda ta juyo tayi magana akansa bace wa yayi daga kanta da tinaninta sbd ganin Zuhrah Ayau ya tsima duka abinda take danne wa da jurewa, Kamannin Zuhrah dinta sun sauya sosai ta koma tamkar ba ita ba duk da tayi haske sosai amma babu abinda kai tsaye yake bayyane a jiki da fuskanta sai damuwa da qunci me tarin yawan gaske da tabbas zata iya rasa ranta da bugawan zuciya, Bude idanuwanta tayi ahankali radadin cikinsu na qaruwa tanajin takunsu har lokacin a bayanta suna tafiya suna nisantar ta. Rufewa idanuwanta da zuciyarta sukai babu abinda take so Bayan sake saka Zuhrah a cikin idanuwanta dan haka ahankali ta juya batareda karfin jiki ba ta nufi cikin itama tana mantawa duka kwata kwata da abinda yasa aka kawo su gurin, Taku sukeyi suna qarasa shiga ahankali a bayansu Zuhrah din Wanda Zuhrah na jin sautin saukar kowane takun Ayanaah din dake bayanta yana karya zuciyarta tana jin a daidai wannan lokacin ma Allah ya cika mata burinta tana taka guri daya tareda Ayanah tana shakar numfashin guri daya da Ayanah,jajir idanuwanta sukai itama tana ci gaba da taku mai sanyi batareda alaman ko juyowa ba kaman yanda itama Ayanah bata dago kai ba kanta a qasa yake tana bin sawun da Zuhrah ke wucewa da idanuwanta kaman ta durqusa ta sumbaci gurin, Ciki gabaki daya inda wani fadeden gurin gyaran jiki da wankan asalin lalle da qamshi dayake cike da pool din ruwan dumi da har wani hayaqi me qamshi yake tashi a cikinsa, Su tara ne cif aka zaba dan haka duk wadda aka shigo da ita ahankali ake tayata zare Kayan jikinta ta shiga ruwan Lallen da qamshi masu dumi Wanda zaa jiqa su a cikinsa tsawon wuni guda kullum haka zaa musu tsawon kwana uku sbd lalle yana tsotsewa da kashe kowace irin cuta dake jikin dan Adam dan haka sai an riqa jiqa su tsawon kwana uku sun rabu da kowace irin cutar wahala dake jikinsu tsaf kafin a fara jiqasu cikin ruwan madarar nonon raqumi shima. Zuhrah dake gaba bayin dake tareda ita ne ahankali suka zare mata Kayan jikinta daga ita sai kamfai irin na jikin kowa Wanda ake raba musu tareda uniform sai qarama rigar halfvest datake kame nonuwansu qarama ce sosai, Kama hannunta sukai suka isa bakin pool din da ita suna riqe da hannuwanta duka biyu ta zura kafafunta ahankali ta shige ruwan idanuwanta da zuciyarta babu inda suke Sai a tinanin Ayanaah dake bayanta wadda itama ahankali aka zare mata nata Kayan take gashinta ya sauka bayanta aka sakota cikin ruwan ahankali ta tako ta iso gefen Zuhrah wadda itace karshen shiga ruwan a tare suka zauna cikin ruwan ahankali gabaki daya jikinsu na shigewa har zuwa sama kirjinsu iya inda ruwan ya tsaya kenan. Wata Mutum daya ce aka sake shigowa da ita ta karshe kafin aka taho da wani sabon lallen mai dan yawa aka zuba a cikin ruwan tareda ruwan zafi dazai qarawa ruwan nasu dumi sosai ta yanda lallen zai ratsa koina a jikinsu sosai. Ana gama zuba musu komai Juyawa maaikatan sukai gabaki dayansu suka fice daga gurin tareda rufe kofar suka tsare bakin kofar sbd bazaa taba budewa ba sai lokacin fitowansu ruwan yayi. Daga Ayanah har Zuhrah babu tinanin dayake ransu Bayan son kasancewa a tare daidai wannan lokacin tareda son jin junansu dan haka gabaki daya sun manta da mummunan qazamin lamarin daya sakosu gurin fatansu daya kawai su kasance tare. Shiru gurin yayi kowacensu su taran da abinda yake ranta na wannan nannauyan kaddarar data hau kansu, Ratsasu ruwan dumin lallen keyi tako Ina suna jin dumin me zafi har cikin zuciyarsu sbd tsoron d suke ciki yafi komai yawa a cikin zama imebēti sbd kowane lokaci zasu iya rasa rayuwarsu dan haka kowa shiru yayi jiki a sanyaye ba kowane irin dogon motsi. Ayanaah ce ta bude idanuwanta da sukai jajir ahankali batareda ta juyo gefenta ba ta kalli Zuhrah da suke shaqan Numfashin guri daya ta miqa hannunta dake wata irin rawa sbd shauqin samun abinda zuciya ke so ta cikin ruwan ta Dora tafin hannunta ahankali kan na Zuhrah wadda tana jin saukan hannun Ayanah a kan fatar hannunta rintse idanuwanta tayi wasu hawaye masu tsananin zafi na gangarowa daga idanuwanta kanta na yin qasa ta damqa hannun Ayanah din tana qanqamewa cikin nata hawayenta na tsananta gudu cikeda shauqi da tsananin farin cikin data manta yaya dandanonsa yake a zuciya, Itama Ayanah hawayen ne ke ciko idanuwanta da sukai jajir tana hana nata hawayen sauka sbd kada a gano halinda suke ciki sedai tata zuciyar harma tafi ta Zuhrah karaya da samun wata irin nutsuwar ruhi da bata taba samu ba tinda rayuwarsu ta wargaje, Qanqame hannun juna sukai batareda sun juyo sun kalli juna ba ko motsin da zaa gane kowa da abinda yakeji a zuciya da gangar jiki, Zuhrah kuka takeyi sosai tana sake sunkuyar da kanta qasa sosai tana rokon Allah kada ya raba hannunta dana Ayanah har sai ranta yabar jikinta. Ayanah ma da kukanta ke komawa zuciyarta kukan zucin takeyi sosai jikinta na wata irin rawa tana sake qanqame hannun da shine hasken rayuwarta. A wannan yanayin suka share duka awannin da aka dibar musu a cikin ruwan har saida ruwan ya wuce salap suna cikinsa tukuna aka bude kofar tareda shigowa da wasu irin tsaftaccin towels masu dan girma farare qal a basket me kyau kowannensu da baiwar da zata basa nasa. A cikin wata irin saa me girman gaske saiga sakinah a cikin masu kawowan wadda kai tsaye gurin Ayanah ta nufa a natse kanta a qasa tana isa ta durqusa gaban a hankali tareda dago mata kyakkyawan kwandon da towel din yake ciki yana fidda qamshi me dadi. Cikin karfin Hali zuciyarsu na yanka suka raba hannuwansu kowacensu na Juyawa ta fice batareda kowa yaji muryan kowa ba sbd basuda daman magana baa basu damar ba. Towel din Ayanah ta dauka ahankali ta daura a jikinta Bayan sakinah ta miqe a natse ta tayata zare halfvst din jikinta, Juyawa sakinah tayi zata bar gurin kanta a qasa idanuwanta suka sauka akan Zuhrah wadda ke fitowa daga ruwan itama take jiri me karfin gaske ya dibeta saura kiris ta kife Allah ya bata ikon tsayawa dakyau tana hana firgicinta bayyana sbd zata iya rasa rayuwarta. Tsurawa Zuhrah idanuwanta tayi tana tafiya kanta na tsananin sarawa da abinda take gani, ‘Zuhrah da Ayanah a matsayin imebēti na Mutum daya?’ Wace irin mummunan qazamiya kuma haramtacciyar kaddara ce wannan? Tayaya Mutum daya zai kusance su kuma su samu cikinsa su haihu? Tayaya ma wannan tashin hankalin kaddarar zata fara? Shin Ayanah da Zuhrahn sunga junansu kuwa? Idan sun gani sun kuwa San menene yake shirin faruwa dasu? Idan har sun sani tasani zasu gwammaci su mutu su dukan dasu yadda da wannan mugun tashin hankalin’ Koda sakinah ta fito daga gurin bata ganin gabanta sosai sbd tama kasa yadda da Zuhrah ce idanuwanta suka gano mata dan bama zai taba yiyuwaba wannan kaddarar a yanzu kam tayi nauyin da kila dole zaa iya rasa dayansu biyun. Su kuwa suna gama daura towels din daya bayan aka nuna musu wata kofa suka shiga toilet ne masu kyau da tsari a jere dan suyi wanka da ruwan dumi sosai kafin su fito kowacensu akaita sabon gurin da zata zauna, Suna shiga gurin a kebe yake dan haka rufe su akai sbd su ayanzu ba kowa akeso yaga jikinsu ba dan kuwa sun zama tamkar Al’aurar da haramun ne ganin jikinsu, Ana rufe su kowacensu ta nufi toilet daya ta shige aka bar Ayanah a tsaye tareda Zuhrah wadda itama take tsaye cak babu Wanda ya motsa a cikinsu tsawon mintina uku, Tsit gurin yayi sai motsin ruwan daya fara tashi ahankali na fara wankan da Sauran sukai, Sai a lokacin Ayanah ta dago ahankali cikin wani irin slow na tsananin mutuwan jiki ta Dora fararen idanuwanta masu kyau da kashe jiki akan fuskan Zuhrah wadda itama dagowan tayi ahankali. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 27 *_UMMU ASLAM COLLECTION_* 08035014107 -Ina mata yan kwalisa masu son burgewa? -Shin Kayan kitchen na zamani masu sauki da rahusa na kitchen din yan gayu dama na gargajiya kike so? -shin abayas na yayi da daukan ido da burgewa kike nema? -kokuwa original misk dahara kuke buqata dan asali? -kokuwa Kayan GHT na Neman lafiya da gyara kike so? -ke harma laces da atampopi na alfarma masu sauki kikeso? To duka kinzo gidansu indai sune abinda kike buqata ba bata lokaci kinzo kin gama samu kawai tintibi UMMU ASLAM COLLECTION 08035014107 duk inda kike zata aika miki batareda bata lokaci ba. ********* Idanuwansu na haduwa sarewa Ayanah taji kafafunta na Neman yi ta dafa bango ahankali wannan Karan hawayenta gangarowa sukeyi suna sauka fuskanta har zuwa kirjinta ta rintse ido wani yanayi na cikata ta sake bude idanuwanta akan Zuhrah dake kuka sosai itama tana jin kafafun nata sun gaza, Ahankali suka tako zuwa juna babu kowa dake ganinsu dan haka suna qarasowa wata irin runguma sukaiwa juna Ayanah na zubewa qasa Zuhrah ta bita qasan suna rungume da juna qamqam kaman zasu shige jikin juna, Kuka sukeyi sosai kaman ransu zai fita mara sauti sbd kada a jiyo su, Hannuwan Ayanah suna wata irin rawa ta kamo fuskan Zuhrah ta tsira mata ido hawaye na gudu sosai akan fuskanta tsawon mintina kafin takai bakinta ta sumbaci goshinta ta sumbaci gefen fuskanta ta sumbaci tsakiyar kanta ta kamo hannuwanta suka ta sumbata koina jikinta rawa yakeyi sbd jin kaman zata Hadiye Zuhrah, Zuhrah kuwa batada Sauran kowane irin kuzari qanqame Ayanah din kawai takeyi tana kuka kaman ranta zai bar jikinta jikinta na rawa itama sosai, Magana sukeyi wa juna amma ba daman hakan sbd zaa iya jinsu dan haka babu Wanda ya iya bude baki a cikinsu sedai ido da hannuwansu ke aiki, Zuhrah duk yanda taso kasa riqe kanta tayi ta gama ficewa hayyacinta kamo fuskan Ayanah tayi da tafin hannuwanta biyu takai bakinta kan kunnenta ta bude baki da wani irin sauti daya saka gabaki daya dan Sauran karfin halin Ayanah rushewa tace ‘Yēne Ayanah(my Ayanah),hiyiwēteni(my life),Yene widi(my precious)’ Rintse idanuwa Ayanaah tayi tana sake qanqame Zuhrah kafin ta bude bakinta cikin tsananin sanyi da mutuwan jiki tace ‘Ina rokon Allah ya zama gatanki Zuhrahna ya baki kariya da juriya tareda ingancin rayuwa, Bazan taba barin a gurbata rayuwanmu da alaqar mu ba, Duk halinda zamu shiga bazamu taba zama a cikin qazantacciyar alaqar da akeson mu zauna ba,zan baki kariya da rayuwata koda bama tare, Zan zabi mutuwa akan a hada mu a qazamiyar shimfidar mu yada mummunan zuriar datake ta Allah wadai a garemu matiqar muka hada shimfida da Mutum daya…..’ Kuka sosai Zuhrah ke qarawa sbd maganganun Ayanaah din dake sake kashe rayuwarta sbd sunzo gabar da kaddarar tayi musu muni me girma bama girma ba, Duk shauqin ganin junansu Ayau Bayan shekara guda bai taho musu da alkhairi ba dan kuwa wannan shine mafi girman quluwar kaddararsu da basusan tayaya zasu fuskancetaba kuma tinda aka zabesu din to tabbas Ana nufin sai sun sauke buqatar sultan din BOYEM Wanda mutuwar dayansu ce kadai zata Hana hakan idan kuma sun fito sun bayyana alaqarsu sbd Kaucewa hakan to dukansu ne zasu rasa ransu sbd sun aika laifi me girma ita kuma a yanzu tanason ko yayane dayansu ya rayu sbd Abaas dayake raye a duk inda yake. Sun jima a hakan kafin daqyar suka iya rabuwa da jikin juna sbd motsin fitowan wasu wanka dan haka kai tsaye a sanyaye suka fada toilet daddaya suma take suka sakar wa kansu ruwa sbd kukan ruwan ya hana aji sautin kukan dasuke fasa a tare. Sun jima a toilet din kafin suka fito kusan a tare suka fito kan kowannensu a qasa batareda sun sake kallan ko inda inuwan juna take ba. Haka aka fice dasu zuwa inda zasu zauna kowannensu da Wanda zai taimaka masa zama a dakinsa dan sai wadda sultan ya kwana da ita zaa warewa bangarenta me girma da bayi idan ta samu ciki zata cigaba da zama idan bata samu ba sultan ya gama yayinta tafiya ake da ita. Kwata kwata ba guri daya aka aje su ba kowa da dakinta daban dan haka suna dawowa ba jimaw aka kawo wa kowacensu lafiyayyun Kayan itatuwa da zallan madarar nonon raqumi me dumi da zuma tareda duk wani abu dazai Kama jikin mace na qarin Ni’iman nace me karfin gaske. Sakinah aka kawowa Ayanah wadda taje taji jikinta ya sake mutuwa Ana rufe musu daki ta zube gaban sakinah tana kuka me karfi da Neman yaya zatai da rayuwarta da wannan sabuwar kaddarar. Sakinah ma kukan takeyi cikin tashin hankali da rashin sanin tinanin yi dan kuwa wannan Karan ko ita batada shawarar bayarwa sbd abu dayane a bayyane tabbatacce kuma shine Allah ne kadai zai Hana dayansu barin duniya kokuma su dukan ma. Kuka sukeyi tare tsawon lokaci kafin aka taba kofar dakin wadda ta sakasu shire hawayensu suna Miqewa tsaye kansu a qasa sakinah ta bude dakin. Tenya ce da kanta tareda masu Binta a baya kaman zasu mata sujjada, Shigowa tayi tana kallan fuskan Ayanaah din wadda fuskanta ta kumbura sosai tayi jajir alaman kuka me karfin gaske tayi, Ajiyan zuciya ta sauke a natse tana sake kallan Ayanah din cikeda mamaki da tinani Kala Kala sbd tinda aka kafa tarihin masarautar babu macen data taba kuka akan zaa kaita shimfidar sarki duk kuwa tsoro da fargaban da matan suke shiga babu wadda ta taba kuka na bayyane sedai na boye na zuci amma Ayau idanuwa da komai na jikin Ayanah bayyanarda tsananin qiyayyrt da hakan yakeyi. Numfashi ta sake saukewa tanajin haka kawai Ayanah din takeson ma idan sultan YASAR ya sauko a Daren ya fara tarawa da ita tsawon sati guda kafin ma a sake kai wata. Murmushi me kyau ta sauke ahankali tana sake qarewa zallan kyau da wani irin sanyi da nitsuwan Ayanah din ido ta bude Baki tace ‘Yaya sunanki?? Sai a lokacin Ayanah ta motsa tareda dago manyan idanuwanta ta sukai jajir ta bude bakinta da sauti me tsananin sanyi da mutuwan jiki tace ‘AYANAH GHAZ’ maimaita sunan tenya tayi cikin kulawa da jin Ayanaah din na shiga tinani da zuciyarta tareda jin tabbas da tanada ‘da namiji yanta Ayanaah din zatai ta aura masa sbd tanada abubuwan da duk takeson mace ta mallaka dan haka koma yayane Ayanah sultan YASAR sai ya maidata cikakkiyar mace. Take ta bada umarnin duk abinda aka kawo na Shan a bawa Ayanah a gabanta ta shanye, Hakan kuwa akai haka aka fara dauko su daya bayan daya Ana bawa Ayanaah din tana shanyewa hawaye masu tsananin zafi suna gangarowa daga idanuwanta Wanda ya saka tenya sake jin Ayanah na zama dole imebēti. Su tenya na ficewa Ayanaah ta darare ta zauna bakin gado tana kallan koina na dakin babu kowane irin abu dazai Baka ikon daukan rayuwanka dan haka zame wa tayi qasa tana jin kaman zata Amayar da zuciyarta. Sakinah na gefe ta rasa abin yi itama se zuru tayi idanuwanta jajir sukai shiru, Zuhrah ma koda aka tafi nata dakin idanuwanta sosai suka nuna abinda idanuwan Ayanah suka nuna amma ita tayi kokari ta hana a gane sbd tasan a duk inda Ayanah take zaa gane yanayinta. A wannan Daren tin daga Ayanaah har Zuhrah babu Wanda ya rintsa a suka kwana cikin tashin hankali da mugun yanayi, Sakinah ma bata rintsa ba a Zaunen ta kwana sbd babu mafita tako Ina a masarautar BOYEM din da gaske komai naka a tafin hannunsu da ikonsu yake, Washe gari yanayin Ayanah sake munana yayi sbd idanuwanta da sukai wani irin mummunan kumburin daya sauya kamannin fuskarta gabaki daya dan haka kai tsaye tenya da kanta yau ta tsaya akan jiqon lallen da akai musu har aka gama tana tsaye ta saka ido babu ta inda ko kallan juna suka samu sukai dan haka suka sake shiga tashin hankali sbd suna tsananin son magana da juna sbd Neman mafitar wannan masifar, Washe gari ma haka tenya ta tsayu sosai da kanta tayi musu komai aka qara tsananta kulawa akansu, Tashin hankali da tsananin tsoronsu koyaushe qaruwa yakeyi sbd kwanakin dake kusanto su, Ayanah gabaki daya rayuwanta ne take jin ta gaji da ita sbd ba iya hadasu da zaayi gurin biyawa Sarkin qasar buqataba da yar uwarta uwa daya uba daya ita kanta batajin har abada zata iya rayuwa a matsayin baiwar biyan buqata a duk lokacinda aka biqaci hakan, Ta zabi mutuwarta a daidai wannan gabar sbd rayuwar da zata yi a yanzu batada banbanci da abinda akaiwa Nurat dinta kafin rasuwarta, Bazata iya zama abinda aka zabeta ta zaman ba dan haka rayuwa gabaki daya ta fita kanta Hutu kawai take buqata daga duniyar. Wannan tinanin ne yake fitar da ita hayyacinta da rashin magana da Zuhrah wadda itama take ficewa nata hayyacin, Wani irin sauyin kamanni ta fara samu Wanda ya saka attention din tenya dawowa kanta sosai ta dauketa ta sauya mata guri kwata kwata aka fara hada mata da maganin saka bacci a cikin abincin da ake bata Wanda bata ma iya ci Sai an tsareta. Fara bata maganin bacci ya saka tinaninta tsayawa cak batada lokacin tinanin komai koyaushe cikin bacci take sbd anason ta samu baccin da zai bawa jikinta lafiya. Zuhrah da baa Ankara da nata tinanin na ganin da gaske babu sauyi a wannan mummunan kaddarar dake tinkaro su hakama kwata kwata ta Dena ganin Ayanah wadda aka kebe daban dan haka zuciyarta ta rasa tinanin kanta batada Wanda zatai magana dashi taji sanyi,batada Sauran hope na rayuwa ko kadan dan haka ta yanke shawarar itama hakura da rayuwan gabaki dayanta dan mutuwarta ce kadai zata hanasu hada wannan kaddarar. A cikin Daren ta cire Kayan jikinta ta saka farcen hannuwanta biyu duka tafara yagar fatar fuskarta da karfin gaske cikin wata irin azaba me tsananin wuyan hadewa tana kukan azaba mara sauyi jini sosai yana fita daga duk inda ta yaga da karfi, Fuskanta da fatar wuyanta zuwa kirjinta da hannuwanta tareda bayanta take yaga tana buga kanta jikin bango sbd azaba, Take jini me yawa yafara lalata inda take karfinta na ragewa ahankali. A daidai wannan lokacin itama Ayanah ta farfado cikin Daren ta tashi Zaune tareda zare Kayan jikinta ahankali tareda daurewa zata rataye kanta dan kuwa bata fatar ganin washe garin gobe da zaa fara musu shirin matakin karshe na isa tirakar sultan YASAR BOYEM. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 28 *_UMMU ASLAM COLLECTION_* 08035014107 -Ina mata yan kwalisa masu son burgewa? -Shin Kayan kitchen na zamani masu sauki da rahusa na kitchen din yan gayu dama na gargajiya kike so? -shin abayas na yayi da daukan ido da burgewa kike nema? -kokuwa original misk dahara kuke buqata dan asali? -kokuwa Kayan GHT na Neman lafiya da gyara kike so? -ke harma laces da atampopi na alfarma masu sauki kikeso? To duka kinzo gidansu indai sune abinda kike buqata ba bata lokaci kinzo kin gama samu kawai tintibi UMMU ASLAM COLLECTION 08035014107 duk inda kike zata aika miki batareda bata lokaci ba. ******* Shigowan sakinah yayi daidai da ture stool din da Ayanah ke Kai da qafa datai idanuwanta a rufe ta fara Wani irin shura qafa da fizge fizge jikinta na rawa sosai sbd mutuwar da gaske ta taho gadan gadan, Sakin Kayan hannunta sakinah tayi cikin mummunan tashin hankali da tsananin tsoro da firgici ta isa gurinta da gudu har tana kifewa ta tashi da rawar jiki tsoronta tsananta ta isa gareta ta riqe kafafunta da sauri koina na jikinta na rawa, Da hannu daya ta dauki stool din duk nauyinsa ta Dora a setin kafafunta ta tsayar da ita kafin a rikice ta taka gadon dake dakin ta taka wardrobe ta zare daurin suka fado qasa tareda Ayanah din tana rungumeta da tsananin karfi tareda fasa kuka Mara sauti sbd tashin hankalin tinanin rasa ayanar da zatayi da bata shigoba a lokacin, Ayanah da gabaki daya jikinta ya sake idanuwanta a rufe suna gangaro da hawaye masu dumi bata iya motsawa ba sedai kukan sakina kawai dake Ratsa kunnuwanta yana sake kashe zuciyarta da batada Sauran tinanin komai sbd ta yanke rai da rayuwa. Kuka sosai sakinah takeyi sbd batasan yaya zatai qarashen rayuwarta babu Ayanah ko daya daga cikin jinin GHAZ ba sbd sune rayuwarta itama sune tamkar nata jinin da batada kowa duniya Bayan su hakama har abada matiqar tana tareda Ayanah ita baiwar tace sbd haryanzu bawai ta yanta bane suna tare ne kawai harma suka manta matsayin junansu sbd sun samu kansu a wata ukubar rayuwar data mantar dasu cewan su din baiwa da uwar daki ne amma har abada koda BOYEM ta yantata matiqar Ayanah bata yantata ba ita din baiwarta ce har qarshen rayuwanta Wanda ita kanta indai tana tareda Ayanaah zata rayu da ita har qarshen rayuwanta to batama buqatar yancin zatai mata bauta ta bita har abada. Kuka sosai sakinah tayi na tsoron halinda Ayanah din ta shiga kafin ta iya sake Ayanah wadda har lokacin yake kaman batada lakar komai a jiki sai idanuwanta dake bude jajir suna fidda hawaye masu dumi dake gangara a hankali. Gadon sakinah ta gyara har lokacin itama idanuwanta hawayen sukeyi ahankali tana gamawa ta kamata ta kwantar kafin ta maida komai inda yake ta gyara dakin kaman babu abinda ya faru sbd duk motsinta ma bata Bari anji komaiba sbd kada asan abinda Ayanah din tayi kokarin yi hukuncin dazai hau kanta bazai taba zamowa me sauki ba, Tana gana gyara dakin ta juyo da idanuwanta da suka sauya sosai ta kalli Ayanaah zatai magana aka taba kofar dakin Wanda ya sakata saurin daidaita kanta tana goge fuskanta ta dauki towels din data shigo dasu dan kaiwa inda zata jere su. Ayanaah ma idanuwanta ta rufe a hankali sbd bata kaunar ganin komai da kowa idan ba yar uwarta jininta ba Zuhrah. Tenya ce aka budewa dakin ta shigo wainda ke biye da ita suna dauke da wasu magungunan gargaji masu tsafta da kyau aka shigo dasu Ana jerewa a table, Idanuwa tenya ta zubawa Ayanaah tana kallanta haka kawai taji bata iya Kyale Ayanah akan zamowanta imebēti wadda koda zata sauya kowa bazata taba sauya Ayanah GHAZ ba komai wuya tanason ganinta a imebēti sbd itace kyanta yakeda tsananin nutsuwan da zai iya girgiza Kyan HAILE da qasar take taqama dashi ita kuwa a nata bangaren batada burin daya wuce takai HAILE qasa ta hanyar samun macen da zata kere ta a gurin sultan musamman idan Allah yasa aka samo LEUL ba a gurin HAILE ba sbd Qin HAILE a jikinta yake tin daga lokacinda ta dauke ran qanwarta uwa daya uba daya da ita kadai gareta sbd kawai ta samu cikin sultan a matsayin imebēti a lokacin da tana yayin dauke rayukan duk macen daya kwanta da ita, Wannan ne dalilin daya saka tenya batada burin daya wuce samar da macen da zata fi HAILE komai da samun gurbi a zuciya da ahalin sultan, A tarihi da doka tareda qaida mai girma a Masarautar BOYEM baa taba auren wadda ba jinin BOYEM ba, Babu macen data taba Matar Sarkin Boyem matiqar ba jinin sarautar BOYEM bace, Duk yanda mace ta shiga ta mamaye zuciyar Sarkin Boyem komai tsananin so da kaunar dayake mata fiye da matansa matsayinta yana tsayawa ne a iya WISHMAH wato lady mistress ita ta wuce matsayin imebēti hakama bata zama matarsa ta aure ba amma kuma matsayinta daya da matansa a duniya a zuciyarsa kuma tama fi matan matsayi, Dan haka a koyaushe burin da tenya take kwana dashi take tashi tayi rayuwa dashi shine ta tabbatarda ta samar da wishmah a BOYEM din yanzu wadda zata ruguza power din HAILE koba duka kwata kwata ba to ta tabata sosai dan babu macen datai darajar HAILE a qasar BOYEM yanzu sbd itace mata kuma uwargidan sultan YASAR haka kuma macen datafi kowace macen kyau da iko a qasar. Duk da Ayanah baiwa ce wadda bauta ta sauya mata abubuwa da dama ita ta hango asalin sirrin kyanta Wanda zai fito fiyeda na HAILE idan ta samu gyara da hutun da fata da gangar jikinta suke buqata ga wata irin sanyi da nutsuwa a tattare da ita wanda zai iya sanyaya zuciya mai Zafin gaske irin ta sultan jinin masu BOYEM da kansu dan haka Ayanah tayi mata tako Ina kuma taci burin fiddo da dukkanin kyanta da kwarjininta da bauta ta boye zata fiddota a matsayin sabuwar wishmah ta BOYEM da aka shide qarnika baa samu ba sbd yawancin sarakunan BOYEM basa soyayya dan bata tsarinsu Sarkin uku ne kadai suka taba wishmah Sai a yanzu datake fatan hakan ga sultan YASAR. Umarni ta bada aka tada Ayanah Zaune wadda take kwance kaman babu inda baya aiki a jikinta, Sakinah ce ta saka mata pillows biyu a bayanta suka tareta aka fara bata maganin masu dumi da wani qamshin nutsuwan dayake ratsa hancinta zuwa cikinta, Gabaki dayansa aka sakata shanyewa kafin suka ajiye cup din akan tray din da aka jero cup da bowl din Dayan maganin masu kyau. Dayan maganin aka Dora mata a baki yafara shiga maqoshinta ta rufe idanuwanta ahankali tana Jin taste din maganin na ratsa bakinta aka buga kofar dakin da nutsuwa Wanda ya saka dukansu kallan kofar Banda Ayanah din dake Jin zuciyarta na Wani irin nauyi ta sake rintse ido. Da ido tenya ta basu umarnin su bude dakin dan haka daya daga cikin bayinta ta juya ta nufi kofar dakin a natse ta bude Kai tsaye tana kallan wadda ta bude dakin kanta a qasa ta bude baki da taushin murya tace ‘Daya daga cikin sabbin imebētin da zaayi ta illata kanta harma tana gap da rasa ranta amma……. Wani irin fesowa abinda yake cikin bakin Ayanaah yayi da karfin gaske idanuwanta na budewa jajir sbd abinda taji Wanda zuciyarta ta tabbatar mata da Zuhrah ce, Wata irin rawa hannuwanta da kafafunta suka fara ta yunqura da karfin gaske tana Miqewa tsaye harshenta karyewa sbd mummunan tashin hankali ko magana ta kasa sai idanuwanta dake rikidewa jajir b Kyan gani……… Sakinah ma da jikinta ya dauki wata irin rawar tashin hankali saurin dafe Ayanah itama tana Jin tabbacin Zuhrah ce dan haka hawaye suka fara ciko idanuwanta sbd Zuhrah tayi hakan ne sbd yar uwarta Ayanaah… Ayanah fizge wa tayi daga riqon Sakinah tana Miqewa jiri mai karfi na dibarta tabi bayan su tenya da suka fice dakin batareda sunsan halinda Ayanah din ta shiga ba. Ko ganin gabanta Ayanaah batayi jiri na dibarta na maganin da aka bata Wanda karfinsa yake dan bugarwa sbd na gyaran mace ne, Wani dishi dishi take gani a idanuwanta da duhu duhu amma a hakan take jefa kafarta duk inda ta samu ta nufi hanyar da Batama San Ina zata samu Zuhrah dinba, Sakinah d gudu taje biye da ita tanason ambatar sunanta amma ta kasa sbd kada wani ya jisu asan sun fito komai y qarasa lalacewa dan haka biye take da ita tana wasu irin hawayen tausayi da tashin hankali tareda baqin ciki tana kokarin kamata amma Ayanaah dinba taqi Bari fizge wa takeyi sbd ko zata rasa ranta Ayau sai taje ga yar uwarta. Ragaita Ayanaah din ta ringa yi tana zagayen Neman inda Zuhrah taje amma koina tsit babu Zuhrah ta zube a tsakiyar gurin qasa tareda dafe kirjinta dake mata Wani irin azababben radadi ta fasa wani irin kuka mai karfi da taba zuciyata tareda ambatar sunan Zuhrah da karfi tana sake dafe kirjinta dake Neman bugawa da sauri sakinah ta zube qasa din itama tana rufe mata baki da hannuwanta biyu tana kukan itama mara sauti jikinsu na rawa su dukan, Kuka sosai Ayanaah keyi mai tsananin karfin sautin gaske amma Sakinta ta riqeta jikinta da karfi ta toshe mata baki sautin kukan baya fita sbd idan batai hakanba koina zai amsa karar kukan nata Wanda takeyi d karfin gaske tana ambatar sunan Zuhrah. Motsin tahowa suka Ji Wanda ya saka sakina janta da karfi cikin tausayawa ta boye bayan wani dakin da ita har lokacin riqe take da ita bakinta a toshe. Zuhrah ce aka dauko tamkar gawa a kan wani qaramin gadon marasa lafiya koina jikinta ba Kyan gani jininta ne yake fita sosai Wanda ya sauya kamanninta dana Kayan dake jikinta, Babu alaman rai a jikinta idanuwanta a rufe hannuwanta a sake Mutum hudu ne maza dauke da ita jini na bin hannuwanta zuwa yatsar hannunta yana diga qasa, Tenya ce ta bude baki Kai tsaye cikin iko da bada umarni mai Zafin gaske tace ‘A kaita kurkukun bauta da ukubar da bayi acan zatai jinya t warke tayi rayuwa har qarshen rayuwarta bazata taba fitowa ko wuya ta dauki ranta ko kadaici da ukuba wannan shine hukuncinta…… Wani irin Juyawa duniya tayi da Ayanaah wadda ta bude baki da karfin gaske ta fasa Ihun kiran Zuhrah cikin rikitaccen kukan daya saka sakinah sake saka karfinta duka tana danneta tareda rufe bakinta d karfin gaske itama tana hana nata Ihun gunjin kukan fidda sauti. Fizge fizge Ayanah keyi tana dukan hannuwan sakinah son qwacewa ta tafi ga Zuhrah kome zaayi musu Ayi tare amma Sam sakinah ta saka karfi sosai ta danneta da gaske sbd tana fita dukansu su ukun rasa rayuwarsu zasuyi dan haka dole ta hana Ayanah dan yanzu ita da zata zama imebēti itace hope dinsu harma dana fiddo Zuhrah cikin wannan mummunan hukuncin na qarshen rayuwa. Gap da su aka kawo Ana wucewa fuskan Zuhrah dake jina jina da jini tana fuskantar saitinsu idanunwata a rufe Wanda ya saka zuciyar Ayanah kasa dauka ta daga hannu tana miqawa zuciyarta na rage bugawa tana sake kokarin fizgewa tana ihu sosai a zare amma Sam babu sauki a riqon da akai mata tana kallo har aka bace da Zuhrah zuwa inda bazata sake ganinta ba har karshen rayuwarsu kila. Wata irin jijjiga takeyi tana Ihun Wanda har jikinta ya fara sakewa ahankali ta some a jikin sakinah din gaba daya numfashinta na tsayawa. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 29 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Cikin tsananin sabon tashin hankali da tsananin tausayin Ayanah dake kashe duka jiki da zuciyarta ta fara girgiza Ayanah din da dan karfi tana ambatar sunanta da sauti qasa qasa amma ba alaman Ayanah din zata motsa ko alamar akwai Sauran rai a jikinta dan haka da sauri ta saka qarfinta ta daukota a bayanta tana waiwayen hanya dan gudun a Gansu ta ringa bin bango a tsorace da firgici ta koma har dakinsu ta fada gado da ita tana sauke wani wahalallen numfashin gajiya da tsoro da firgici, jikinta na rawa ta miqe tazo kofa ta rufe da sauri hadda saka keyi kafin ta dawo inda Ayanaah din tana sake girgiza ta tana ambatar sunanta da sauti mai bayyanar da tsoronta na rasa Ayanah din ga kuma tausayin Zuhrah dake sake sako mata kukan daya kasa ma fitowa zuwa lokacin sedai jan ido da rawar jiki, Ruwa ta dauko hannuwanta na rawa ta zubawa Ayanaah din wadda bata motsa ba saida ta zuba mata ruwa sosai tukuna ta motsa kadan idanuwanta da sukai mummunan ja suna budewa ahankali ta saukewa sakinah su batareda ta kyafta ba ko motsawa tamkar gawar da baa shafe wa idanuwa ba, Hawaye ne masu tsananin zafi suka gangarowa sakinah ta sunkuyar da kanta qasa tana dauke kallanta daga kan fuskan Ayanah da ko kyaftawa idanuwanta basu yi ba tana mata kallan da batasan na menene ba amma dai koma na menene tasan akwai kallan yanke kauna a cikinsa dan haka jikinta yayi sanyi hawayenta na tsananta gudu ta bude baki koina na jikinta na qara sanyi tace ‘Allah ne ya kaddaro muku hakan da gani har ke har Zuhrah babu Wanda zai iya sauya hakan, Allah ya fini sanin dalilinsa na yin haka hakama yafi ki sani yafi Zuhrah sani harma da duka masarautar BOYEM din, Ga dukan alama kaddararki ce ta sako mu halinda muke ciki sbd Allah ya riga kila ya kaddara tarayyarki da sultan YASAR Wanda matiqar akwai rabo a tsakaninku to shine yayi sanadin komai daya faru dan zuwanmu nan, Komai daya faru ya samu yan uwa da iyayenki ki yadda da rabo mai karfin dayake tsakaninku ke kila ya haddaso hakan dan haka ko a yanzu rabon ke dince ya saka yar uwarki sadaukar da rayuwarta sbd bazata iya qazantar dake shirin shiga tsakaninku ba ta hada shimfida daya da Mutum daya ku haifa masa yaya ku hada yayanku uba daya Kina raye tana raye, Kinyi kokarin daukan taki rayuwan Amma Allah ya Hana hakan sbd kece wadda kila ya kaddarowa hakan, A yanzu Zuhrah ta Riga takai karshen tata kaddarar kila dan kuwa har abada mutuwarta ce kadai zata fiddo da ita inda aka kaita waton gawarta ce kadai zata fito idan zaa rufeta kenan, Tsananin so da kaunar da kike mata da saka rayuwarki a halakar da zaku rasa Ranku gabaki daya bazai taba sauya kaddar datake boye a cikin wannan lamarin ba, Lokaci yayi da zaki rungumi kaddarar da gaske AYANAH GHAZ, Zamtowanki imebēti ki haifi jinin BOYEM ko mace ko namiji shine zai baki hope na koba yanzu ba zaki fitar da yar uwarki daga wannan ukubar data Riga ta shiga sai mutuwa, Zamtowanki cikakkiyar imebētin sultan YASAR BOYEM shine gatan da zakiyi wa yar uwarki da komai dade wa bazata cire rai daga samun ceto daga gareki ba dan kuwa tayi abinda tayi dinne dan ke ki samu zama imebētin ke kadai bada ita ba dan tasan zaki taimaka mata daga lokacinda kika samu daman tashi daga baiwa hakama matiqar kika zama imebētin kika tashi daga baiwa ko ba yanzu ba Kinada Sauran saka ran samun yancin Neman dan uwanki Abaas da shima matiqar yana raye yasan indai Kina raye wata ran Zaki iya nemansa, Ke kadai kika raye a GHAZ wadda yan uwanki suka Dogara dake dan Allah Nima Ayau Ina rokonki ki jure ki daure ki rayu ko dan yan uwanki Dani kaina……. Wani irin kuka mai tsananin ratsa zuciya ne sakinar ta sake tana sake sunkuyar da Kai tace ‘Matiqar kika jure kikai sadaukarwa tabbas ranar da zaki fiddo yar uwarki zata zo harma Kuyi rayuwa a tare idan bazaki iyaba ki daure ki iya kiyi sadaukarwar da yar uwarki tayi ki jure kiyi yaqi da komai ki ceto yar uwarki….’ Rufe idanuwa ahankali Ayanah tayi wasu hawaye masu dumin gaske suna gangarowa daga cikinsu batareda ta motsa ba har lokacin, Shiru sakinah itama tayi hawayen na gangarowa daga cikin idonta babu Wanda ya sake motsawa a cikinsu hawayen Ayanah takeyi sosai hatta gashin jikinta sun kwanta gabaki daya tamkar sun mace, Babu Sauran rayuwar data rage mata a yanzu da batada kowa a rayuwarta bayan sakinah, Dukkanin kuzari,farin ciki,ruhi da bugun zuciya da hasken idanuwanta an rabata dasu babu ko daya a tattare da ita dan haka babu Sauran abinda ya raye komai na rayuwa bayan gangar jikinta da yanzu itama zata zama ba nata ba saina biyan buqatan wani Wanda zai watsar da ita ya manta ita da duk abinda ya rabata dashi ta zama fanko sauransa har qarshen rayuwarta, Batada Sauran zabin daya wuce wannan din matiqar ranar da zata fiddo yar uwarta zatazo tabbas zata zama fankon ragi da Sauran wani din har karshen rayuwarta sbd daman babu abinda ya rage a rayuwan Bayan gangar jikin. Hawayen ne suka cigaba da gangarowa gefen idanuwanta dake rufe batareda ta motsa ba har lokacin sedai sakinah ce ta saka farin qaramin handkerchief mai tsafta tana share mata hawayen ahankali suna saika Akan kyallen batareda ta sake cewa Ayanah din komaiba sbd ba abinda ya rage ma fada. Shiru dakin yayi ko numfashinsu Baka Ji har tsawon Daren haka suka shafe sa cikin toshewan zuciya babu motsi, Sallan asuba ce ta saka Ayanah din motsawa bata iya tsayuwa daidai ta miqe sakinah na riqe da ita har toilet. Dukkaninsu sallah sukai suka ringa kuka mai tsima zuciya suna fadawa Allah damuwa da quncinsu har gari ya fara haske lokacin sakinah ta fice zuwa dakinsu tayo wanka ta sauyo uniform ta taho tafara aikinta ita kuwa Ayanaah na Zaune zuru ta kwantar da kanta a gwiwan kafafunta seti da window ta zubawa waje ido bata ko kyaftawa. *********Ayau din aka taho aka kawo masu fara mata gyara ma Musamman Wanda zai qarasa dawo sa asalin kalar fatarta fara sol da gyaran fata da qamshi na musamman Wanda tinda masu gyaran suka iso bata iya cewa komai ba ko kuzarin komai duk yanda akai da ita tana Zaune babu gardama ko hayaniya ta zama tamkar Mutum mutumi dan haka suma suka zags sosai sukai aikinsu hankali kwance a natse, Har kusan dare Ana abu daya da jikinta kafin suka tafi sai kuma gobe, Washe gari ma haka suka taho sukai aikinsu suka tafi, Tsimata akeyi cikinta da fatarta da asalin zallan madarar raqumi da lalle da zuma tareda wasu Hadi masu tsananin qamshin da hatta gashinta dayake Shan gyara qamshi yake fiddawa me sanyaya zuciya da kwantar da hankalin mai shaqa tareda basa nutsuwa da mutuwar jiki, Sati guda akai Ana mata gyaran daya sauya kalarta da kamanninta asalin Ayanah dinta ta dawo sedai duk tsawon lokacin nan babu Wanda ya taba Jin koda muryanta sbd gabaki daya ko magana ta dena ido ne kadai se Numfashi ya rage mata sai kuma yanda akai da gangar jikinta ta sauya gabaki daya ko sakinah bata samun maganarta se dai ido kawai. A cikin sati biyu tenya ta gama samun duka abinda takeson samu a gurin Ayanah na zama imebēti kafin zuwa wishmah dan kuwa hatta yatsun kafafun Ayanah dama hannunta abin kallo da daukan hankali ne sbd ta fito asalin balarabar ANJOM GHAZ dinta, Haskenta da kyanta wani daukan ido yake yana fizgar hankali, Qamshinta kuwa daya gama Kama kowane saqo na jikinta da gashinta tana tinkaroka zakaji qamshin asalin Larabawan BOYEM yana tashi a jikinta musamman idan tai motsi haka zakaji sa yana ratsa zuciya da gangar jikinka dan haka kwata kwata aka hana kowa ganinta bare Jin qamshinta bayan sakinah da ita kadai ce baiwar da tenya ta yadda ta Barwa hidimart sbd labarin Kyan Ayanah GHAZ na isa gurin HAILE zata iya yanke mata hukuncin Kisa Kai tsaye tin kafin sultan ya mallaketa a shimfidarsa dan haka tenya ta saka ido sosai da tsaro akan AYANAH GHAZ kaman yanda take kiranta kafin ta hau shimfidar sarki sunanta ya tashi daga hakan. Tsaro sosai Ayanah GHAZ take samu daga tenya wadda daga qarshe dauketa tayi daga bangaren gabaki daya ta dawo da ita gurinta sbd barazanar datake ji a jikinta na kusanto Ayanah din sbd kyanta da yayi Wani irin yawan da itama idan ta kalleta Jin takeyi gabanta ma faduwa. Dawowan Ayanah gurin tenya ya sakata sake shiga ran tenya sbd shirunta daya zamo tamkar nutsuwar datafi ta kowa data sani a rayuwarta hakama hakanan takejin a ranta Ayanah zata iya sauya musu kaddara dan yanda take Jin nacin son kasancewanta imebēti kota halin yaya dan haka ta matsu safiyar Washe garin ranar ta wanye dan sultan YASAR na kan jirgin sauka BOYEM Wanda a Daren goben ne zata isar da Ayanah shimfidarsa da insha Allah take masa fatar samun rabon haihuwa da ita. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 30 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* A Daren Ayanah bata rintsa kona minti daya ba kwance kawai take amma babu ta inda bacci ya tinkaro idanuwanta sbd koda Yazo na iya ido ne babu kowane sauki da sassaucin dayake bawa ruhi da zuciyarta sbd a daidai wannan gabar ta rasa nutsuwa da farin ciki tareda walwala ko sakewa har abada sai kuma ranar data iya saka daya daga cikin jininta biyu da suke raye a idonta dan haka zata rayu ne kawai gangar jikinta na aiki amma Banda zuciya wadda itama bugawa kawai take amma duk abinda zata samu a duniyar nan yanzu bazai taba bata farin ciki Kona seconds ba sbd ta gama rufe babin rayuwarta babu farin cikin dazai shigo bayan qarasa rayuwa da qunci daddabe a ranta kuma a hakan zata bar duniya. Daga Daren yau shima tana kwana a shimfidar ‘da namiji zata tashi daga AYANAH GHAZ dinta zuwa macen da batada Sauran amfani a duniya Bayan biyawa namiji buqata, Zata tashi daga Ayanar Ammanta da Abaa dinta harma da Abaas dinta Wanda ya gwammaci mutuwansa akan ganin an keta haddinta Shiyasa ubangiji ya rabasu sbd kada yaga wannan mummunan ranar da Ayanaah bazata taba aure ba har abada,auren dayake fata tayi ya hada zuria da ita,auren dayake da mafi girman Buri akansa sbd shine yayi alkawarin bada aurenta ya karbi zinariya da azurfar sadakin aurenta a hannunsa koda yana qaninta wannan Alkawari ne daya dauka kuma mahaifinsu ma ya yaddar da cika masa wannan burin na shine zai bada auren Ayanah dinsa, Duka wannan Buri kashe a iya mafarki da Buri zai tsaya, Aurenta a matsayin ‘ya babba ga shugaban ANJOM kuma mace mafi kyau a GHAZ shine abinda garin ANJOM gabaki daya da ahalinta suke jira sbd sake daukaka darajarsa a garin gabaki daya, Ashe kaddararta ma babu aure a cikinta kwata kwata Ayau gata zaa kaita a matsayin abar biyan buqata da sauke shaawa batareda daraja ko daya ba, Ayau itace ranar yancin jiki da sunanta na qarshe sbd daga yau din bazata sake sunanta Ayanaah ba dayake da daraja sosai ga iyayenta da yan uwanta daga yau sedai a kirata da imebēti Ayanah har karshen rayuwarta, Daga yau ta haramta ga kowane irin namiji har karshen rayuwarta dan haka aure sedai taji sunansa kokuma taga Ana yinsa…… Lumshe idanuwanta tayi ahankali radadin dayake cikinsu ya ratsa har zuciyarta yana sauka maqoshinta ta hadiyesa zuwa cikinta da babu komai a cikinsa sai tarin quncin da dashi zata mutu. Har asuba bata rintsa ba bata kuma iya dogon Motsi sbd Sam hanayaniya ya dade da fita rayuwarta bare doguwar magana dan haka sai hakan yake sake qara mata kaman aji da nutsuwa, Nafila tayi kafin lokacin sallar asubar yayi tayi sallah ta sake miqa dukkanin lamarinta ga ubangiji har gari ya waye sosai tana Zaune kanta akan kafafunta shiru idanuwanta Lumshe tamkar fresh fulawa sabon tsiro. Karfe tara na safe aka shigo dakin nata aka sake hada mata wasu ruwa masu fitinanniyar qamshi da wani abu a cikinsu aka sakata cikinsu Zafin su na ratsata zuwa cikin jikinta take gashin jikinta suka miqe tanajin hatta kanta saida ya sara yayi mata nauyin daya sakata bude idanunwata data Lumshe ta rufe Bayan shigarta ruwan, Ruwan ta kalla cikin sanyi kafin ta sauke Numfashi me dumi tana Ji suna sake shigarta sosai suna saka jikinta daukan dumi sosai, Tsawon awa kusan biyu tayi a cikin ruwan kafin aka fiddo da ita aka fara shafe jikinta da Wani irin hadin danyar madarar datake hade da manshanu danye da baa rabasu ba, Ahankali ake shafe jikinta Ana murzawa tamkar Ana gudun fatarta ta yage, Ana gama shafe wa wani turaren hayaqi aka fara mata yana saka abinda aka Shafa mata kama fatarta da shiga tsigan jikinta dan kuwa hatta dogon gashinta saida aka shafe sa tas dashi, Tenya ce da kanta ta shigo Ana biye da ita dauke da farar kakkaurar madarar shanu me Zafin gaske ta dauka da hannunta ta miqawa Ayanaah din wadda hannu kawai ta miqa batareda ta dago ba ta karba takai bakinta ba musu ba cewa komai ta fara sha a natse jikinta sanyaye. Sai data shanye kafin aka kawo ruwa masu zafi da kyau da qamshi aka fara zubawa a jikinta Ana wankewa tana Zaune cikin pool din da babu ruwa daga ita sai abinda iya nonuwanta kadai ya rufe sai wandon da shima baida banbanci da pant Wanda shima kusan har ciki an shafa komai, Wanketa tas akai kafin aka bata damar wanka da ruwan sabulu masu tsananin tsada da qamshi, Ta jima a ciki gurin wankan kafin ta fito sbd acan din kukane mai tsananin karfi da sosa zuciya tayi sosai kafin tayi wankan ta fito. Komai da a yanzu ake kawo mata tana amfani dashi na musamman ne dan haka body lotions ne masu tsada hadin qasar BOYEM da body oils tareda turaren da ya gama kama jikinta dan kuwa ko bata shafa komai ba ko batai wanka ba wani qamshi ne yake fitowa a jikinta Wanda ya gama kama koina har gashin jikinta dan yanda ake turara Kayanta haka ake tirara ta. Bayan ta gama shiryawa cikin wata doguwar rigar qasar kuwait black da mayafinta a kanta daure kalan daurin al’adar qasar breakfast aka kawo mata Sai a lokacin tayi tana gamawa lokacin sallah yayi tana sallah batasan lokacinda bacci ya dauketa ba a kwance kan lafiyayyan gadon dakin sbd madarar da ake bata akwai maganin saka bacci dan samun nutsuwar gangar jiki data Kai gashi duk tsayin Daren bata rintsa ba dan hakanne baccin ya samu daman dauketa sosai. **********Karfe hudu na yammar ranar motoci sama da goma ne suka isa airport din BOYEM dan dauko SULTAN YASAR ALMAZ BOYEM Wanda a duka kaf motocin babu Wanda bata haura mahaukatan millions ba kudin siyanta, Ko motocin securities din masarautar ba qanana bane dan haka kusan 30 min kafin saukar private jet dinsa suka isa airport aka zagaye koina na hanyar fitowa da securities masu tsananin gaske hakama daga lokacin da jirginsa ya sauka airport din babu motar da zata bar airport din sai motocinsa da securities dinsa sun wuce sbd matsayi da tsantsan ikon da Masarautar BOYEM take dashi take kuma bugawa kaf zamanin babu me matsayin dayake bugasa komai muqamin kasar dakake dashi. Jirginsa na sauka ba bata lokaci motoci suka iso har bakin jirginsa suka daukesa aka bar airport dashi cikeda tsaro ba hayaniya zuwa Masarauta, Tafiya bame tsayi sukai ba aka iso gida tin daga nesa securities sukai saurin bude gate suna mimmiqewa tsaye qame a jere kansu a qasa. Haka motocin suka wuce ciki kaf har zuwa gate na biyu Wanda taron yan fadarsa suke duk matsayin su da muqaminsu da suke dashi na masarautar matiqar sarki yayi tafiya ya dawo dole ne suka tarbesa duk da baa dawowa dashi ya tsaya koina sai cikin tirakarsa sai daga baya yake fitowa fada koma Washe gari ko Bayan kwana biyu amma duk da hakan dole ke duk tafiyar da yayi ya dawo duk wani me matsayi a Masarautar BOYEM sai ya fito ya tarbesa, Ana isa gate na uku mota biyu ce kadai ta wuce ciki wadda daga wadda yake ciki sai wadda babban amintaccensa da securities dinsa na hanyar tirakarsa suke ciki. Motocin na shigewa gate din na uku aka rufesa ruf babu kuma mai iya ganin sultan din sai ranar daya gama hutawa ya fito iyalansa kadai ke suke da ikon ganinsa a wannan gabar dan haka koina ya sake daukan tsit me qasar BOYEM ya dawo komai nisan kilometers din dake tsakaninka da ina yake matiqar kana cikin BOYEM palace din to Ka tsananta nutsuwa da kama jikinka dan kuwa yana dawowa akwai sautin da ake bugawa Wanda kusan duka babban garin saiya dauka. Idan akace Aljannar duniya gurin tsara bangaren sultan YASAR to an taqaita ne kawai sbd Kai tsaye kana shiga tin daga hanyar da zata kaika palon farko na isa tirakarsa zakaji jikinka ya mutu ko kafafunka sai kayi daqyar kake dagawa, Doguwar hanya ce datake tsit tiles din da zaka Dora kafafunka kayi tafiya ya dauki Wani irin sanyin da duk Taku kake jinsa har cikin qwaqwalwarka, Qamshi da zakaji yana ratsa hancinka zuwa qwaqwalwarka haka zaka jisa yana shigarka cikin nutsuwa tamkar umarni ake basa sbd nutsuwar kamshin datai yawa, Komai dayake hanyar fari da golden ne dayake daukan ido yana sakaka sanin Kai ba kowa bane a qasar BOYEM ma gabaki dayanta bare masarautar ita kanta, Tsit gurin yake ba motsi ba hayaniya securities ne tin a karfon kofar da wata security camera datake bin motsi duk inda yayi amma iya kofar shigowa ne kadai securities din suke kana shigo doguwar hanyar tsit kawai sai mutuwan jiki, Idan Ka wuce doguwar hanyar palon farko zaka iso wanda kana shigar sa Ajiyan zuciya ce zata kufce maka me sanyi itama da nutsuwa sbd komai na palon ladabtarwa kawai yakeyi dan asalin dukiyar duniya ce a cikinsa, Komai na palon brown and golden ne Wanda idan Ka jima a ciki Kai tsaye zaka iya yadda da labarin da ake bawa duniya n cewan komai dayake cikin masarautar BOYEM indai Golden ne zinariya ce kawai sbd kusan akwai guraren da adon nasu da gaske akwai zinari a cikinsu. Wasu luxury leather Turkish royal sofas ne brown da suke daukan ido sun dauki sanyin ac da wani sanyayyan qamshi har sun gaji, Premium luxury winter velvet curtains ne a palon da suka sake maidasa tamkar ba a duniyar mutane ba sai Sauran abubuwan dake palon masu tabbatar da duniyar masu arziki daban take ko a ina ne, Kana wucesa yar qaramar tafiya ce da bata wuce Taku hudu zuwa hudu Ka isa palon dake gabansa Wanda shima tsaruwarsa ta wuce na farkon sedai shi komai na cikinsa milk da golden ne Wanda shi nasa tsarin English settin ne ba kamar na farkon dayake komai na royalty ne, Kana wucesa qaramin palo ne a karshen Wanda komai nasa yafi zama mai sanyin tsari da nutsuwan kala dan kuwa milk sky blue ne da golden mara Kala sosai hakama baida kaya sosai sai burgewa da zallan class,anan asalin lafiyayyan bedroom din sultan YASAR me BOYEM yake Wanda fadar tsaruwarsa bata lokaci dan kuwa gadonsa kadai dayake tsakar tsakiyar dakin ya isa ya sakaka tsayawa kallansa dan kuwa komai na dakin coffee brown da golden ne dayake nuna asali da ainihin tsarin royalty dan hatta wani tsadadden smart automatic curtains dake zagaye da gadonsa da baa ganin Wanda yake ciki sedai Inuwansa abin kallo da daukan hankali ne harma da tsoron dukiyar datai yawa a masarautar. Qamshi da sanyin dayake fara sauka a Fuskanka zuwa hancinka na daban ne idan Ka sako Kai dakin Wanda duk duniya babu me shigarsa idan ba matansa ba suma sai kuma macen da zai kwanta da ita Wanda yake tamkar saar duniya garesu. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 31 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Masu aikin bangaren Sultan daban suke gurinsu daban yake Sam baa hadasu da kowa hakama koyaushe cikin kiyaye lafiyar su ake akai akai sbd tsaro da bawa komai daya gangancesa tsaro da kariya daga koman qanqantar cuta. Ayau din daya dawo daga doguwar tafiyar kwanaki da satika harm da wata gabaki daya matansa harma da wasu daga cikin imebētinsa sun shirya sosai sunci burin samun gayyata zuwa shimfidarsa sbd dole bazaa rasa tarin buqatar mace daya dawo da ita ba tinda tsawon lokaci baya tareda mace, Matansa su biyu sunsan dole ne zuwa turakarsa yi masa Barka da dawowa harma da kwana acan amma ba lallai su samu yaji buqatan kwanciya dasu ba dan saukewa Kai buqata haka dan hakanne kusan kowacensu tayi shiri tana fatar ta kasance itace wadda Ayau zai saukewa buqatarsa. Daga matansa harma da imebētis dinsa gabaki dayansu sun san an shirya masa wasu sabbin imebētin wainda zai samu nutsuwa dasu sosai amma duk da hakan basu cire ran samun gayyatarsa dan haka a ranar babu macen data fito sbd tsima kansu da sukai da Qamshi da abubuwa daban daban. Wanka yayi a cikin ruwan da aka hada masa masu zafi da qamshin itatuwa masu sanya nutsuwa tsawon lokaci a cikin ruwan saida yar gajiyansa ta sake ta wartsake kafin ya fita ruwan yayi wanka da shower da ruwan dumi har suna fidda hayaqi tukuna ya dauro towel me kauri da girma ya fito wani irin qamshi na biyosa daga toilet din. Koda yayi fito HAILE na dakin ta iso tana Zaune haskenta na daukan ido qamshinta me sanyi ya gauraye dakin daya sakasa dan Lumshe ido yana qarasowa ya zauna a kujeran dake gaban dresser Sai a lokacin ya dago fararen idanuwansa tas masu girma da tsananin kwarjinn dayake tsinkar da duk Wanda ya kallesu ya sauke a fuskarta ya mata kallan nutsuwa yana sake yadda da babu mace mai kyanta duk da babu soyayya a ransa ta kowace mace amma yadda da HAILE itace mace mafi daraja a Masarautar BOYEM yanzu. Bude baki yayi ya amsa gaisuwarta a taqaice yana maida kallansa ga madubin dake gabansu ta saka towel ahankali tana goge masa jikinsa a natse da kulawa tareda tsananin sonsa datake Jin koyaushe kaman zai kasheta, A rayuwarta bata taba rasa komai datake so ba, Babu abinda batada dashi a rayuwarta tin daga kan dukiya da mulki da kyau da iko amma sultan YASAR BOYEM shine abinda ta kasa mallaka ita kadai yanda take so, Shine Wanda takejin tana yiwa so kamar ma fiyeda yayanta sbd babu namiji a cikinsu, Shine Wanda take iya yin komai a Kansa ciki kuwa harda daukan rayukan mutane datake Jin ba komaiba, Shine Wanda bazata iya taba barin ya San soyayya ba idan ba akanta ba dan kuwa ita kanta haryanxu tasani sultan yasar bai taba son kowace mace ba harsu da suke matansa babu asalin soyayya a tsakaninsu kawai dai yana aurensu kuma yana samun yanda yake so a tattare dasu hakama yana tareda dasu ne sbd sanin kowane sarki baya taba cika ko zama Sarkin saida mata da iyali a kansa, Idan har sultan Yasar ba ita ze so ba har abada bazata taba barin ya dandana menene soyayyar gaskia da gaskia dan kuwa a littafinta baa ma haifi macen da duk duniya sultan Yasar zai so ba Bayan ita. Harta gama goge jikinsa ta dauki mai me Laushi da qamshi tana shafa masa bata Dena kallansa ba kaman zata hadiyesa kaman zata bude zuciyarta ta sakasa ta rufe kowa a duniya ya Dena ganinsa Bayan ita kadai. Cikin Kayan Shan iska da hutawa ya shirya ya Dora jallabiya milk me kyau da tsada tareda santsi ya nufi gurin sallar dake cikin dakinsa ya tada sallar laasar, Yana idarwa abincin dayafi karfin cikin kusan Mutum goma aka kawo aka jere reras a makeken dining table din dake palon sa na biyu acan ya isa yaci abinci daidai cikinsa, Yana gamawa Maraki na shigowa itama da tata hidimar dole HAILE ta fice tabar bangaren, Baccin nutsuwa da sake samun wartsakewa yayi nai dadin gaske har yamma sosai tukuna ya farka yayi wanka ya sauya kaya zuwa jallabiya mai duhu da wata black and golden kyabba mara nauyi data fito da haske da zallan kyansa na asalin jinin BOYEM. Sallar magrib ya fito a babban masalaccin dayake cikin fadarsa Wanda securities ne dashi shima masalaccin hakama manyan Masarauta ne suke sallah a cikinsa, Koda ya fita baya dawowa ciki sai yayi sallan ishai Wanda yana shigewa kuma babu me sake ganinsa sai wata safiyar. Karfe takwas da rabi harma da mintina ya shige kuma yana shigewa ake rufe kowane gate na Masarauta babu shiga babu fita sai kuma Washe gari dan haka koina y sake kamuwa da nutsuwan tsit dan kuwa dole kowa ya gama abinda yake ya shige ba hayaniya koda kuwa kana nesa ne. ****Adaidai wannan lokacin Ayanah ce a cikin pool din da zatai wankan zuwa tirakar Sultan a daren, Bayi sama da hudu ne a kanta suna zuba mata ruwan dumi da qamshi a hankali tin daga kanta suna sauka kan fuskarta da gangarowa jikinta da santsi sbd fatarta datai Wani irin Laushi da santsi me yawan gaske, Idanuwanta a rufe suke bata iya budewa ba sbd bata buqatan kallo ko ganin komai da ake mata, Sakinah na cikin masu gagarumin shirin nata Wanda dukkanin kowane motsin sakinar jinsa takeyi yana yanka da Sosa zuciyarta sbd ganin yanda Ayanaah ta gama mutuwa daga gangar jiki har zuciya babu abinda ya rage hakama daga daren yau Ayanah ta tashi daga ayanarta sedai sabuwar uwargijiyarta a karo na biyu, Koma dai menene yayane tana fatar daga Daren yau rayuwar Ayanaah tayi sauyi zuwa mafi alkhairin rayuwa da ci gaba tareda warakar dukkanin baqin cikin dayake dunqule a zuciyarta. Mintina kusan arbain aka share zuwa awa daya aka gama wankan kafin aka bata damar datai wankan karshe da kanta tukuna ta fito daure da towel brown gashinta dayake a jiqe ya kwanta manne a fatar wuyanta zuwa bayanta hatta ruwan dayake diga daga gashin nata qamshi suke fiddawa sbd yanda akai mata wankan turare. Sakinah ce ta riqo hannunta daya a cikeda tsantsar ladabi da kulawa kanta a qasa sbd daman jiran fitowarta suke jira bisa umarni. Gaban babbar madubin dake dakin mai tsari da Kayan shirinta birjik jere a gabansa suka nufa ta zaunar da ita sbd Ayanah din ta koma tamkar makauniya sai yanda akai da ita kawai. Goge mata kanta suka fara yi zuwa bayanta aka tsane ruwan kafin aka dauko handryr aka fara busar da gashin Ana turara masa turaren wuta masu qamshi na larabawan BOYEM tareda fesa turare da man gashi mai qamshi Ana fesawa Ana drying gashin dan haka koda ya bushe tareda qamshin da mai ya bude yafara daukan ido yana fidda sirrin qamshi me sanyi, Man da aka shafe jikinta dashi shi kansa me samu da qamshine har aka gama aka gyara gashin aka kawo mata Kayan sakawa tenya ce da kanta ta kawo mata har dakin ta Dora mata tray din a hannu kowa ya fice Banda sakinah da tenya tace ta tsaya ta tayata shiryawa sbd ganin kusanci da shaquwansu. Bayan ficewan kowa dagowa ahankali Ayanah tayi ta zubawa kanta ido ta madubin dayake gabanta batareda cewa komaiba ko motsawa wasu hawaye masu dumi da sanyi suka gangaro mata ahakali ta Lumshe ido tareda Miqewa ahankali Sakinah ta tayata saka komai batareda kowannesu yayi magana ba har saida ta gama shiryata tsaf tukuna ta tsira mata ido gashin jikinta take suka miqe ta bude baki cikin tsananin faduwar gaba da rawar murya tace ‘MashaAllah Ka quwwata illa billah’ Bayan hakan bata iya cewa komaiba sbd tsoron Kyan Ayanah ma taji tanaji a Karan farko sbd wata irin kwalliyace akai mata wadda ta saka gashin jikinta Miqewa sbd kyau da Allah ya halitta a gurin, Motsawa ahankali Ayanaah tayi tana Lumshe idanuwanta daga kallan sakinah sarkar hannunta tayi wani sirrintaccen kukan adon mata Wanda ya saka sakinah Jin jikinta na mutuwa kuka na son zuwar mata amma ta danne sbd kada ta qara karya zuciyar Ayanah. Rungumeta take son yi amma shikenan ta Riga ta rasa wannan damar dan haka ta sunkuyar da kanta hawayenta datake riqewa suna sauka ahankali, Hannu Ayanah ta daga a hankali takai zata dago fuskan sakinar amma sakinan taja baya a natse tana girgiza Kai sbd daga yanzu babu Wanda yakeda iko kona dogon kallan Ayanah bare taba jikinta sai kuma tabaro tirakar sultan. Bude kofar akai tenya ce tareda bayi sama da goma wainda suka sauyo uniforms dinsu sunyi fes dan haka babu bata lokaci tenya ta kalli Agogo karfe goma sha daya da rabi na dare dan haka a natse aka buda mata hanyar data sakata sauke ajiyar zuciya mara sauti babu Sauran abinda ya rage a yanzu kam sai fuskantar sabuwar kaddararta da batasan me ta kunsa. Takawa tafara yi ahankali babu Sauran kuzari a jikinta ko kadan kanta a qasa. Kai tsaye duk Wani bawa dayake a masarautar a yau ya shige sbd baa buqatan ganin kowa lokacin Kai imebēti dan haka koina tsit sai sautin kukan sarkar zinarin datake kafar Ayanah dake fidda sauti me dadi da nutsuwa har zuwa kofar isa tirakarsa inda take securities sukai qasa da kansu suna bude mata kofar da sauri cikin nutsuwa, Daga ita sai tenya ne suka shiga Sauran bayin anan suka tsaya gefe kansu a qasa, Duk Taku daya da Ayanah ke tsananta qunci da nauyi kafafunta keyi tana sake macewa ciki da wajenta har suka isa palon karshe Wanda anan tenya ta tsaya koina yayi dum babu haske an rage sosai dan haka daga nan Tenya ta tsaya ta miqawa MARAKI Ayanah GHAZ wadda itace zata kaita har kofar master bedroom dinsa ta sakata ta juyo. Tinda MARAKI ta kama hannun Ayanah taji tamkar duniyarta ta tsaya cak sbd abinda idanuwanta suka gane mata da kamshin da hancinta ya shaqar mata Wanda ya saka zuciyarta bugawa dan Kuwa Kyan data gani kusan tsoro itama ya bata Ayau din. Rawa kafafunta sukeyi harta isa babbar kofar dakin kaman yanda duk takun Ayanaah daya itama yake jijjiga zuciya da ruhinta harta isa ta bude kofar Kai tsaye ta sakata a natse ta juyo ta fice tareda rufe kofar sai kuma da asuba zaa taho a Jere zafaffuyar madara da inibi tareda dabino me kyau da zuma. Tana fitowa tareda tenya suka fito har waje ita da bayinta dake jiran fitowarta suke wuce ita kuwa tenya da nata bayin gadin kofar zasuyi a tsaye zasu kwana har asuba su koma da Ayanah dan haka rufe kofar karshen securities sukai tareda kashe wutar koina ta ciki daga wajen. Acan ciki kuwa tsayuwar minti daya Ayanah tayi batareda ta iya Jan Numfashi me kyau ba sbd zuciyarta dake Neman tsayawa cak, Ahankali ta motsa tareda Taku daya cikin tsananin nutsuwar data saka sarkar kafarta fidda sautin daya saka sultan dayake Zaune dagowa ahankali cikin qasaita da kamewa ya sauke fararen idanuwansa tas a kanta. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 32 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Cak Ayanah ta tsaya tareda dawo da kafarta baya datai Taku daya anan ma kusan sake bada sauti sarkar qafarta tayi Wanda ya sakasa gangaro da idanuwansa kafafunta ya zubawa fatar kafarta qal datake daukan ido, Ajiyan zuciya ya sauke tareda Miqewa Kai tsaye daga shi sai shigar baccin da iya dogon wandon bacci ne se Rigar da gabaki daya gabanta yake a bude fadadden kakkarfan kirjinsa dayake bayyanarda karfinsa a bayyane shima tasa fatar na daukan idanuwa, Duk qamshin data shigo dashi sai da nasa ya shiga hancinta Wanda ya saka gabanta mummunan faduwa a Karan farko sbd qamshin ke sake tabbatar mata da Ayau namiji zai kusanceta ya rabata da martaba da sunanta da iyayenta suka haifeta suka sanya mata cikeda alfahari Ayau zata rasashi ta ringa karba sunan imebēti har karshen rayuwarta, Qasa ta sake yi da kanta sosai idanuwanta cikowa da wasu irin hawaye masu dumi da tsananin qunci, Qamshinta dayake cika hancinsa batareda ta iso garesa ba ya sa saka sa sake dagowa idanuwanta a Karan farko daya kalli asalin fuskanta yana zuba mata idonsa daya saka gashin jikinta Miqewa gabaki daya ahankali ahankali duk da bata dago kanta ba amma jikinta gabaki daya yaji kallan. Sanin abinda ya kawota da bazata taba gujewa ba har abada ya sakata rintse ido da dan karfi hawaye masu dumi suka gangaro mata ta daga kafarta cikin tsananin mutuwan jiki tafara tako wa a sanyaye zuwa garesa yana tsaye kwarjinsa ya cika naimar dakin gabaki daya amma har lokacin kanta na qasa Sam ta kasa dagowa. Duk Takunta daya motsa buqata da karfin sha’awarsa yakeyi idanuwansa na sake Binta takunta da kallan nutsuwa sbd baa taba tsayawa bata masa time a lokacin dayake cikin buqatuwa sai Ayau din dan haka Kai tsaye bakin makeken lafiyayyan gadonsa ya isa miskilance ya zauna jikinsa na sake daukan dumi me nutsuwa na buqatar mace dan kuwa har wani ja idanuwansa suka fara ga qamshin daya gama dauke niimar dakin na mace me daukan hankali da motsa tsananin shaawa da sanyi, Daqyar kafafunta suka kawota har bakin gadon inda yake ta silale jikinta na sake macewa da quncin da babu mafita ta durqusa gabansa a bisa umarni da koyarwar da duk imebēti ke masa, Hannuwanta biyu na wata irin rawa da kakkarwa me bayyanarda sanyin jiki ta Dora Akan mayafin dake rufe da kanta zuwa fuskarta dake dan rufe kadan da transparent black mayafi me kyau da shine yake saka hasken fuskarta da kyanta na sake fitowa sosai, Ahankali ta fara janye mayafin daga fuskarta zuwa kanta harta saukar dashi daga kafarta zuwa qasa dogon gashinta dayake a sake bayanta yana fidda sirrin kamshi ya bayyana, Kanta dayake qasa ta fara dagowa shima ahankali tana kasa dago idanuwanta da sukai dan ja ta Hadiye wani mummunan baqin ciki da qunci daya wuce maqoshinta ta kasa bude baki tayi gaisuwar daya kamata tayi sbd tana bude baki zata iya hadiyar zuciya ta mutu dan haka hannunta biyu dake rawa ta sake kaiwa gaban rigar datake jikinta me fadi sosai datake da wani kyakkyawan zip a gabanta daga sama zuwa qasa ta fara bude zip din tana Jin zuciyarta na yanka ta budesa har qasa take maroon din qaramar rigar dake jikinta mai masifaffen daukan hankalinta bayyana ko hannu batada shi hakama wasu irin crystal stones ne a jikinta masu shegen kyau da suka saka rigar kyau sosai a farar fatarta da babu tabon komai a jikinta taji kyaran daya sakasa zubawa fatar ido yana miqa hannu ahankali ya shafi fatar tareda fizgota jikinsa ya Kai fuskarsa cikin gashinta ta wuyanta ta baya ya shaqi wani fitinannen kamshin daya sakasa mannota da jikinsa sosai yana zura hannuwansa duka biyu wuyanta kaman zai shaqota ya birkitota suka fuskanci juna ya sake cusa kansa wuyanta ta gaban ya Lumshe ido duka shaawarsa gabaki daya tana qarasa tasowa, Fatar hancinsa ce ta gogi fatar wuyanta ta rufe ido ahankali tsikar jikinta na tashi sbd jikinta da bai taba haduwa dana namiji ba ta wannan sigar, Tashin tsigar jikinta ya saka tasa tsigar jikin tashi yana bude bakinsa ahankali cikeda wata kakkarfar shaawa ya dora lips dinsa a fatar wuyanta ya sauke wani gigitacen Kiss din daya saka hawayen idonta gangarowa suka sauka Akan fatar gefen fuskarsa ya kuma Ji saukansu amma bai dagoba sbd wata zazzafar wutar data kuma kunnuwa a jikinsa sbd babu macen daya taba kwanciya da ita kaf rayuwarsa data kuka ciki kuwa hadda matansa, Kowace mace a duniya da zata kwanta dashi a gurinta ba abin kuka bane abin farin ciki ne dan haka komai azabar da suke sha na kwanciya dashi din basa tana nunawa bare zubda hawaye Wanda Ayau ya fara ganin hakan Wanda haka kawai hawayen Raunin datai ya sake hura wutar shaawarsa dan kuwa ayau ya samu daman sanin Raunin mace a gurin kwanciya da jarumin mazan BOYEM irinsa. Zame rigar jikinsa yayi a hankali ta fadi qasa ya saka hannunsa daya ya zagayota yana mannota kirjinsa fatarsu ta hade ya sauke ajiyan zuciya ke sauti tareda Kama fuskarta da hannunsa daya yayi mata kallo daya ya saka bakinsa Akan nata yafara kissing nata cikin karfin buqata da qwarewa, Bata iya kissing ba hakama tsoro da quncinta tsananta gudun hawayenta sukai tanaji ya saka hannunsa daya yayiwa zip din Bayan rigarta zara daya data saka saida ya fice gabaki daya ya fadi qasa tareda rigar a lokaci daya….. Haduwar asalin fatar kirjinta da kirjinsa da babu kaya ya sakasa fidda numfashin daya saka kanta girgiza ya gangaro da fuskansa kirjinta yana fita hayyacinsa ya fara mata abubuwan daya saka hawayenta zama kuka Mara sautin dayake shiga kunnuwansa direct suna harbawa cikin kwakwalwansa komai na sake tsimasa, Yanda yake kissing yana lasar fatarta da cakuda kirjinta ya saka kukanta cigaba da tsananta shi kuwa loosing control yayi Kai tsaye cirata yayi sama yayi ya shige lafiyayyan gadonsa dake zagaye da mahaukatan net curtains ya baje ta a gadon yana sake jiquwa da shaawarta sbd kukanta dake sake kunnasa, A yanda yake cikin karfin shaawa babu abinda yake tsananin buqata Bayan dandana niimar dake jininta wadda har wani dumi yakejin tana sakasa Ji dan haka babu wani sauki ko sassaucin da zata samu daga garesa Kai tsaye ratsata yayi yana maidata cikakkiyar macen Sarkin Boyem, A yanda fatar jikinta take da dumi mai sake dumamasa haka cikinta yake da Wani irin dumi Wanda asalin gashi da turaren tsuguno ne daya ratsata ya saka har cikinta dumi ne dashi dan hakanne ya sake loosing control nasa gabaki daya. Sauti sosai kukan Ayanaah ya fara fitarwa sbd azaba da zafaffen baqin ciki da quncin dayake yunquro mata tana rintse idanuwanta tareda qanqamesa tareda tsanar rayuwarta da duka abinda zai biyo bayanta jikinta har wata irin jijjiga da kakkarwa yakeyi sbd ba qaramin girmansa da karfinsa yake sauke mata cikin Jin yana samun dukkanin gamsuwa da dumin jiki. Tsawon lokaci ya dauka kafin ya samu cikakkiyar nutsuwa ya barta kaman babu rai a jikinta idanuwanta a rufe hawaye na bin gefen fuskarta tana fatar inama ranta ya fita a lokacin tabar duniya ta huta da fatar Allah kada ya bata rabon samun ciki. Wanka yayi da ruwa masu Zafin gaske jikinsa na samun duk wata nutsuwan dayake buqata ya fito ya shirya a wasu kayan ya kwanta. A cikin daren Ayanah ta fito bata iya ko Miqewa tsaye daidai bare tafiya yanda ya kamata idanuwanta jajir ko gani sosai batayi zuciyarta rufe da quncin duniya hannuwanta biyu dauke da danyar zinariyar daya doro a hannunta wadda tinda ta fito su tenya suka miqe tsaye idanuwan tenya a kanta bata ko kyaftawa zuciyarta na harbawa Sauran kuwa gabaki daya da securities qasa sukai da kansu. Tenya dake Jin zuciyarta kaman zata fado hannuwan Ayanah din ta zubawa ido kafafunta har rawa sukeyi a natse Ayanah ta qarasa fitowa idanuwan tenya suka sauka Akan hannunta da zinariyar ke haskawa tana daukan ido taje tenya ta sake wata irin ajiyan zuciya me karfin gaske a boye tana Lumshe ido da Jin Wani irin sanyi fada farin ciki na cikata sbd zinariya alama ce ta gamsuwa sosai da zamantowanta cikakkiyar imebetin da a yanzu kawai yake buqatan zuwanta shimfidarsa har zuwa lokacin da zai qoshi da ita tukuna ya sauya Wanda kullum ta kwana a gurinsa zata fito da tukuicin danyen zinari a hannnu duk ranar data fito babu tukuicin komai a hannunta kuwa daga ranar ya gama da ita sauyi yake buqata duk ranar data fito da sarkar daham din dayake dauke da sunansa kuwa daga ranar kuwa ta zama wishimarsa ta har abada da mutuwa ce kadai Zata rabasu Wanda wannan ranar itace babban burin da tenya take dashi mai karfin gaske a zata iya komai Akan hakan sbd Ayanah GHAZ ta zamo wishmah ta uku a tarihin masarautar BOYEM ta duniya. Ayanah na isowa gaban tenya zubewa tayi qasa tana dakin zinariya dake hannunta da saurin gaske tenya ta tareta jikinta tana kuma tare zinarin ta hanasa isa qasa tana Jin Wani irin kuka mai karfin gaske mara sauti daya tahowa Ayanaah din tana rintse ido sosai. Bayin tenya dake gefe da sauri suka gyara wa Ayanah rufarta data zame daga kanta suna kara mata kujeran zaman da zaa turata da ita dan komawa da ita. Tenya ce ta sakata ciki kujeran tareda shafa kanta ta bude Baki ta jero mata wata tsaftacciyar adduar tsari da fatan samun zuriar da duniya zatai alfahari da ita. Turata sukai zuwa bangarenta sabo da wannan ranar kawai ake jira dan kuwa itama complete bangare aka bata me dauke da manyan palo guda biyu da suka jiqa da luxuries tako ina da bedroom guda uku Wanda daya yake nata daya na abinda zata Haifa saina ukun dake hanyar kitchen dinta ta baya Wanda yake na bayinta da aka ware mata ne guda uku, Dukiya da daula ce irin wadda idan imaninka baida karfi zaka shagala sosai da duniya a cikinta aka zuba mata a bangarenta da gari na wayewa aka saka masa sunan GHAZ chamber. A cikin daren suna isowa Kai tsaye ruwan zafi da wasu tsaftattun maganin gargajiya na al’adarsu aka sakata a ciki tana Jin wata irin azaba na ratsa jini da gangar jikinta harma da zuciyarta. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 33 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Kakkarwa jikinta keyi yana daukan zafi sosai idanuwanta har lokacin a rufe hawayen dake fitowa ma sun qafe koina na jikinta ya sake sai yanda sukai da ita tana Jin komai amma bata motsaba ko kadan, Tenya ce da kanta da sakinah suka gasata a cikin ruwa Kala uku da suka saka jikinta Dena kakkarwa hakama karfi na dan dawo mata, Ba qaramar shiga yayi mata ba wadda ta sakata samun yan qananun raunikan da azabar tayi mata sosai amma dan karfin Hali da taurin zuciyar data gama mutuwa, Yanda jikinta ke fizga yana jijjiga ne a cikin ruwan yake tabbatar musu da azabar datake ciki na gurzuwan datai a inda ba damar fada bare magana, Wani jiqon da gyara na musamman da tattali ta samu daga tenya da bayinta kafin aka hada mata wasu ruwan masu tsafta da Zafin gaske tayi wankan tsarki ta fito daure da towel bata iya tafiya me hayaniya a natse kanta a qasa idanuwanta jajir gashinta na tsiyayan ruwa suna bin fatarta dake da santsi, Ko data fito babu kowa dakin bayan sakinah data fidda mata kayan sakawa doguwar rigar bacci me kauri datakai mata qasa sosai tareda saka mata qamshi me sanyi, Isowa tayi gaban mirror ta zauna har lokacin idanuwan basa kallan koina bata iya cewa komai kaman bebiya, Sakinah da jikinta yake a tsananin sanyaye itama idanunwata Jan sukai tanason yiwa Ayanaah din kuka amma kuma zuciyarta na hanata hakan sbd insha Allah kaddararsu zata sauya ne daga yanzu, Towel sabo dake hannunta ta saka ahankali ta fara gogewa Ayanah din gashinta cikeda kulawa kafin ta dauko hand dryer tafara busar mata da Kai cikin nutsuwa da kulawa tana kasa kallan fuskar Ayanah din har ta gama ta dauko mata undies sabbin tareda kayan baccin ta kawo mata har gabanta ta juya ahankali zata fice kaman daga sama taji anriqo hannunta. Cak ta tsaya tareda rufe ido tana Hadiye hawayenta da suka ciko idonta kafin ta juyo ahankali ta kalli Ayanah din wadda bata dagoba bata kuma bude Baki ba, Shiru sukai dukansu babu Wanda ya motsa hakama sakinah hawayenta Neman kasa riqewa sukeyi dan haka ta daga hannunta daya zata rufe bakinta Ayanah ta fada jikinta ahankali daga Zaunen tareda zagayeta da hannuwanta biyu ta rungumeta cikin wani tsananin sanyi tareda rufe idanuwanta ta fasa wani irin kuka mai tsananin sanyi da ratsa zuciya tana qanqame sakinar cikin mutuwar jiki. Sakinah dake tsaye Jin tayi kafafunta na Neman gazawa sbd mutuwan jiki da kasa riqe kanta datai itama ta fasa kuka Mara sauti tana rungume kan Ayanaah tsananin tausayinta na rufe zuciya da idonta. Kuka mai yawan gaske Ayanah ta yi sosai a jinin sakinah har saida zazzabin jikinta yayi tsananta kafin sakinar ta taimaka mata ta saka kayan takaita inda zatai sallah tayi sallar ta kwantar da ita a gado daidai lokacin Dayar baiwar me suna Nimah ta shigo dauke da tray din dayake jere da madara me zafi da magani ta iso dasu ta miqawa sakinah. Karba tayi ta bata a bakinta ta shanye tas sbd batason bata lokaci da tsayawa gardama Akan hakan, Tana shanyewa ta miqa musu cup din Tasha magani ta zame ta kwanta a hankali sakinah ta rufeta da wani qaton lallausan bargon da taushi sa kadai zai qarawa baccinka karfi. Kashe wuta da saita sanyin ac tayi kafin ta fice daga dakin aka rufe kofar. Sai a lokacin sukai gaggawar zuwa tasu sallar tin kafin lokacinta ya wuce, Bacci sosai da zazzabi Imebēti Ayanah ghaz ta samu na tsawon lokacinda bata sani ba sedai koda ta tashi tasan rana tayi dan haka Kai tsaye toilet ta nufa cikin rashin qwari tayi wanka da alwala ta fito a lokacin ne sakinah ta shigo ta gyara dakin ta sake fito mata kayan d aka kawo dan sakawanta aka cike wardrobe dasu tareda duka wani abin buqatarta masu yawa da tsada. Breakfast aka kawo mata tana gamawa kyautikan matan sultan suka iso gareta sbd cika al’adar zamowanta imebetin da zata cigaba da zuwa tiraka, Kyautar MARAKI ce ta fara isowa na wata doguwar sarkar zinari mai hade da yan kunne suma dogaye da sarkar kafa, Godia tayi cikin sanyi kafin kyautar haile ta iso daga baya ita kuma sarkar Kai ce ta zinari da awarwaro masu kowane hannu babbiyu, Itama godia tayi kafin su sakinah suka karba sukai ciki dasu tukuna daga nan tenya ta zaunar da ita t fara jero ma tsauraran sharuddan suka biyo matsayin datake dashi yanzu, Duk abinda ake fada mata baya iya ko motsawa ba idanuwanta da sukai ja ne har lokacin take zubawa komai kawai idan ta gaji kuma ta Lumshe idanuwanta da sauke Numfashi ahankali, A hakan ta wuni babu kowane irin kyakkyawan kuzari ko magana sedai ido kawai daga qarshe ma daki ta qarasa wuni ita kadai komai na rayuwarta na dawo mata farko da karshe, Yammar fari nayi masu gyaranta suka iso da tenya haka aka kuma gasata a wasu ruwan magani masu zafi da ratsa jiki har magrib tukuna aka gama suka fice, Tinda aka gama jikinta ke Wani irin tashin tsikar jiki haka har Bayan ishai tenya tazo aka sake shirinta a karo na biyu tareda sauya mata kaya zuwa wasu fitinannun kayan baccin data kasa kallan kanta ta rintse ido tana Jin kaman zuciyarta zata fashe Amman batada zabi sai wannan a yanzu, Karfe goma sha daya na Daren kaman jiyan haka aka kaita har kofar palon karshe tenya ta juya ta barta tsaye tana sauke Numfashi me sanyi ahankali. Ta share mintina tsaye a gurin batareda ta dago kanta ba kafin tashin dago kan a sanyaye tareda bude idanunwata masu kyau ta kalli kofar shiga master bedroom dinsa tana Jin dukkanin wani abinda yayi mata jiyan yana dawowa fatarta tamkar lokacin abin ke faruwa. A hankali ta miqa hannunta cikin nutsuwa tai knocking dakin Wanda sai datai mintina a tsaye kafin kaman baa duniyar ba taji muryansa da taushi da ikonta ta bada umarnin shigowa, Sai data sake sauke Numfashi me zafi da mutuwan jiki kafin ta bude ta sako kafarta ta dama a natse kanta a sunkuye sedai ba sosaiba kuma Ayau din babu rufa a fuskarta, Zaune yake Akan lafiyayyan couch din dake bedroom dinsa mai Laushin gaske daga shi sai dogon wandon kayan bacci masu kauri fari qal sanyin ac na ratsa lafiyayyar fatar sa dake daukan ido, Taku hudu tayi ta tsaya tsakiyar dakin batareda tasan inda zata ba sbd idanuwanta ma da basa gani sosai sbd quncin dayake cikinsu, Qamshinta ne da har yanzu bai sake dakinba tin jiyan yake sake gauraye dakin yana shiga hancinsa, Yanayin daya samu kansa a jiyan ne yafara dawo masa cikin Kai sbd qamshin da direct yake shigar masa hanci dan haka a cikin iko da nutsuwa da kamewa ya dago manyan idonsa ya sauke mata a karo na biyu jiya da yau, Daga inda take tsayen taji idanuwansa akanta suna sakar mata jiri a hankali ta dago kanta batareda ta iya kallansa ba sbd bazata iyaba, Rigarta ta saman ta sake a hankali ta fadi qasa fitinanniyar shigar da akayo mata t bayyana Akan idanuwansa da suka qurawa kirjinta dake cikin transparent curve na kayan baccin jikinta komai na jikint yana gani fes, Sautin sarkar hannunta data motsa ya shiga kunnensa shima take y sakasa Lumshe ido yana kunnuwa gabaki dayansa take ya ajiye wayar dake hannunsa gefe tareda daga hannu daya yayi mata Wani kira da yatsa biyu yana mata Wani mayen kallo. Duk sautin takunta daya sake kunnasa yakeyi dan haka koda ta iso garesa ya gama tsimuwa Akan kafafunsa ya dorata tareda kama kanta da hannunsa ‘daya ya hade da fuskarsa take bakinta ya fara yiwa wata tsotsan data sakata rufe idanuwanta hawayenta na gangarowa jikinta na mutuwa, Batareda rigar jikinta ba yayi sama da ita a jikinsa zuwa shimfidarsa inda ya ringa bata wata irin rayuwar da batama San da itaba a duniya kwata kwata dan kuwa ko Ayau din ba qaramar gamsuwa ya samu da ita ba dan haka yau dinma da wani tarin danyen zinari ta fito Wanda ya saka tenya samun tabbacin burinta zai cika a Sannu a Sannu insha Allah, Haka aka koma da ita aka sake bata kulawa kaman jiyan sai datai sallah ta kwanta bacci, A hakan sati daya tayi cif tana gamsar da sultan YASAR, Tin jikinta bai saba da azabar ba har yafara sabawa ta rage shiga mummunan Hali sosai kuma a hakan tenya bata taba wasa ko sanya gurin gyara da shirinta ba, A wannan satin daya babu ranar da bata fitowa da tukuicin dayake sake nisantata da rayuwarta hakama a wannan satin dukiya ce ta fara taruwar mata wadda batasan abinda zatai da itaba sbd batada kowa bare rayuwar da zata kashewa kudin dan haka anan dakinta sakinah take mata ajiyar su batareda itama tasan me zasuyi da dukiyar ba, Tana cika sati matansa suka karbesa inda kowacensu zatai sati tana zuwa itama dan haka tsarin yake sai sunyi kaman satika suna juyin kwana a tsakaninsu kafin imebētinsa ta sake Kai masa ziyara, Wata daya da sati daya Ayanah tayi batareda an sake kaita ba tana samun Hutu da nutsuwar data riga ta kauracewa rayuwart kafin aka sake shirin kaita, A watan nan guda datai babu ranar da tenya bata tsimata da gyarata gashi zamanta cikakkiyar mace ya sauya abubuwa da dama a jikinta dan hakanne ta koma tamkar wata fitila sbd hasken Hutu da gyara dan kuwa tsawon watan bata taba fitowa ba ko kofar fita GHAZ chambers. Ayau da aka kaita kaman ita din yake jira sosai ya huta da ita har kusan saida akai kiran asuba tukuna ta fito daga bangaren, Washe gari ma haka ya samu nutsuwa fiyeda yanda yake tsammani, Sati guda ta sake sharewa Wanda yasa ya ankare da ita fes tin daga kamanninta da sunanta da matsayin datake dashi na basa cikakkiyar nutsuwa da gamsuwa dan haka Kai tsaye aka rage ranakun hutunta zuwa sati uku. Watanta uku cif da zama imebēti yanayinta ya fara sauyawa Wanda ya saka tenya Kai tsaye aika sakon kiran masu duba lafiyar imebētis dan tabbatarda abinda yake damunta. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 34 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Wani irin Kyalli da daukan ido fatar Ayanah din ta qara Wanda ya saka kwata kwata ko bayin ba kowa ne tenya take Bari yana ganinta sbd bata kariya daga ido da Baki tareda mugun nufi dan haka hutun datake samu da zuwanta shimfidar namiji ya budeta harda bulbul tayi ta ciko sosai duk da batai Qiba ba Amma ta sauya, Babu abinda y rage daga kuncin dayake zuciya da rayuwarta dan kuwa har lokacin bata doguwar magana bare son hayaniya, Daga tenya sai sakinah ne kawai suke samun maganarta sai kuwa shi kansa me gayyar idan ta bude Baki ta gaidasa Wanda shima nutsuwa da kamun kanta ko a magana daban yake duk da babu macen da bata biyayya me girman gaske a gabansa amma a cikin tata girmamawa nutsuwa da sanyinta a bayyane yake, A ranar da masu dubata a daren gurinsa ta kwana inda shine da kansa ya fara tabbatarda sauyin datai dan kuwa komai nata cika da taushi fatarta ya qara sosai, Baisan yaya ake gane mace mai ciki ba dan haka Kai tsaye baisan menene sauyin daya samu daga gareta ba amma yaji yanason sauyin, Da daren ranar tenya ce da bayinta su sakinah suka kaita a mutumce da kulawa da bata kariya ta shige a sanyaye sbd haryanzu ta kasa sabawa da komai Dan bata Dena zubda hawayenta ba a duk lokacin da zai kusanceta, Yauma tana shiga da sanyinta yana fitowa wanke daga shi sai towel din daya sakata yin qasa da Kai tana kasa kallansa shi kuwa tako wa yayi ya zauna gaban mirror dinsa tareda miqa mata qaramin towels guda biyu daya sakata dole tako wa cikin sanyi ta miqa hannunta zata karba ya lallai zara Zaran yatsun hannunta farare tas da suka dauki hankalinsa daya sakasa dagowa a natse ya kalli fuskart. Itama a Karan farko ta dago idanuwanta masu Wani irin haske da nutsuwa ta kallesa take ta maida kanta qasa sbd bata dauka ita yake kalla ba da bazata taba dagowa ba dan tinda ta zama imebētinsa bata taba dagowa ta kallesa ba dan hakanne batasan cikakkun kamanninsaba sai Ayau din da kwarjinsa ya sakata kasa sake dagowa yanayin fuskanta bai sauyaba, Tafin hannunta ta Dora a natse kan fatar bayansa wadda ta sakasa Lumshe idanuwansa ahankali sbd a Karan farko data fara Dora hannunta a jikinsa da kanta, Ita kanta saida hakan ya sakata rintse ido ahankali tukuna ta bude ta motsa ahankali tafara goge masa ruwan wankan jikinsa cikin sanyinta dayake saka yanda take goge masa ruwan basa wani yanayi me kashe jiki da dumi, Cigaba takeyi da goge masa jikin a tsananin sanyin jiki yana Jin dumin numfashinta na sauka a kan fatarsa Kai tsaye yana shiga jikinsa dan haka tana zuwa wuyansa hannunsa daya ya daga ya Dora Akan nata yana tsayar da ita batareda yace komai sukai shiru a hakan, Janyo hannunta yayi ta fado masa ahankali kafin ya zagayo da ita gabansa kan kafafunsa yana kallan fuskar dake qasa batareda tsammanin duka su biyun ba bakinsa ya bude cikin zallan mulkin dayake yawo a jikinsa yace ‘GHAZ’ Fadar sunan GHAZ a bakinsa da wani sautin muryan kakkarfan namiji ya sakata dagowa gabaki dayanta ciki nutsuwa ta sauke idanuwanta fes a kansa Wanda hakan ya saka idanuwansu shiga cikin na juna suna wa juna Wani irin kallan daya hanata Jin tsoro ko shakka shi kuma se Ayau kaf rayuwarsa Bayan mahaifiyarsa ya samu macen data iya kallan cikin idanuwansa batareda jikinta ya dauki kakkarwa da tsantsan tsoro ba sbd kwarjinsa da ikonsa. Numfashi me sanyi mara sauti ta sake tana kokarin sauke kanta ya tallafe fuskarta da hannunsa daya yana mannota jikinsa da hannun daya kirjinsu ya hade ya Lumshe ido ahankali ya sake bude su akanta, Karo na biyu ya sake jeho maganarsa da ambatar cikakken sunanta ‘IMEBETI AYANAH GHAZ meyasa kike riqe da matsayinki har tsawon wannan lokacin?’ Tambayarsa da bata buqatar amsa ta sakata sake kallansa wannan Karan mamakinta na dan bayyanuwa Wanda ya sakasa kallan cikin idanunwata sbd first time data nuna kowane irin reaction tinda take zuwa, Bude Baki tayi zatai maganar da batasan me zata fada ba itama bakinta ya huro masa wani mayen qamshin daya sakasa katse maganarta ta hanyar saka yatsarsa daya a bakinta ya lakato yawunta Kai tsaye ya kai bakinsa ya lashe dan Jin dandanon kamshin daya sakasa Jin koma menene a ciki yanason sa a bakinsa, Baiji taste din komai ba dan haka ya kalleta yana bude Baki yace ‘Menene wannan din shi a bakinki ina buqatansa’ Kasa kallansa tayi ta dan dauke idanuwanta ta bude Baki a natse tace ‘Tenya ce’ sai kuma tayi shiru tana kasa qarawa daga hakan Da mamaki ya kalleta sbd bai dauka zata iya fada ba kuma ta tsaya, Kamo fuskarta yayi da hannu biyu ya hade da tasa cikin wani irin sanyi da nutsuwa ba gaggawa ya hade bakinsa da nata yana zura harshensa cikin bakin ya tsotso bakin inda Sai a lokacin qamshin koma menene yake shigarsa yana basa wata lafiyayyar shaawa mai nutsuwa, Tsotsanta yakeyi yana riqe da fuskarta a natse tsawon mintina kafin ya saketa ahankali yana kallan yanda fatarta wuyanta zuwa kirjinta ke glowing, Hannuwansa biyu ya saka ya zame babbar kyabbar dake jikinta mara nauyi zuwa baya ta zame qasa, Black transparent net rigar bacci ce a jikinta da babu abinda baa gani na halittar kirjinta da suka qara Wani irin girma ya zubawa kirjin ido yana Jin numfashinsa na sauyawa cikin salo ahankali, Hannunsa daya ya zagayeta dashi ya mannota jikinsa kirjinsu ya hadu da kyau kafin ya saka dayan hannun ya Kama kirjinta daya dayaji sa kaman ya Kama wata auduga sbd taushi da tsayuwansu qam take yawunsa ya fara tsinkewan daya sakasa sake Kama bakinta ya tsotsa yana fincike rigar jikinta ya jefar ya fara lasar fatar wuyanta zuwa kirjinta yana tada tsigar jikinta data fara Miqewa, Da yayiwa kirjinta wata irin kamu batasan lokacin data qanqame wuyansaba tana rintse ido da karfi shikuwa hakanne ya saka karfinsa sake kawowa dan haka dagata yayi ya zaunar da ita kan kafafun nasa suna fuskantar juna yana ya Kama gashinta ya cusa hancinsa ya shaqi kamshin daya kasa samu a gurin kowace macen daya sani dan kuwa kamshinta na jiki da gashi dana Baki daban yake daga abinda ya Saba shaqa,hakama dumin daya riga ya Kama jikinta ciki da waje shine kadai abinda fatarsa gangar jikinsa suke so a koyaushe dan kuwa cikakkiyar macen datake Kama zuciya da bawa namiji gamsuwa da nutsuwa itace Ka shiga jikinta kaji sa can ciki da dumi shine lafiyarta itama dan daya wa macen da namiji ke gamsuwa da ita fiyeda wata macen idan samu shine Namijin ya shiga mace yaji can cikinta da dumin dazai ratso sa har kwakwalwa bawai Ka shiga kaji sanyi ba, A koyaushe ya kusanceta dumin cikinta ne yake kokarin kashe masa shaawa da iya Jin kusantar kowace macen idan ba itaba dan da yawan matan hadda rashin samun cikakkiyar nutsuwa a gurinsu yake sakasa kwanciya da mata sabbi akai akai amma a yanzu yana samun abinda yake samar da nutsuwa da gamsuwa ga shaawa da buqatarsa. Akan couch din dasuke Zaunen ya ringa bin fatarta datai Laushi da wasu irin kisses da lasar data sakata sakar masa jikinta gabaki daya idanuwanta jajir suna cikowa da hawaye masu dumi, Yanda yakeso ya ringa Juyata kukanta na sake tsimar dashi ya samar musu da nutsuwa anan inda suke Wanda hakan yayi masa fiyeda yanda yakeso. ****su tenya dake kafar chambers din suna gadin fitowarta har akai kiran asubar farko shiru suna tsaye sanyin ratsowan asubar na ratsa su suna tsaye duk sun qame sbd tsananin sanyi kamar kilishin da aka shanya, Kira na biyu akai na asubar amma har lokacin shiru kuma idan wani Daren zata Kai bata fitoba haka zasu jira a gurin har sai ranar data fiton, A zuciyar tenya farin ciki ne da wahalar tsayuwa da sanyi suka tarar mata su kuwa Sauran bayin Ka dagowa har lokacin bazasu yiba ba daman nuna gajiya ko gazawa dan haka tsit kake ji, Abinda bai taba faruwa da kowace imebēti ba shine ya faru Ayau din dan kuwa saida gari ya fara haske tukuna suka samu fitowarta a kasalance take tafiyar bacci ne sosai a idonta. Suna barin bangaren HAILE na isowa sedai ko data shiga bacci yakeyi Wanda tasan batada ikon ko dogon motsin dazai tadasa amma zuciyarta na cikin mummunan halin da bazata iya riqe kanta ba matiqar da gaske ne imebētinsa da gaske ta wuce lokacinda kowace mace take dauka a tirakarsa, Juyawa tayi ta fice zuciyarta na Wani irin cizo kaman zata feso wuta dan kuwa kishinta batajin ko yayan daya Haifa bazata iya hallakawa Akan sultan din ba dan haka gabaki daya a yanzu tinaninta da hankalinta zai koma Akan imebētinsa ne da haryanzu bata taba ganinta ba. Ayanah tinda suka dawo a ranar kwance ta wuni cikin rashin kuzari da dumin jiki na alaman zazzabi kadan kadan dan haka babu hayaniya kwata kwata a bangaren sbd bata damar hutawa, Inda Allah ya taimaketa ranar ce karshen kwanakinta dan haka zata huta Sosai kafin satikan su dawo. Da daddare sosai tenya ta iso da masu duba Ayanah din sbd batason wasa da duk abinda zai taba lafiyar Ayanaah dan kuwa Ayau datakai har safe tirakar sultan labarin zai isa kunnen matansa harma da imebētis dinsa dan haka hakan zai iya zama hadari gareta sosai sbd kishin mata masu hadarin gaske ne zai rufeta tako Ina Wanda ta hakanne imebētis da dama suka rasa ransu Shiyasa duk yanda sultan keda imebētis da yawa kalilan ne a raye wainda suma kadan kadan kake Jin Ana cewa an wayi gari kawai sun mutu, Akwai Wani irin qalubale da hadari mai girman gaske a zama imebētin da zata samu ciki a masarautar BOYEM dan haka a yanzu indai zarginta ya tabbata ciki ne da Ayanaah tabbas zata bata kariya kota halin yaya saita Haifa abinda ya dauka bazata Bari kasheta a banza ba dan hakanne ta Nemo masu dubawar cikin dare sbd Hana maganar cikin fita. Koda masu dubawan suka shigo da Daren tenya ce a gaba su suna bayanta har zuwa Dayan lafiyayyan palon hutawar Ayanaah din suka zauna ita kuma ta kalli sakinah tace a fito da Ayanah din. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 35 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Sakinah dake tsaye kanta qasa zuciyarta na cikin yanayin dayake na sallar tsoro da fargaba harma da tashin hankalin abinda yake shirin faruwa dan kuwa har abada bazaso Ayanah ta dauki cikin sultan din BOYEM ba sbd mummunan hadarin da zata shiga harma ta iya rasa rayuwarta dan kuwa babu wata rai datake da mahimmanci a BOYEM Bayan ta asalin jinin BOYEM din, Ta ina ta yaya zata iya bawa Ayanah kariya tana matsayin baiwa Bayan tana ganin yanda imebētis ke qasqantarciyar mutuwa ta rashin mahimmanci kuma sun mutu kenan a banza a wofi babu me sake tinasu sai ‘yaya idan sun haifa, Wani irin nauyi kirjinta yayi lokacinda tenya tace ta korawo ayanah tanajin gabobin jikinta na sanyi idanuwanta na cikowa da hawayen fatar ba abinda ake tinanin bane, Dakin Ayanah din ta nufa ta taddata kwance ba bacci takeyiba amma idanuwanta a rufe suke tayi shiru lafe a lallausan gadon zuciyarta a narke da damuwan data zamar mata jiki, Zuba mata ido sakinah tayi tana qure kallanta akanta zuciyarta na sake shiga matsanancin tsoro da tausayi me karfin daya saka hawayen idonta fara gangarowa ta saka hannu ahankali ta shafe hawayen tana kallan sauyi sosai dayake bayyane a jikin Ayanaah din. Ayanaah din ce ta bude idanuwanta masu haske ahankali kan sakinar sbd taji shigowanta hakama tanajin idanuwanta akanta dan haka a sanyaye ta bude ido ta saukewa sakinar batareda tace komai ba. Itama sakinar qasa tayi da kanta sbd bazata iya cigaba da kallan Ayanaah ba zata iya fasa kukan dayake cizon zuciyarta, Numfashi mara sauti ta sauke ahankali tareda bude Baki a natse da sanyi ta sanar da ita kiran tenya. Tana fada ta juya ahankali ta fice daga dakin sbd kallan da Ayanah ke mata na karaya da rayuwa koyaushe. Sai datai mintina biyu a kwancen tana kallan kofar da sakinah ta fice kafin ta tashi Zaune a hankali tareda ziro kafafunta qasa ta miqe tsaye slippers masu taushi a kafarta ta nufo kofar ta fito sanye da doguwar rigar qasar me kyau black kanta rufe da qaramin Gyale me hade da niqap din dayake da adon sarka me rawa ta zinari sbd tasan da zaa kawo masu dubata sbd zazzabinta amma bata San abinda zasuyi Bayan hakan ba kuma doka ce me karfin gaske babu namijin dazai iya ganin fuskarta tinda ta zama imebētin sultan me BOYEM gaba daya. Ko data sako Kai a palon Qamshinta ne ya fara cike palon kafin fitowanta data saka likitocin biyu dauke kansu gaba daya daga kallan hanyar datake tahowar, Tenya ce take kallanta su sakinah ma gabaki dayansu ficewa sukai kansu a qasa zuwa kitchen ayyukansu, Sakinah hankalinta gabaki daya kwata kwata yana kan abinda zai faru a palon tana tsananta adduar Allah yasa Ayanah bata dauke da jinin boyem a cikinta, Cikin nutsuwa likitocin suka nutsu suka gudanar da bincikensu Akan Ayanah wadda dukkanin tambayoyinsu ta amsa a sanyaye. Bayan dan lokaci suna bincike da bin harbawan jijiyanta suka bar bangaren dan tafiya da sample dinta da zaa auna dan tabbatarwa kafin bude baki ga fadar kowane irin sakamako ne. Ayanah bata buqatan sanin menene yake damunta sbd ba damuwanta bane ta rayu ko sabanin hakan, Tenya kuwa Miqewa tayi itama ta fice ta aika aka saka mata ido sosai a cikin sirrin dan tsaro da kiyayewa batason kowa ma yasan da duk abinda zaa fada. Jiran wuni guda tenya tayi tana jiran sakamakon Wanda ya hanata dukannin sukuni da nutsuwan zuciya hankalinta na kan koma menene, Daga qarshe tenya da kanta ta isa bangaren lafiyyyar clinic din dake cikin masarautar, Sai dare ta isa batareda barin kowa yasan da inda ta nufo din ba sbd tasan sosai akwai Idon HAILE Akan duk wani motsinta da abinda ya shafi Ayanah. Ko data iso Kai tsaye babban likitan ne da kansa ne ya zauna suna fuskantar juna ya sauke Numfashi ya koro mata bayani Kai tsaye ciki ne da Ayanaah qarami. Ajiyan zuciya da Numfashi mai karfi tenya ta sauke tareda kallan likitan Wanda ta ciro silan danyan zinari ta ajiye gabansa matsayin tukuicin zancen sa ta miqe ta juya ta fice tana Jin yanayi na farin ciki da samun nutsuwa dan Kuwa adduarta a yanzu zata sauya zuwa Allah yasa wannan Karan haihuwan LEUL BOYEM ne tazo mai albarka dazai zamo abin alharinta da uwarsa dan kuwa shine karshen baqin ciki da haukar da zata Kama HAILE dan samun namiji a gurin wata macen da ba ita ba yana nufin zarewanta. Koda tenya ta isa babu Wanda ta sanarwa da maganar cikin imebēti Ayanaah sbd fitar zancen cikin tamkar miqa rayuwar Ayanah ce ga halaka dan haka ta zabi tayi shiru ta Hana kowa sanin cikin saiya bayyana. Sakinah Jin shiru kwana daya kwana biyu harma kwanaki babu sakon labarin samun ciki ga Ayanaah ya sakata Jin dan sassaucin abinda take ji na tsoro da tashin hankali ta dan kwantar da hankalinta duk da kullum sake sauyawa Ayanah ke yi alaman mace me ciki yana sake bayyana gareta batareda itama tasan cikin ne yake dauke dashi ba. A haka satikan hutunta suka cika aka fara shirin fara zuwanta tiraka sedai wannan Karan tenya bata bada umarnin anyi mata shiri me karfi ba Wanda hakan ya tado tsoron sakinah sedai kuma indai har cikin ne da Ayanah dole Ayau zasu sani kuka kowa ma dake masarautar zai gane dan bazata qara zuwa ba, A al’adance duk macen data samu cikin sultan matiqar an tabbatar tenya ce takeda ikon sanar masa idan takai mace kwanan karshe shi kuma daga wannan ranar zai sallamota ne ta hanyar alamar rashin bata tukuicin kwanciya Wanda hakan na nufin ya gama da ita kenan shikenan kota haihu kawai matsayinta dayane ta haifar masa jininsa, To wannan alamar ce take sakawa kowa dake masarautar yake sanin mace ta samu ciki sai kuma Bayan lokaci nai dan tsayi kafin a fara shirin zabar masa wasu imebēti din, Tenya duk wani shiri na nutsuwa da qamshi me sanyi na bankwana da tirakar sultan shi tayiwa Ayanah tanajin damuwan sanin cikin da zuwa yanzu kowa zaiyi, Karfe goma sha Dayan dare suka iso tirakar tasa wadda kowannensu ya tsaya cak inda shine gurin tsayuwarsu, Silan zinari dayake da adon hoton tafin kafar jariri a jiki tenya ta bude hannun Ayanah ta saka mata batareda cewa komaiba, Wucewa ciki Ayanah tayi batareda ta bude hannunta ba bare tasan sakon menene amma dai sanin yawancin sakon masarautar da alama a silan zinari suke Aikasa dan haka a sanyaye ta isa dakin Wanda yayi sanyi sosai qamshin sa datai sati uku bata shaqa ba yayi shiga hancinta yana ratsa kanta cikin sanyi ta dan Lumshe idanuwanta t bude a natse kafin ta fara Takawa da sanyinta sautin karar sarkar kafarta dayake daban dana matansa yana tashi a kowane takunta yana shiga kunnensa da sautin yakewa dadi, Isowa tayi har inda yake Zaune sanye da Riga da wando masu dan kauri farare qal d suka sakasa komawa tamkar matashin saurayi, Kanta na qasa ta zube qasa ta miqa masa gaisuwanta da muryanta da babu hayaniya a cikinta ko kadan, Amsa gaisuwar yayi yana kasa dauke idanuwansa daga kanta dan kuwa zuwa yanzu ya gama yadda da koma menene Ayanah na basa nutsuwa da sukuni fiyeda kowa dan kuwa ko yayansa baida Wanda zaice gashinan shine yafi so ko ji a zuciya, Bayan kujeran mulkin BOYEM yanajin a yanzu ne ya sake samun abinda bazai taba iya bawa wani ko barin yafita hannunsa dan Hak……. Bai qarasa abinda yake zuciyarsa ba ta dago hannuwanta biyu sama kadan ta bude masa su sakon na bayyana kan idanuwansa kanta na qasa. Qurawa tafin hannun nata ido yayi batareda y kyafta ba dan kuwa wani abin da bai taba ji ba yaji ya soki kirjinsa yana ratsawa na asalin girgiza da mamaki, Bai taba mamakin samun ciki ga mace dayake kwana da ita ba sai kan Ayanah GHAZ wadda ya dauke idanuwansa daga tafin hannun nata ya maida Akan fuskarta data dago ahankali itama Jin shiru idanuwansu suka shiga cikin na juna ya tsareta tsaf da idanuwansa yana kasa motsawa, Duk hadarin dayake cikin samun cikinsa Reno da haihuwansa ya sani Shiyasa sai kakkarfan tsarin Allah suke labari, HAILE batada imani ko tausayi ko kadan Akan kishi da tsananin cika burin duk abinda take so amman bai taba damuwa ba dan itace macen da ikonta yakai tayi duk abinda take so dan itace uwargida kuma mace mafi daraja a BOYEM kasancewanta matarsa kuma bazai taba goge hakan ba amma kuma bayajin Ayanaah GHAZ zata iya wannan rayuwar hadarin, Hannunsa ya miqa ahankali Akan tafin hannunta ya dauki silan ya damqe a tafin hannunsa ya bude Baki cikin nutsuwa sosai yace ‘Ina tayaki Murnar daukan jinin BOYEM, Ina maraba da duk abinda zaki Haifa Ayanah Ghaz.’ Zuru tayiwa idanuwanta akansa sbd kasa fahimtar abinda yake nufi ta kuma kasa bude Baki ta tambaya sedai ta samu kanta a tsananin son fahimtar me hakan ke nufi sbd Wani irin nauyin da kirjinta yayi Abinda ya fada mata shine abinda ake fadawa kowace macen amma ganin irin dauke wutar datai ya sakasa Dora mata da cewa ‘Ina fatan cikin dayake jikinki ya zamo na cikar burina dana qasata gabaki daya’ #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 36 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Wani irin jiri ne ya dibeta me karfin gaske daya sakasa tarota jikinsa yana rungumeta sosai a cikin jikinsa Wanda a yake yaji yana Jin tamkar karfin Mararta datai tudu. Ajiyan zuciya ya sauke yana miqa hannunsa ahankali cikin rigarta zuwa mararta da taurinta ya tokaresa ya shafi cikin a Karan farko kenan rayuwarsa daya shafi cikin tsatsonsa, Lumshe ido yayi tareda jan wani Numfashi mai dumi ya bude ido tamkar yana buge a kanta, Jajir idanuwanta sukai zuciyarta na wata irin harbawan datake nunawa har a kirjinta ya zubawa kirjin ido, Wasu irin hawaye masu tsananin Zafin gaske ne suka gangaro daga idonta suka sauka Akan fatar hannunsa yana kallo bai motsa ba baice komaiba sai kawai yaji sautin kukanta mai tsananin ratsa zuciya ya fasu ta qamqamesa tana kukan jikinta har wata rawa yakeyi tana cusa kanta a kirjinsa. Bai motsa ba baice komaiba kukan ne kadai sautin dayake tashi a dakin Wanda ya sakasa tinani Kala daban daban sautin kukan na ratsa kunnuwansa zuwa cikin kansa da babu komai a cikinsa yanzu Bayan na saiya tabbatarda ta Haifa jininsa koda bazai zo da rai ba saiya kuma mata Wani cikin amma tabbas yanason jininta a cikin yayansa. Kuka sosai tayi a jikinsa har karfinta ya qare tayi lahu dukkanin tinaninta ya toshe babu komai a cikin Kanta empty yake tas, A wannan daren babu abinda ya shiga tsakaninsu a Karan farko haka suka kwana ya sakata a jikinsa sosai dumin jikinta kadai yana basa nutsuwa da sukuni. Asubar fari fitowan Ayanah ta saka su tenya gyara tsayuwarsu jiki duk a mace sbd wannan shine zuwansu na karshe. Tin daga duhun doguwar hanyar isa palon sa na farko tenya zubawa Inuwar Ayanah din ido tana kalla cikeda Wani irin sanyin rashin samun yanda taso, A darare Ayanah take tako wa kafafunta sun mata Wani irin nauyin gagarumar damuwan data kame duka gabban jikinta da idanuwanta tareda kwakwalwanta ko gani sosai batayi take isowa. Kyallin dayake haskowa daga hannuwan Ayanah dan dake gaba ya saka tenya bude idanuwanta da kyau cikeda tsananin tsoro da mamaki sbd babu macen data taba samun ciki ta koma shimfidarsa a tarihi idan ba matansa ba dan haka ganin silallan zinari kaya guda a hannun Ayanah dake gap da rasa ranta sbd tashin hankali da qunci ya sakata Jin kaman tsoro n kamata sbd alamar cigaba da zuwanta tiraka kenan maana indai tenya ta fahimci sakonsa daidai kariya ce ga Ayanah da cikinta dan kuwa cigaba zuwanta na nufin babu Wanda zai zan da akwai ciki a jikinta kenan. Rawa kafafun tenya suka fara dan kuwa wannan lamari ne me girma ke shirin faruwa boyon ciki a masarautar har zuwa haihuwansa. Zufa ta sharce tana tare Ayanaah data kusa faduwa sbd jiri take suma Sauran bayin suka matso dan gaggawar barin gurin da ita, Sakinah kuwa tinda idanunwata suka sauka Akan tukuicin kwanciya da ake bada wa kullum taji zuciyarta tana sanyi da samun nutsuwa godia ta ringa jero wa sbd babu ciki kenan a jikin Ayanah din. Cikeda kulawa aka isa da ita bangarenta daqyar tayi sallah ta sunkuyar da Kai ta fasa kuka mai cin zuciya tana dagawa Allah hannuwanta biyu da Neman sassaucin wainanna kaddarorin nata da basa qarewa daga wannan se wannan dan ayanzu bata San ta ina zata faraba da ciki a jikinta, Bata taba Jin zata iya cigaba da rayuwa a BOYEM ba daga ranar da Allah ya bata ikon fiddo da jininta Zuhrah daga kurkuku, Bata taba Jin kaunar cigaba da rayuwa anan din ba daga ta samu yancin fidda tata yar uwar amma yanzu ga jinin BOYEM a jikinta datasan babu ta yanda jinin BOYEM zai taba barin BOYEM hakama itama batajin zata iya Hana kanta tsananin son abinda zai fito daga cikinta ba, Wace irin kaddara ce wannan zata kawo yarta duniya ta fuskanta a matsayin yar imebeti. Kuka takeyi sosai tana Neman sassauci a gurin ubangiji tareda Neman zabi mafi alkhairi, Haka ta wuni batareda barin kowa ya ganta ba ko sakinah sedai ta kawo mata abinci ya juya babu wata magana fata shiga tsakaninsu sbd ita sakinah samun nutsuwarta shine koma menene tinda ba cikine da Ayanaah ba to da sauki, ita kuma Ayanaah bata iya maganar cikin kwata kwata da kowa ma dan kuwa zata sakawa ranta babu komai a jikinta tabarwa Allah zabi Akan zuwansa duniya yayi rayuwa ko kuwa sabanin hakan Allah zai zabar mata. Da daddare cikeda farin ciki da Wani irin shauqi tenya da kanta ta shirya ta na musamman takaita tiraka, Shi kansa sultan din Ayau wasu shafikan gamsashiyar alaqa ya bude musu daga shi har Ayanah din wadda batada zabin daya wuce duk yanda yayi da ita, Haka ta share sati tana basa sabuwar nutsuwar da bai taba samuba sbd baya kusantar macen dayake ciki koda matarsa dake haihuwa ce Hutu yake bata saita haihu yana yarta tayi wayonda baa zuwa da ita shimfida tukuna take dawowa. A sati Dayan nan ya samu sauyi da sabbin feelings da dama Akan mace haka ya barta ta tafi hutunta. Batareda sanin kowaba Ayanaah ta fara Renan cikinta da ko sakinah batasan dashi ba sbd Sam kwata kwata tenya kowa duniya Bayan ita bata Bari yasan da cikinba sbd tsaro da tsananin kiyayewa. Ana hakan ne faree ta rasu batareda ta haifi abinda yake cikintaba hakan ne ya saka tenya tsananta kariyarta Akan Ayanah, Abinci da ruwa da duk abinda indai Ayanah ce zata ci sa sakinah kadai ce ta yadda da ita kuma ita tabawa babban matsayin da komai na Ayanah itace kadai yake da haqqin kulawa dashi. Ita kanta Ayanah Wani irin yanayi yafara sauyawa a rayuwarta na tsananin son abinda yake cikinta dayake shigarta ahankali Wanda a lokaci daya kuma tsoro yake shigarta dan kaman yanda bata iya rabuwa da yan uwanta yake tsananin sonsu fiyeda kanta ko Bayan baya tareda dasu haka takejin bazata taba iya rabuwa da abinda zata haifaba koda hakan na nufin bada rayuwarta. A Dayan bangaren sakinah ta samu sanin cikin dayake jikin Ayanah sbd fitowan daya fara yi dan a yanzu yana cikin wata na shida harda kwanaki kuma har lokacin tsananin tsaro take cikinsa na rashin sanin cikin Wanda sultan din da kansa ne bai bata Sallamar da zaa San tana dauke da ciki ba, Babban gagarumin abin mamakin dayake sake saka tenya da MARAKI ma tsoro sosai shine tsawon watannin shida kenan da HAILE ta bugaci samun hutu daga sultan sbd rashin lafiya dan haka tsawon wannan lokacin babu Wanda yake ganinta tana bangarenta a killace tana hutawa, Sultan ya bata hutun datake buqata batareda ya buqaci wasu sabbin imebētis dinba sbd samun kwanaki masu yawa na kasancewa sa AYANAH GHAZ wadda cikinta yake girma a hannunsa da jikinsa dan kuwa sati biyu cif yakeyi da ita kafin yayi sati uku da maraki, HAILE ciki ne da ita da manyan bokayen qasa suka tabbatar mata da haihuwar da zaayi a yanzu kafin kowace haihuwa a BOYEM ta ‘da namiji ce Wanda taurari biyu suke gani a duk lokacinda suka duba da Wanda yake a miqe da Wanda ya karkace amma basu samo maanar hakan ba tukuna amma dai sun bata tabbacin namijin ne jinin dazai sauka a masarautar wannan Karan. Wannan tabbacin da aka bata ya sakata daukan kakkarfan alwashin kashe duk mai cikin da zata rigata haihuwa dan hakanne aka wayi gari faree tabar duniya sbd kada ma a samu akasin wata ta rigata haihuwa ta Haifa namiji tinda sun bata tabbacin namiji ne zaa Haifa bawai kuma lallai sai ita ba. Wannan cikin datake Reno a boye tanada Wani irin Buri da quduri mai tsaurin gaske akansa hakama daga kansa batajin daga kansa sultan zai sake haihuwa da kowace mace Bayan ita duk wadda Allah yasa ma ta dauki cikin to tabbas zata bar duniya dan babu wani dan da zata yadda a haifawa sultan Wanda zaiyi gasar karban mulkin BOYEM da ‘danta sbd kujeran BOYEM ta ‘danta ce shi kadai koda kuwa rayuka da dama ne jininsu zai ringa gudana a shirye take ba sauki ko kadan, *****a lokacinda HAILE ke boyon cikinta dake qara kusantar lokacin haihuwa itama Ayanah nata cikin yana gap da kusantar haihuwa kuma har lokacin sultan samun nutsuwa yakeyi da ita wadda a yanzu ne yake sake ciki da wajen mace dan kuwa cikinta ya bayyanar masa da abubuwa da dama dayake fatar taci gaba da haihuwan dukkanin yayan da zasu rage masa ya Haifa dan kuwa Ayanaah ghaz takai dukkanin matakin dabai kamata ba ta isa a zuciya,ruhi da gangar jikinsa da ayanzu bata appreciating kowace mace a shimfidarsa idan ba ita ba dan kuwa labarin imebeti a zamanin sa na Neman shifewa dan Bayan ita haryanzu babu imebetin daya karba an tsaya daga nan. Want haihuwan Ayanah ya tsaya hankalin tenya da sakinah yafara tashi sun duqufa tareda maida dukkanin adduarsu ga Allah Akan samun ‘dan da duniya gabaki daya zatai alfahari dashi, Irin adduar dasu sakinah kewa cikin da ita kanta Ayanaah din ya saka take samun karfin gwiwan haihuwan da fatan haihuwar cikin sauki da aminci. Kamar a mafarki Ayanah ta bude fararen idanuwanta da sukai nauyin bacci ta saukewa fuskar sultan dake gabanta Zaune yana mata Wani kallan dayake Jin kaman zai sauya kaddararta zuwa wadda babu me iya sake ganinta a duniya, Hannunsa dake wuyanta tabi da Wani irin kallo tana Jin zuciyarta na bugawa da karfi ta sauke idonta a wuyanta da sarkar wishmah ta bayyana wadda ya saka mata a cikin baccinta, Wani irin mummunan Juyawa taji kanta nayi Wanda ya saka mararta murdawa da karfin gaske a take wasu ruwa masu karfin gaske na haihuwa suka fashe mata duka sbd mummunan girgiza da shock mafi girma a rayuwanta na zama wishmah ta uku a tarihin BOYEM kaf.. Gadan gadan naquda me karfin gaske ta taso mata take aka shigo aka fita da ita mahaukaciyar sarkan daham din data saka BOYEM gabaki daya girgiza tana wuyanta. Tenya da duk Wanda aka daukota dasu Wani irin shook suke shiga na ganin abinda anfi shekaru dari kafin wani ya sakata a wuyansa se ayau, Kamar a mafarki aka saki qararrawar datake gauraye BOYEM har cikin gari dayake sanar da kakkarfan labarin sabuwar WISHMAH Masarautar BOYEM, Labarin sabuwar wishmah a qasar da labarin naqudar datake yi a yau din lokaci daya ya buga kunnuwan mutane musamman manyan BOYEM da kusan kowa ya fara shirin gaggawar isa fada inda duk wani babba me babban matsayi a BOYEM zasu zauna tareda sultan jiran dakon lokacin naqudar har zuwa haihuwa sbd sanarwar haihuwar wata gagarumin lamari ne tinda magajin BOYEM ake jira dan haka take masarautar tayi tsit komai ya tsaya cak sai ta haihu zaayi bikin qaddamar da ita wishimah Wanda yake tamkar daurin aure ne. A daidai wannan lokacin sautin qarar bayyana da tabbatuwar wishmah a BOYEM ya shiga kunnuwan HAILE wadda ta miqe daga Zaunen datake kanta na Wani irin mummunan sarawa kafin ta bude Baki baiwarta ta iso da sauri kanta a qasa ta zube gabanta ta isar mata da imebētis Ayanah ghaz na naqud….. Bata rife Baki ba jini ya ballewa HAILE tareda ruwan naquda masu karfin gaske tana dafe cikinta da tsananin karfin gaske sbd naquda mai Zafin gaske data taso mata gadan gadan itama. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 37 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Cikin gaggawa da tsananin sauri babbar jakadiyarta mai suna fatto ta iso tana riqeta hannuwanta na rawa da kakkarwa ta riqeta tana sanar da bayin suyi gaggawar gyara dakin da zatai naqudar. A take kuwa duka bayin dake babban bangaren nata suka hau shirin gaggawan tarban haihuwar, Ruwa da wasu abubuwan al’adah suka fara gaggauta hadawa wasu kuma na gyara Wani lafiyayyan daki daya a cikin tarin dakunan dake bangaren nata, Jini ne sosai yake zubar mata Wanda ya saka hankalin fetto da Sauran manyan bayin nata tashi take akai gaggawar isa da ita dakin da akaiwa shirin karban haihuwar tata aka kwantar da ita idanuwanta a rantse cikeda wata mummunar azabar datake sake tsananta tafasa jininta dake wata irin tafarfasa, Budewa idanuwanta tayi da sukai wani mummunan ja zufa na jiqata ta sako wani azababben nishi tana bude baki da karfi cikin azabar datake ratsata tace ‘Sultan yasan da cikin kuma yaci gaba da kwanciya da ita a tirakarsa……. Wishmah a Masarautar BOYEM yanzu? Qarni qarni sun shude harma tarihin samun wishmah a BOYEM yana shirin shudewa shine yanzu rana tsaka sabuwar wishmah zata bayyana Akan sultan YASAR? Me take dashi wannan imebetin? Wace ce ita? Tayaya zata samu matsayin wishmah dake kusan nuni da itace macen datake zuciyarsa fiyeda matansa na aure……… Wani Ihu mai tsananin qarar gaske ta sake jikinta na wata irin jijjiga da fizga, Azabar naquda takeji tana ratsa dukkanin qasusuwan jikinta amma kuma baqin cikin dayake ratsa jininta shi takejin yana Neman kasheta dan kuwa Ayau da ba tata naqudar takeyiba wlh tallahi bazata Bari Ayanah ghaz ta haihuba, Wani irin yunqurin azaba ta fara gabobinta na amsa wata kakkarfar azaba sbd bazata iya yadda Ayanah ta rigata haihuwa ba dan kuwa a tabbacin bokayenta sun tabbatar mata da duk haihuwar da zaa fara a BOYEM yanzu to tabbas namiji ne taurari sun buga sun buga sun tabbatar da hakan dan haka ko zata yage saita turo abinda yake cikinta ya fado duniya, Cikin tsananin kulawa babbar yarta ta iso bangaren cikeda damuwa da kulawa ta iso ta gefen mahaifiyars tata batareda tana ganin wasanta dake rufe kare da wani babban kyalle green su fetto da likita mace daya da suka kirawo sai babbar baiwarta daya suna kokarin karban haihuwan duk sun hada Wani irin gumi, Nauyi da azaba tareda rikice wa naqudar tayi wadda take sake saka jini fitowa da sauri fetto ta kalli HAILE din wadda azabar tayiwa yawan da tana kokarin ficewa hayyacinta ta bude baki zatai magana cikin girmammen baqin ciki da ukuba HAILE tace bata bawa kowa ikon ce mata komai ba matiqar ba haihuwan suka tayata yiba, Likita data dago yin maganar dole suna buqatar kiran Sauran likitocin da zasu taimaka mata Jin abinda Hailen ta fada ya sakata yin shiru tana hada zufan tashin hankali sbd akwai Sauran time dan kuwa service dinta baima gama budewa ba dan haka sunada aiki sosai ga naqudar bame sauki bace yakeyi tinda shock ne Kai tsaye ya tado naqudar, Fetto Kai da kawo ta fara tana fitowa tana komawa cikin tsananin tsoro da tashin hankali me girma ga Masarautar tayi Wani irin tsit babu motsin komai bare kowa alaman duka manyan BOYEM sun taru a fada jiran naqudar Ayanah ghaz wadda itace wadda kaf BOYEM yanzu ake jira dan haka a kakkarfar doka da baa takewa ta Masarautar gabaki dayanta shine duk jinin BOYEM idan zaa Haifa Ana fara naqudar sa babu me sake fitowa bare kaida kawo tsit akeyi har sai ta sauka dan Kai tsaye duk Wanda tsautsayi ya sakasa fitowa ko kaida kawo a hanya cire kansa daga gangar jikinsa ya halasta, Dan haka ne Ayau dinma babu motsin komai bare hayaniyar komai koina tsit ne tamkar babu dan Adam ko daya a cikin masarautar BOYEM din, Duka tarin bayin daka bangaren Haile sun gama shirin tarban abinda zata Haifa dan haka a tsaye suke qyam babu kowane motsi dayake tashi suka anan din sai fetto daka Kai da kawo kaman zata rasa hankalinta ta zare, Zufa sosai take hadawa gashi ba ikon magana so take taje ta isarwa sa sultan labarin naqudar Haile amma ba damar fita dan fitarta daidai take da kwananta kabari Ayau din dan saita bar duniya dan haka babu damar fita, Su kansu bayin dake bangaren duka babu Wanda ma yakeda ikon motsi bare fita zuwa isar da sako dan haka ta rasa yaya zatai da rayuwarta fa naqudar sai abu daya ake kwata kwata babyn bai fitoba, Ita kanta likitan kokarin tsayar mata daya jinin tayi da taimkon da zata iya bata amma dole haihuwa sai lokacin da Allah yace babyn ya fito zai fito dan haka dukansu zufa suke hadawa ba qarami ba suna rasa abin yi har HAILE din tayi Laushi sosai amma taqi yadda kowa ya tsaya hutawa sbd baqin taurin ranta Akan kada Ayanah ta rigata haihuwa, Tana tsananin buqatar likita amma babu me ikon fita dan kuwa koda Ka isa ka isar da sako tabbas zaka karbi hukuncin barin duniyar Ka dole Shiyasa kowannensu yake hada zufa suna Kai da kawon taimaka mata gurin samun sassaucin abinda take ji, Zufan fuskarta zuwa wuyanta ake goge mata da tsaftataccen farin towel qarami suna Jera mata Sannu da kokarin ganin ta haihu lafiya, magani kuwa haka ake kawo mata shi tana sha tana dawo da wani sbd tafara Nisan da bata iya Shan komai amma a zuciyarta ta kasa sake adduar datake yi guda daya tak wato ‘Allah ya bata ‘da namiji koma yayane kuma Allah yasa itace zata fara haihuwa’ Wannan adduar take ta maimaitawa tana kasa sakewa dan tabbacin datake dashi na Allah yana karban adduar me naquda dan haka har a tafara ficewa hayyacinta bata roqarwa kanta ko ‘yayanta komai sai wannan adduar gida biyu. ****A daidai wannan lokacin naquda sosai AYANAH GHAZ takeyi me tsanani itama Wanda ya saka itama nata bangaren da bangaren imebētis din kaf yin tsit babu ko abu daya dayake bada sauti sbd Masarautar wannan Karan tafi kowane karo yin tsit dan kuwa mamaki biyu ne yake ci da kashe kowa amma b damar magana a yanzu wato shine Wishmah data tabbata Bayan qarnika da kuma haihuwar da baa San da cikinba kuma a hakan taci gaba da zuwa shimfidar sultan, Wannan duka wasu abu ne da suka girgiza masarautar da duk Wanda yake cikinta cikeda tsoro da mamakin dayafi Kama da firgici kowa yake, Masu rubuta tarihin qasar BOYEM da Masarautar BOYEM kuwa a daidai wannan lokacin suna can sun fara rubuta wa a cikin kundun tarihi, A cikin fadar sultan ma a inda ake Zaune tsit abu daya kowa ke jira wannan Karan sunfi kowace lokaci daukan tsit sbd Ana magana a tsakaninsu duk zaman jiran da akeyi amma a wannan Karan sultan YASAR babu abinda ya bude baki ya furta hankali da nutsuwar sa kaf suna ga jiran sakon haihuwan Ayanah ghaz dake saka zuciyarsa cika da Wani irin nauyi da yanayi na tsumayi dabai taba shiga b duk haihuwan da ake masa, Sosai yakejin kowace daqiqa tana wucewa ne da bugu wan zuciyarsa mai karfin Akan haihuwar yau dayake jinta har jini da bargonsa dan haka take duk Wanda yake fadar ya dauke wuta sukai tsit suma suna shiga tsimayin jira da Jin tsananin son labarin haihuwan wishmah ta farko data sauya tarihi da dama na masarautar qasar BOYEM gabaki dayanta dan haka sai sukejin haihuwan ta jinin BOYEM wannan Karan ta daban ce a gurin sultan da wannan dalilin suka ta zama ta musamman din tinda kuwa wishmah ce zata haihu kowa yasan haihuwan soyayya ce bata saurauta ba. Tenya data kasa ta tsare ko motsawa batai ba daga gaban Ayanah dan kuwa duk inda hannuwan likitoci suka taba a jikinta idonta na Kai sbd tsananin tsaro da rashin yadda da kowa, Sakinah ma a wannan lokacin tana riqe da hannun Ayanah gamgam suna hada zufan tare tana Jin duk radadin da Ayanah ke ji a zuciyarta tana Jin tsananin matsuwa da son haihuwan Ayanah lafiya tana saka mata addua mai kyau a bakinta, A bakin Ayanah din addua ce guda biyu rak take fita wato Allah ya zama gatan yan uwanta dasuke raye ya kawo sauyi a rayuwarsu sai kuma adduar Allah ya tsaya Akan kowane irin lamarin babynta da zata Haifa,Allah ya haskaka rayuwarsa ya basa kariya daga duka Sharrin duniya’ Wannan adduar itace take maimaituwa a Baki da zuciyar Ayanah da sakinah harma da tenya da ita iya babyn takewa adduar Allah ya basa kariya har qarshen rayuwa kowannensu a zuci yake adduar. Sosai azabar tayi mata yawan data fara galabaita tsananin tausayinta na saka zuciyoyinsu sanyaya dan haka suka dage da addua da karfi da imaninsu suna Neman mata sauki a gurin ubangiji, Sakinah jiqe take shar kaf da zufa tana tsananta adduarta a fili tana share zufan Ayanah suna sake qanqame hannun juna Ayanah na Jin kaman bazata rayuba rayuwarta zata tsaya ne daga nan sbd abinda take ji tabbas shine kowace uwa takeji yayin jeho yaya a duniya idan har ta mutu anan ta tabbatarda tayi shahada dan haka take Jin inama zata mutu anan din ta huta. Lokuta masu tsayi suka dauka dukansu suna naquda me tsayi da rashin sauki, Babu wadda bata Kai qarshen jigata ba a cikinsu tareda fita hayyaci, Duk wainda suke tareda su sun sare sun shiga tsoro da fargaba tsawon wunin da babu komai cikinsa sai jiran azaba, Karfe shida na yamma a lokacin da baby ya turo kai fitowa jikin HAILE gadan gadan take su fetto suka shirya tsaf ma tarbansa cikin tsananin matsuwa sbd suna sane da har lokacin Ayanah ghaz bata haihu ba dan akwai sautin karar da ake sakewa masarautar ta amsa gaba daya idan an haihu dan haka tinda basu ji komai ba sun San bata haihunba gashi yanzu tasu zata far haihuwa babbar matsalar shine fita a wannan lokacin batareda haihuwan Ayanah ba zuwa isar da sakon haihuwar. Cikin azababbiyar azaba da Nishin dayake hade da ihu mai karfi Haile ta saki tana qanqame hannuwan yarta da karfin gaske ta sunbulo babyn dayake cikinta ya fado a hannun likitar dake gabanta idanuwan fetto kaman zasu fado qasa sbd jiran ganin abinda aka Haifa, A daidai wannan lokacin itama Ayanah ta sauke wani kakkarfan nishin daya fito da nata babyn duniya itama Wanda ya fado a hannun tenya Wanda jikinta ya dauki mummunan kakkarwar abinda aka Haifa tama kasa yadda da abinda ta gani. #MAMUH #THE LION ARRVL HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 38 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Doctors din guda biyu na masarautar tin tsawon shekaru masu dan dama da basa karban kowace haihuwa sai ta asalin Matar sarki qananun su ne suke karban haihuwan imebētis amma Ayau sune sultan da kansa ya bada sakon umarnin kiransu amsar haihuwan wishmansa Shiyasa Haile bata samu damar samunsu a masu karban haihuwant wannan Karan koda kuwa Ana iya samun damar dan aike ya fita a lokacin naqudar to ba samunsu zatai ba sbd suna Akan wishmar BOYEM, Ajiyan zuciya suka ringa saukewa suna kallan babyn Wanda kukansa mai karfin gaske ya cike dakin da bangaren gabaki dayansa harma daga wajen GHAZ chambers Ana jiyo kukan nasa. Ita kanta tenya ajiyar zuciyar ta ringa jerowa ba kakkautawa kafin ta bude Baki da karfi tana cewa ‘MashaAllahhh,Barakallahu laka fi’l-mawhubi lak,wa shakarta’l wahib,wa balagha ashuddah,wa riziqta birrah. ALHAMDULLILLAH YA ALLAH’ ta qarasa fada da karfi tana karban lallausan showel fari tas hannuwanta na rawa ta dunqulesa tana dawo da kallanta Akan Ayanah cikin rawar murya tace ‘Allah ya qara miki Nisan kwana da lafiya tareda albarka me dorewa UWAR BOYEM GABAKI DAYANTA TA YANZU, UWA GA ZAKIN BOYEM, UWAR MAZAJEN BOYEM, UWAR ME BOYEM NA GABA. Sakinah rawa jikinta ya dauka da karfin gaske tana juyowa da karfi ta tsira wa babyn hannun tenya din ido bata ko kyaftawa. Ayanah ma duk da bata hayyacinta bata dawo daidaiba bude jajayen idanunwata tayi zufanta na qaruwa ta zubawa hannun tenya ido tana kasa gasgata da gaske namijin da qasar BOYEM da qasoshi da dama suke jira shi ta haifa, Hawaye ne suke kokarin ciko idanuwanta na fargaba tsoro da tsananin tausayi da son danta da rikicin qasar gabaki dayanta yake jiransa. A daidai wannan lokacin bangaren HAILE shima wani Tiriri ya dauka na samuwar cikar Buri dan kuwa itama namijin ne ta haifa Wanda ya sakata kokarin tashi da kanta dan isar da sakon haihuwar ‘da namijin ga sultan tin kafin Ayanaah ta haihu sbd farin cikin samun cikar burin shekaru ya mantar dashi Ayanah da kowa menene zata haifa. Hanata Miqewa likita ke kokarin yi tareda yarta harma da fetto sbd jinin da babu sosai a jikinta kuzari tareda azabtuwar datai sosai tayi pale sosai suka dage cikin tsananin kulawa da kauna dan komai ze iya faruwa da ita idan ta tashi tsaye amma Sam taqi yadda da hakan rungume take qam da babyn tana kokarin Miqewa zuciyarta a rufe bata Jin ko zata rasa ranta zata iya jiran Ayanah ta haihu batareda sultan yafara sanin ta haifa Zakin qasar BOYEM ba, Miqewa tayi suka miqe dukansu tareda riqeta zuciyoyinsu da hankalinsu duka a tashe da mugun tsoro da tashin hankalin hukuncin laifin da suke kokarin aikatawa na Binta su fita, Wani jinin ne ya kuma gangarowa daga qafafunta Wanda ya saka hankalinsu sake tashi dake sauri bayi biyu sukai saurin durqusawa suna goge mata jiki da towel me dumi da suka matse daga ruwan Zafin da aka goge mata jiki gabaki daya. Sake shiga tashin hankali su fetto da likitar sukai harma da ‘yarta sbd hatta ita Haile din hukunci zai iya hawa kanta dan babban tsatsauran dalilin daya saka wannan tsaurin yake a masarautar lokacin haihuwan kwace mace shine hana cutatar da kowace jaririn da zaa haifa ko uwarsa kokuma sace jarirai musayarsu dan haka baa yanzu wannan dokar take ba tin asalin asalin kafa masarautar yake. Jiri ne sosai da rashin isashen jini ke Neman zubar da ita amma a haka suka riqeta dan suma bazasu taba son imebetin ta haihu batareda sultan yasan an samu magajin BOYEM ba, Taku daya biyu sukai suna daga qafafunsu su hudun a tare zasu fito dakin wata kakkarfar sautin qarar da baa taba kada wa ba tin tsawon shekarun da sultan YASAR ya hau mulki bace ta ratsa kunnuwansu cikin sanyi da rikitaccen yanayin daya saka dukkaninsu Sakinta cikin mugun firgita da ficewa hayyacin dan kuwa sautine dayake fadawa BOYEM da duniya gabaki daya MAGAJI kuma ZAKIN BOYEM ya sauka a duniya tsohuwar imebeti sabuwar wishmah AYANAH GHAZ ta haifosa. Shigar sautin kunnuwan Sultan YASAR da gabaki daya manyan masarautar boyem a lokaci daya suka zube qasa suna yiwa Allah sujjada batareda ma sun sani ba, Haile kuwa Numfashi daya ta fitar bugun zuciyarta ya tsaya cak sakamakon sautin sakon daya ratsa kunnuwanta ya Harba cikin kwakwalwanta ta zube a gurin jaririn hannunta yana subucewa daga hannunta zuwa qasa, Cikin wata gaggawa da tashin hankalin dayake Ninkuwa Akan mugun shock din dasuke ciki fetto ta tare babyn koina na jikinta na rawa da kakkarwa, ‘Yarta Aslam ce tayi saurin tarota jikinta itama jikin nata yana rawa sosai da firgici tareda tsananin tsoro sukai qasa har ita har mahaifiyar tata sbd batada karfin da zata iya riqeta tinda jikinta a sake yake kaman babu rai a jikinta, Dr Kadee ce tayi saurin bin Aslam din qasa tana tayata riqe Hailen itama jikinta rawa yakeyi da firgicin yanda duk wahala da azabar da suka sha ta tashi a iska labarin haihuwan Ayanaah ghaz ya fara shiga kunnuwan sultan YASAR da qasar BOYEM harma da duniya gabaki daya. Fetto babyn ta rungume jikinta tareda budesa sa sauri taba duba idan yana raye babu abinda ya samesa daga faduwar taga lafiyarsa kalau sedai tinda aka haifesa baya wani kuka saida ya fadin ya fasa kuka sosai Wanda ya sakasu sauke ajiyan zuciya suna tattalar HAILE din dan maidata shimfida a bata taimakon gaggawa. ***A daidai wannan lokacin kuma sautin qarar ya ratsa kunnuwan Zuhrah dake Zaune daqyar sbd azaba da rashin lafiyar da kowace gabar jikinta keyi a cikin wani irin kurkuku mara Kyan gani, Tinda aka sanar da Masarautar kaf cewa imebeti AYANAH GHAZ na naquda ta tashi Zaunen idanuwanta dake ciwo basa gani sosai ta bude su tareda daga Kai sama ta qurawa sama ido tafara jerowa Ayanah da abinda zata haifa addua jikinta na rawa tana fadawa Allah adduarta Akan yar uwarta Bata Dena addua da fadawa Allah ya tsayu Akan rayuwar babyn ayanah dinta ba har saida sautin ya ratsa kunnuwanta Wanda ya sakata rufe idanuwanta ahankali tana silalewa qasa kwance tareda fashewa da Wani irin kuka mai ratsa zuciya tana gode wa Allah da bai karbi ran ayanarta gurin haihuwa hakama wata irin tsananin kewarta da kaunar son ganinta a lokacin ta saka sabbin hawaye gangaro mat a tana Jin tsananin so da ganin abinda Ayanah ta haifa musu ta rungumesa a jikinta taji duminsa tareda sakawa rayuwarsa albarka da fada masa sun yafe masa ita da ‘yan uwanta da basa raye sbd kaddarar haihuwansa a jinin BOYEM ce ta lalata tasu rayuwar da babu gyara a cikinta har abada. Rufe idanunwata tayi hawayen data manta rabon datai yi su sbd kuka ma kansa ya gujeta sai Ayau din datake Jin kewa da tsananin son Ayanah da ‘danta suna ratsata. ****A kuma wannan lokacin ne sultan YASAR ya dago daga sujjadarsa ya daga hannu sama yayiwa Allah godia yana jerowa dan nasa addua me tsananin karfi, Danyen zinari aka fara fitowa dashi a tray mai shegen kyau aka fara kyautarsa a matsayin tukuici hakama duka manyan dake cikin farin ciki mai tsanani da annashuwa suka fara gabatar da tukuici ga AYANAH GHAZ da kyautar data ringa girgiza mutane da tabbatarda Ayau burin qasar BOYEM ya cika na shekaru, Ko da tenya ta fito daga babban kofar fitowa bangaren Wishmah gabaki daya wasu irin securities ne da bayin da zasu rakata har zuwa fada Sbd Mai BOYEM dayake hannunta. Gabaki daya Wani irin Juyawa tenya taji kanta na yi sbd tarin bayi da securities da suka cika hanyar dan kawai rakiyar Magajin BOYEM ga mahaifinsa. Kafafunta sanyi sukeyi mata a duk lokacinda tayi Taku daya na tafiya zuwa fadar mai girma sultan YASAR dauke da jaririn dayafi kowane ‘da daraja a qasar BOYEM yana dunqule cikin farin lallausan bargon daya babu hannun Wanda ya shiga duniya Bayan nata saiya shiga hannun mahaifinsa kafin ma ya shiga hannun mahaifiyar data haifesa, Kai tsaye hanyar fada suka isa babyn na rungume a jikin Tenya data ke Jin sabuwar duniya ce yake kafuwa a BOYEM daga lokacin da ‘dan nan ya gado duniya. Isowarsu bakin kofar fadar da Wani irin tsit akai tareda wangale mata kofa Sauran securities da bayin suka tsaya daga kofa ta sako kafarta ta dama ta shigo tana Takawa cikin nutsuwa tana nufar karagar mulkin BOYEM da sultan yake Kai idanuwansa masu tsananin kyau da kwarjini suna kan hannuwanta biyu dake rungume da hasken dayake tsaya zuciya da idaniyarsa, Dukkanin Wanda yake cikin makekiyar fadar da Taku ne me yawa kafin Ka isa karagar daga bakin kofa kowa idanuwansa Akan hannun tenya yake suna fidda silallan zinari a gabansu suna ajiye wa qasa inda duk tenya ta taka ta wuce matsayin tukuici gareta ita kanta Wanda hakan ke saka kafafun tenya rawa da farin cikin datake Jin kaman zata some tin daga lokacin da magaji ya shiga hannunta. Ko data isa gaban sultan YASAR a hankali ta zube Akan gwowowinta tareda daga masa magajin BOYEM tana miqa masa kanta a qasa tana zuba masa Wani irin Kirarin daya saka fadar dama masarautar yin tsit sautin muryanta me karfi ce kawai taje tashi tana amsa Amon kirarin datake wa sultan YASAR da magajinsa. Wasu manyan sarkokin zinari ne aka fito dasu Ana tsayawa gefenta dasu Sultan da hannuwansa ke rawa miqawa yayi ya dauki babyn dake kan hannunta yana ambatar sunan Allah da sautin daya saka kowa maimaita sunan Allah din, Ita kuwa tenya sultan na dauke babyn daga hannunta aka fara dora mata sarkokin zinarin tukuicinta tayi qasa da Kai tana zubda hawayen farin cikin samun cikar Buri. Addua da huduba sultan ya daga babyn yayi masa tareda rungumesa jikinsa tsawon mintina uku kafin ya dago idanuwansa da kwarjinsu ya sake cike niimar gurin ya bude Baki da sautin daya saka tsigar jikin duk Wanda yake gurin tashi ya ambacesa da sunan daya saka masa Wanda duniya zata kirasa dashi, ‘LEUL NU’AB ALMAZZ YASAR BOYEM’ #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 39 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* A take gabaki daya fadar kowa ya miqe tsaye suna sakawa LEUL NUAB albarka cikeda wata irin girmamawa da shauqi Su kuwa bayi gabaki daya cikin fadar dana kofa da waje zubewa sukai qasa kawunansu a qasa suna masa adduar securities ma qame wa sukai suna sare maza da addua. Tenya da gashin jikinta ke tashi yana qarawa bude Baki tayi ta ringa jero sabbin kirari da addua kafin sultan ya maida mata Almazz din hannunta ta amsa Bayan ta miqa tukuicinta ga bayinta kafin ta miqe tsaye A lokacin ne aka fara fitowa da wasu sabbi trays masu dauke da sarkokin da suka sakata rungume LEUL da kyau sbd rawan da hannunta yakeyi, Tukuicine ga Wishmah AYANAH GHAZ na hasken idanuwan da ruhin data basa Wanda zuciyarsa bazata taba mantawaba da wannan feeling din da itace tafara basa shi dan kuwa koda zai samu wani haihuwan namijin a gaba to tabbas wannan feeling din na farko na daban ne daya bude zuciyarsa ga abubuwa da dama ya kuma kulle wasu kofofin dake zuciyar tasa da dama. Bayin tenya dana wishmah dinne suka fara shigowa a hankali suna jeruwa suna daukan tukuicin Ayanah Wanda ya ringa fitowa daya bayan daya daga masu boyem dake cike a fadar harma da wainda ke isowa a lokacin da securities dinsu dan samun raya farin cikin lamarin batareda bata lokaci ba, Tukuicin MARAKI ne itama ya iso a lafiyayyan tray din silver mai kyau an rufesa da wani golden kyalle mai kyau da daukan ido itama set din sarkar kafa ce data Kai sai sarkar hannuwa biyu duk na gwal masu kyau marasa nauyi, Karba akai Bayan ansanar daga inda kyautar ta fito take bayi suka zube suna miqa godia ga jakadiyarta data kawo sakon tareda bayi biyu. Tarin kyautar isowan LEUL duniya harya fi na mahaifiyarsa da aka bata tukuicin haihuwar sa dan kuwa shi haka ake zuba silallan zinari a cikin kyautar da ake masa kaman baa san zafi da ciwon su ba tamkar abin banza, Shiru babu dan sakon Haile na miqa taya Murnarta ga sultan bisa ga wannan gagarumin cikar burin da babu kamarsa da Allah ya cika masa, Tenya data matsu a koma da LEUL gurin mahaifiyarsa ta sakasa a jikinta itama taji duminsa zuciya da ruhinta su samu sassauci shima ya samu shiga jikin mahaifiyar data haifesa duminta ya ratsashi Miqewa tayi tana sake godia suka juya zasu fice tareda tarin kyautitikan da zasu sauya rayuwarsu da duk ahalin da zaa haifo a zuriar su, Taku biyu tayi aka qwalla sanarwar shigowan me isar da sako daga bangaren Haile dan haka take tenya ta daya cak sbd dole ne tsayawan kowa idan zaa isar da sakon masu boyem, Fetto ce ta sako Kai a cikin fadar kafarta ta dama itama ta fara sako wa a cikin fadar koina nata rawa yakeyi amma ta kanne zuciyarta babu abinda take tsananin marari Bayan isa gaban sultan ta isar da labarin haihuwan magajin sa daga Haile datake matarsa ba imebeti ba dan kuwa a tsatsaurar dokar boyem matiqar akwai ‘da namiji daga Mata to ‘dan imebeti bazai taba zama magaji ba dan haka da confidence mai girma ta tinkaro tsakiyar fadar dauke da farin showel itama a hannunta babyn dake ciki na kwance A ciki yana bacci hankali kwance. Tenya kafe idanuwanta tayi a hannun fetto din zuciyarta na dan bugawa da tinani masu tsauri da girma Kala kala sbd idan idanunwata suna gani daidai baby ne a hannun fetto din Wanda da alama shima baa jima da haihuwansa ba, Gabaki daya wainda ke fadar tsaida idanuwansu Akan hannun fetto sukai cikeda mamaki da shiga tinanin ko yan biyu Ayanah ta haifa Sai yanzu Dayan ya fito to amma ganin jakadiyar HAILE kuma sako daga bangaren Haile akace ya saka kowa aje tinanin yan biyu aka haifa. Fetto na isowa tsakiyar fadar me girman gaske zubewa qasa tayi ahankali kanta na qasa ta daga babyn cikeda kulawa da girmamawa me girma tafara zubo masa kirari kafin daga karshe ta sanar dashi queen HAILE ta sauka awa daya da mintina arbain da tara da suka wuce Wanda sakamakon cikin datake Reno ne ya sakata karban hutun zuwa tiraka kuma tayi hakan ne sbd kebe kanta ta samu jinya da Renan ciki mai nutsuwa kuma a cikin yardar Allah ta haifo asalin magajin boyem. Da tsananin mamakin daya dakatar da komai kowa ke kallan hannun fetto din shock na kama kowa, Tenya ma wani irin dum taji kunnuwanta sunyi ta rungume LEUL da karfi kirjinta tana kasa dauke idanuwanta Akan hannuwan fetto zuciyarta na nauyi da tsananin mamaki da tashin hankalin maganar fetto din kafin ta maida idanunwata Akan sultan YASAR da shima shiru Yayi idanunwansa Akan fetto tsawon seconds kafin ya maida idanuwansa Akan babyn hannun nata ya kallesa yana mamaki mai tsananin daya dan bayyana. Tsit koina da kowa yayi Ana rasa abin fada sbd magana dai a Kai tsaye take babu wani kwana kwana kowa ya fahimci komai da fetto ta fada babu abinda kowa zaice bai ji daidai ba kokuma Neman karin bayani akai Kai tsaye itama HAILE magaji ta haifarwa Masarauta. Sultan da yayi shiru yana kallan babyn kawai suke jiran bayani daga garesa Wanda shima kai tsaye yaji komai daidai ba buqatan kowace tambaya Akan qarin bayanin komai, Mintina aka share kafin sultan ya sauke Numfashi me sanyi tareda dauke ajiyan zuciya mata sauti zuciyarsa na ratsuwa da wani sabon farin cikin samun wani hasken idanuyar da baima San dashi ba dan haka hannuwansa ya miqa a natse cikeda kulawa da soyayya mai karfi ta uba ga ‘dansa ya amshesa tareda rungumesa a jikinsa na mintina shima yana masa addua kafin yayi nasa huduba ya daga sa sama ya ambacesa da, ‘LI’ULI ASIM YASAR ALMAZZ BOYEM’ (prince Asim yasar almazz boyem) Take kowa ya maimaita sunan suna saka masa albarka tareda addua duk da baaji shauqin na ratsa jini da kwakwalwaba kaman farkon amma shima sunyi Murna sosai da kasancewansa sabon prince din boyem hakama yau rana ce mafi girma da tarihi tinda aka haifar musu jaruman babys biyu a daya rana. Kyauta da tukuici aka fara fiddawa Ana bawa fetto itama sedai kasancewan baa San da haihuwan ba bata samu kyauta irin wadda tenya ta samu ba sultan kuwa kyautarsa da tukuicin sa daidai iri daya yayi da wadda yayiwa NU’AB, Cikin karfin Hali da dake wani zuciya fetto ta karbi ASIM tareda dagasa tayi masa kikarin daya saka kowa yin tsit dan kuwa Kai tsaye da asalin magajin sarki ta kirasa bayan sultan ya riga ya Ambaci NUAB da magajin BOYEM. Dagowa sultan yayi da fararen idanuwansa da sukai wani haske da kwarjini sbd yanayin dayake ciki a yau din zai kalli fetto sbd lokacin data fada cewan an haifi ASIM ALMAZZ tabbas kenan ya riga NUAB fadowa duniya sedai kuma NUAB ne Wanda ya fara shiga hannuwansa, NUAB ne Wanda ya fara cike zuciyarsa da yanayin dabai taba shiga ba na samun magaji, NUAB ne Wanda labarin haihuwansa ya fara ratsa kunnuwansa da kunnuwan duk Wanda yake BOYEM da zagayenta, NUAB shine Wanda ya fara dagawa duniya ya ambacesa da LEUL BOYEM….. Ganin tinanin da sultan yayi shiga Akan tsakanin ‘yaya biyun waye magajin gasken ya tenya zubewa qasa da Wani irin saurin gaske tana daga NUAB da ladabin gaske ta bude Baki tace ‘Allah ya qarawa jini da ruhinka tsarki sultan me BOYEM uban LEUL BOYEM,uban magajin BOYEM,uban NUAB ALMAZZ Zakin boyem, Ayau magajinka daya ne da duniya zata sani wato Wanda ya fara haskaka zuciyarka da hasken da aka dade Ana jira, Li’ul ASIM zakinmu ne shima da babu tamkar sa, Shi din haske ne dazai haske masarautarmu da Zuwan LEUL NUAB ya fara haska mana, Jini daya ne yake gudana a jikinsu biyun Wanda yake asalin jinin boyem me tsarki da karfin iko da adalci, A tarihin boyem mai daraja data kafu Wanda ina saka ran jakadiya fetto ta manta dashi shine…….. Kaman daga sama aka rangado sanarwar isowan Queen Haile da kanta. Gabaki daya duk namijin dayake fatar qasa yayi da idanunwansa cikeda girmamawa da bin al’adar Qin sauke ido ga mace me daraja a BOYEM wato uwargidan sultan YASAR BOYEM. Bayi da fadanni kuwa qasa suka zube a lokaci guda gabaki dayansu suna qasa da kansu. Aslam da Meryam ne ‘yayanta biyu suke tareda ita a gefe da gefenta tana tsakiyar su Akan kujera me kyau dr na turota. Aslam da meryam sanye suke cikin shigar sarautarsu dogayen riguna masu tsananin kyau da suka dan Kama daga sama suka baje sosai daga qasan har suna dan ja da qasa koina na jikin Kayan qyallin stones da bead harma crystal sukeyi, Aslam dark purple ce a jikinta sai meryam kuma black kowacensu da qaramar rufa a kanta zuwa saman idanuwansu dan basa bude fuskokinsu sosai a bainar mutane dan ba kowane yakeda iko ko damar ganin fuskokinsu masu daraja ba kasancewan su jinin sarautar boyem. Zuba musu manyan fararen idanuwansa sultan yayi da mamakin zuwansu fada a wannan lokacin batareda ya buqaci hakan ba ya aika musu gayyata dan kuwa kowa yasan iyalan sarautar a killace ganinsu tamkar wata qaramar haramun ne, amma ganin halinda HAILE take ciki da kuma abinda yake gabansu na waye magajinsa ya sakasa kallansu a natse cikeda iko dayake yawo a jininsa ya tsayar da kallansa kan Haile da tana farfadowa kasa nutsuwa tayi Jin takeyi kaman zata rasa ranta sbd tafarfasa da qunar dayake komai baya iya gani daidai sbd asalin baqin cikin daya gauraye kowane jini dake zagayawa cikin jijiyoyin jikinta da zuciyarta dan haka idan bata iso ba bazata ita ji tana gani ba a bawa ‘dan imebeti sunan magajin qasar boyem ba dan kuwa sunansa matacce har shi har uwar tasa dan kuwa bazata taba sauke Numfashi da shaqar iska me albarka ba matiqar ba ganin sun bar duniya tayi ba dan kuwa karshen tozarci ne a gareta macen da ake ganin yafi kowace mace daraja a qasar ace rana tsaka sultan yayi wishmah wadda hakan na nuna alamar SO ne kuma duniya zata sani gabaki daya hakama shikenan matsayinsu daya cif da ita. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 40 *_ZUZEAM VENTURES_* 08144015291 Bononza bononza Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Duk yanda yayanta da dr suka nuna kulawa da kaunarsu sosai akanta ta hanyar hanata zuwan hakan Sam bai samu ba dan kuwa ta gwammaci ta mutu a hanyar zuwa tasan tayi kokarin isa ranta ya bar jikinta Akan tana kwance a bawa ‘dan mistress matsayin ‘danta da babu kalar shirkar da bataiba akansa da kisa, Itama doguwar riga me adon gaske ce a jikinta da kawai aka goge jikinta ya sanyo sai mayafi mai adon sarka data Zaune a fuskarta ta rufe rabin fuskarta, Cikin nutsuwa da kamewa tareda iko mai tsanani daya sirka da kulawa ya kalleta ya bude baki da zallan mulki yace ‘Ina taya queen HAILE murnar haifowa boyem sanyin idaniya jarumin boyem kuma jinin me boyem ina miki fatan samun lafiya da wadattacen farin ciki me dorewa, Wane irin tukuici kike buqata daya kawo ki da kansa?. Ajiyan zuciya me zafi mara sauti dake sake yunquro da mummunan baqin cikin datake ciki ta sauke a cikin mayafinta kafin ta bude Baki a hankali tana Hana tsananin weak din datai sbd azabar data sha kuma take ciki bayyana cikin sautin dazai isa kunnuwan manyan fadar dake fadar suma suna cikin tsimayi da mamaki tareda jiran menene yake shirin faruwa dan kuwa tabbas fetto ta fada magana. ‘Allah ya qarawa sultan me boyem tsawon rai da tsarki tareda karfin iko uban LEUL ASIM ALMAZZ magajin boyem, A tarihi da dokar Masarauta me girman daraja da iko ta boyem ‘dan imebeti bai taba zama magajin LEUL BOYEM ba matiqar a kawai ‘dan da Matar sunnah ta Haifa, Ayau ni HAILE YASAR BOYEM na haifo jinin sultan YASAR Wanda Koda imebetin sultan ta riga haihuwa to babu ikon danta ya zama LEUL sbd ni Matar sultan na Haihu a qarqashin igiyoyin aure dan haka sultan da manyan masarautar BOYEM duka gakunan a Zaune nake Neman Adalcin bin doka da kaidar BOYEM tin asalin tarihinta a bawa ASIM matsayinsa.’ Tana gama fadar hakan Aslam da meryam suka zube qasa cikeda girmamawa kansu a qasa da sauti me bada girma sosai suka hada Baki suna cewa ‘Allah ya qara maka tsawon rai da lafiya tareda iko ya Abbi me BOYEM muma muna son Ayi adalci ga kowa a bawa me matsayi matsayinsa’ Tsit fadar ta dauka sbd wani girmammen lamari daya ratsa, Manyan fada kuwa kowa maganarta ta shige sa sbd abinda ta fada haka yake babu gargada babu shakka, Haile data ga maganarta ta shiga manyan fada wani Numfashi me sanyi da rashin sauti tana Jin sassaucin muguwar azabar datake ji a kirjinta na zallar baqin ciki da tashin hankali hakama abinda ya sa ta zabi maganar anan gaban manyan fada sbd sunada iko me karfi ta wannan bangaren da duk zai shafi goben Masarauta da ikonta da kaidojinta dan haka tasan dole ya yanzu basai gaba ba zaa bawa danta magajin sultan tasan shine tin yanzu me jiran gado. Sultan idanuwansa ya zubawa HAILE yana ankarewa da abinda tayi din na zuwa fada ta fada adalci take nema wa ‘danta, Bai taba tinanin zaa fara samun jayayyar matsayin magaji ba da wuri hakan Wanda fara faruwan hakan na nuni ne da zazzafan hadarin da zai biyo Bayan rayuwar mutane da yawa Akan matsayin da rayuwar magajin BOYEM koma wanenen, Masana sun sanar da duk magadan suka fara jayayyar matsayi a masarautar BOYEM fitina ce da zazzafan hadari yake tafe a cikin Neman mulkin kota yaya dan haka take yaji wani yanayi na tinanin taka tsantsan yabi komai a natse da lissafi dan bada kariya ga Wanda yasan zasu cutu a yaqin mulkin amma ita HAILE a bayyane ya gane me takeson yi na Neman matsayin wa danta ta hanyar ikon manyan fada wainda zasu iya yanke hukuncin waye magajin BOYEM, Juyar da idanuwansa yayi ga tenya Wadda idanuwanta suke a qasa amma irin riqon datai wa NUAB ba Wanda zata iya shiru bane a bakin rai take da tsayuwa Akan lamarinsa dana uwarsa da batada kowa a duniya tinda baiwa ce da aka saka kudi aka siyo. Numfashi mai nuna isa da iko ya sauke yana komawa sultan dinsa dan tabbatarda girman matsayin da tenya zata iya zuwa Akan Ayanah ghaz da ‘danta ya bude Baki batareda ya kallo kowa ba idonsa Akan ASIM yace ‘Tabbas Li’ul ASIM ALMAZ BOYEM ‘dan queen Haile Wanda……. Da karfin gaske cikin tsananin girmamawa tareda gitta rayuwarta tenya tayi saurin daga NUAB tace ‘Allah ya qara maka daraja me BOYEM ina Neman gafarar sauke kalaman da ake nemarwa Magaji na biyu adalci sbd a yanda tarihi da dokar Masarauta me karfi ta tabbatar shine matsayin Matar dake dauke da igigoyin auren sultan takeda shi to dukkanin wannan cikakken matsayin da iko wishmah tana dauke dashi hakama a doka mai kakkaifan karfi ta Masarauta idan har wishmah ce ta haihu ba imebeti ba to tabbas ‘danta nada cikakken iko da matsayin da ‘dan matar sunnah take dashi…… Cikin murya me amsa Amon mulki da iko HAAT(wazirin Sultan da shine mai riqon qasa idan sultan baya nan kuma sune masu hukunci yace ‘Ki bude bayaninki Kai tsaye Maleketenya dan kuwa cikakken bayani zai qaddamar da waye zai yi riqon magaji a cikinsu’ Da gwiwowinta ta juyo bangaren da Haat din yake ta sauke kanta qasa cikin tabbatarda son karban matsayin NUAB daga hannun kowa tace ‘Da daaham din shedar zamowanta cikakkiyar wishmah imebēti AYANAH GHAZ ta fara naqudar magaji na daya dake hannuna a yanzu Wanda hakan ya tabbatarda babu kowane iko ko jinin dayake yawo jikin mai girma ASIM dayafi na LEUL mai jiran boyem, Zamtowan mahaifiyarsa wishmah kafin ta diresa a duniya ya wanke tareda tsaftace masa kowace irin hanya data Halasta masa cikakken ikon BOYEM gabaki dayanta da zagayenta…..’ Tsit fadar ta kuma dauka mai karfin gaske wadda ta saka HAILE fara jiqe wa da wani mummunan zufan daya daga jininta ya fara hayewa take dan kuwa ta manta da Ayanah ghaz ta zama wishmah kafin fara naqudarta Wanda tabbas hakan ya halastawa ‘dan ta komai. Saukar idanuwan sultan Akan tenya yayi mata kallo daya ya maida kallansa kan haat Wanda take ya karbi NUAB daga hannun tenya ya nunosa gabansa ya ambacesa da magajin sultan YASAR ALMAZ BOYEM, Matiqar sultan yana raye shine yakeda ikon hawa mulkin BOYEM sbd ‘dan kwarkwara ce ta haifeka bakada cikakken gado dan haka idan sultan ya rasu kafin saukarsa mulki bai doraka ba to tabbas bazaka hau karagar mulki ba. Da sanin wannan sharadin ne wani mafi girman burin Dora NUAB ALMAZ Akan kujeran mulkin BOYEM ya tsiru a zuciyar sultan YASAR sbd zamowan ‘danta Akan mulkin BOYEM ko baya raye zata kasance macen datafi kowace mace power da tsaro a boyem. Tenya cikin tsananin farin cikin gaske ta ringa zuba godiyarta ta miqe ta fice dan Kai NUAB ga mahaifiyarsa da kuma yi masa wankan al’adah da baayi masa ba. ******a daidai wannan lokacin Ayanah ce riqe da hannun sakinah gam suka riqe juna sbd kukan da Ayanah keyi zuciyarta kaman zata Dena bugawa sbd tsabar gajiya da baqin ciki da damuwan da itace take yawo a kowane gaba na jini da jikinta, Duk Wanda yake masarautar ko a wane lungu me nisa kake labarin haihuwan magajin BOYEM ya isar maka tareda sunan wadda ta haifesa dan haka babu shakka tasan zuhranta taji haihuwan kuma tana can cikin tsananin kadaici da tsantsan buqatan zuwa gareta kaman yanda a yanzu babu abinda take tsananin so da buqata irin saka Zuhrah a idanunwata su rungume juna tareda rungume abinda ta haifar musu a tare sbd yanda take Jinta Bayan haihuwan kaman bazata Kai labari ba, Cikin tsananin rashin karfi da mutuwar jiki tareda damuwan datake bayyanar da quncin dayake ranta ta Lumshe idanuwanta tareda bude su Akan sakinah tace ‘Ina tsananin buqatar ganin Zuhrahta kafin rayuwata tabar jikina, Ina son haduwa da ita koda hakan na nufin rasa rayuwata tinda inada jinin dazan bari a duniya, Zuhrah na cikin halin da Bansaniba na qunci da azaba Bayan ni ina nan cikin wata rayuwar ta daula daban, Bazan taba farin ciki ba har qarshen rayuwata matiqar Zuhrah tana cikin wannan ukubar, Duk tsananin son da zanyi wa abinda na Haifa son danake wa ‘yar uwata uwa daya uba daya bazai taba rayuwar da har zan iya farin ciki dan na haihu na manta da azabar data zaba dan bani rayuwa me….. Tenya data kusan kifewa qasa sbd rawar da kafafunta suka dauka da abinda kunnuwanta suka jiyo mata cewan Zuhrah da Ayanah uwa daya uba daya saurin riqe babyn hannunta tayi tana tsatsafo zufa a rikice tana kasa yadda da abinda taji ya saka sakinah ma Miqewa a rikice jikinta na daukan wata irin rawa cikin mummunan tashin hankali tana kallan tenya dataji abinda suke boyo tin shekaran da suka sako kafa a BOYEM dan tsiratar da rayukansu daga zazzafan hukuncin BOYEM da baa taba dagawa ko takewa. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 41 *_MAMAN YUSUF LIKITAR MATA_* 07069711327 GYARA SHINE MACE *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻 -Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata -Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi, -Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji, -Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki, -Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ba, -Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki, -Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso, KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers 07069711327 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata. ************ Tenya data kasa yadda da fahimtar zancen komai a kwakwalwanta Wani irin tsoro da firgici taji tana shiga sbd abinda taji wani gagarumin sabo ma ne da zai iya daukan rayukan mutane da dama a ciki harda su dukan da ita da kunnuwanta suka Ji,rai daya ne zai tsira a cikinsu shine babyn dayake hannunta amma Bayan shi wannan mummunan masifar da kunnuwanta suka ji mata hukuncinta Kai tsaye shine sauke kan kowane me rai daga kafadarsa dayake bangaren AYANAH GHAZ gabaki dayansu sai ita da kila matsayinta na wishmah dazai ceta rayuwarta ta fita a lissafi, Idan bata manta Zuhrah Ghaz ba itace wadda ko ita ta tambaya alaqar sunan daya zo iri daya suka sake bata tabbacin ba alaqar komai ta jini sai sunan gari daya, Zuhrah itace wadda ta raunana kanta taso daukan rayuwarta Akan zama imebēti, Zuhrah itace wadda aka yankewa hukuncin qarasa rayuwa a gidan yari har abada, Wannan zuhrahn itace wadda kunnuwanta ke Jin cewa uwa daya uba daya take da wishmah, Jini daya ne yake gudana a jininsu? Jinin mahaifiyar LEUL ne yake yawo a jikinta itama, Kanwar mahaifiyar LEUL kenan?? Wani irin mummunan zufa mai Zafin gaske ne ya gangaro mata ta qaraso tsakiyar dakin kafafunta a sanyaye batada karfin jiki ko kadan idanuwanta na sauyawa jajir dan shikenan ta shiga masifar da batasan Yaushe suka qulla abar su ba, Dagowa tayi ta kalli Sakinah da duka jikinta ke tsananin rawa da fizga idonta jajir hawaye ma sun qafe mata sbd tashin hankali tana kallan tenya din da tinani Kala Kala a ranta na yanda tenya zata dauka lamarin nan me girma, Dawo da idanuwanta tayi Akan Ayanah da bata damu da rasa rayuwarta da zatai ba kuka takeyi sosai mara sauti sbd zata rasa ranta ne batareda ta ceto yar uwarta ba zata tafi ta barta a qangin bautar da kila zatai har qarshen rayuwarta. Kukan Ayanah dake saka har jikinta jijjiga ahankali ya saka tenya kasa cewa komai saima miqa mata NUAB a hankali jikinta a sanyaye yana dan rawar tashin hankali itama dan kuwa ita datake masarautar tafi su sanin girman tsantsar hadarin abinda suka aikatawa masarautar. A hannuwan Ayanah din ta Dora NUAB daka motsa ahankali cikin showel dinsa ita kuwa Ayanah tsayawa kukanta yayi cak jinsa a cikin hannuwanta ta bude idanuwanta da sukai jajir akansa ta zuba masa ido tana kallan fuskarsa me kyau da daukan Idon da babu abinda ya Bari a cikin kamanninta se gurbin mahaifinsa daya dauko, Kammanin duka yan uwanta dasuke Kama guda daya da ita da mahaifinsu ya dauko tinda komai nata irin na yan uwanta ne musamman Nurat da Abaas sunfi Kama sabanin Zuhrah da Ammansu tafi Kama da ita dan haka fuskokin yan uwanta da mahaifinta take gani suna yi mata yawo a fuskarsa zuciyarta na Wani irin shiga radadin rashinsu a tareda da ita Ayau data haifar musu ‘dan kanta, Wasu hawaye masu radadi da sanyi ne suka gangaro mata ahankali suka sauka Akan gefen fuskarsa ta rufe ido tana sake fasa sabon kuka Mara sauti tana dagosa jikinta ta saka a kirjinta ta rungume tsananin radadin rashin Abaas na dawo mata sabo a zuci da ruhi sbd shine Wanda a duniya yafi kowa fata da son ganin wannan rayuwar a rayuwarsa wato ranar da zata haifar masa ‘dan zai dauka ya rungume a matsayin nata sbd irin tsananin son dayake mata, A koyaushe ya aurar da ita ta Haifa zuriar da zata hadu da tasa shine adduarsa da fata da burinsa tin yanada qananun shekaru gashi Ayau Allah ya raba rayuwarsu da basusan ko iyaka cin rayuwar da zasuyi kenanba, Tsima zuciyarta kukanta keyi ta sake qanqame NUAB kirjinta tana adduar ‘Ya Allah kada ya dauki ranta sai ta hadu da ‘dan uwanta rabin jikinta hasken idaniyarta Abaas, Ya Allah kada ya dauki ran Abaas batareda burinsa ya cika ba na ganin zuriarta data haifa a duniya.’ Sakinah dataji adduar da Ayanah ke yi a bayyane zubewa tayi qasa kan gwiwoyinta tana fidda hawaye masu tsananin Sosa zuciya itama tana sunkuyar da kanta qasa tana Jin radadin rashin Abaas din itama yana dawo mata sabo tareda wargajewan ahalin GHAZ din da basuda burin daya wuce ganin wannan rana ta ganin jinin da Ayanah zata haifa dan Bayan Abaas Nurat ce me tsananin son ganin jinin Ayanah na farko sbd tace itace zata zama uwarsa duniya da lahira Ashe itama bazata gani ba tabar duniyar gabaki daya a cikin Hali mafi muni da har su mutu bazasu dena tinawa ba., Irin kukan da Ayanah ke yi tana sake qanqame ‘danta da yanda ke buga kanta a qasa itama tana yi da sauti me kashe jiki da tsima zuciya ya saka tenya jikinta mutuwa tsoronta da fargabanta na komawa tausayi da fatar rage radadin dayake zukatansu da babu komai a cikin rayuwarsu tin farko da kunci da damuwan da bata taba ganin ta gushe daga idanuwa da zukatansu ba. Tsawon lokaci suka dauka suna kukan qunci da ciwon rayuwarsu daya dawo musu sabo kafin sakinah ta rarrafo ahankali batareda ta dago ba kanta a qasa ta miqa hannuwanta biyu ta Dora a kafafun tenya dake tsaye a kansu ta rintse idonta dake jajir hawaye masu dumi suka gangaro mata tareda sauka Akan babban yatsar kafar tenya din ta bude Baki cikin mafi karyewan sauti tace ‘Kinji sirrin da muka dauki lokaci muna karewa da rayuwarmu Wanda kuma muke da niyar cigaba da karewa har karshen rayuwar tamu dan kawai mu tsira mu rayu ko baa tare ba, Har abada Ayanah bazata taba rayuwar farin ciki ba duk duniyar da zata samu kuwa sbd ta rasa duka abinda yake bawa rayuwa farin ciki ta hanyoyi mafi ciwo da kasa fincikewa….’ Dago kanta tayi da idanunwata da sukai jajir ta kalli tenya tace, Ni baiwa ce matsayina be kaiba Banda yanci da ikon rokon kowace irin alfarma ce koda ta numfashin da zan shaqa ne kuwa amma ina rokonki alfarmar da zata hana LEUL tashi maraya babu uwa dan kuwa bayyanar gaskiar alaqar dake tsakanin Zuhrah da wishmah zai iya yin iyakacin ranta dan kuwa ko baa rabata da ranta ba ita ta tsira aka kashe Zuhrah to tabbas zaa iya rasata itama har abada dan haka dan nake bada rayuwata ki rufa mana wannan asirin alfarmar wannan jaririn dayake hannunta ki badan a matsayin wadda take yar uwa ga Zuhrah ni a dauki rayuwata na sadaukar da ita dan bada kariya ga duka su biyun., Wani kallan sabon zallan mamaki da shiga matsanancin tsoron dake tada gashin jikinta tenya ke kallan sakinah sbd alamu dai sun sunma tabbatarda ita kanta sakinah duka sunada alaqa kenan Wanda Masifafen hadarin hakan yafi rikitar da tinaninta dan kuwa tana isar da wannan sakon babu Wanda zai kara ko awa daya a duniya cikinsu, Babban tashin hankalin dake sake jijjigata zufanta na sake jiqata tsoronta na bayyana shine itama hukuncin bazai wuce kanta ba sbd tsawon fiyeda shekara tana tareda su suna qarqashin kulawa da saka idonta amma ace ta kasa gane akwai alaqa a tsakaninsu Wanda hakan shine ya gama tabbatar da hukunci daya akansu da ita dan hakan take Jin hankalinta na tsananta tashi, Fadar laifin hukuncin barin duniya,boye laifin tareda su kuma duk ranar daya fita kaf zuriarta ne zasu amsa hukuncin kisar tareda su masu laifin dan hak taji kafafunta na silalewa qasa tana zame wa qasa Zaune, Dago idanuwanta da sukai ja tayi itama ta zubawa Ayanah ido wadda kwata kwata bata cikin firgici ko tashin hankali na bayyanar zancen alamar kowane lokaci bata tsoron fuskantar mutuwa kamanma duniyar ta isheta mutuwar kawai take nema ta dauketa ta huta sbd qunci ne a dabaibaye a rayuwarta duk Wanda ya kalleta zai iya ganin hakan, Dawo da idanunwata tayi Akan sakinah ta bude Baki muryanta na rawa tace ‘Kunsan me hakan ke nufi kuma kuka aikata? Kina maganar a sauya ki a maimakon wishmah shin Kinsan ba iya ke kadaice zaki rasa ranki ba hadda Zuhrah din a tare zaku rasa ranku gabaki daya dan a tare kuka aikata laifin da……… Bata qarasa ba Ayanah ta ajiye babyn hannunta ya sauko gadon babu kuzari a jikinta ko kadan koina na jikinta rawa yakeyi ta zube gaban tenya taba dago idanunwata da suka saka gaban tenya faduwa ta bude Baki cikin ficewa hayyaci tafara rokonta kada ta Bari Zuhrah dinta ta rasu tana mata Wani irin roko hayyacinta baa jikinta ba wata rawan daya saka tenya sake shiga tashin hankali jikinta keyi. Yanda Ayanah ke yi kaman hankalinta ya gushe jikinta gabaki daya yana rawa tana yiwa tenya Wani irin rokon ta cetan mata zuhrah ya saka tenya riqeta da hannuwanta biyu tana kokarin mata magana Ayanah din ta fasa wani irin kuka mai qarfi da taba zuciyan daya saka sakinah ma fara kukan mai sanyi tana dagowa ta kalli tenya batareda tsoro ko shakkar abinda zai iya biyowa baya ba ta fara bata asalin labarin komai na abinda ya faru a rayuwarsu tin kafin watsewan ANJOM GHAZ dan kuwa a daidai wannan gaban data tabbatarda qarshen rayuwarsu Yazo gwara asan waye su da kaddarorin da suka fuskanta sbd Bayan barinsu duniya Ayanaah bazata taba dawowa hayyacinta ba da zata iya tina ko waye ita bare tina labarinta. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 42 *_MAMAN YUSUF LIKITAR MATA_* 07069711327 GYARA SHINE MACE *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻 -Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata -Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi, -Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji, -Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki, -Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ba, -Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki, -Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso, KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers 07069711327 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata. ************ Tenya da idanuwanta sukai jajir hannuwanta na rawa ahankali dago jajayen Idon tayi ta saukesu Akan fuskar Ayanah dake rintse da ido kanta cikin kafafunta tana Wani irin kuka mai tada tsikar jiki sbd rasuwan Nurat data dawo mata sabuwa da rashin Abaas harma da rabuwa da Zuhrah da irin rayuwar da sukai ta qangin bauta a hannun wainda bazata taba mantawa ba kusrawa. Ita kanta sakinah data bada labarin kuka takeyi sosai komai ya dawo musu ‘danye da harma suke Jin sun yadda mutuwar suke so su huta kawai, Tenya duk yanda taso riqe kanta saida zuciyarta ta kasa tayiwa Nurat kukan daya sakata Miqewa tana juya musu baya tana yinsa sosai sbd yanda komai da akai mata ya ringa ratsa kunnuwansu tin farko har gamawa da yanda Abaas ya koma macen da duk wannan tsawon lokacin bai taba bude Baki ba ya bayyanarda azaba ko baqin cikinsa ba yan uwansa su kaji muryansa ba har suka rabu rabuwarda shikenan har abada. Tsit dakin yayi dukkaninsu sunyi kukan da har karfinsu ya qare musamman Ayanah da daman karfinta ya tafi gurin naquda da haihu. Sakinah ma karfinta ya qare babu me kuzari a cikinsu hukuncin tenya kawai sakinah ke jira Banda Ayanah da kamar ma bata hayyacinta dan kuwa zuru tayi bata iya ko dagowa da babynta a jikinta da kila rabuwa zatai dashi take ji kaman yanda ta rabu da kowa nata. Tenya Ayanah ta zubawa ido zuciyarta gabaki daya ta karye akanta, Acan baya tana tsaye a kanta da duk lamarinta ne sbd cikar burinta na wargaza duk abinda HAILE zata so a rayuwa amma ayanzu Jin tsananin kauna da tausayi tareda sonta takeyi yana ratsa jini da zuciyarta a tsaftace babu sirki babu wani Buri, Shi NUAB tinda ya fado duniya a hannunta ya fado take kaunarsa mara sirkin komai ta shigeta da zata iya komai akansa amma ayanzu dataji waye mahaifiyarsa sabuwar kaunarsu ce mai karfi da zata iya bada ranta akansu ta shigeta dan haka take daukanwa kanta alaqawarin tsayawa a kansu da lafiya da rayuwarta har inda tata rayuwar zata qare, Cuta da hadari kowane iri ne indai zata gansa ko jisa zata basu kariya kota halin yaya dan haka a yanzu da gaske qiyyyar HAILE take ji a jininta da batajin zata iya barin kowace burinta Akan Ayanah ya cika dan shi LEUL jinin BOYEM ne kuma magajin kujeran BOYEM duk Wanda yayi gangancin tabasa tamkar miqa rayuwarka ne kayi ga zakunan da zasu ci namanka da ranka a gangan,tinda Yazo a jinin sultan YASAR ai yagama samun kariya duk duniyar da zaa bawa kowane irin me rai dayake BOYEM bazai iya cutatar dashi ba dan haka mahaifiyarsa ce a hadari da buqatan me tsaya mata a kowane irin yanayin da zata samu kanta. Cikin yanayin daya saka su dukansu biyun dagowa suka kalleta ta kafe idanuwanta Akan Ayanah da sauti me cire tsoron hadarin da zasu iya shiga su dukan tace ‘Kinada alfarmar fiddo Zuhrah daga kurkuku amma bakida damar ‘yanta ta sbd hakan zai iya zamowa hadari fiddota da yantata, Kinada matsayin wishmah dazai Baki cikakkiyar daman da zaa cika miki Buri uku na rayuwarki, A ranar da zaayi bikin sunan NUAB a ranar zaa yi taron Baki cikakken matsayinki na wishmah a kuma ranar ne zaa Baki damar fadar Buri uku da kike dasu Wanda Kina fadar su Sai an cika miki su, Bazan fada miki abinda zaki fada ba sbd bansan burin da kike dashi ba a rai amma dai zan fada miki Abu daya idan har kinason zuhrah ta rayu rayuwa me kyau wadda ko bakwa tare zata samu rayuwar nutsuwa da kwanciyan hankali Wanda hakan shine burinki to kada ko fiddata daga kurkuku kuma ki yantata a lokaci daya dan kuwa kika yin hakan Zaki iya rasata gabaki daya dan sedai ki tashi Washe gari ki ga gawarta kwance a gabanki, Na miki alkawarin Zuhrah zata samu rayuwa me kyau da gata tareda kwanciyan hankali amma idan zaku iya sadaukar rabuwa da rayuwa batareda juna ba har abada….. Wasu hawaye ne masu dumin gaske suka gangaro daga idanuwan Ayanah tana kasa dauke kallanta daga tenya cikeda Wani irin yanayin dayake sassara rayuwarta zuwa matakin qarshe na qunci da radadin zuciyar datake mutuwa daga Sauran walwalan rayuwa. Itama sakinah rintse idanuwanta tayi ahankali jikinta na sakewa wani dumi na zagaye jikinta da sarawar Kai. Tenya tasan ba abune me sauki ba ko kadan hakan kuma qunci ne sabo da zai dasu a zuciyar Ayanah na har abada amma hakan shi kadai ne mafita dan kuwa matiqar zasu yadda ita tayi alkawarin da dubararta zata kawo sauyi da aminci a rayuwar Zuhrah duk da har abada su biyun zasu rasa rayuwarsu kenan ta walwala ko farin ciki dan kuwa zasu tabbata ne a quncin rashin juna suna ji suna gani. Girgiza Kai Ayanah ta fara yi ahankali da karfi tana fizga kafin sakinah ta riqeta jikinta da karfi tana rungumeta tana Gyada Kai tana hawaye tana cewa ‘Indai Zuhrah zata fito zatayi rayuwa me aminci zaki iya Ayanah,Zaki iya Ayanah….’ ‘Bazan iya ba,bazan iyaba shine abinda take fada da karfi tana qwacewa amma dole sakinah ta saka karfi ta riqeta harta gaji dan kanta tayi Laushi.’ Ganin tayi Laushi ya saka sakinah da tenya da kanta suka kamata zuwa toilet inda hadaddun ruwan Zafin wanka ke jiranta suna fidda hayaqi da dan qamshin wani maganin al’ada na wankan haihuwa. Su biyun ne sukai mata gashin wanka me nutsuwa dukansu jikinsu a sanyaye kaman yanda ita kuma ta koma tamkar batada sauran hankali ko kuzari a jikinta. Sun dauki lokaci sosai kafin suka fito sakinah ce ta tsaya tayata shiryawa tamkar yanda aka Saba gashinta ta goge mata ta busar dashi ta Kamasa sako sako sbd karya dameta ta dauko mata Kaya tana miqa mata tana sakawa kamar wadda bata gani. Abinci da lafiyayyar dafaffiyar madarar datasha hadin Kayan qamshin da zafi sosai aka kawo mata tenya da sakinah ne suka tirsasata taci aka kwantar da ita take bacci me nauyi ya dauketa sbd akwai maganin bacci a cikin madarar. NUAB ma sabon wanka da shiri tenya tayi masa da kanta sbd bata yadda da kowaba Akan Ayanaah da shi yanzu, Wuni Ayanah tayi tana bacci sai yamma lis ya farka aka sake hada mata ruwan Zafin da aka kuma gasata da kyau ta shirya ta zauna a daki ita kadai sakinah ta saka mata NUAB a hannunta San shayar dashi, A lokacin data masa shayarwar farko Jin tayi wani abu ya ratsata Wanda ya sakata kafesa da idanunwata da suka qanqance sbd kukan baqin cikin rayuwarta da baya qarewa, Addua ta bude bakinta a sanyaye ta fara jero masa tana fatar rayuwarsa ta haskaka hasken da zai haskaka rayuwar duk wainda basada gata ko yanci a rayuwar nan. Dan qanqamesa tayi ahankali da hannuwanta tanajin tamkar ruhinta yana zame wa yabar jikinta na rabuwa da zatai da Zuhrah wannan Karan da gaske kenan har abada sbd hakan shine kadai zai bawa kowannensu rayuwar da ba ita suka so ba, Indai Zuhrah zata rayu ta samu kwanciyan hankali nutsuwa da walwala tabbas zata zabi rayuwa da gurbin da babu me cikesa idan ba Zuhrah din ba har abada,zata zabi rayuwa babu digon farin ciki bare walwala har abada indai Akan samun rayuwar Zuhrah ne dan haka a yanzu NUAB ne kadai jininta dayake rage mata a rayuwanta da batada komai sai qunci a cikinta, NUAB shine gata,rayuwa,ruhi,zuciya da hasken idaniyar daya rage mata Wanda kuma zata ci gaba da rayuwa sbd shi. Da wannan tinanin da quncin ta kwana da ‘danta a jikinta datake Jin tsananin sonsa fiyeda rubabbiyar rayuwarta. Washe gari haka akaita hidima a masarautar ta farin ciki da murnar jarumai biyu da aka samu, A bangaren Haile kuwa kwance take rigis hawan jini da ciwon zuciya yana mata karfi dole aka aika mata kwararrin likitocin da zasu tsayu a lafiyarta, Tenya kuwa sosai ta sake kafewa Akan kiyaye komai na bangaren ayanah sbd abubuwan daya fara gani. ******* babban bangare daya dayake komai iri daya dana HAILE da MARAKI a kuka bangaren da suke aka bude Anai masa wani irin gyaran daya saka ko MARAKI da bata damuwa shiga damuwa da fargaban matsayin da wishmah take dashi gurin Masarauta gabaki daya, Duniya guda aka zuba a bangaren da a cikin kwana shida aka gama zuba masa dukkanin wani luxuries Ayanah da babynta suka tare harma da bayinta da tenya wadda aka dawo da bangarenta anan itama bisa ga umarnin sultan daya saka ciwon hawan jinin HAILE yin sama dan babu matarsa da jakadiyarta ta taba zama kusa da ita. Ranar da kwanaki bakwai suka cika a ranar akai gagarumin nadin sunan daya girgiza BOYEM da wajen BOYEM gabaki dayanta dan kuwa duk wani babban mai sarauta da mulki na kasashe daban daban suna qasar BOYEM dan radin sunan magaji da dan uwansa tareda babbar hidimar qaddamar da wishmah ta uku a tarihin BOYEM. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 43 Gagarumin radin sunan NUAB ALMAZZ YASAR BOYEM aka fara yi kafin na ASIM YASAR ALMAZZ BOYEM aka ringa barin dukiyar data ringa jijjigar bayin fadar sultan sbd daukan kyaututuka zuwa bangaren iyayensu mata wato bangaren Ayanah dana HAILE dukda yawan kyautikan bangaren uwar magaji ta ringa sauka sbd yanda aka ringa barar masa da dukiya. Da dare ne bikin wishmah dan haka anfi kwana uku Ana shirye shirye da decoration na fadar inda zaa qaddamar mata da matsayinta Wanda kowa saiya sheda kuma ya bata matsayinta datake dashi na macen farko data karbi matsayin Bayan shekaru masu yawa gata kuma uwa ga ‘da na farko daya haske zuciya da idaniyar mahaifinsa da zuwansa duniya. Masu kwalliyar wishmah da kanta kusan su biyar ne sbd ado ke na musamman da Ayau zai nuna Itace mace ta farko da kyanta zai dake na queen HAILE hakama macen data motsa zuciyar mai girma sultan dan haka wasu irin sarkokin zinari masu daukan ido da kyau ne aka fara shigowa dasu a tray Layi Layi kowa da abinda ya dauko a cikin bayin da suka fara shigowa suna jeruwa, Tenya ce ta shiga qarshensu dan itace a tafe dasu, Fara daukan sarkokin akai aka saka mata Akan wata irin lafiyayyar kwalliyan da akai mata ta maroon doguwar rigar datake jikinta data bi jikinta ta lafe daidai shape dinta mai tsari kaman bata haihuba, Wasu irin stones dake daddabe a jikin rigar masu daukan ido suka dan sitirta shape dinta daya fito sosai a jikin rigar suka sake qarawa kyanta da adonta kyau, Gyalan rigar Maron shima akai rolling akanta Ana rufe gashinta mai tsayi daya qarawa kwalliyanta kyau kafin aka saka sarkoki da chains na zinari akaiwa rolling din nasa adon gaske me Kyau kafin aka saka babban transparent mayafin Kayan still mai tsayi sosai haryana ja da qasa aka Dora Akanta aka rufe rabin fuskarta da babu Wanda ya isa ya gani shima akai masa nasa adon da chains na zinari take ta fito tamkar macen da aka saka golden biro aka zana dan kuwa komai nata daukan hankali d jan hankali yakeyi. Tenya Jin tayi duniyarta ta sake haskaka da farin ciki suka fito da ita a daidai lokacinda zaa fara tana dauke da NUAB a hannunta. A bisa dolen al’adah sai matansa sun fito sune zasu tarbesa su rakota a tare har inda yake dan haka koda akai sanarwar isowanta kofar fadar tareda bayinta da securities din dake tsare da NUAB da jakadiyarta take HAILE ta Hadiye wani kakkarfan busashen yawun daya saka hannunta rawa tana yagar fatar Dayan hannun nata da karfi yana yagewa, Cikin sauri da basarwa Aslam dake kusa da ita ta Dora hannunta Akan hannun mahaifiyar tata tareda dan kallanta a natse tana girgiza mata Kai kada kowa ya gani. MARAKI ma dagowa tayi zuciyarta na daukan Wani irin nauyin zazzafan kishi mai tsananin ciwo da dumama jini ta zubawa AYANAH GHAZ idanuwanta tana kallan Wani irin fitinannen sirrin kyau daya saka kusan koina tsit sbd duk da tana rufe amma gyalan yayi shara shara din da babu abinda basa gani na halittar da Allah ya qera a gurin, Akan sultan MARAKI da HAILE suka sauke kallansu a lokaci daya zuciyoyinsu na shiga wani nannauyan kishin da babu wadda batajin kaman ta Hadiye zuciya a lokacin ta mace. Wani irin kallo ya dago fararen idanuwansa masu kyau da girgiza dan Adam ya saukewa AYANAH GHAZ daga lokacinda ta sako kafa a cikin fadar batareda ya kyafta ba dan kuwa duniya biyu ne aka hade masa guri guda a gabansa ita da NUAB datake rungume dashi suna tinkaro sa. Yan jarida da televisionsa da duk wani dan media suna gefe daya da aka ware musu sbd tsari da Kyan fadar daga can suke daukan hotinan da flashers kawai ake gani tana haskowa babu kakkautawa. Haile da maraki ne suka iso gefenta kowacensu da adonta mai kyau da tsari tareda daukan ido itama suka fara tako wa tareda da ita dukansu idanuwansu Akan sultan ta cikin nasu rufar Ayanah kuwa kanta a qasa shi kuwa nasa idanuwan Akan ‘dansa dake hannun Ayanah kawai yake kalla taqaita kallansa daga gareta hana kishinsu Kai illa ga zukatansu. Isowan AYANAH GHAZ gabansa suka zauna inda aka tanada dan zamanta da nasu take aka fara gabatar da kosher din Wanda yake tamkar daurin aurensu ne zaayi. Dukiyar kosher datake tamkar sadaki aka gabatar daga jinin BOYEM na manyan cousins din sultan dake qasashe daban daban suna rayuwar mulki da daula tareda hutawa a qasashen turai daban daban dayake dik jinin BOYEM indai suna raye ko a ina kake Ka Halarta dan haka masarautar take shaqe da masu duniya a hannunsu. Irin dukiyar da aka bayar ya saka masarautar jijjiga take aka karba dukiya aka bawa jakadiyarta sbd itace gatanta wadda kadai take da ita aka fara adduar kosher din tsawon lokaci kafin aka rufe da Amin Wanda Amonsa sbd yawa ya ringa amsawa har wajen Masarauta. YUNAR KAREEM ALMAZZ BOYEM Shine babban dan wan mahaifin YASAR Wanda yake Zaune a qasar Kuwait da matarsa daya da Yaya uku sai yaya hudu daga imebētinsa daya dan haka shine ya isar da cika Burikan wishmah guda uku Wanda Kai tsaye budar bakinta idanuwanta a kafe kan NUAB dayake kan kafafunta muryanta na tsananta sanyi da karfin Hali tace Abu na farko datake so shine a yanta bayi dari a cikin bayin dake kurkukun masarautar, Sai Abu na biyu shine tanason a ‘yanta mata baiwarta daya tak sakinah, Na ukun shiru tayi zuciyarta na yin Wani irin rauni da sanyi ta dago idanuwanta da sukai ja ta saukesu Akan sultan tace tanason ko tana raye ko baya raye idan NUAB ya girma kada a tirsasata hawa mulkin Masarautar BOYEM matiqar baida raayi idan ba shine yayi raayi ya hau dan raayin Saba. Tsit kowa yayi koina ya dauki Wani irin shiru mamaki na kashe kowa musamman sultan da HAILE da Wani irin sanyi a Karan farko ya dan ratsa zuciyarta ta kafe Ayanah din da ido tana mata kallan mahaukaciyar data rasa tinaninta dan kuwa batada labarin cewa tinda ta fada wannan burin saiya cika koda zata mutu Akan sauya hakan, Tayaya zata ce idan danta baida raayi kada a basa mulki? Ta kuwa san menene samun mulkin Masarautar BOYEM? Sultan kuwa kafeta yayi da idanuwansa Wani irin daci mai karfi yana Sosa zuciyarsa dan kuwa tamkar Kai tsaye ta kallesa ta yaga burinsa daya kullata koda zai mutu ne ta yaga a gaban idonsa, A matsayin datake dashi harta isa samun wannan tinanin? Menene nufinta na fara lalata burinsa Akan dansa tin yanzu? Tabbas tayiwa burinsa na shekara da shekaru tabon da har abada bazai goge ba musamman idan abinda ta fada din ya tabbata. Manyan fada dik da shock din da suka shiga take aka sanar babu burinta da baama gama cika wa dan haka take aka bada umarnin a saki bayi dari biyu ma da suke kurkukun, Sakinah ma take aka yantata tareda kyauta me tarin yawan data saka Ayanaah din rufe idanuwanta ahankali hawaye masu dumi na gangaro mata sbd samarwa sakinah yancin da sukam bazasu samu ba har abada. Har tsakar dare sosai Ana hidimar sai kusan gap da asuba aka gama kowa ya watse zuwa masaukinsa. Washe gari da sassafe aka saki bayin da akace a saki, Koda aka fara fitowa dasu tenya na bakin kurkukun dan cika sabon aikin daya hau kanta na hadawa mai girma YUNAR BOYEM sabuwar imebeti a matsayin tukuicin dukiyar kosher daya bayar ta wishmah daga mai girma sultan YASAR, Tin farko tasan daman zaa bada tukuicin imebeti ga duk Wanda ya bada dukiyar kosher din wishmah a matsayin tukuici Shiyasa ta fadawa Ayanaah sadaukar da zatai na rabuwa da Zuhrah har abada sbd ita zata bayar dan hakanne zaisa itama ta samu rayuwar da har zata haifa nata yayan amma sun yafe juna kenan har abada sbd daga ranar da aka gane jininsu daya duka su biyun zasu rayuwarsu matiqar ba yayansu sunyi girman da zasu sassauta musu hukuncin hakan ba kuma a yanzu Ayanah ta yadda da hakan matiqar zasu rayu Zuhrah ta Gina tata rayuwar harma zuriar kanta, Hakanne ya saka tenya take tsaye a lokacinda aka fito da Zuhrah wadda ta fita kamanninta gabaki daya Kai tsaye gurin duba lafiyarta tasaka aka wuce mata da ita dan shiri da gyaran gaggawa zaa fara yi mata na tsawon wata daya cif kafin a Kai masa ita ya wuce da ita qasar kuwait. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 44 A daidai lokacinda Zuhrah ta sako kafarta wajen kurkukun fata shafe Sheka daya da watanni a ciki a daidai wannan lokacin Ayanah ghaz datake tsaye zuciyarta na Wani irin harbawa da Wani irin zallan kewar datake ratsa ruhi da zuciyarta kafafunta na dan rawa tanaji a jikinta Zuhrah na cikin halinda itama take tsananin son ganint su shaqar da rahamar ganinsu. Sakinah dake tsaye gefen Ayanah din itama zuciyarta cike take da yanayi na sanyi da mutuwar jiki tareda tsananin so da kaunar ganin Zuhrah wadda shikenan wannan Karan sun rasa juna kenan da gaske har abada. Tenya ma dake tsaye wajen kofar kurkukun zubawa Zuhrah idanuwanta tayi babu kyaftawa tana Jin tsananin tausayin Ayanah da zata iya rasa ranta idan taga Zuhrah a halinda take ciki daidai wannan lokacin. Barin sukai da zuhran wadda bata iya Miqewa qyam tsaye sbd yunwa da wahala hakama fatarta tayi duhu gabaki daya ga gashinta duk ya zama abin tsoro da qyama, Suna barin gurin tenya ta aika baiwa ta isarwa da wishmah sakon Zuhrah ta fito kurkukun da babu komawa insha Allah har karshen rayuwarta. Sakon yana isowa wishmah Lumshe idanuwanta tayi ahankali tareda silalewa qasa tana bin bango ta zube qasa tana bude idanuwanta Akan sakinah data riqeta tanason magana ta kasa sai kawai ta sake rufe idanunwata tana dora hannunta daya Akan kirjinta dake mata radadin azabar da har abada bazai dena ba sai ranar da ranta yabar jikinta dan kuwa baqin ciki ne da quncin da baida magani. Sakinah da samun yancinta bai saka taji zata iya barin Ayanaah ba har abada itama sanyaye jikinta yake hakama ta shirya zama baiwar Ayanah har qarshenta ko da yanci ko babu yanci zata bauta mata ta kuma bauta ma ‘danta har girmansa. ******acan tenya kuwa Kai tsaye bangaren gyara ta isa da Zuhrah ta fara bada umarni aka wanke Zuhrah tas aka ringa cire datti harma da wasu qananun qwari a jikinta tsawon kusan wuni guda, Taso a yanke gashinta amma sbd imebeti zaa turata tana buqatan dogon gashin dan haka sai aka barshi shima ya ringa Shan wanki kan wanki, Ana gamawa gyaran kafafunta da hannuwanta akai na farce tukuna aka kirawo likitoci suka duba lafiyarta, Magani dasu multivitamins aka bata sai kuma tenya data bada umarnin aka hado mata mai na gargaji dayake goge tabo a qanqanin lokaci dan goge tabon raunikan data yiwa kanta duk da sun warke sun fara bace wa da disashewa saura dakan Wanda shine kila bazai fita ba sai sun hada masa da magani. Har dare sosai tenya bata huta ba tana kan lamarin Zuhrah da babu wani lokacin batawa matiqar tanason jefata a matsayin imebēti tana buqatar tsayuwan gaske a gurin gyaranta. Ayanah kuwa a nata bangaren tinda Zuhrah ta fito sai taji jikinta yayi sanyi ta sake raunana da komai, Ta bawa sakinah dukiya me yawa Akan ta tafi ta samu yanci tayi rayuwarta amma sakinah Sam bazata iya barinta ta kafe zata zauna da ita har karshen rayuwa, Batada Sauran walwalan daya rage mata kokuma shaawar rayuwa dan haka bata takura sakinah dinba dan kuwa daman ita kadai ce a yanzu ta rage mata a asalin rayuwarta hakama tana buqatan Wanda zai tsaya mata ya tayata bawa danta kariya duk da ta zabar masa yancin zabar abinda yakeso da kansa ba tirsasawa tin yanzu Akan mulkin datake tsoron kada a illata mata shi akai, Hakaman tayi hakan ne dan basa kariya daga masifu da hadarin da zai fara fuskanta ta ko ina tin yana jinjirinsa so yanzu zaa bar mata shi yayi rayuwa a cikin aminci tinda an riga an cika mata wannan alkawarin sai kuma idan ya girma idan yanada raayi hakan zai zama barazana ga Maqiyansa da masu so. A bangaren sultan YASAR kuwa Ayanah ghaz tayi masa babbar sukar data rage mata matsayi a zuciyarta dan kuwa duk irin soyayyar da jinin BOYEM zaiwa mace baya taba sauya abinda yake yawo a jininsa dan ako Yaushe harkar mulkinsu da iko tareda abinda suke Buri yana gaban kowace irin soyayya da kauna, Duka shekarun daya Debo na tsananin burin samun ‘da namiji sbd hakan ne, Sbd tabbatarda magaji Akan karagarsa bama batareda ko yanada raayi ba ko bayada raayi amma a Karan farko na tarihin masarautar ta zabawa ‘danta kaddararsa tin yana zanin haihuwansa, Yanada wani magajin Bayan NUAB da zai iya gadon karagar amma abinda tayi masa ya sakasa Jin ko zata rasa ranta sai ‘dansa da yayi raayi ya mulki BOYEM koda hakan na nufin fizge ta daga matsayinta sedai amma zuciyarsa na kasa barin sa ga aikata hakan dan kuwa kaman yanda jinin BOYEM da bazai taba barin burinsa ba yake a jininsa haka soyayyarta take a jininsa dan haka idan bazai iya cireta a zuciya da jininsa ba to zai iya cireta daga dukkanin qudurinta da bazai taba cika ba. Haile a yanzu ne ta samu damar sassautawa zuciyarta ta fara Neman lafiyarta da gaske dan kuwa a yanzu ta samu tabbacin tanada dama me karfi ta qwatowa ASIM matsayinsa da aka bawa ‘dan mistress, Bazata taba hutawa ba ko samun bugawan zuciya daidai har abada idan ba ganin ASIM BOYEM tayi ba Akan kujeran mulkin BOYEM, Batada Buri ko kudirin daya wuce saka ASIM a zuciyar sultan YASAR fiyeda dan mistress dinsa, Zata tabbatar ta dawo da matsayi da ikonta a hannunta na juya rayuwar kowace macen datake imebētinsa, Zata ninka tsoronta da zafinta akansu ta yanda bazasu taba iya kallan Ayanah da ‘danta da darajar data wuce mistress ce da dan mistress dan kuwa a yanzu ne zata tada asalin rashin imaninta Akan abinda takeson ‘yayanta su mallaka, Ko rai nawa zata kashe batada shakka zata kashesu tamkar dabbobi sbd saita tabbatarda Ayanah ko kallan inda take babu me yi bare bata girman matsayin datake dashi. ****Burika ne suka cike zukatan dukkanin masu jinin sarautar BOYEM Wanda hakan ya fara bayyanarda wasu manyan Zafafan hadari da rayuwa zata fara fuskanta dan kuwa a qanqanin lokaci kadan bayin Ayanah uku suka rasu batareda ansan menene yake ajalinsu ba amma kuma masu bincike sun tabbatarda koma menene kaman poison ne, Wannan lamarin shine ya fara daga hankalin tenya da sakinah harma da sauran imebētis kowa ya shiga mummunan tsoro da firgici, Ayanah bata shiga damuwan komaiba sbd rayuwarta data gama mutuwa ayanzu kwata kwata bata San komaiba Bayan qunci da baqin ciki se kadaici dasuke cin lafiya da hankalinta ahankali ahankali batareda sanin kowa ba, NUAB ne kadai Wanda take Zaunawa ta rungume tana kallansa batareda kyafta wan ido ba tanajin akansa ne kadai take rayuwa yanzu, A duk lokacinda take kafesa da ido tayita kallansa rabin jikinta Abaas ne kadai take ganin fuskarsa Akan tasa yana yawo kewa da tsananin sonsa na tsananta ciwon dayake cin zuciya da ruhinta dan hakanne a yanzu Abaas kadaine zuciya da rayuwarta take nema. Tenya na cikin matsanancin tashin hankali da rashin nutsuwa mai yawan gaske da duk ta firgice itama sosai sbd hankalinta daya rabu biyu Akan kulawa da Zuhrah datai wa Ayanaah alkawarin saita tabbatarda ta miqa rayuwarta inda zata rayu cikin aminci kafin ta huta da kuma hadarin datake ganin yana kusanto Ayanah da ‘danta dan kuwa komai ya rikice ga dukkanin imebētis din dake masarautar sun koma tamkar yan amanar HAILE duk abinda ta sakasu shi sukeyi sun bayyanar da tsanarsu me karfi Akan Ayanah da ‘danta, A bangare daya ma kaf ‘yayan da suke na sultan tsana me karfi sukewa NUAB da Kai tsaye suke ambata da ‘dan mistress kaman yanda HAILE da kanta take kiransa, Duk wannan abin Ayanah batasan anayi ba sbd bata cikin cikakken hankalinta na tinanin kowa Bayan na danta da kwanakin dake qaratowa na rabuwa da yar uwarta da bata saka a ido ba kuma shikenan bazasu saka juna a idonta. Tenya sake dage wa tayi Akan aikinta Wanda a yanzu Zuhrah ta sauya sosai tamkar ba ita ba tayi Wani irin Kyan gani da haske sosai duk da haskenta bai dawoba amma ta ciko tayi kyau sosai sai kalar sabuwar fatar tata mai dan duhu tayi mata kyau ta sake sauya kamanninta daga yan uwanta tinda a yanzu tsawon wata daya harda sati guda kenan, Duk wannan gyara da Jin dadi tareda lafiyayyan Hutu da cima me lafiya da kyau da ake bata itama rayuwarta bata taba cire quncin datake ciki ba koma minti daya itama, Rayuwarta ta jima da mutuwa kaman yanda ta ‘yar uwarta ta mutu kuma bazasu taba samun sauyin hakan ba duk zuriar da zasu tara quncin daya shigesu ya riga ya tafi da ruhinsa zasu rayu a mistresses din jinin BOYEM zasu tsufa a hakan zasu mutu tarihin zuria ahalin GHAZ ya rufe shikenan. Da kewa da tsumayin son samun ganin yar uwarta karon karshe Zuhrah take kwana a kowane sare kuma take tashi, Duk yanda qunci da tarin baqin da damuwa suka fara taba lafiyar Ayanah haka zuhran ma sun dade da fara taba lafiyar kwakwalwanta da ita kuma tafiya inda iyayenta sa Sauran yan uwansu suka tafi take buqata dan gwara Ayanaah a yanzu tanada ‘dan cikinta da shine zaisa ta iya cigaba da rayuwa ko babu dadi ita kuwa batada kowa Bayan Ayanah din kuma a yanzu gashi zasu rabu rabuwan da shikenan. A Daren da zaa gabatar da Zuhrah a matsayin imebētin da akaiwa mai girma YUNAR tukuicinta a wannan Daren itama wishmah zata fara komawa tirakar sultan Wanda tinda akai bikin basu sake haduwa da juna ba NUAB ne kadai Wanda kowace rana se ankai sa tareda bayi masu tsaron lafiyarsa. A tsawon wannan lokacin bata taba tinaninsa ba sbd batada tinanin kanta saina ‘dan dayake gabanta da Zuhrah da Abaas sai Ayau din da aketa shirinta Ana mata gyara na musamman da wasu irin tsare tsaren daya ringa tina mata rayuwarta ta farkon zamowa imebetin. Tenya data har zuciyarta takeson hadasu suyi ganin junan karshe sbd tana iya ganin tsananin halinda kowacensu take ciki hakama matiqar basu ga juna Ayau din ba shikenan dan kuwa Zuhrah daga wayewan garin gobe zata bar qasar zuwa inda ba dawowa dan koda hidima zata kawo YUNAR a boyem to bazai taba zuwa da ita ba matiqar ba matsayin wishmah din itama ta samu ba dan haka zaman daular sa zatai ta ringa hayayyafa har qarshen ranta. Daga Ayanah har Zuhrah yau damuwansu da quncinsu ya ninka na kullum sbd daga yau ne karshen da zasu shaqi iskar gari daya dan haka kowacensu babu inda yakeda dogon amfani a jikinta. Karfe goma sha Dayan dare aka fito da kowacensu dan tafiya tiraka duk Taku daya da Ayanah keyi tamkar Ana zare mata ruhinta daga gangar jikinta take ji idanuwanta sunyi jajir daga ita sai sakinah da bayi kusan shida ne suke tafe tareda da ita sakinah na dauke da NUAB sbd tenya tana tareda Zuhrah da doka itace zata kaita har babban bangaren YUNAR dayake da nisa sbd duniya ce guda me zaman kanta zube a bangaren sa. Tafiya sukeyi Ayanah na sake rasa kanta daidai kusan isarsu tenya ta Ambaci sunanta daga bayanta Wanda ya sakata tsayawa cak batareda ta juyoba kanta na mummunan sarawa. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 45 Kasa juyowa Ayanah tayi idanuwanta na fara wani radadi sbd rashin hawayen dake cikinsu zuciyarta na harbawa da Wani irin karfin dayake nuna tashin isashiyar lafiyan zuciya sbd jikinta ya karba yanayin daya tabbatar mata da Zuhrah ce a bayanta, Daqyar gangar jikinta ta dawo aiko daga wutar data dauke ta iya motsa kafafunta ahankali tana juyowa hannuwanta na rawa ta damqesu tareda qarasa juyowa gabaki dayanta ta fuskancesu suna bayanta daga nesa kana tsaye, Akan Zuhrah jajayen idanuwanta da taka suka ringa rikida suna qara rinewa suka sauka tana tsaye tsakiyar tenya da babbar baiwar da aka ware mata tareda wasu bayin sunkai goma a bayansu, Navy blue Kayane a jikinta da adonsu yake daukan ido fuskanta a rufe da mayafi mai Shara shara da ake iya ganin fuskanta amma ba sosai ba hakama itama tana iya ganin na waje amma ba sosai ba, Kasa motsawa Ayanah tayi daga inda take tsaye hakama idanuwanta basu motsaba daga kafe Zuhrah datai dasu kaman yanda zuhran itama ta kafeta da nata idanuwan dake son tsiyayo hawaye amma sun qafe qaf sbd halinda zukatansu ke ciki, Tsananin son ganin fuskan Zuhrah ne Ayanah taji yana danne kirjinta kaman zai kasheta amma Dukkaninsu babu Wanda yakeda ikon bude mayafin daya rufe da fuskarsa batareda ya isa ga Wanda shine kadai yakeda ikon budewa ba dan haka basuda daman ganin fuskokin juna da suke tsananin doki fiyeda komai na duniyar, Tsit duniyar tayi musu da gurin ma gabaki daya, Rawa jikin Ayanah yakeyi ahankali tanajin kafafunta na kasa daukanta bakinta wata rawa yakeyi amma ya kasa budewa dan ta Ambaci yar uwarta, Zuhrah kasa riqe kanta tayi ta daga kafarta tayi Taku daya dan zuwa ga yar uwarta amma tenya ta saka hannu ta riqe hannunta daya batareda tace komaiba ta girgiza mata Kai tana Hana idanuwanta cikowa da hawayen tausayinsu sbd iya abinda zata iya musu kenan na ganin juna amma bazasu taba magana ko rungumar juna ba Bare nuna sanin juna sbd tarin bayin datake tareda su da kuma cameras dake koina dan haka haka sake riqe hannun Zuhrah dake Wani irin rawan jiki tayi gam tana dagowa ta kalli Ayanah dake tsaye kaman an dasata ko baa fada ba kowane lokaci zuciyarta zata iya bugawa dan haka Juyawa tafara yi da Zuhrah a hankali zasu bar gurin Ayanah ta Lumshe ido ahankali ta rufe tana kokarin zubewa kan gwiwanta sbd kafafunta da suka gaza sakinah tayi saurin riqota duk da NUAB yana jikinta, Zuhrah ma kasa daukanta kafafunta ke kokarin amma tenya ta hanata kaiwa qasa ta tareta jikinta suna ci gaba da tafiya can qasan kunnenta ta rada mata ‘Kada ki Bari sadaukarwar yar uwarki da rayuwar data zaba miki ta tafi a banza dan sbd ki samu rayuwar da zaki rayu da aminci ta zabi rabuwar koda hakan zaiyi sanadin mutuwarta ta riga ta zaba inganta rayuwarki dan haka ki saka dangana indai kunada rabon sake haduwa Allah zai hadaku cikin yadda da amincinsa idan kuma babu rabon sake haduwan shikenan kuwa juna fatan alkhairi ko a raye ko mace amma daga nan kaddarar ku ta riga ta rabu’ Wasu irin hawaye masu tsananin Zafin da Zuhrah batasan dasu bane suka gangaro daga idanuwanta suna sauka fuskarta tanajin tamkar an zare mata Wani hasken rayuwarta yabar jikinta dan haka tenya tafara tafiya da ita batareda tasan inda take Dora kafafunta ba har suka bace wa gurin batareda kowannensu ya sake waiwayowa ba har suka bace sukabar su Ayanah gurin tsaye wadda ta kasa dauke idonta daga Zuhrah harta bace wa ganinta ta sake rintse idanuwanta ahankali tana Jin Wani nauyi ya danne kirjinta daya saka numfashinta kasa fitowa ta daga hannunta ahankali tana son dorawa Akan kirjinta amma hannun bai qarasa isaba bakinta ya feso Wani irin jini da karfin gaske daya fesu a Fuska da showel din NUAB dake hannun sakinah. Jajir idanuwanta sukai tana bude su ahankali zata sauke Akan ‘danta hakan bai samuba ta zube a gurin, Wani irin gigitaccen raruma sakinah takai mata tana rungumota jikinta ta hada da NUAB data kasa bawa kowa tana kankamesu tafara kiran sunan Ayanah din da karfin gaske koina nata ma rawa da shiga mafi girman rudanin rayuwarta, Bayin dake tsaye suma duk tashin hankalin suka shiga inda take akaje da gudun gaske aka kirawo doctors aka dauketa zuwa bangarenta cikeda matsanancin tashin hankali da rikice wa. Babban tashin hankalin da Masarautar ke shirin shiga shine rasa macen da a wannan Daren duk Wanda yake Masarautar ya tabbatarda itace cikar rayuwar sultan YASAR ALMAZ BOYEM dan kuwa take a qanqanin lokaci wishmah ta zama abar tsananin tausayi da tsoro sbd yanda ta koma fara tas tamkar babu digon jini a jikinta hakama babu alamar ma zata farfado dan hakanne likitocin dake kanta hankalinsu ya tashi da suka gama tabbatarda ciwon zuciyane mai tsananin gaske yake Neman rabata da ranta da a yanzuma basusan yaya ma zasu fara ba dan kuwa tinda ta riga ta fara aman jini abin yayi Nisan da sai wani ikon Allah. Mummunan labarin na isa kunnuwan sultan kasa yadda yayi da zai rasata dan haka da kansa ya iso cikin bangaren matansa a Karan farko ya isa bangaren Ayanah wadda take kwance fayau dasu oxygen da komai kamar ba ita ba a lokaci daya Allah ya maidata abar tausayin da kowane lokaci zata iya barin duniya. Tenya da sakinah da duk bayin da suke bangarenta suna cikin tashin hankali da damuwan da batada sauki a cikinta ko kadan sbd ganinta kadai Wani irin kuka mai tsima zuciya yake saka sakinah da idanuwanta harsun fara qanqancewa. A kuma daidai wannan lokacin yar uwarta daya tak datake da ita a duniyarta datake mutuwa dan babu tabbacin rashinta a wannan kwanciyan datake duk wani mai kaunarta kuka a wannan lokacin ne ake maidata cikakkiyar macen da itama tata zuciyar gap take da bugawa sbd daci da mataccen yanayin dake cikinta tareda sanin yar uwarta na can rai a hannun Allah a lokacin sbd labarin masarautar a take ake sanarwa dan kowa ya kiyaye. ******koda gari ya waye sultan yana Zaune a daddumar da yayi sallah sbd koda minti daya bai rintsa idanuwansa ba rokon Allah yakeyi yana qarawa ya raya AYANAH GHAZ koda shi ne zai tafi a madadinta zaiyi fatar ta rayu sbd dandana farin cikin da bai taba gani a idanuwanta ba ko so daya, Yana fatar ta rayu taga abinda ‘danta zai zama koda hakan zai bata farin ciki da murmushi koda so daya ne a rayuwarta kafin mutuwarta hakama bazai taba son NUAB ya rayu a hannun kowace macen daba mahaifiyarsa ba dan haka ya ringa fadawa Allah ya tashi kafadanta. Masarautar BOYEM ta dauki zafi dan kuwa duk manyan likitocin qasar kaf suna cikin masarautar dan Neman lafiyar Wishmah wadda take sake fading kaman ba macen da kyanta yake cike Idon duk mai kallanta ba. Tenya da sakinah ne tsaf a gurin kulawa da bada kariya ga NUAB Wanda Bayan sultan kaf duniya babu Wanda yake daukansa sai su biyun sbd tsaro, Ita kanta wishmah din tsaro sosai sultan ya saka a bangarenta na gaske dan kuwa akwai barazana sosai da hadari a yanayin datake yanzu dan haka sosai aka saka ido da tsananin tsaro babu me shiga gurinta idan ba doctors da tenya da sakinah ba sai kuwa shi mai gayyar Wanda hakan y saka HAILE kusan rasa hankalinta. Tinda aka kafa tarihin masarautar BOYEM babu Sarkin daya taba taka kafafunsa Yazo dakin macensa sai sultan YASAR Wanda hakan ya kafa Wani irin tarihi mai girma da shakka a zukatan matansa da manyan fada da suke ganin kaman zai iya rasa kansa Akan wishmah dinsa dan haka suka fara janyewa daga kaunarta rashin yadda da yar tsana na maye gurbin. MARAKI ma da batada matsala zuwan sultan bangaren ya saka hankalinta tashi ta qullaci Ayanah har zuwa matakin karshe tana yadda da itace macen data samu zuciyar da shekarun aurensu da jininsu bai samar musu ba dan haka kishinta ya fara komawa qiyayya me karfin gaske datake Neman take ta HAILE a fili. *****A Karan farko da tsoro da shakka suka darsu a zuciyar sultan me BOYEM gabaki daya sbd ganin macen da zai iya bada rayuwarsa dan karewa tako Ina hadari mai girman gaske yana dabaibayeta dan kuwa manyan fada da gaske a yanzu sun janye duk wata alfarmar su da kaunarsu akanta da gaske a iya matsayin mistress din suke kallanta, Hakama bangare daya zazzafan kiyayyar maraki akanta ta fito fili ga kuma HAILE da ita har abada yasan idan tanason abu zata iya komai akansa dan haka rayuwan Ayanaah daya NUAB bazata taba fita hadari da halaka ba a masarautar. Damuwa mai tsananin gaske da tsaro ya qara Akan Wanda yake basu gashi har lokacin bata farfado ba, Sakinah ma da tenya ta ko ina komai yayi musu zafi dan kusan so uku duk tsaron da ake bawa bangaren Ana samun attempt ta kawo karshen rayuwarta. Da wannan tashin hankalin sultan da kansa ya dauketa daga qasar zuwa Germany. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 46 Daga sultan har su tenya saida suka isa qasar Germany suka samu nutsuwan jinyar wadda cikin ikon Allah ta farfado amma bawai samun lafiya gabaki daya ba, Farfadowanta sabuwar damuwa ya haifar musu sbd gabaki daya ta sauya daga Ayanah zuwa wata halittar daban, Baqin cikinta ya ninka, Quncinta ya ninka, Damuwanta ya ninka, Shiru da rashin kuzarinta ya ninka sosai ta yanda bata magana kwata kwata hakama bata kallan kowa NUAB ne kadai Wanda take kalla a koda Yaushe. Wata hudu suka share a qasar Germany na jinya kafin sukai guda daya na hutawa suka tattaro suka dawo BOYEM inda tarin abubuw suke jiransu ciki harda sabuwar rayuwar da basu tana tsamammanin Ayanaah zata samu ba daga sultan dan kuwa sauyi ne me sanyi yafara nuna mata ta hanyar dauke kulawansa kwata kwata akanta da NUAB a bisa wani sirri da shi kadai yabar wa kansa, Masarautar a yanzu ta dauki Zafi iya zafi na kowa ya zabi inda zai tsaya sbd shirin karban matsayi da mulki tako wane Hali idan lokaci yayi, Asalin bayyananniyar qiyayya da tsana me Zafin gaske ake nunawa Ayanah a bayyane tareda rashin imani dan kuwa koyaushe cikin ciwo take da aman jini Wanda ya saka take kokarin rasa ranta gashi maraki da imebētis din sultan sun hade Kai guri daya duka a qarqashin HAILE wadda ita babban burinta daya ne kota yaya Ayanah da NUAB subar zuciyar sultan da duniyar gabak daya ita kuwa maraki zuciyar sultan takeson Ayanah ta Bari kwata kwata. *****da farko Bayan dawowan Ayanah daga Germany lafiya kalau ake kaita kwana gurin sultan dayake nuna mata kaunar da babu me nuna mata ita a duniya amma a hankali ahankali hakan ya fara ragewa, A haka haka su NUAB suka fara girma an yaye su sunfara wayo sosai da girma, Sultan dayaga babu sauki a rayuwan Ayanah dake rasa rayuwanta sauyi me girma ya kawo a rayuwarta daya fara mantar da ita rayuwarta ta baya batareda saninta ba, Likita daya mace da amanarta take daban data duka likitocin masarautar ya bawa umarnin Dora Ayanah Akan maganin da zai maidata weak ta mantar da ita rayuwarta data rasa koma wace iri ce sbd ta dena magana kwata kwata, ***Ahankali ahankali Ayanaah ghaz tafara manta rayuwarta da wace ita tana zama weak tamkar batada amfanin komai a rayuwa, Duk wani qunci da baqin cikin rashin yan uwanta ahankali ahankali yafara barin kwakwalwanta yana shafewa, Mutum biyu ne suka tsaya cak qyam a ranta da ko a cikin baccinta su kadai take gani babu memory dinsu ko daya daya fita a kanta sune ABAAS da NUAB, Memory din Abaas bai taba fita kanta babu kuma tinaninsa ko daya daya fita a kanta amma Sauran yan uwa sa iyayenta Sam tinaninsu shafe mata yake ko ta tinasu sai tanajin su tamkar baqi a cikin kanta, Tsananin so da kaunar datake wa dan uwanta Abaas itace ta zama abinda babu dare babu rana take tinani da Jin bazata iya rayuwa ba batareda ta sake sakasa a idonta ba koda ranarta ta karshe ce a duniya tanason Allah ya hada fuskokinsu. Rayuwa tana qara ja sultan yana qarasa janye dukkanin wata kulawansa da soyayyar sa Akaan wishmah da NUAB Wanda yafara girma a cikin tsangwamar yan uwansa dasu HAILE Akan zamtowansa dan mistress wadda batada cikakken hankali koyaushe shiru take tamkar hoto a Zaune, Tenya tana cikin qunci mai tsanani da damuwan da itama ta zamar mata ciwo ahankali ahankali Akan yanda sultan ya cire Ayanah da danta kwata kwata daga ransa da lamuransa a yanzu ASIM ne Wanda yake nunawa duniya yafi kauna Wanda hakan ya saka HAILE ajiye maganar Ayanah da NUAB kwata kwata sbd ta samu abinda take so, MARAKI ma kusan Bayan lokaci yaja sosai ta ajiye Ayanah daga ranta sultan dayayi watse dasu itada danta Ayanah din ta koma tamkar macen da batada amfani kwata wata a rayuwarsa dan kuwa ko sauran imebētis din sunfita gata da matsayi a Masarautar, Wannan dalilin ne ya saka a yanzu babu Wanda yake b takan Ayanah da danta sun koma tamkar wainda babu su a masarautar labarinsu ya shafe babu me Tinawa dasu rayuwa ce sukeyi a cikin qunci da gori da tozarci a tsakanin iyalan sultan din Wanda duk abinda yake faruwa yana sane, Sakinah da tenya sune gatan Ayanah da NUAB da suke tsaye akansu dukda a rayuwar Ayanah yanzu kamar hoto ce babu abinda takeyi ko kukan ma yanzu tintini ta dena iyaka cinta ido a komai, Abu Daya ne yake motsa zuciyar wishmah AYANAH GHAZ shine soyayyar ‘danta LEUL NUAB ALMAZZ BOYEM sai kuma dan JININTA ABAAS kaman yanda take fadawa dan ta sunansa a kunnensa koyaushe zata ce masa ‘BANASON MUTUWA BAN HADU DA JININA ABAAS BA,KAFIN NA MUTU NUAB KA CIKAMUN WANNAN BURIN SHI KADAI’ Wananna shine kalmar da NUAB ya tashi da ita a cikin kunnuwansa da zuciyarsa wadda shine kadai abinda kawai mahaifiyarsa ke iya furta wa koyaushe, Shi kadai ne takewa magana a rayuwarta Wanda shima duk maganar da zatai masa saita fada masa hakan dan hakanne maganar ta girku ta kafu a zuciyarsa tin yana qaraminsa dan hakanne tin yana qanqani ya fara girma da wannan Alkwarin na cika wa mahaifiyarsa wannan burin koda kuwa zai rasa rayuwarsa da tsallake mutuwa dari. ********LEUL NUAB Ya taso ya rayu a cikin masarautar datake ta ubansa cikin baqin cikin ganin rayuwar da mahaifiyarsa takeyi a cikin matansa da imebētis dinsa, Mahaifiyarsa itace rayuwarsa da zai iya komai da tsayawa gaban kowa akanta, Mahaifiyarsa itace fullstop dinsa da akanta ne kadai yake iya tsayawa ga duk abinda yakeji, Matan sultan suna Qinta, Yayan sultan suna qinta, Imebētis din sultan suna qinta, Yayan imebētis din sultan suna qinta, Manyan fadar masarautar BOYEM suna qinta, Shi kansa sultan din yana qinta….. Hakan daya taso yana gani ne a bayyane ne ya saka zuciyarsa fara bushewa daga dukkanin wata kauna datake duniyar gabaki dayanta, Ciwo yakeji mai Zafin gaske, Radadi yake ji mai azabar gaske, Fushi yake ji mai wutar gaske, Rashin kauna yakeji ga kowa mai karfin gaske duka sbd Shi itace rayuwa da duniyarsa gabaki dayanta, Bai damu da rashin kauna da shaquwan dake tsakanin sa da ubansa da duka wani jininsa ba sbd baya buqatan kauna ko soyayyar kowa a duniyarsa iya ta Amminsa da babu wata rai me daraja a gurinsa Bayan tata sun ishesa, Mutum biyu ne rak a duniyar Bayan mahaifiyarsa daya cirewa hular Zafi da tiririn da kansa yake fitarwa sune Wainda su kadai ya taso da sanin masu kauna da kulawan Amminsa da zasu iya bada ransu akanta wato MAA TENYA dinsa da MAA SAKINAH Wainda su kadai ya taso ya gani a rayuwarsu shi da uwarsa, ‘Dan mistress yan uwansa suke kiransa Wanda shi hakan bai taba sosai ransa ba sbd hakan na nuna cikakken identity dinsa kenan da uwarsa wadda akanta shi sunan mistress yafi masa darajar sunan sultan me mulkin qasar gabaki daya, Tin da qananun shekaru zafi da hayaqi sa ya bayyana ga duniyar masarautar BOYEM dan hakanne ya saka yan uwansa mata fara shakkarsa dan tamkar mahaukacin Zakin da baida hankali ko daya yake ga duk Wanda ya shiga huruminsa da baya buqatar kowa a cikinsa Bayan Mutum ukun nan da sune kadai ya saka a duniyarsa, Zafi da tiririnsa ya saka zuciyar sultan shiga damuwan abinda zai iya zama sbd babu tsoro ko daya bare shakka a rayuwarsa, Bai taba risinawa kowa ba a masarautar kaf dinta sbd har abada bazai taba risinawa duk Wanda baya kaunar mahaifiyarsa ba koda hakan na nufin bakin ransa to zai bada ran da hannunsa. Ta bangare daya Li’ul ASIM ya taso mai tsananin tsoro da rashin wayo da dubara ko kadan, Baida jarumta,jarumta baida kwazo baida jajircewa hakama baida dubara da tinani ko kadan duk abinda uwarsa ta dorasa haka yake hawa ba lissafi dan hakanne suka taso duniya biyu mabanbanta shi da LEUL kwata kwata duniyarsu bama iri daya bace dan shi hatta matan uban nasa mamaki da shakkar Zafin kasan da rashin tsoron sa sukeyi tareda fargaban abinda zai iya zamowa idan ya qarasa girma. Da wannan tsoron sultan ya tattara sa yakai sa qasar RUSSIA karatu tareda bada umarnin bazai taba dawowa ba saiya gama karatunsa gabaki daya ya zama cikakken mutum tukuna zai sako Kafa a masarautar. Wannan hukuncin ya masa Zafi da ciwo amma kuma sbd mahaifiyarsa da saiya tabbatarda tabar hannun sultan ta dawo hannunsa gabaki daya har qarshen rayuwarta ya Aminta ya tafi dan kafa duniyarsa da bayason ko kadan ta hadu data masarautar daya tsana a zuciyarsa fiyeda komai. A hannun tenya da sakinah a tafi yabar mahaifiyarsa data kasa barinsa ta qanqamesa saida aka banbareta daqyar tana kukan da fiyeda shekara nawa bataiba sai yanzu da aka rabata da danta dan haka Bayan tafiyar sa rayuwarta ta sake komawa inda ta fito. Barin NUAB ALMAZ qasar BOYEM ya bawa HAILE cikakkiyar damar fara yaqin maida danta cikakken jarumin da babu tsoro ko daya a zuciyarsa sbd sultan ya dorawa a mulkin dayake shakkar Dora NUAB ayanzu sbd zafinsa dayayi mummunan yawa, A Morocco qasar iyayenta aka tura ASIM karatu amma shi yana zuwa Hutu a duk lokacinda yaso sbd Sam taqi yadda dayayi nisan dazai hanasa samun kusanci me karfi da sultan Wanda yasan a yanzu ne yaqi da qalubalen matsayin magajin BOYEM zai fara irin Wanda zai kawo fitina daban daban a tsakanin magajin biyu da duniyarsu ta banbanta, Babban abinda yake saka zuciyar sultan girgiza shuke irin rayuwar da NUAB zaiyi a kusan shekaru masu yawan gaske batareda mahaifiyarsa da itace duniyarsa ba wadda shi kansa ayanzu bayajin har abada duk yanda zai shareta zai iya rabuwa ko barin ta fita hannunsa dan da itace zai iya riqe NUAB a hannunsa. A ranar da NUAB ALMAZZ BOYEM yabar qasar a daidai wannan ranar aka bugo daga daular YUNAR dake kuwai imebeti zuhrah ta haifar masa yan biyu namiji da mace Wanda tukuicin haihuwan biyun a lokaci daya ya saka ya yantata tareda aurenta ya maidata cikakkiyar matarsa. Koda labarin ya isowa su sakinah sujjada sukai cikeda tsanani farin cikin daya jima shekaru da barin rayuwarsu sbd Ayanah, Kallan Ayanah sukai dake Zaune zuru suka fara fada mata amma bata ce komai batai reacting ko wane iri ba saima binsu takeyi da ido batareda ta tina matsayin Zuhrah akanta ba sedai suka gaji jiki a sanyaye suka kyaleta tinda dai ba haukacewa tayi ba memory kawai tayi loosing da walwala sai suke Jin sassauci a zuciyarsu hakama Bayan tafiyar NUAB babu ranar da baya video call da dukkaninsu yana magana da mahaifiyarsa da shi ne Wanda yake saka aji sautin muryanta Wanda a haka shekarun suka shude tamkar a mafarki. #MAMUH #THE BEGINNING #THE GREAT LEUL NUAB ALMAZZ BOYEM HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 47 Masarautar BOYEM mai cikeda tarihi daya gabata na can baya qarni qarni da tarihin daya gabata a shekarun da basu Kai qarni qarni ba haryanzu tana cikin wadataccen arzikinta da daular datake sake ninkuwa ako Yaushe sbd arzikin da Allah yayi musu Wanda baya qasa koyaushe sedai gaba, Shekarun da suka shude anyi su ne a cikin tinani da wasi wasin waye zai zama magaji a cikin jini biyu da sultan YASAR me mulki haryanzu daya haifa? Akwai ‘dan asalin matarsa uwargidansa wato queen haile wadda take zuba taqama da ikon da kaf masarautar ake shakkarta Bayan sultan idan aka cire manyan fada wainda sune fada, Itace macen datafi kowace mace daraja haryanxu a masarautar da wajen masarautar sbd tini aka shafe tarihin fada da tsantsar soyayyar da sultan yakewa wishmah dinsa wadda tarihinta yayi bacci gabaki daya bata cikin kowane lissafi, Queen Haile ta karbi kowane irin iko,taqama da isar tsayawa ta tsayar da ‘danta ASIM ga zama cikakken mai jiran gado na karagar mulkin BOYEM kuma hakan ta Zaune dan kuwa masarautar da duniya gabaki daya sun gama shedar da hakan sun gama yadda da sanin ASIM ALMAZ ne Sarkin dazai mulki BOYEM Bayan sultan YASAR sbd shine a tareda mahaifinsa da qasar sa yanzu. Rayuwa ta dawowa Masarautar BOYEM sabuwa dal da Kama hanyar cikar Buri sbd kowa abinda yake tsananin so ne yake ganin yana Kama hanyar samu musamman queen haile wadda komai datake tsananin so shine ta samu hawan ASIM ALMAZ kujeran BOYEM ne kadai ya rage mata Wanda shima a yanzu yanda take ganin kusancin ASIM din da sultan tasan bama zai taba Hana masa ba sbd ya manta cewan yanada wani magajin kwata kwata tinda bai taba yiwa kowa maganarsa ba tinda yabar masarautar da suke ganin kaman ma korarsa yayi amma aka boye cewan karatu ya tafi dan haka haile ta gama samun dukkanin abinda take so itada danta ASIM Wanda yake zuba nasa iko da mulkin a cikin masarautar sbd ganin shine sultan na gaba kuma hakan ne ya saka gabaki daya BOYEM shakkarsa akeyi da basa tsananin girma duk da babu tausayin Jamaa ko daya a ransa amma mahaifiyarsa ta koya masa boye hakan sbd sake samun damar haye matsayin da suke tsananin buri kuma a shirye suke tsaf da iya kashe kowace rai da zata shiga tsakaninsu da abinda suke so dan haka kowa yasha jinin jikinsa akansu, MARAKI ma a yanzu ta rasa dukkanin power datake ita sbd haile ce me yaya take zuba iko da mulkin cikin gida, Hakama imebētis kaf da yayansu da duk wani me matsayi a cikin gida tsananin tsoronta ya ninka a ransu sbd a yanzu itace uwa ga sultan na gaba dan haka babu me iya ko dago Kai ya kalleta komai na mulkin Masarautar ma ya qara tsanani da wasu irin dokar da bayi basuda shaqat ko kadan. MARAKI duk da daman can kishin tsagwaron soyayyar data hango sultan yana yiwa wishmah da ‘danta ne suka sakota gaba ta sakawa zuciyarta zazzafar kiyayyar Ayanah da NUAB sbd bata taba kishin haile ba dan bata taba ganin soyayyarta data ‘yayanta a idanuwan sultan YASAR ALMAZZ kaman yanda taga wutar son Ayanah da danta naci a idanuwa da ruhinsa ba dan hakan a yanzu data shedar da sunyi tazarar da babu Sauran soyayya a tsakaninsu hankalinta ya dan kwanta ta tattara komai ta ajiye ta koma rayuwarta ta Hutu da kwanciyan hankali bata shiga matsalar da duk ba tata ba dan kuwa ko taya HAILE kishin nema wa danta mulki batajin zata iya sbd sanin ba lallai komai Yazo a sauki ba dan tayi imanin da idan ma sunyi nasarar cire Ayanah a idanuwan sultan to ba lallai sun cireta a zuciyarsa ba bare LEUL NUAB dayake jinin AYANAH GHAZ bazai taba fita a zuciyarsa ba dan haka ta cire kanta a wannan fadan iya abinda ta samu ya isheta ita a yanzu dan haka rayuwa sabuwa ta bude itama ta kwanciyan hankali da nutsuwa, Imebētis din sultan kuwa da damansu ahankali ahankali sun rasa rayukansu a hannun uwar dakin tasu wadda a yanzu Bayan ita bata buqatan kowace mace a rayuwar sultan Wanda ya rufe shafin karban kowace imebētin a rayuwarsa tinda ya samu Ayanah ghaz kofar shaawansa ga kowace mace ta rufe kwata kwata matansa ne kadai suma haqqin su ne kadai yake saukewa gashi rayuwar ma tayi tsayi yanzu tsufa da manyanci ya taho musu, A yanzu imebētinsa daya ce rak a raye itama ta jima da komawa tamkar baiwa ga haile ta zama kunnuwanta na dauko mata labarai da sirrin duk inda Hailen bata saniba dan hakanne take raye kamar fanko dan kuwa shi kansa sultan din tintini ya mance da ita baama maganarta a haka zata gama garari a masarautar ta tsufa ta mace, MARAKI batada kowane irin amfani itama a gurin sultan Bayan na biyan buqatan sauke hakkin aure a ganin HAILE kenan Shiyasa bata damu da ita ba ta tattara ta watsar tinda batada ko ‘dan kanta a duniya kuma tanada daman daukan ‘ya daya ko biyu ma daga cikin yayan imebētis din sultan ta riqe tamkar ta haihu amma Sam batada raayin hakan tin acan baya da akwai Sauran yarinta bare yanzu da duka sun manyanta hakama yaran da yawansu gabaki daya an aurar dasu Masarautu manya masu daula da iko daban daban gabaki daya a yayan sultan din manyan yayansa ne kadai basuyi aure ba wato yayan Haile su biyu Aslm da meryam ta ukunsu neesat tayi aurenta sbd rayuwarta akwai sauki sabanin ta yan uwanta, Rashin aurensu nada nasaba ne da rashin shaawan auren da basu da shi sbd raayin hakan da mahaifiyarsu ta cusa musu sbd batason su taba aure Masarautar da batai ko kusan matsayin ta mahaifinsu ba, Duk masarautun da ake aurar da yayan masarautar BOYEM basuyi ikon Masarautar boyem dinba sbd ta boyem din itace wadda babu kamarta dan hakanne dole sai wadda bata kaitaba amma suma Masarautun baa baya sukeba ko kadan ga tarin arziki da dukiyar da bata Jin kashewa tareda iko da mulki me karfi ta qasashe daban daban amma duk da hakan HAILE ta kasa barin yayanta su zaba ko daya daga cikin duk masauratun da ake kawo musu tayin aure gashi a al’adar BOYEM sukuma mazan ne kadai basada ikon auren macen daba jinin ahalin ba amma matan Ana aurar dasu wani gurin kuma Sam baa taba yiwa macen datake jinin BOYEM auren tilas saida cikakken raayinta sbd zataje ne qasar daba tata ba idan akai mata tilas zata rasa ahalinta kuma taje tayi qunci dan haka basa tilas tin farko ga matan boyem, Wannan dalilin ne ya saka yayan nata suke Zaune masarautar mahaifinsu haryanzu hakama a tsaye suke qyam Akan tabbatarda karban mulkin dan uwansu Wanda tsufa ya kamasu a gida batareda sun ankare ba takai sultan ya rufe kofar Neman aurensu kwata kwata hukuncin su sai ranar da aka nada sabon sultan a Masarautar BOYEM shine zai bude musu kofar Neman aurensu daya rufe, Hukuncin ya rikitar da rayuwarsu kwata kwata ta juye ta zama baqin cikin da babu Sauran hasken sauki a cikinsu sai zallar rashin imanin yadda da hakura daga abinda suke so dan kuwa indai wannan hukuncin dake kansu zasu jira to ko zasu kashe rai nawa suma saisun tabbatarda ASIM ne ya zama sultan dan kuwa idan ba shidinba ya hau babu me dauke wannan hukuncin zasu tsufa su mutu ne ba aure dan haka babban burinsu na rayuwa Akan tasu dalilin na tsananin son aure ya karfafa kudirinsu Akan hawan ASIM boyem dan yanzu wannan ne ma babban dalilinsu na jajircewa, Ita kanta queen HAILE wannan shine dalili na biyu me karfi daya sakata tsayuwa Akan qudiri daya na tabbatar da ASIM ya karbi mulkin boyem sbd ganin yayanta zasu suna shirin tsufa su mutu babu aure ga qanwarsu neesat dake aure Masarautar Malaysia yayanta hudu babban ‘danta ma yana kokarin shiga university amma su Sauran suna gida manyanci yana sako musu Kai dan kuwa shekaru ashirin ake magana yanzu ko Bayan Barin NUAB ALMAZZ kasar idan aka hada da shekarunsu na baya ma suna hararar shekarun da suke Neman na wuce aure ma. *******wishmah Ayanah tinda ‘danta hasken idaniyarta da zuciyarta ya tafi bata taba sake walwala ba a tsayin shekarun nan, Bata taba manta tsananin soyayya da kaunar datake masa ba kona daqiqa daya, Bata taba manta kamanninsa ba, Bata taba dena kewa da tsananin son ganinsa ba duk da babu ranar da baya wuni kiransu akai akai yana video call da itaba sbd tsananin kauna da soyayyar dayake mata wadda ta zarta rayuwarsa da babu komai a ciki sai emptiness da Wani irin Zafin jinin sarauta dayake yawo a jininsa fiyeda mahaifinsa, Wishmah a hankali taci gaba da manta komai da kowa harta gama mance komai a rayuwarta bata tina komai da kowa Bayan mutane biyar da sune rayuwarta,sune ji da ganinta a yanzu datake tamkar sabuwar haihuwa, Qunci da baqin cikinta sun wanke babusu a zuciyarta sbd Manta komai datai dan haka rayuwarta take simple fayau ba damuwa da tashin hankali Bayan damuwan rashin HAYATEEM dinta da baya tareda ita Wanda shima hakanan koyaushe take rasa dalilin daya saka bakinta yake furta masa kada ya dawo qasar BOYEM Wanda shi kansa NUAB din wannan furucin nata ne ya hanasa dawowa qasar wadda har abada ya fitar da ita cikin ransa baida niyar dawowa rayuwa a cikinta. Mutane biyar da su kadai ne a zuciya da kwakwalwan wishmah sune, Shi kansa HAYATEEM din nata sai Mahaifinsa sultan data kasa cirewa a cikin kanta Wanda duk tsawon shekarun nan babu ranar da shima baya video call da ita kowace asuba sedai bata cewa komai haka zai kira ya zuba mata idanuwansa yana kallanta tana masa shiru batareda cewa komaiba itama tana kallansa harta gaji ta kife wayar tayi kwanciyarta tenya tazo ta dauki wayar ta fice da ita Wanda hakan wani sirri ne da babu Wanda ya sani a duniya daga sultan din se tenya wadda itama ta rasa dalilin sa na hakan a kowace asubar bayan kuma ya Riga ya nunawa duniya wishmah da ‘danta basa gabansa. #MAMUH #LEUL NUAB ALMAZZ BOYEM #BOYEM LEUL #ALMAZZ NUAB HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 48 Bayan NUAB da sultan YASAR dake zuciyar Ayanah ABAAS ne Wanda bakinta bai taba qasa da kasa fada ba hakama zuciyarta bata taba mantawa da tsananin sonsa da kaunarsa ba hakama bakinta bai taba gazawa da fadawa NUAB yayi mata alkawarin kawo mata Abaas kada ta mutu bata gansa ba ta sake rungumar sa a jikin taba Wanda ba ita kadaiba zuwa yanzu babban kudurinsa na rayuwa ya zama na bawa mahaifiyarsa abinda takeso, Sauran mutum da sukafi kowa zamowa rayuwarta ta yau da kullum Bayan ‘danta da Abaas sune sakinah da tenya da suka sadaukar da rayuwarsu tin daga Sauran yarinta da suke da ita har zuwa yanzu da manyanci ya Kama su dukan sun tsaya da lafiyarsu da lokacinsu da rayuwarsu sun bata kariya da kulawa kuma sun shirya hakan har qarshen rayuwarsu data rage musu dan haka itama duk da a yanayi na rashin memory da rashin nutsuwa da lafiyar tinani sune wainda ta sani kadai a rayuwarta datake jinsu har jini da ruhinta da suka zame jininta koda basu hada jinin ba a yanzu sune asalin jininta datake kalla dan a lokuta da dama idan dan tinaninta da ya hau daidai takan zauna ta qura musu ido ta ringa kiransu da Zuhrah da Nurat tana hawaye tana rintse ido sbd ciwo da radadin na taso mata a kirji da baa son kwata kwata taba tinawa da wannan kuncin sbd lafiyarta da kome zai iya faruwa idan wannan quncin da baqin cikin ya dawo mata cikin kwakwalwa dan hakanne kwata kwata Bayan kokarin kulawa da sake mantar da ita komai babu abinda su tenya ke kokarin yi, Baa iya zuciyar wishmah sukeda matsayi me girma ba a zuciyar NUAB ALMAZZ su din taurari biyu ne da bazai taba iya biya ba har qarshen rayuwarsa, Su din haske ne a rayuwarsa da suka bawa halittar datafi komai na duniyarsa daraja kulawa da tattalin datake buqata a lokacin da bata kowa a duniya Bayan shi kadai kuma aka rabasa da ita, Sun kular masa da ita tin baizo duniya ba harma Yazo duniyar ya zama abinda ya zama yanzu Amma haryanxu sune suke tsaye akanta Bayan Wanda take full responsibility yayi watsi da rayuwarta batada amfanin komai a rayuwarsa baya buqatanta bayin matarsa ma sunfita daraja. Bayan zallar kauna mai girma da darajar su dayake gani matsayin iyaye mata da tamkar sune suka haifesa yake basu dan hakanne kowacensu takejin sa Aranta tamkar itace ta haifesa musamman sakinah da bata taba sanin menene namiji ma bare haihuwa dan haka take Jin LEUL NUAB tamkar dan data haifa da cikinta hakama tenya dake da yaya biyu mata da tini sukai aure basa masarautar jinsa tamkar ‘da namiji da Allah bai bata ba, Da wannan rayuwar bangaren wishmah AYANAH samun nutsuwa da kwanciyan hankali a tsakaninsu da bayinsu gida bakwai dake hidimar bangaren komai nasu a kebance hankali kwance da nutsuwa, Basu taba damuwa da komaiba a yanzu da komai na masarauta tinda komai baayi dasu sun koma kamar babu su, Sultan ya yafe wishmah bata ma cikin masu zuwa tiraka tin shekarun da suka gabata hakama babu wata hidimar dake tasowa ta fito sbd yanayinta, ‘Danta da ake tinanin matsayinsa a Masarauta shima baya nan dan haka basa lissafi Sam idan ba tozartasu zaayi ba baama ambatar su dan haka suka zama bangaren dayafi kowane bangare shiru da rashin hayaniya, Tenya tini ta rasa matsayinta sbd anrufe karban imebeti dan haka Kai tsaye ta koma tamkar yaya kuma jakadiyar wishmah da LEUL da babu ranar dawowansa. Tinda NUAB ALMAZZ yabar qasar boyem tsawon shekarun sultan YASAR baitaba maganarsa da kowa ba kaman yanda bai taba Nemansa ba hakama NUAB din kansa bai taba Neman mahaifinsa ba sbd sun rabu Akan zazzafar zuciyar dake cin kowannesu ta jini daya dake yawo jikinsu, NUAB ya tafi da Wani irin ciwon da har abada bazai barsa ba wato ciwon ganin idonsa yanda mahaifinsa ya wulaqanta masa mahaifiya batareda tinani da tausayin ciwon datake rayuwa a cikinsaba, Ya tozartata ya bawa duniya da dabbobin dake duniyar harma da ‘yayan dabbobin tozartata, Littafin tarihi ya buga sunanta a matsayin daba kowa ba face mistress din da batada kowane irin muhimmanci da daraja a Masarautar da a gurinsa takarmin Ammin tasa ya fita daraja a idonsa da zuciyarsa, Duka wannan bai isa ba saida ya rabata da ‘danta tareda saka dokar karya taba dawowa masarautar saiya gama karatunsa duk sbd a quntata rayuwarta….. Da wainnan abubuwan waye Sultan din da zaiyi fari a zuciyarsa? Bayajin laifin mahaifiyarsa ne data zo a matsayin imebēti zuwa wishmah dan haka babu Wanda duniya ya isa ya wulaqanta masa uwa batareda ya takasa ya shayar da nasa dabbobin jininsa ba Bayan mahaifinsa Wanda shima daraja ce da girmansa na uban dayayi cikinsa aka haifesa yake ci amma kaf boyem babu Wanda bazai iya tara jininsa a pool yayi wanka dashiba indai Akan wishmah AYANAH GHAZ ne. Bayan gama karatunsa sultan dayake biye da kowane irin motsinsa a rayuwa jiran dawowansa ya fara yi sbd ya zama abinda yakeson ya zama din wato mai cikakken tarin ilimi da rashin tsoro da Izzar dake yawo jininsa amma ga mamakin sultan mai girma NUAB ALMAZZ babu boyem a ransa ya shafeta kwata kwata har abada bai niyar dawowa dan babu ita a ransa ya cire, BOYEM bata cikin abinda yake da shirin dawowa a tsari da qudirin rayuwarsa mai karfi daya shirya. Wata irin rayuwa mai karfin gaske da power data fara saka zuciyar sultan nauyi NUAB ALMAZZ ya fara ginawa a Russia wadda ta fara bayyanar da irin karfi da power din dazaiyi wadda hakan zata ma iya zama hadari da boyem sbd babu ta yanda boyem zata zama Abokiyar gaba ko fada da ‘dan daya fito daga jininta. A zuciyar NUAB ALMAZZ ya jima da goge boyem a rayuwarsa dan kuwa tabbas baida niya ko raayin komawa har abada aransa, Baida kowa da komai da zai sakasa komawa Bayan Amminsa wadda yakeda kudirin daukota ya dawo da ita hannunsa itama tabar BOYEM kenan har abada, Duk Wanda yake duniyarsa yasan alaqa daya ce ta rage wadda ta liqesa da Masarautar boyem wato mahaifiyarsa dake hannun masarautar haryanzu, Buri da babban qudurinsa dazai qarasa yanke masa boyem a rayuwarsa shine Amminsa ta kasance a hannunsa to daga ranar ko sunan boyem bazai sake bayyana a cikin sunansa ba bare wata bayyananniyar alaqa….. Sultan YASAR ya dade da sani da fahimtar hakan daga NUAB ALMAZZ dan haka shima yake a shirye tsaf da jiran wannan ranar da zai tinkari boyem da buqatan mahaifiyarsa wadda shima a nasa bangaren babu abinda har abada zai sakasa barin AYANAH GHAZ se mutuwarsa amma duk da hakan babbar dama ce daya tak Allah ya basa Akan ‘dan cikinsa daya zama Zakin da duk abokan Huldarsa da jamaar sa suke shakkar datake tamkar Sarkin dayake kere sarakunan gaske dan haka yana nan yana jiran ranar da dansa zai nemesa Akan hakan Bayan shekarun da suka dauka babu huldar komai a tsakaninsu. ********** GHAZ VILLA No 1148 Arbat Moscow Russia Securities ne zagaye da villa din jefi jefi sbd security room din dake gefen gate din shigowa villa din a ciki suke bin security cameras din villa din da kallan tsaro akai akai Wanda hakan ne ya saka jefi kadan ne na securities dake zagaye da gidan kuma basada kowane irin barazana da suke fuskanta ko hadari dan haka duka securities din dake gate dana security room basa cikin hayaniya ko daya dan wannan tsari ne da dokar aikinsu da maigidansu baya buqata ko kadan wato hayaniya da tashin hankali dan hakanne koina na villa din tsit yake komai a natse ake yinsa ake kuma aikatawa, Tin daga securities dake villa din har maids da cook da Madame din da kula da maaikan Vilar babu Wanda ba zallar nutsuwa ce yake aiki da ita ba sbd villa ce da babu inda ake buqatan garaje ko gaggawa a cikinta, Villa ce da kaf maaikatanta sukeda ilimi me kyau da iya aiki dashi dan baa buqatan kowane aiki da babu ilimi a cikinsa, Villa ce da duk Wanda yake cikinta yakeda yanci da sakewa a cikin masu aikinta amma kuma hatta takawansu a tsari da ilimi sukeyinta ko a gurin aikin nasu dan hakanne duk wani mai aikin GHAZ villa nutsuwansa ta musamman ce duk da akwai lokutan da suke sakewa a tsakaninsu suyi raha da dariya da sakewa sosai amma idan mai villa din kanta yana gida atmosphere din na musamman ne, Kudi da rayuwa me nutsuwa da tsaron da yake tabbatar musu da sun gama samun Saar rayuwa duk wani maaikacin villa din suke samu Wanda ya saka suke sake Jin babu wata rayuwar gata data fi musu zama masu aiki a karkashin NUAB ALMAZZ har qarshen rayuwarsu, NUAB ALMAZZ me GHAZ villa da GHAZ Empire gabaki dayanta dake buga lokaci da daukaka a qasar da wajen qasar harma da qasashe da dama a bangaren harkar business da kuma qera jirage, NUAB ALMAZZ Wanda yake cikin shekarunsa na daukaka da suna ya tsayu ya kafu ya kuma kafar da duniyarsa da babu Wanda zai iya girgizata idan ba Allah daya kafasaba, Tarin dukiya da daukaka da arzikin dayake nuni da shi din jinin boyem ne ba matsalar datake gabansa bace dan kuwa ya tara dukiyar da Bayama lissafa wa hakama babu ta yanda zuriar sa shima zasuyi talauci har qarshen rayuwarsu insha Allah dan kuwa Allah ya tsaya masa Akan kowace huldarsa da businesses nasa, Shi din dan business ne kuma shugaba ne na tsayayyun matasan da basu da gata harm da qananun yara maza wainda da uwansu sun rasa iyaye sun fada wata rayuwar da batada kyau, Bayan zamansa babban tsayayyen business tycoon a qasar da wasu qasashen kallan riqaqqen mafia boss ake masa wato shugaban yan taadda sbd kasancewansa jarumin daya zama cikakken gatan duk wani dan taadda da rayuwarsa ta lalace kuma ya zame musu tamkar uba yana kawo sauyi a rayuwarsu , NUAB ALMAZZ ya zamo uban marasa gatan da rayuwarsu ta lalace ne sakamakon Tsintar matashin da aka kashewa uwa da uba da Kanwa aka cinye masa gadonsa duka sbd son zuciya irin ta dangan mahaifinsa sanadin hakan ya fada harkar taaddanci mai karfi a haka aka kamasa aka shiga kotu dashi aka yanke masa shekaru biyar gidan yari tin yana da Sauran kuruciya, Shekaru biyar yana fitowa gidan yari NUAB ya daukesa ya tsayawa rayuwarsa tsaf saida ya tabbatarda ya samu adalcin daya kamaci iyayens da basa duniya. #MAMUH #LEUL BOYEM HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 49 Tin daga wannan lokacinda ALEEY KUAS ya zama babban yaron da babu kamarsa a gurin NU'AB Almazz, Aleey ya sadaukar da rayuwarsa ga kowane hukuncin NU'AB ALMAZZ da zai iya sadaukar da rayuwarsa ya bada ita batareda kowace irin second tinani ba indai Akan NUAB ne, NUAB ya Inganta rayuwarsa ta hanyar sakasa ya qarasa karatun da bai qarasa ba ya hada takardunsa ya zama cikakken mutum da ayanzu ilimin sa yake daukan businesses da mahaukanta kudin da bai taba tinanin a rayuwa zai taba iya ko lissafowa a mafarkinsa ba, Ya tsayu ya kafu a cikin manyan businesses na qasashe daban daban yana tsayuwa a gaban mutanen da bai taba tinanin zai iya ganinsu idan ba a news paper ba ko tv amma a yanzu a gabansa yake ganinsu tareda boss dinsa harma kusan shine yake gabatar da abubuwa da dama na haduwar da businesses din dan haka rayuwarsa tayi Wani hawa da saman da badai masu qananun matsayibama sedai manyan duniya duk ta Sanadin Ubangidansa da ko rai yace ya dauka to tabbas bazai qara mintina biyu batareda ya cika umarnin ba, Duk abinda NUAB ALMAZZ yake so ko menene shi aleey yake so ba me kyau bane kuwa hakama abinda NUAB ALMAZZ yakeso to aleey yana sonsa da dukkanin rayuwarsa dan hakanne burin Ammi ya zama qudurarren burinsu da dukkanin Wanda yake qarqashinsu na Neman Abaas a duk duniyar dayake koda hakan na nufi zasu juya nahiyoyi da dama. Tin daga kan aleey NUAB ALMAZZ ya zama gatan kowane mara gatan, Sama da daruruwan yan taaddan qasashe daban daban da kaddara ta sakasu fadawa taadanci da shaye shaye NUAB ya tallafi rayuwarsu ya sakasu jikinsu ya kawo sauyi a rayuwarsu suka zama Yaransa cikin sauyawa zuwa masu abin yi, Duk Wanda bai gama karatu a cikinsu yana sakasa ya qarasa karatunsa ya fara aiki a qarqashin sa wainda kuma Sam basuyi karatun ba suma aikin da zasu iya a duniyarsa yake sakasu dan haka kusan duka wainda suke a qarqashinsa ire irensu ne amma kuma ilimin sosai suke samu dayake ratsa su sun zama yan business din gaske da kamar da saa kowannesu yake yawo dan kuwa tako ina cigaban GHAZ empire ake samu, Tamkar zakuna suke a cikin duniyar manyan business tycoons sbd tsananin ilimi da saarsu harma da qwanjinsu dayake bayyane Akan zasu iya komai akai ubangidansu da ayanzu kusan koina duniya ta sansa sbd tarin yan amanarsa kuma yan taaddansa dan duk da sun sauya rayuwa sun taka matsayin cigaban rayuwa wannan rayuwar ta rashin sauki da rashin tsoro yana nan a tattare dasu, Ilimi da kudi tareda power da suke samu daga shugabansu NUAB ALMAZ ya qarawa rashin tsoro da zuciyarsu kafin gaske da basa shakkar komai da kowa a duniya idan ba shi dinba da babu Wanda baya sauke masa Kai idan ya fito sbd girmamawa dan shine ya jasu cikin jikinsa da dukiyrsa ya maidasu mutanen da kowa yake shakka a yanxu dan haka duk da wasu sun girmesa wasu kuma tsarin shekarunsa ne da wainda ma ya girma gabaki dayansu a uban dayafi kowane uba daraja kimar da zasu iya tasa yaqin duniya akansa suke kallansa, Tsoronsu akeyi shakkar su akeyi sosai sbd uba gidansu yana dukiyar da suke juya duniyar yanda suke so, Kusan dukkanin yaran nasa babu Wanda baiyi zaman gidan yari ba sbd rashin adalcin sharia amma ayanzu sun Kai sun taka matsayin da koda a gaban mutane zasuyi Kisa babu Wanda zai dago ya kallesu amma kuma ba irin rayuwar suke yiba yanzu dan kuwa business suke me tsafta da class da tsari amma duk da hakan kallan yan taadda masu karfin gaske ake musu Ana tsananin shakkarsu. Yaransa sune yan uwansa, Sune danginsa, Sune yake shiga cikinsu yayi nutsuwa ko babu hayaniya sune ahalin da suka cike gurbin ahali da dangin da baida kaman yanda shima shine ya cike gurbin iyaye da yan uwan jini da suka rasa dan haka Bayan komai akwai kauna mai tsananin karfi a tsakaninsu dasuke wa juna su dashi, Iya kafuwa da tsayuwa GHAZ empire ta tsayu, Manyan qasashe da Masarautu ne da manyan tycoons na karshe ne abokan huldarta dan hakkanne NUAB ALMAZ yayi suna da fice a duniya da yake da Wani irin matsayi da girman gaske a idanuwan duk wani marasa karfi da galihu, A cikin abokan huldarsa kuka shi din Zakin dayake yawo ne da saa a rayuwarsa, A gurin tarin yaransa da uwansu ya kere na Masarautu da dama shi sarki ne da a duniyar nan idan yace A to A dince idan yace kuma B ce to dince kawai ko uban kowa ya yadda ko kada ya yadda, Shi sarki ne da ko masarautar ubansa yace su tayar bazaa kwana ba saisun saka jini gudana a cikinta ta shefe kaman baayi kowa a cikinta ba. Duk suna da tambarin da ake masa Akan zamowa gatan yan taadda bai taba bawa ko yan jarida daman fira dashi ba Akan hakan sbd baya buqatan yiwa kowa a duniya bayani kawai dai yasan yana samun feelings na nutsuwa daga sauya musu rayuwan da yayi hakama kusan yanajin radadin daya sauya rayuwarsu zuwa ga illa sbd yasan ciwo da radadin abubuwa ire iren wainda suke tinda shima tin da qananun shekaru aka rabasa da tasa uwar da haryanzu baiji dumin jikintaba taji nasa, Fushi ne a zuciyarsa da haryanzu bai huceba, Zafi ne a cikin kansa da haryanzu wutarsa bata mutu ba, Qiyayya ce me karfin gaske dayake wa jamaar Masarautar BOYEM da haryanzu bai sauka ba sai ranar da mahaifiyarsa ta shigo hannunsa ne kadai komai zai iya fara sassautowa. Duk wani Zafi da fushinsa a zuciyoyi da kan Yaransa take ci batareda sun San menene a ransa ba dan haka iya gane menene zuciyarsa amma dai tinda suka sansa sukasan da wannan wutar dake ci a cikin idanuwansa dan haka tasu zuciyar da ruhin basu taba Dena ci da wutar Zafi ba da jiran kowane umarnin sa Akan koma menene ba. Duka wannan rashin tsoron da rashin shakkar da GHAZs kaman yanda ake ambatar su sbd sunan komai nasa daya mallaka a rayuwarsa sunan mahaifiyarsa ne amma iya GHAZ din suke dashi sun samo izzar hakan ne daga ubangayyarsu LEUL NUAB ALMAZZ da babu sunan shakka ko tsoro bare fargaba a cikin littafin rayuwarsa datake tsaye cak kaman mashi, Komai Zafi da rashin saukewa kowa Kai a duniya idan ba shi ba basu kamo sa ba ya dame dukansu ya shanye babu Wanda kaf duniyar baya iya dagowa ya kalla da idanuwansa idan ba iyayensa mata ba sai kuma ubansa dabai San yaya zai kallesaba tinda basa tare shekaru. Izzar dayake bugawa da iko tareda taqama da tsananin power dayake Juyawa da ita sun hadu hade ne da jinin dayake yawo a jikinsa na sarautar BOYEM, Duk wannan shekarun yayi su ne yana jiran ranar da Amminsa zata furta masa ya taho ta janye kamalanta na kada ya dawo, Daga ranar da Amminsa ta furta masa tana son zuwansa to tabbas a ranar bazai kwana ba sai jirginsa ya saukesa qasar BOYEM hakama bazai Baro ba saiya tabbatarda uwarsa ta dawo hannunsa. Wannan kiran shine kiran dayake jira daga mahaifiyarsa kowace daqiqa dan haka aleey ma koyaushe a shirye yake tsaf da jiran kiran ya shirya saukar su BOYEM da me BOYEM din gabaki dayanta duk da baya buqatan mulkinta. Villa dins datake kamar gari guda kusan fiyeda rabin Yaransa dake Russia suna cikinta bangare daban daban Sauran yaran nasa kuwa suna qasa daban daban inda yake da companies dan haka villa din akwai tsaro mai tsari da rashin hayaniya, Duk Wanda yake karkashin GHAZss baya cikin wahala ko talauci Bayan kwanciyan hankali da rashin hayaniya sai zallar iko da rashin tsoro dan Sam baya kaunar lusari ko sakaran namijin da bazai iya tsayawa namiji ya cire tsoro a zuciyarsa ba a karkashinsa dan hakanne ya kasance duk Wanda yake karkashin GHAZss babu Wanda ba tsayayyen namiji mai zarra ba hakan ne ya saka koina suke kwarjinsu daban yake bare ace uban kwarjinin nasu na guri. ******* Hayaqi ne da qamshi yake fitarwa me nutsuwa yake cike da gauraye toilet din  mai tsananin girman da koina daukan ido yakeyi sbd kyallin tsaddan luxury vinyl tiles da komai na Duravits toilets dayake tsare a toilet yana saka jikin duk Wanda ya kalla mutuwa, Qarar shower ce yake tashi a cikin luxury steam and sauna shower room dake cikin toilet alamar wanka akeyi da ruwan dumin da hayaqinsu yake bada qamshin shower gel dinsa na the Noir, Tsawon mintina a ciki kafin ya kammala Hannunsa me tsananin haske da lafiyar fata ya bude kofar kafin kafafunsa suka fito ya fito gabaki dayansaa ruwa na gangarowa daga lafiyayyar farar fatarsa da Hutu da lafiya kawai take bayyana wa tana daukan ido, Ruwan ko zama basa yi a farar fatarsa Kal sbd santsi da lafiyarta gangarowa sukeyi kawai suna sauka qasa. Gurin da towels suke a Jere a tsare kaman bundles na kudi ya nufa ya miqa hannunsa daya ya dauko daya ya daura a kuqunsa kafin ya sake daukan daya a natse cikin asalin nutsuwan sarauta dake yawo a jininsa ya Dora a kan gashin kansa dayake tamkar na mahaifiyarsa yafara gogewa ahankali kafin ya fito sanye da fararen soft sole bedroom slippers yana nufar makeken dresser mirror din dayake closet dinsa mai girman dayafi na daki biyu dan kuwa tarin sutura ce a Jere da basada adadi babu kalar designer din data amsa sunanta da babu a gurin tin daga kan bangaren agogunansa da suke bugun mahaukatan dollars har zuwa kan takarman sakawansa da suke cin manyan kudi da bangaren wandunada shirts da suits da underwears hatta ties na wuyansa da socks dinsa kowanne da bangarensa daban inda aka jerasa. Ga turaruka suma da pins da combs nasa suna kowanne baida adadin number dan babu abinda ake siya kadan hakama akai akai ake qaro wasu Ana jibgawa. Cikin nutsuwa da rashin hayaniya ya shirya tsaf a cikin navy blue loro pianas vicuña polo shirt da Michael kors trousers fari tas ya komai na jikinsa na fidda wani tsadadden qamshin Gaultier elixir na yana gauraye niimar duk inda ya wuce da inda yake tinkara a cikin sanyi. Palonsa na hutawansa y wuce Kai tsaye cikin nutsuwa zuwa palon da dining room dinsa yake inda zaiyi breakfast da aka gama cike dining din a tsare da aji, Tin daya doso qamshin sa ya sanar da aleey fitowan sa dan haka ya miqe daga Zaunen dayake riqe da iPad me girma dayake wani aikin report da aka turo daga kamfaninsu dake Brazil. Ajiye iPad din yayi yana dago Kansa ahankali ya sauke Akan hanyar da NUAB ALMAZZ din daya fito kwarjinsa da Kyansa dayake sake cika idanuwan duk me kallansa na cike gurin gashinsa dayaji tsadaddun mai yana sake a kafadarsa ya dago idanuwansa da babu abinda suka Baro na mahaifinsa ya Dora Akan aleey din yana qarasowa kenan wayar sa da iya mahaifiyarsa kadai ke kiransa da wannan layin tayi haske tana ringing mara qara. Dago wayar da hannunsa yana dakata wa cak ya fasa isa dining din ya isa kan wasu mahaukatan luxury sofas dake palon ya zauna a natse tareda ajiye Dayar wayar hannunsa a gefensa kafin ya daga wayar cikeda nutsuwa da kulawan da baya bawa kowa duniya sai ita ya bude Baki muryansa mai tsantsar nutsuwa da Izzar sa da bata boyuwa yace ‘Ya Ammi…. Katsesa maganarta da muryan data tada tsikar jikinsa gabaki daya da cewa ‘HAYATEEM Inason kasancewanka a tareda ni duk lokacinda Ka samu daman hakan…… #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 50 Gashin jikinsa ne suke qarasa miqewa ahankali maganarta ta ratsa kunnuwansa zuwa kwakwalwan kansa da zuciyarsa data tsaya cak gurin bugawa, Numfashi me sanyi mara sauti ya sake a natsensa dan gasgatar da maganar Ammin tasa da bata taba raayin dawowansa BOYEM ba haka kawai amma Ayau kunnuwansa na jiye masa sabanin kalamanta na koyaushe da kullum, Bude bakinsa yayi cikin sautin da ita kadai yakewa magana dashi sbd sanyinsa da nutsuwansa yace ‘Ammi,kina buqatan ganina? Akwai abinda yake damunki Ammi?’….ya qarasa maganar da zallan kulawansa da kaunarsa akanta yana jiran amsarta dan karantar yanayinta dayake cikin sautin muryanta. Shiru tayi itama acan bangaren nata tana rufe idanuwanta ahankali sbd muryansa dake ratsata a duk lokacinda zata ji muryansa tsananin kaunar danta kaman zata qarasata takeji amma hakanan take daurewa shekaru masu yawa sbd koyaushe zuriyarta na hanata barinsa dawowa sbd kada aci gaba da kiransa dan mistress Wanda ako Yaushe aka ambacesa da hakan har cikin ranta da zuciyarta take Jin radadin hakan musamman data ga sunan yana kokarin zama abin alfaharinsa dan baitaba Jin ciwo ko damuwan abinda ake ambatar sa dashiba amma su sunajin ciwon hakan, A yanxu zuciyarta takai maqurar kasa daurewa da hakurin rashin ‘danta a tareda ita musamman da zuciyarta take cikin rashin sukuni sosai da Wani irin tsoron da batasan na menene ba dan haka jikinta yake Neman rikicewa sbd ko bacci kwata kwata ta rage sosai Wanda shima yake qarawa lafiyarta illa me girma dan haka su tenya da sakinah suke cikin tsananin damuwa da rashin yaya zasuyi gashi basuda ikon sanar da sultan suke gani tinda bata gabansa babu abinda yake gabansa nata likita dayane tinda ya nadasa mai duba lafiyar Ayanah din shikenan baitaba fasa zuwa bibiyan lafiyar taba koda Yaushe a tsawon shekarun nan, ‘Ammi’ ya Ambaci sunanta cikin sanyi da kauna me girman gaske tareda nutsuwan da bayason damar da ita sbd jinta shiru. A sanyaye ta sauke bayyananniyar Numfashi jikinta gabaki daya a mace ta bude Baki tace ‘NUAB,Yene HAYATEEM,Yene LEUL idanuwana suna son ganinka, Zuciyana da ruhina duka san ganinka sukeyi kafin na…..’ Katseta yayi da tsananin nutsuwa da cewa ‘AMMI’ sbd yasan kalman mutuwa ne zata qarasa dashi, Tsigar jikinsa ne suka sake tashi a hankali Wani irin yanayin da mahaifiyarsa ce kadai ke motsa zuciyarsa na ratsashi sbd ya tabbatarda akwai abinda yake damunta ko zuciyarta dayayi girman datake buqatan ganinsa harta furta da bakinta, Dole wata damuwarce take faruwa da kila batasan tayaya zata iya gane wa ko fada masa ba kawai ta buqaci ganinsa sbd zuciya da ruhinta su sanyaya, Numfashi mara sauti ya kuma saukewa tareda dagowa idanuwansa farare tas masu Kayar da gaba da suka sauya a take suna dan rikida da ja ya bude Baki a natse yace ‘Ammi bakida lafiya ne? Girgiza masa Kai tayi a hankali da sanyi kaman yana kusa da ita Wanda sautin ya shigar masa kunne a cikin sanyi dan haka ya rufe idanuwansa ahankali ya kuma bude su yace ‘Akwai abinda yake damunki Ammi? Nan ma girgiza Kai tayi a natse batareda tinanin ba lallai ya fahimta ba, Nan ma yaji Gyada kan sbd akwai yan kunnen zinari masu dan fidda sauti kadan a kunnuwanta Wanda ya saka idan ta girgiza Kai sautin su ke shiga kunnuwansa suna narkar da zuciyarsa da babu abinda take tsananin so da kauna a duniya idan ba ita din ba ‘Ammi akwai Wanda ya saka miki damuwa’ Girgiza Kai tayi ya sauke Numfashi me sauti wannan Karan ya bude baki zaiyi magana muryanta ta Katsesa a sanyaye tace ‘Idan zaka taho kazo da Abaas,ina son ganinsa HAYATEEM’ Rufe idanuwansa yayi a Wani irin yanayin da zuciyarsa ke cizo da radadin kasa bawa macen da ita kadai ce rayuwansa abinda takeso sama da shekaru masu yawa. ‘Ammi zan taho gareki ba tareda Abaas ba amma nayi miki alkawarin indai Abaas yana raye zan kawo miki shi a gabanki, Nayi miki Alkwarin indai Abaas yana raye zan Nemo miki shi zai qarasa rayuwarsa a gabanki bazai taba barin gabanki ba har sai mutuwa ta rabaku….. Wasu hawaye ne suka gangaro idanuwanta da suka saka hankalin sakinah dake tareda ita a palo Zaune tashi sbd bata kuka Sam a yanzu sbd kuncinta da baason ya dawo dan haka a natse ta iso gurinta ta zauna gefenta ta kalli wayar hannunta ta miqa hannu tace ‘Nima zan gaisa dashi’ Miqa mata wayar Ayanah tayi cikin nutsuwa tana cewa ta yadda da NUAB zai cika mata wannan alkawarin ko Bayan ranta ne zai nema Abaas. Maganar tata har kunnuwansa ta sauka ta shigesa a hankali ya Lumshe idanuwansa yana Jin wata wuta mai Zafin gaske tana kunnuwa a zuciyarsa ta son kasancewa da mahaifiyarsa da tabbas lokaci yayi da zai dawo da ita hannunsa dan kuwa daman magana daya ce duk ranar daya saka kafa a BOYEM to bazai taba tafiya batareda mahaifiyarsa ba, Babu me buqatarta a masarautar da qasar gabaki daya hatta Wanda take zamansa baya buqatanta ya watsar da ita tin tanada kuruciya dan haka shi babu abinda yake buqata a rayuwarsa sama da ita a basa ita kawai shine cikar duk wani burinsa na rayuwa Bayan hakan baya buqatar komai a rayuwarsa. Saukar muryan Maa sakinah a kunnuwansa ya sakasa bude idanuwana jajir yana bude baki a natse da kulawa yace ‘Maa akwai abinda yake faruwa ne?? Akwai abinda ya kamata na sani ne?? Amminah na da damuwa ne? Akwai abinda yake faruwa a masarautar ne daya taba Amminah? A Jere ya jerowa Maa sakinah tambayoyin da suka saka jikinta sanyi ta sauke ajiyan zuciya mara karfi tareda bude Baki cikin nutsuwa ta manyanci tace ‘Babu komai dayake faruwa kawai dai yanayi ne na kewanka datake yi shine kadai ya saka amma ka damu babu abinda yake faruwa’ Shiru yayi itama Maa sakinan yana karantar yanayin muryanta datai sanyi sosai, Kai tsaye yace ‘Maa akwai abinda yake damunki kema? Menene yake faruwa a masarautar nan? Waye ya tabaku? Katsesa tayi da sauri tana kokarin daidaita kanta cikin sauti da dan sauri sbd Jin yanda muryansa ta fara sauyawa tana daukan Zafi da fushinsa da babu me iya kashe wutarsa tin yana yaro tace ‘Babu komai Ka yadda da hakan LEUL,kada Ka bata ranka ko kadan dukanmu muna cikin kwanciyan hankali da lafiya’ Kasa nutsar da zuciyarsa dake daukan zafi yayi ya bude Baki cikin sassauci yayi sallama da ita Kai tsaye wayar Maa tenya ya kira yana bude idanunwansa da sukai jajir Akan Agogon dayake palon dan kuwa matiqar yaji ya tabbatarda akwai damuwan dasuke ciki babu abinda zai Hana jirginsa sauka BOYEM kafin fitowan alfijir din asubar gobe. Maa tenya dake dakinta ta gama sallar nafila wayarta dake kan marble center table din dayake lafiyayyan dakinta da babu duniyar da babu a cikinsa koina na Qamshi da sanyin ac tafara ringing. Hannunta ta miqa a sanyaye ta dauki wayar tareda dauka ta Dora a kunnanta cikin sanyi tayi sallama tana miqa masa gaisuwan data zama kaman dole kasancewansa jinin BOYEM kuma asalin magajin karagar mulkin. Bai amsa gaisuwan sarautarsa ba ya miqo mata tasa gaisuwan ta zamanta uwa a garesa kafin ya Dora da cewa ‘Maa idan akwai abinda yake faruwa ki sanar dani sbd ina rasa hankalina anan sbd Amminah akwai abinda yake damunta kuma Inason saninsa koma menene’ Ajiye Numfashi me sauti sosai tayi kafin ta sake shiga sanyi da nutsuwa tace ‘Allah ya qara maka lafiyar zuciya LEUL BOYEM Amminka jikinta yana Neman dawowa sosai a kwanakin nan rikicewa kawai lafiyarta ke kokarin yi Wanda tabbas tana buqatan ganinka takeso kafin ta qarasa rasa cikakken hankalinta ta manta waye Kai………. Shiru da tsit yaji duniya gabaki daya tana masa sai yanajin muryan Maa din tamkar sautin dayake tahowa daga nesa sbd straight zuciyarsa labarin ya caka yanajin dumi na gauraye jikinsa koina musamman idanuwansa da sukai jajir. Kasa iya cewa komai yayi sai sallama da yayi mata yana kashe wayar idanuwansa na tsananta ja ya da dago ya saukewa aleey su dayake tsaye gefe yana jiran umarnin koma menene yakeson Ayi. Kallan da yayiwa aleey Wanda ke kallansa cikeda nutsuwa da girmamawa take aleey ya fahimci umarnin sa dan haka Kai tsaye cikin girmamawa da cika umarni yace ‘Aiit B’ iPad din hannunsa ya daga yafara dannawa yana fidda wayar sa itama ya saka kira yana Juyawa yabar gurin yana fara aikin da baya buqatan bata lokaci dan kuwa kome zai tsaya cak sai LEUL BOYEM ya isa fadar da tasa ce gabaki dayanta. Shi kuwa ajiye wayar hannunsa yayi tareda Dora kafarsa Ka daya a hankali yana jingina bayansa da kujeran dayake Zaune yayi folding hannuwansa duka biyu kirjinsa yana Lumshe idanuwansa ya rufe dan kuwa a yanzu komai na rayuwarsa ya tsaya cak har saiya isa yayi tozali da mahaifiyarsa wadda shekaru masu yawa jikinta bai taba tashi ba sai yanzu Wanda a qasan zuciyarsa yasani dole akwai abinda yake faruwa daya saka lafiyarta fara rawa Wanda yana fatar koma menene ya kasance ba wani ne ya aikata komaiba dan a yanda jininsa ke tafasa komai zai iya faruwa Akan koma waye. Dayar wayar ce ta fara ringing Wanda ya sakasa miqewa tsaye ya isa bakin makeken Windownza mai tsare da lafiyayyan grey velvet smart automatic curtains ya zubawa waje idanuwansa da a wannan lokacin da zai sauke maka su zaka iya zubewa qasa kan kafafunka gabansa batareda Ka sani ba. Aleey kuwa yana ficewa daga palon nasa lafiyayyan palon dayake hade da babban bedroom dinsa ya nufa ya fara wayo yi yana aika wasu sakonnin ta iPad Akan tafiyar da zaa hada batareda bata kowane irin dogon lokaci ba ko tashin hankali da hayaniya kawai dai umarni ne da zaa cika a cikin lokacin da sai Wanda ya isa yake iya samun cikawar hakan a qanqanin lokaci. Wuni guda aleey bai zauna ba bai bata kowace daqiqarsa Akan komai ba Bayan shirin hada tafiyar isar LEUL BOYEM zuwa qasar BOYEM din tareda manyan GHAZss dinsa da baya tafiya koina saida su sune manya a cikin kaf Yaransa da kaf duniya bayan aleey daya san kowanne qanqanin sirrinsa da komai na rayuwarsa sune amintattun dan haka aleey baida Sauran kowace nutsuwa saiya gama tabbatarda komai na tafiyar ta kammala a cikin lokacin da ubangidansa yake buqata. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 51 A Daren ko bacci na minti daya NUAB ALMAZZ me boyem baiyiba a Zaune yake daram idanunwansa na bayyanar da ‘daci da Zafin dake cikinsu babu boye wa sbd karshen ‘daci da zafi zuciyarsa takai dan babu tinanin da bai taho kansa ba Akan abinda ya faru da mahaifiyarsa dan haka jininsa ma ahankali ahankali yake qonuwa yana tafasa da Zafin daya mance radadin sa na shekaru sbd a duniya abu dayane ke tafasa jininsa yana qonasa da radadi me Zafin gaske shine banzatar da uwarsa dashi da mahaifinsa yayi Wanda wannan zafi ne wutarsa ke ci bazata taba mutuwa ba dan kuwa babu abinda ma zai kashe masa ita a zuciyarsa, Duk duniya babu Wanda ya isa ya saka ransa radadi da tafasa irin wannan idan ba mahaifin daya haifesa ba dan kuwa shine ya kunna masa wannan wutar dake cin kowane lungu da gaba ta jikinsa, Da ciwon abin yayi wayo a duniya ya tashi dashi harya fara girma dashi harya rayu dashi haryanzu a ransa, Mahaifin daya haifesa ya ajiye macen daya kamata yaso fiyeda Sauran matansa tinda ya bata matsayin wishmah a masarautar sa amma ya kasa tsaya musu ya basu kowace irin kauna da kulawa koman qanqantarta saima watsi da yayi dasu ya nunawa duniya su din ba kowa bane face mistress dinsa da ‘danta da babu abinda zaiyi dasu sbd yanada ‘dan da Matarsa ta Haifa masa ta qarqashin igiyoyin aure dayake fatan ya gadesa…….. Bai taba baqin cikin Zamtowan mahaifiyarsa mistress ba hakama yana nunawa duniya gabaki dayanta ba qaramin alfahari yake da zamtowansa dan mistress ba, Indai mahaifiyarsa ce zata ci gaba da haifosa a duniya to ko zaa maidasa ciki a sake haifosa zaici gaba da zabar fitowa a ‘dan mistress dan haka baitaba sanin menene kunya ko abinda take nufi bama ita kunyar Akan fadar shi din dan mistress ne, Fada yakeyi da isa da izgili da iko da Izza shi dan mistress ne Wanda akanta zai iya tada nahiyoyi da dama ya shafe tarihinsu ko a qundun tarihi. Kaman yanda LEUL BOYEM bai rintsa ba haka aleey bai rintsa ba aiki tamkar computer ya kwana yi shima dan tabbatarda tafiyarsu da wasu shirye shiryen tafiyar tareda qure cikakkun qurewan bincike Akan Masarautar BOYEM da kaf ahalinta na baya da wainda suke rayuwa a cikinta yanxu sbd babu inda LEUL ya taba saka kafarsa batareda ya tabbatarda yayi full bincike Akan gurin ba sbd baya wasa ko mance kowane irin lamari dazai iya shafar LEUL NUAB ALMAZZ dinsu da tsaron da suke basa mutuwa ce kadai da ubangiji zai aikota da kanta zata iya daukansa shiru cikin aminci amma mutum dai da koma menene yake taqama dashi sedai Ayi mutuwar kasko idan ma yanada rabon iyawa dasu kenan. Sauran yaran nasa kuwa tin daga lokacin da zancen akwai tafiya a gaban LEUL take suke cikin shiri dan kuwa a shirye suke tin jiyan kowane lokaci akace yana fitowa to zai samesu tsaye a jikin motoci suna jiransa. Komai na tafiyar ya gama kammala karfe biyu da rabi harma da mintina jirginsu zai tashi na rana dan haka koda karfe da arbain tayi gabaki daya Yaransa da zaayi tafiyar dasu suna tsaye harabar gidan cikin shiri jere a jikin motocin da zaa tafi airport dasu kowannnsu sitirar datake nuni da rayuwar buga kan dala dala sukeyi sbd designers ne a jikinsu duk da basuyi tsadar ta boss din nasu ba suma suna cikin sitirar kudi, Gabak dayansu black kayane a jikinsu duk da kowannesu kalar tsarin kayan dake jikinsa daban amma duka black ne sai sirkin wata kalar da zaa samu a ciki daban hakama mutum hudu a cikinsu sanye suke da fcaps masu kyau da suke sake fidda kalar farar fatarsu ta nahiya daban daban duk da kusan dukansu farar fata ne amma daga nahiya daban daban suke, Sauran mutum shida a cikinsu kuwa gashinsu ne suka tara a sake wasu kuma sun dauresa sai daukan ido yakeyi sbd gyara da tsafta tareda aji dan kuwa ko securities dinsa da Yaransa class ne dasu, A cikinsu babu Wanda kakkarfan karfi baya nunawa a halittar jikinsa sbd wasu irin qwandinan hannu da suka murde ne ke fara Baka tsoro da shaawa a jikinsu sbd geamin din da suke yi dan kuwa idan da zasu cire rigunansu a gaban mata sama da ashirin to kusan sha biyar sai sun Kai qasa sbd mutuwar jiki da shiga confusion, Sauran securities na gate da cikin harabar villa din duka a tsaye suke bakin aikinsu suna jiran fitowansa dan bude masa gate batareda bata lokaci ba. Karfe biyu saura mintina tara Aleey ya fito sanye da Ash original Nike half quarter sweatset da iPad tareda wayar sa a hannunsa daya Dayan hannun kuma agogon bvlgari ne a daure dashi yana kallan time kyakkyawar farar fuskarsa sanye da Prada sunglasses yana tin karo motocin, Ganin aleey ya fito ya tabbatarda LEUL yana hanyar fitowa dan haka kowannesu ya maida kallansa a hanya cikeda asalin kauna da sake sadaukar da rayuwa akansa suke kallan hanyar kowa a shirye da tafiya ko lahira ne yace a tafi, Kamshin Gaultier elixir ne ya fara doso wa a natse yana gauraya niimar gurin da kowannensu yake shaqa dan haka Kai tsaye aka bude masa mota daidai lokacinda ya sako Kai yana bayyana a idanuwansu dake cikewa da zallar asalin kwarjinin sa na jinin sarautar BOYEM da sarautar GHAZ, a natse suka dauka idanunwansu duka daga kansa suna buda masa hanya tareda masa Barka da fitowa, Sanye yake da navy blue asalin original Ralph Lauren shirt da wando sai takarmin original Salvatore ferragamo sai Cartier glasses baqi, A kansa kuwa navy blue melin fcap ce da bata rufe gashinsa dayake daure a bayansa ba duka, Wani irin daukan ido da bada nutsuwan zuciya kyansa da kwarjinsa keyi tareda haskensa Wanda yake saka komai nasa sake zama na musamman, Cikeda nutsuwa da izza da kamewa ya iso hannunsa daya yana riqe da wayoyinsa yana qarasowa Kai tsaye motar da aka bude masa ya shige yana duba time din diamond Rolex agogon dayake hannunsa dan sanin time din dazai dauka kafin dira qasar dazai ga mahaifiyarsa daya dauke shekaru bai gani a gabansa ba. Aleey gaban motar da LEUL din yake ya shiga take aka rurrufe aka fara barin harabar cikeda fatan dawowa da abinda zaaje nema. Suna isa airport babu bata lokaci akai duk abinda zaayi jirginsu ya daga zuwa qasar BOYEM me cikeda tarihi. ********Tsakiyar dare gap da asuba jirginsu ya sauka a qasar BOYEM wadda take qasar arziki da daula itama, Tin a jiyan Aleey bai kwana ba saida ya kammala aikin tanadar da duka mahaukatan motocin dayasan ubangidansa na hawa, Direct yayi magana da manyan companies din motacin dasuka kowanne dake qasar ya siya motocin da duka a Dare guda aka buga business din aka kwashe dan haka Kai tsaye motocin airport ya bada umarnin a kawosu su tarbesu, Hakan akai dan Koda suka sauka a qasar expensive luxury Genesis G70 suna airport din suna jiran saukarsa da babu Wanda yasan da shine zai sauka qasar sa Bayan shekarun da yayi baya nan tin yana yaro. Kai tsaye Sauran formalities din na siye motocin aka qarasa aleey ya saka hannu a komai suka karba komai da key take suka fada motocin guda biyar da suke Wani irin daukan Idon da shedar da ko waye a cikinsu zaman kansa yakeyi bana kowa ba, Map location Kai tsaye sukai amfani dashi batareda an damar dashi da maganar komai suka doshi masarautar BOYEM a lokacin har anyi sallar asuba da sukai tin an airport dan haka gari ya fara haske sosai. Tin daga nesa securities din gate na farko suka hango motocin a tafe suna daukan ido Kai da Kai kamar kumurcin maciji haka sukaga motocin na doso wa cikin wani irin rashin sauti a Jere da juna babu wani space dama ko mashin zai iya bi a tsakaninsu. Suna gap da isowa motar farko ta qaro Wani irin gudu tayo gaba dan isar da sakon a bude gate kafin isowan Sauran motocin da baa buqatan tsayar wa dan basuda lokacin batawa a nan Hutu maigidansu ke buqata kawai. Yanda motar ta doso da gudun ne ya saka securities miqewa suka jeru a kofa tareda daga mahaukatan bindigoginsu suna seta motar. Tin kafin motar ta iso aka sauke glass tareda daga fiddo wata turar datake dauke da sunan LEUL NUAB ALMAZZ BOYEM Baro Baro a jiki da saka hannun sultan YASAR Wanda itace shedar tabbatar dawowan magaji tin ranar da aka tafi dashi aka basa ita, Ware idanuwa dakyau tarin securities din sukai tareda kafe idanuwansu Akan turar dake buqata iskan a sama da sunan NUAB Baro Baro take sukai qasa da bindigoginsu suna ja baya da cikin wata irin girmammiyar mamaki da kidimaa, Cikin gaggawar da bata fi minti daya ba aka fara ware mahaukacin gate din suna bada hanya a Jere dan bayyanarda mafi girman girmamawansu ga me BOYEM daya dawo. Haka motocin suka iso da gudu suna wucewa ciki kamar walkiya batareda tsayawaba Kafin isarsu gate na biyu tini sako ya isa daga gate din farko ta wayar tsaro dan haka a gate na biyu yana isowa aka wangalesa tareda buga sautin qarar daya tashi masaurata ya isa kowane lungu da sako na isar da sakon dawowan LEUL NUAAB ALMAZZ BOYEM. a daidai wannan lokacin HAILE na bacci cikin Nisan baccinta kunnuwanta suka jiyo mata sautin daya sakata bude idanuwanta a lokaci daya batareda ta motsa ba, #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 52 Cikin kunnuwan HAILE sautin qarar ke sake ratsawa tana shiga kunnuwanta zuwa qwaqwalwarta datake kokarin warware wa tinaninta menene yake faruwa, Har lokacin bata motsaba daga kwancen datake idanuwan nata ne a bude tana kallan sama, Duk inda kaji wannan sautinqarar ya tashi a masarautar ya karade ta to sanarwa ce ta ME BOYEN ya dawo maana sultan idan yayi tafiya kokuma ya fita masarautar to wannan sautin shine yake sanar da duk Wanda yake masarautar ya dawo yana cikinta, Tsayawa cak idanuwanta sukai daga motsawan da sukeyi tana tashi Zaune cikin wani irin slow da kasa gasgata abinda kunnuwanta ke jiyo mata, Sultan yana masarautar bai tafi koina, Idan sultan na cikin Masarautar BOYEM wannan sautin yake tashi waye ya shigo masarautar da sautin dawowan jinin BOYEM yake tashi yana wargaza baccin dukkanin mai rai dayake masarautar ba bayi ba bamasu mulkinba…… Zuro kafafunta qasa tayi zata miqe tsaye Aslam da bata gani sosai sbd mummunan tashin hankalin data shiga da sanarwar da itamaa a cikin baccinta taji saukar sautin ta miqe tsaye zuciyarta na harbawa da Wani irin karfin gaske dan kuwa a yanzu kaf duniya idan ba sultan ba baa buga wannan qarar sai kuma Wanda yakeda matsayi da ikon mulkin BOYEM dan haka a duniya kaf yanzu ASIM ne kadai zaayi wa wannan karar sai kuma ‘dan da har abada bazai taba dawowa BOYEM ba, To idan sultan da ASIM duka suna cikin masarautar waye zaa bugawa wannan sautin idan ba Wanda baya nan ba kenan shi dinne ‘dan mistress din BOYEM ya dawo Bayan shekaru masu yawa. Jin Aslam tayi tana Neman rasa ganinta sbd shock da mamaki mai girma dan kuwa kwana da wuni sukeyi tareda kowace daqiqa ta rayuwarsu suna rokon Allah ya hanasa dawowa Masarautar da rayuwar sultan har abada dan haka ayanzu datake kasa yadda da shi dinne ya dawo doguwar Rigar sarauta me fadi da tsayi tareda adonta janyo ta Dora Akan Kayan baccin dake jikinta ta nufi kofa ta fice zuwa bangaren mahaifiyarta da a lokacin take tsaye tanason daga kafafunta zuwa toilet amma komai nata yayi nauyi takeji hakama kwata kwata kanta ya kasa dauka ko kawo tinanin LEUL BOYEM zai taba dawowa Masarautar BOYEM din sbd an tabbatar mata da babu alkhairi ko kadan a dawowansa gareta da zuriarta dan haka bata taba yin qasa a gurin aikin da har abada bazai taba dawowaba amma alamu sunata nuna hakan bazai samu ba dan haka aiki akeyi tuquru Akan mahaifiyarsa bazata taba shaawan dawowansa ba zataita hanasa dawowa duk kuwa yanda take Jin tsananin so da kewansa bazata iya bude Baki tace ya dawo ba dan haka wannan ya saka hankalin HAILE kwanciya koma dai menene su samu ASIM ALMAZZ ya hau mulkin BOYEM idan ya hau ko yaushe NUAB ya dawo din sun sai riga sun samu abinda suke so buri ya cika. Aslam na isowa Kai tsaye bedroom din mahaifiyarta ta nufo jakadiya dake palon karshe na hutawan HAILE tana bawa masu gyaran palon umarnin tsarin da zaa sauya cikin girmamawa ta kalli Aslam din zata gaidata amma ko ganinta Aslam bataiba ta wuce ciki Kai tsaye daidai lokacin da HAILE ta isa kofar toilet din mai girma da tsari zata shiga, Shigowan Aslam ya saka Hailen dakata wa cikeda mamaki mai dan girma idanuwanta Akan Aslman din sbd ganin lokacin da Aslam din ta taho Bude Baki tayi zatai magana Aslam ta rigata da cewa ‘Ya dawo, Shine ya dawo Bayan shekaru Mamee, Ya dawo Masarautar BOYEM, ‘Dan mistress din Sultan ya dawo Mamee, Ya dawo a daidai lokacinda muke kokarin ganin mun cimma burinmu kota yaya, Mamee tayaya zaki kawar da sultan daga duniya ASIM ya hau mulki a yanzu wannan yana masarautar? Tayaya zamuyi aure yanzu? Tayaya komai zai tafi yanda mukeso a yanzu da wannan din ya dawo? Tayaya sultan zai bar duni…….. Wani lafiyayyan mari HAILE ta sauke mata cikin kidima da rikicewa zuciyarta na wata irin rawa sbd gabaki daya Aslam wata irin mahaukaciyar zuciya ne da tinani da ita, matiqar zata shiga tsananin baqin ciki da bacin rai haka zata ringa tona asirin zuciyarta cikin tsananin baqin ciki da Zafin zuciya dayake fiddata hayyacinta dan hakanne ya saka haile bata barinta magana koina sbd zata iya aikata kuskuren da zaiyi karshen rayuwarsu gurin magana idan takai maqurar bacin rai, Marin da HAILE tayi mata ita kanta hayyacinta barin jikinta yakeyi da abinda Aslam din ta fada dan kuwa bazai taba yiyiwa ace NUAB ALMAZZ ya dawo Masarautar BOYEM din ba dan haka tafi yadda da sultan ne ya fita kila ya dawo batareda saninsu ba dan haka Kai tsaye toilet ta fada kafafunta na dan rawa hakama zuciyarta na tsalle. Alwalar sallar asuba zatai amma gabaki daya ta rikice hannuwanta rawa sukeyi bata Kama ruwa ba alwala tayi ta fito har lokacin kafafunta rawa sukeyi zuciyarta data kasa yadda da abinda Aslam ta fada amma sai bugawa takeyi sosai tana Jin batada Sauran nutsuwa idan zuwa tayi ta tabbatarda waye ya shigo akai wannan sanarwar. Kallan Aslam dake Zaune cikin matsanancin yanayi tayi zuru ta bude Baki tace ‘Kije kiyi sallah zan tabbatarda me yake faruwa idan na kammala komai da kaina zan tafi gurin sultan dan tabbatarda komai.’ Miqewa Aslam tayi batareda tace komai ba sbd jikinta dayake matiqar a sanyaye babu kowace irin kuzari a tattare da ita dan kuwa a duniya babu abinda zai iya kashe zuciyarta lokaci daya ta buga irin ace bazata samu cikar burinta na aure ba Wanda shine maqasudin ragewansu Akan ASIM ALMAZZ ya hau mulki, A yanzu rana tsaka idan NUAB ALMAZZ ya dawo BOYEM tabbas zasu samu babban katangar da zata iya shiga tsakaninsu da burinsu duk da bawai yadda zasuyiba zasu iya aikata komai Akan cikar burinsu ciki kuwa hadda kawar da rayukan wainda baa taba tinani ba. Ficewa Aslam tayi zuciya da gangar jiki ba nutsuwa hakama HAILE tada sallarta tayi itama zuciyarta babu sukuni. *****Motocin daya bayan daya suna zuwa can quryar harabar da iya jinin sarautar suke isa can a Jere suka fara Parkin daya bayan daya cikin tsarin da suka saba motar LEUL dince a tsakiya Kai tsaye suka fara fitowa daya bayan daya aka bude kofar da LEUL BOYEM yake Zaune ya ziro kafafunsa cikin izza waje kafin ya fito gabaki dayansa yana shakar iskar Masarautar datake jininsa, Lumshe fararen idanuwansa masu kyau da kwarjini me zafi yayi yana Jin Wani bangare na zuciyarsa yaja cikewa da gurbi me Zafin dayake ciki da wani sanyi me ratsa zuciyar sbd Ayau gashi inda mahaifiyarsa ke rayuwa yana shaqar iskar Numfashi daya da ita, Gabaki dayansu a tsaye suke qyam babu alaman gajiya ko buqatan Hutu a tattare dasu ko kadan saima karfinsu mai daga hankali dayake sake bayyana. Sarkin bayi ne cikin wata irin gaggawa ya iso gurin tareda tarin bayin da suka zube qasa gabaki dayansu kansu a qasa suna gaidasa batareda sanin yabar gurin ba Kai tsaye bai jira komai da kowaba ya doshi bangaren mahaifiyarsa shi daya tak sbd babu me hurumin shiga bangaren matan sarki idan ba ‘yayansu ba dan haka gabaki daya Yaransa suna tsaye a inda motocin su suke babu alaman sauki ko rahama ko daya a fuskarsu. Aleey ne ya sanar da sarki bayi LEUL BOYEM ya Riga ya wuce bangaren mahaifiyarsa nasa bangaren suke buqatan a kaisu dan tabbatarda tsaronsa. Babu bata lokaci Kai tsaye aka wuce dasu bangaren nasa me girma Wanda yake part guda mai tsari da kyau, Duk da baya nan babu shekarar da baa sauya furnitures da komai na bangarensa sbd haka doka da kaidar take, Komai na sauyin da ake masa ahankali ahankali yana tafiya ne da cigaban zamani da ake samu har zuwa yanzu da aka zuba duk wani luxury na rayuwa da zai basa Hutu da nutsuwa isasu, Komai a tsare yake da duk abinda zai saka yaji kaman yana gidansa na Moscow kawai dai yar qura ce sosai itama a take Sarkin bayi ya fara bada umarnin a fara gyara. Dakatar dashi Aleey yayi cikin nutsuwa da buqatar full control na kulawa da komai daya danganci lamarin LEUL komai qanqantarsa, Babu abinda babu a Masarautar BOYEM na Jin dadi da biyan buqata dan haka take Aleey ya bada umarnin a fara sauya komai dake bangaren a cikin kankanin lokaci dan haka ba bata lokacin Sarkin bayi ya saka a fara fidda Kayan a fara shigo da wasu da suka fisu komai. ******Sultan YASAR a daidai lokacin da sautin qarar dawowan magajin dayayi shekaru yana jiran wannan ranar ta dawowansa a wannan lokacin wayar sa ne da wishmah ayanah ghaz wadda a tare sautin ya shiga kunnuwansu ya isa ga zuciyarsa yana sanyayar da wani gurbi me girma da yayi shekaru a zuciyarsa, Ahankali sautin yake sake ratsashi ya rufe idanuwansa masu kyau da kwarjini yana jan wani Numfashi me dumi ya saukesa a hankali tareda bude idanuwansa Akan fuskar Ayanah dake bayyane kan screen dinsa shiru ta zuba masa ido a sanyaye bata iya cewa komai. A natse cikin sanyin nutsuwa ya sauke ajiyan zuciya datake dauke da shirin zartarwa da shirin fuskarta abubuwa da dama a masarautar da wainda suke cikin masarautar dan kuwa wannan ranar yake jira Wanda NUAB ALMAZZ zai kawo kansa masarautar da kansa amma kuma fitarsa da kansa ya rasa kenan saida umarnin sa dan kuwa shine yake riqe da cokalin juya rayuwarsa yanda yaso har sai ya cika masa burinsa daya dauka akansa tin daga ranar daya diro duniya, Burinsa daya saka ya banzatar da abinda yakeso fiyeda komai da rayuwarsa. Kallan Ayanah yayi a natse ya Lumshe ido akanta ya sake budesu akanta kafin ya bude Baki cikin mulkin dayake yawo jininsa shima da sautin daya shigeta yace ‘HAYATEEM dinki Zaki me BOYEM ya dawo gareki a matsayin cikakken namijin da BOYEM ke buqata’ Motsa idanuwanta tayi akansa tana Jin maganar tasa ta sauka cikin hankali da tinaninta harma da gangar jikinta dan haka ta motsa tana tashi Zaune da kyau duk da bata karfi ko kadan sbd rashin lafiyan datake cinta, Juya kanta tayi ahankali zuwa kofar ficewa bedroom din nata datake ciki daidai nan sultan ya kashe wayar yana jinginar da bayansa ga lafiyayyar kujeran dayake Zaune ta bedroom dinsa tareda dake rufe idanuwansa ahankali zuciyarsa na yin dum tareda shiga tinanika da dama. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 53 Ahankali tafara Takawa tana nufar kofar bedroom din nata idanuwanta na kafe kofar da idanuwanta tanajin jikinta na qara rasa karfinsa da kuzari, Duk takunta daya nauyi kirjinta qaruwa yakeyi ta daga hannunta da baida karfi ta Dora a kirjinta tana dafe sa sbd kaman gangar jikinta bazata iya daukan nauyinba Wanda tsawon shekarun tana jinsa amma Ayau yayi tsananin da jikinta ke sake sakewa ta isa kofar ta zubawa hannun kofar idanuwanta da sukai jajir a take batareda tasan menene takejiba a yanxu kuma, NUAB kuwa tinda ya doso bangaren bayin dake hanyar gabaki dayansu suke zube qasa kansu na yin qasa dan idanuwansu basuyi darajar da zasu kallesa ba dan haka ko motsi me sauti babu me yi tsit hanyar ta dauka badan babu mutane ba Sedan tsananin bada girma ga jinin BOYEM. Tinda ya tinkaro din shima kowane takunsa dawo masa da kowane Taku da yayi a ranar barin masarautar yake,dawo masa da takun da yayi a ranar daya rabu da mahaifiyarsa,rayuwarsa sanyi da hasken idaniyarsa wadda se yau ze sake haduwa da ita, Babu hanyar da zata isar da shi bangaren mahaifiyarsa ko daya data bace masa duk da akwai manyan gyare gyare da sauyi da aka samu me yawa amma dai mahaifiyarsa na nan inda ya barta dan haka babu jiran komai Kai tsaye gurinta yake nufa. Koda ya iso kofar bangarenta dayake dauke da sunan wishmah Baro Baro a jiki wani irin Numfashi me sanyi ya sauke yana dawo da kallansa kan Maa sakinah datake fitowa a hankali cikeda mutuwan jiki da mamaki idanuwanta na sauyawa da wani irin kallan datake masa zuciyarta na sake narkewa dan kamannin jinin GHAZ dayake bayyane a fuskarsa musamman Abaas Wanda yafi Kama da Ayanah sak dan haka kasa cigaba da kallansa sakinah tayi tana qasa da idanunwata hawaye na taruwa a cikinsu, Maa tenya ma a sanyaye take fitowa dan tarbansa a matsayinta na jakadiyar Amminsa dan haka saukar da idanuwanta qasa tayi daga kallansa tana jinin Wani irin girmammen farin ciki da mutuwar jiki a lokaci daya dan haka bude Baki tayi zata fara gaisuwa da kirarin dayake dolenta….. Katseta yayi Kai tsaye da muryansa data saka bayin dake bangaren sake Shan jinin jikinsu kansu a qasa, ‘Na dawo Maa’ ya fada a natse Kai tsaye yana kallansu su biyun zuciyarsa cikeda kauna da girmansu, Tenya ce kauna da matsayin dayake dashi a cikin ranta ya danne matsayinta na jakadiyar sa data mahaifiyarsa ta dago tana fidda Wani murmushin farin ciki mai sanyi tace ‘Barka da dawowan me BOYEM da kansa, Barka da dawowan Hayateem me zuciyar uwa da uba, Barka da dawowan Zakin mazan boyem, Barka da dawowan me jinin boyem da ghaz, Barka da dawowan magajin asali na BOYEM, Barka da dawowan LEUL me uwa uku’ Numfashi kawai ya isa saukewa yana kallan Maa sakinah da adduoin tsari kawai take jero masa a zuciyarta da ko bata bayyana ba ya sani haka take ita koyaushe bakinta a cikin adduar basa kariya da tsari daga kowane Sharri take kuma baa fili ba, Ciki suka juyo suna qarasowa suna gaba yana bayansu dan yi masa iso ga inda mahaifiyarsa take, A babban palon suka tsaya dukansu suna basa hanyar wucewa palo na gaba shi kadai dan isa ga mahaifiyarsa, A natse ya wuce ya isa kofar ya saka hannunsa ya bude tareda saka kafarsa ciki idanuwansa na dagowa kallan kofar dakinta data bude itama tana fitowa da tsananin sanyin kafafu idanuwanta da sukai ja suna sauka akansa batareda ta kyafta ba Shi kansa idanuwansa jajir suka a lokacinda ya kafeta dasu yana mata kallan da kowace gabar jikinsa ke amsa tsananin kaunar dayake mata. Kasa motsawa tayi daga inda take cak duniyarta na Wani irin Juyawa sbd kasa yadda da abinda idanuwanta ke gani, Da gaske ne NUAB dinta ne a gabanta kokuwa ire iren gizon da yake mata ne shi da Abaas, Shi kansa mutuwar tsaye yayi a gurin dayake yake din yana kallan kowane yanayi da mahaifiyarsa ta koma Wanda hadda manyanci dayake nuna tsufa Yazo a tattare da ita ga ciwo fa qunci da damuwa da kadaici tareda rashin cikakken tinin kanta dan haka kan idanunwansa suke sake yin ja radadin rashin lokutan mahaifiyarsa da aka rabasa dasu tin kuruciya suna dawo masa dan kuwa an hanata yarintar ‘danta kaman yanda aka hanasa yarinta a gaban mahaifiyarsa, An hanasa samun kulawa da tattalin a lokutan ciwonsa da baqin cikinsa kaman yanda kowane ‘da yake samu daga mahaifiya ko mahaifansa, Shi shikadai yake ciwo yayi jinyar kansa ya kula da kansa ya tsayawa kansa yayiwa kansa komai tamkar marayan da baida uwa baida uba baida gata, A lokutan ciwo mai tsanani da dama yayi kukan rashin mahaifiyarsa da dumin jikinta kadai zai iya basa warakar dayake nema da sassaucin kowace irin azaba amma duka an hanasa samun hakan an hana mahaifiyansa samun basa hakan daga karshe dai Bayan shekaru Ayau Allah ya hadasu haduwan da mutuwa ce yanzu kadai zata rabasa da ita badai kowane ‘dan Adam ba komai matsayinsa kuwa a duniya. ‘HAYATEEM’ bakinta ya bude ya furta a hankali cikin wani irin sautin daya saka gabaki daya tsigar jikinsa tashi ya tako bai tsaye komaiba ya janyota jikinsa ya rungume da Wani irin karfi yana rintse idanuwansa da har wani radadin yaji suke masa. Sake ambatar sunansa tayi da sautin daya sake tada duk wata tsigar jikinsa tana Qanqamesa ta fasa wani irin kuka mai qarami da sanyayar sauti tana Jin nauyin kirjinta yana fadawa qasa ahankali ta sake qanqamesa tana ambatar sunansa. Dagota yayi ya Kama fuskarta da tafukan hannuwansa biyu yakai bakinsa tsakiyar kanta yayi kissing cikeda tsananin kaunarta ya sake juya gefen fuskarta yai kissing ya dago hannuwanta duba biyu yayi kissing kowanne ya sake rungumeta jikinsa tsamtsam yana Jin kaman bazai taba iya rayuwa ba daga ranar da wani mummunan abu ya sameta dan itace kuzarinsa kuma itace weakness dinsa dazai iya bada komai nasa da kansa akanta. Kuka takeyi sosai tana Jin zuciyarta kaman zata fashe da tsananin kauna da son ‘danta Wanda bata taba ji a ranta zata gansa a gaban idonta ba,ta cire rai daga ganinsa har rayuwarta ta fita tabarta, Da kewa da radadin rashin sa take kwana take tashi tareda wuce kowace daqiqar rayuwarta amma bakinta kaman an riqe bata taba iya cewa ya dawo koyaushe sedai kada ya dawo bama zata iya tina yaya bakinta ya iya furta masa tana son dawowansa ba kuma duk da ta furta din bata saka ran zuwan nasa ba bare ganinsa ba dan haka take Jin Wani yanayi na tsananin farin cikin rayuwarta a karo na farko Bayan shekaru masu yawa cikin qunci da baqin ciki Ayau ruhinta ya dandana dandanon farin ciki da samun abinda zuciya ke so dan haka take sake qanqamesa da rashin kuzarin datake fama dashi tana rufe ido sbd kuka. Sun jima a hakan tsawon lokaci kafin a natse ya zaunar da ita Akan sofa mai Laushi yana riqe hannunta cikin nasa cikeda dukkanin kulawa da bayyananniyar kaunar datake shigarta tana sake kashe jikinta akansa tana kasa dauke idanunwata Akansa farin cikinta a bayyane. Hannunta ta daga ahankali ta Dora Akan fuskansa ta shafa tareda sakin murmushin daya saka idanunwansa qarasa rikidewa jajir sbd Ayau itace ranar farko dayaga murmushi Akan fuskar mahaifiyarsa tinda ta haifesa, Bude Baki yayi da Wani irin sauti daya sake sakata shafa fuskarsa tana ganin kammanin da bazata taba mancewaba shimfide a fuskarsa yace ‘Ammi,Ammi na dawo gareki bazan taba sake rabuwa dake ba koda zan rasa komai Akan hakan, Ammi bazan iya sake rabuwa dake ba, Ammi zan nema miki lafiya da duk abinda kikeso nayi miki Alkwarin cika miki shi, Ammi zan tafi dake na Nemo miki Abaas a duk inda yake fadin duniyar nan na kawo miki shi gabanki, Ammi ina son ki cire dukkanin damuwa da quncin dayake ranki sbd lafiyarki, Ammi……. Hannunta ta Dora a bakinsa cikin nutsuwa kafin ta rungumesa tana kwantawa gefen kafadarsa ta bude Baki tace ‘Zan bika duk inda zaka tafi dani HAYATEEM, Bazan iya rayuwa ba idan Ka tafi Ka sake barina, Zuciyana bazata iya sake daukan rayuwa babuka ba HAYATEEM, Karka banni Ka tafi dani ko ina ne zan bika na rayu tareda Kai sanyin idaniyata…. Yanda take maganar ya sake Sosa zuciyarsa fiyeda yanda zai iya boye wa dan haka hannuwansa suka dan ringa rawa ya rungumeta sbd akwai alaman rashin lafiyan jiki da tinina sosai a bayyane da sautin maganarta. Maganganu ya bude Baki yafara jero mata masu nutsuwa da samar da nutsuwa a kwakwalwanta yana bayyanar mata babu abinda zai qara rabasu sai mutuwa dan haka ta kwantar da hankalinta ta cire damuwan komai dan babu inda zashi batareda ita ba. A daidai wannan lokacin aiki akeyi gadan gadan a bangaren me girma LEUL din Yaransa suna tsaye qyam Akan aikin Wanda take aleey yayi ordern wasu manyan Kayan da abubuwan da suke buqata na ubangidansu daga wajen masarautar kuma aka kawo cikin gaggawa suka duqufa sbd kafin ya gamo ganawa da mahaifiyarsa suke buqatan komai na bangaren ya kammala daidai da hutawarsa, Acan bangaren wishmah dinma Maa sakinah ce a tsaye tareda masu aiki da bayi Ana aikin abinci na musamman me tsari da tsaftar gaske tareda lafiya daidai da taste dinsa tin na yarinta duk da sunsan ya sauya tako ina amma dai sunsan zai kaunaci komai da zaayi masa sbd kewansu da kewan kulawansu akansa da girkinsu. Maa tenya kuwa take qwanjinta da kuzarinta harma da walwalanta ta dawo a lokaci daya Jin kanta takeyi tenya dinta ta baya da zata iya tsayuwa ako ina dan bawa NUAB da Ayanah kariya da duk abinda sukeso dan haka take ta bada umarnin a tara bayin da zasu ringa hidimar bangaren LEUL boyem da kanta zata zabesu ta basu training me karfi da kyau dan kuwa karfinsu ya dawo fiyeda ma Wanda suke dashi a baya dan kuwa a bay suna shakkar a cutatar musu da NUAB suna basa kariya amma a yanzu shine Wanda zai basa kariya a karkashin iko da karfinsa. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 54 Tin asubar da sautin karar dawowan LEUL BOYEM ta shiga kunnuwan duk wani babba me matsayin dayake masarautar a tsaye suke suna kaida kawo cikin mamaki me girma da shakka tareda tinani kala kala Wanda rashin tinanin kamawa ma yafi yawa a cikin kwakwalwansu sbd a tsawon shekarun nan sun manta sun shafe magana da tarihin LEUL boyem daga masarautar babu Wanda ko a maida zance ya kuma tada maganarsa kaman yanda sukaga sultan bai taba maganarsa ba saisu ma suka watsar dashi da zancensa kaman yanda aka rufe babin mahaifiyarsa kwata kwata baa ma sakota a lissafin matan sultan kokuma wanzuwarta ako wace hidimar masarautar da ake buqatan halartar matan sultan din dan duk inda akace matan sultan to su uku ne keda cikakken ikon sunan sbd zamantowanta wishmah duka ya Halarta mata wannan suna da matsayin, Ayau Asuba tsaka kawai cikin bacci da rashin tsammani ko a mafarki sukaji sautin sanarwar dawowansa batareda aiko da sakon dawowan tasa ba kaman yanda yake tilas kawai suka samu dirarsa a masarautar, Babban abinda ya girgiza kaf manyan fadar masarautar shine a bayan ASIM ALMAZZ suke sun shirya tsaf sun yanke kuma sun kudirta shine sultan na boyem dan kuwa daga ranar da aka wayi gari babu sultan bazaa qara awa biyu ba batareda sun nada ASIM ALMAZZ ba wannan Alkawari ne da burin da kowannensu yake dashi. Dan hakanne dawowan LEUL BOYEM ta girgiza su jijjiga me karfi sbd basu taba saka ran dawowansa ba Sun shirya goge sunansa da uwarsa a cikin tarihin boyem daga ranar da sultan YASAR yabar duniya hakama sun saka rai sun kwanta da tinanin koda zai dawo qasar to sanar da daya daga cikin iyayensa sun mutu. Meya dawo dashi kwatsam haka babu zata ba tsammani? Menene dalilinsa na dawowa Bayan shekaru masu tsayi? Idan ma yana tinanin ya dawo ne karban matsayinsa to tabbas ya makaro dan bazasu taba Bari ba korasa zasu sake yi inda ya fito wannan Karan ma shi da uwarsa kila dan haka a shirye suke dashi zasu nuna masa karfin matsayin da suke dashi Wanda sunada ikon zartarwa, ASIM ALMAZZ ne sultan na gaba Wanda da karfi zasu tabbatar masa da hakan ya tattara ya koma Gagarin dayake yi bada gatan masarauta ba hakama dole zai amsa kiran shugabannin Masarauta ya fuskanci hukuncin dokar daya taka ta masarauta ta zuwansa batareda ya aiko manzon aike ba da wannan zasu hukuntasa ya koma inda ya fito. Hakan ya saka kusan dukkanin manyan suke a cikin tinani daya da shiga tsananin son ganinsa da isar dayake ji da ita dan haka suke a cikin shirin isa fada da gaggawa sbd ko sultan dole yana can cikin bacin rai da fushin abinda LEUL din yayi. Koda karfe goma na safe ta buga duk Wanda yake masarautar ya samu cikakken labarin isowan sa, Hakama waje da garuruwan dake qasar sun fara samun labarin dawowan LEUL BOYEM, Yan jaridu ma da television tini suka fara yada Labaran Wanda Aleey ne da kansa ya basu cikakken bayanan ta waya sbd qasar BOYEM ta shedar da zuwan magajinta koda kuwa ziyace kadai ya kawo ba zama Yazo yiba, Yanda zancen ya ringa yaduwa da shiga koina ya saka mutane dama yan jaridu fara jefa maganganun to a yanzu waye asalin magajin da zai mulki BOYEM, Waye asalin me BOYEM a cikin magajin guda biyu da ake dasu, Waye sultan zai zaba bawa mulkin da kansa kokuwa jira zaiyi saiya bar duniya Allah ya bawa me rabo saa? Wannan maganganun ne suka fara daga hankalin wainda sai daga baya labarin dawowan LEUL BOYEM din ta samesu maana ASIM ALMAZZ kenan da HAILE wadda ta tabbatarda NUAB ALMAZZ dinne ya dawo da gasken gaske kenan. Gabaki dayanta da yayanta a Zaune suke babban palonta na hutawa sunyi shiru kowa da abinda yake ransa idanunwansu jajir babu Wanda jininsa baya tafasa yana hawa sbd tsagwaron zallan baqin ciki bawai dan suna tsoron sa ba sbd basa tinanin yanada abinda zai sakasu tsoron sa ko shakkarsa kawai dai sultan da suka gama samun cikakken kansa Akan tinanin yama gama Dora ASIM ALMAZZ a mulkin BOYEM yanzu kuma wannan ya dawo zai rikitar musu da tinani da raayin sultan dan haka suke cikin baqin ciki me tsanani amma Bayan hakan Sam sunsan tako ina babu inda zai kamo kafar ASIM a komai dan haka sukai shiru cikin takaici da baqin ciki, ASIM ALMAZZ dayake Zaune a kujeran datake ta Mutum daya idanuwansa a dan rufe yayi shiru da zurfafa a tinani bude idanuwansa yayi ahankali ya sauke Akan mahaifiyarsa kafin ya bude Baki cikin tasa Izzar da Wani irin yanayin dayake ji a ransa na babu Wanda ya isa ya rabasa da matsayinsa dayake Kai da Wanda yakeso a duniyar nan batareda ta aikasa inda ya kamacesa ba yace ‘Mamee babu abinda zai faru ki kwantar da hankalinki kokarinki na shekaru bazai taba tafiya a banza ba zan tabbatarda da hakan, Indai ba nine magajin karagar mulkin BOYEM ba to tabbas BOYEM zata rasa magaji da sultan din da zata kira nata, Kawai dai a yanzu ku Bari wannan dan gudun hijirar daya dawo ya gama abinda ya kawosa ya tattara mistress din mahaifinsa ya qara gaba da ita zuwa yawon bin yan taaddan da akace yanayi.’ Karban zancen HAILE tayi cikin wani irin radadin zuciya da cewa ‘Banda rashin tinani irin na Ubansa da tsufan dayake cinye kwakwalwansa tayaya zaiyi tinanin ma sauya Ka daga zama mai mulkin BOYEM Akan Wanda yagamo yawon duniya da taaddanci’ Numfashi meryam kawai ta iya saukewa me zafi tana fatar koma menene kowa zeyi yayi itadai buqatarta ASIM ALMAZZ ya zamo me mulkin BOYEM ya dauke hukuncin dayake kansu ta auri koma Wanene zata samu. Aslam kuwa can qasar zuciyarta Wani irin tsoro da fargaba takeji Wanda yake hanata cewa komai dan kuwa koma yayane dawowansa su dai ba alkhairi ce a garesu ba, ASIM ma a qasan zuciyarsa wata shakka ce ke son shigarsa da matsuwa da son haduwa da NUAB ALMAZZ dan yaga menene yake dashi a yanzu sannan ya sheda cewa shi ASIM ALMAZZ yanzu ya fisa komai musamman ilimin daya samu cikakke me kyau Wanda ko hakan zai saka a basa mulkin shi a hana masa dan babu ta yanda dan taadda zaiyi mulkin BOYEM baa taba ba kuma bazaa taba farawa ba. HAILE ma kusan bazasu taba gane abinda take ji a zuciyarta ba sbd har abada indai NUAB ALMAZZ yana raye batajin akwai ‘dan da sultan zai so kamarsa duk da baya tareda NUAB din shekara da shekaru amma hakanan take Jin bai taba Dena sonsa ba kawai abinda ya sakata kwantar da hankalinta shine koda yana sonsa baya tareda shi yana tareda ‘danta ne kuma gaggawar datake yi shine a Dora ASIM kafin ranar dawowan NUAB tayi gashi yanzu ya dawo batareda burinta ya cika ba dan haka yanzu sabon yaqi ne garesu su dukansu Akan tabbatarda burinsu ya cika kota halin yaya. *****Se karfe goma da mintina ya Baro bangaren Amminsa Bayan yaci abinci tareda ita cikeda kwanciyan hankali sun samu kasancewa da juna yanda yakeso tukuna ya fito ya fice. Lafiyayyan gyaran da akaiwa bangarensa ya saka yana zuwa Kai tsaye bedroom dinsa ya nufa Wanda yake da Wani palon hutawansa a ciki kafin asalin bedroom din. A jikin bangaren nasa akwai manyan bedrooms guda biyu da sukeda girma sosai da toilets a ciki anan Yaransa suka sauka aleey kuwa bedroom daya dayake cikin bangaren nasa ya sauka dan haka dukkaninsu shigewa sukai sbd lokacin hutun LEUL ne. Wanka yayi da dukkanin abinda ya saba amfani dashi sbd babu abinda yake amfani dasu da aleey bai siyo ba baa. Dogon wandon bacci na lebarto ya saka mai wani irin santsi da Laushi sbd tsadarsa sai farar rigar wandon Kwantawa yayi ransa da ruhinsa cikeda nutsuwa take baccin hutun dayake buqata ya daukesa. Gabaki daya bangaren da zagayensa tsit yayi sbd Yaransa da suka tabbatarda hutawa yakeyi babu kowace hayaniya da ake buqata. Daga shi har Yaransa Hutu sukeyi Bayan an bada cikakkiyar umarnin kada Wanda ya tinkaro bangaren. Acan fada kuwa kowa ya cika duk wani babban masarautar yana cikin fada Zaune, Hakama duk Wanda yake gari ko qasar datake kusa da BOYEM indai jinin BOYEM ne sun iso suna cikin masarautar wadda ta dauki dumi dan kuwa a cike take da masu fada a ji na mulkin BOYEM, Shi kansa sultan Bayan dogon lokaci daya dauka kafin fitowansa ya fito daga karshe Bayan kowa ya gama Halarta kenan shi kadai ake jira da LEUL din Wanda baima San mesuke yiba, Zaman fada da meeting din zafi ya fara dauka Wanda ya saka sultan yake sake jin baiyi danasanin aika dansa ba harma ya zama koma menene ya zama yanzu din dan kuwa a bayyane wata irin zazzafar qiyayya ce yake gani tako ina a idanuwa da kalaman duk Wanda yake fadar Akan sai hukunci yahau kan duk Wanda ya taka dokar Masarautar BOYEM koma wanene. Sultan da abu dayane yake cikin zuciyarsa yana Juyawa shine rashin zuwan NUAB din garesa Bayan shigowa sa masarautar da shine yake mulki da ikonta hakama shine uban daya haifesa komai Zafin kansa da ikonsa wainda a gurinsa cikin jininsa ya gajesu, Dagowa yayi ya kalli taron manyan qasar BOYEM din gabaki dayanta da idanuwansa da tsananin zallar mulki da ikon dayake jininsa yana bayyana, Umarnin suke jiran ji dan haka akai tsit Ana kallansa tareda jiran abinda zai fada kowa zuciyarsa har rawa takeyi sbd jiran umarnin da sultan din zai bada. ASIM da idanunwansa sukai jajir zuciyarsa har wani fizga takeyi ya kafe sultan din da ido yaja baza kunnuwansa jiran abinda zaa fada, Bude bakin sultan umarnin kiran LEUL BOYEM ya bada tareda tabbatarda umarni ne me karfin gaske. Dan aike Koda ya isa tin daga nesa ya zube qasa bakin kofar bangaren yana daga muryansa ya isar da sakon cikin tsananin girmamawa. Dukkanin sakonsa a kunnuwan Yaransa ya isa amma babu Wanda yakeda niyar isar da sakon sbd lokacin gurinsa bai qareba dan haka manzon sakon yana zube a qasa bai tashi ba sbd Sai an amsa masa sakon zai tashi koda kuwa zai kwana ya wuni a hakan. Shiru shiru ba dan sako Wanda ya saka fadar sake daukan zafi babu Wanda ya iya cewa komai sedai xukata sun dauki Zafi. Awa kusan biyu manzon sakon ya shafe a durqushe cikin rana kafin me BOYEM din ya tashi baccin sa Kai tsaye ya shiga toilet yayi wanka ya bata lokaci sosai kafin ya fito daure da towel fari qal daidai nan wani manzon sakon ya sake isowa sedai wannan Karan bayi biyu ne daga bangaren mahaifiyarsa aka turo Wanda hakan ya sakasa Dakatawa cak daga abinda yakeyi sbd bayin saida suka gabatar da kansu suka isar da sakon ya kuma San me ake nufi da aiko bayin mahaifiyarsa Wanda take zuciyarsa ta fidda Wani irin Numfashi me dumi ya ajiye towel din dayake hannunsa na goge Kai ya juyo ahankali cikin isa da wata irin izza ya nufo kofa ya fito. Aleey dayake palo a tsaye yana jiran fitowansa yana ganin fitowansa da towel take ya dauko sunglasses na Versace ya miqa masa hannu kadai ya saka ya karba yana nufar kofa Kai tsaye wadda tini aka wangale masa ita, Yana fitowa umbrella biyu a take aka bude take a kansa batareda ya tsaya ba suka biyosa dukkaninsu tamkar zasu fashe sbd karfi ga tattoos nasu daba wasu dake bayyane sai daukan ido sukeyi, Cikin mummunan tsoro da firgici bayin dake kofar bangaren sukai qasa da kansu jikinsa na wata irin tsima sbd firgice wa, Wani irin daukan ido fatarsa keyi wadda azababben Hutu ne ke bayyana a kowane babu na jikinta, Kai tsaye fadar ya isa cikin wata irin izza gashin kansa yana zube a bayansa towel din dayake qugunsa yana sake fidda lafiyar kakkarfan jikinsa dayake a murde, Tin daga nesa securities din fadar da kaf bayin dake hanyar suka zube qasa kawunansu a qasa zuciyarsu na wata irin harbawan da kansu yake kasa dauka. Wasu irin samudawan da babu alamar rahama ne ASIM yaga suna shigowa fadar jikinsu na zanen tattoo din da idanunwata sun gane masa daidai guda uku daga cikinsu fuskar NU’AB ALMAZZ ce zane a jikinsu matsayin tattoo, A kofar shigowa suka tsaya daidai nan LEUL me BOYEM ya sako Kai cikin fadar cikeda Wani irin zazzafan iko da izza, Gabaki daya wuta daukewa duk Wanda yake fadar tayi cikeda matsanancin rikicewa da girgiza me tsananin gaske suka zubawa kofar daya sako Kai ido bakunansu a sake suna wata irin rawa. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 55 Takowa yakeyi kansa tsaye cikin isa da Zafin kansa dayake a bayyane sbd sun samu kunna inda baa kunnawa a zuciyarsa dan aika bayin mahaifiyarsa Kai tsaye kunnasa sukai shi kuwa a gurinsa bayin mahaifiyarsa sunfi duk Wanda yake cikin fadar daraja a gurinsa idan aka cire uban da yayi cikinsa. Duk takunsa daya zuwa tsakiyar makekiyar fadar girgiza zukatan duk Wanda yake gurin yakeyi sun kasa Nemo tinaninsu da kalamansu, Qasa suke yi da idanuwansu cikeda sake shiga mugun shock daya wuce firgici dan bama zasu iya kallan fatar jikinsa dake Wani irin daukan ido kakkarfan jikinsa dake murde yana sake shigar dasu rudewan shin a fadar BOYEM suke ko kuwa, ASIM da idanunwansa suke rarrabuwa Akan samudawan dake tsaye a kofar wani yawu ya Hadiye da karfi a sirrince sbd tsananin mamakin dayake Neman rudar dashi Sake bude idanunwansa yayi da kyau Akansu daya baya daya yana San tabbatarda shin fuskar NUAB ce yake gani zane a dantsen hannunsu wasu kuma a wuyansu wasu kuwa kirjinsu dayake dan bude sbd rigar da bata rufe ba botiran sama na rigar a dan bude, Yana yana yaji idanunwansa sunayi ya maida kallansa da sauri Akan aleey dayake tsaye riqe saida waya da iPad da baya rabo dasu sbd koyaushe a shirye yake da buga waya ko aikatar da sako ba delay, Zancen tattoo din jikin Aleey ya qarasa rikitar da tinanin ASIM sbd ‘LEUL BOYEM’ ne Baro Baro rubuce a hannunsa tin daga gwiwan hannun har zuwa gurin da tafin hannunsa ya fara, Juya fuskarsa yayi a slow yana maida kallansa inda NUAB yake ya Dora idanunwansa da suke cikin rudani akansa ya kafesu akan bayansa dayake daukan ido sbd haske da lafiyar fatarsa idanuwansa suka sauka Akan tsakiyar bayansa da sunan ‘GHAZ’ yake rubuce cikin wani irin rubutu daya sakasa saurin dauke idanuwansa Akan rubutun yana miqewa kafafunsa na wata irin rawa ya Riga NUAB saurin isa tsakiyar fadar ya zube gaban sultan a hankali yana sunkuyar da Kai ya bude Baki zaiyi magana daidai nan NUAB ya iso gurin ya tsaya cak tareda dagowa ya zare shades din fuskarsa ya saukar da idanuwansa da suke zak na ubansa da suka sauya babu abinda yake bayyana a cikinsu Bayan zallar wutar bacin rai na shakaru ya sauke su Akan sultan Wanda idanuwansa suke kafe Akan NUAB din tin daga lokacinda ya sako kafarsa a fadar yana takowa a cikin takun dayake tabbatarda shi din jininsa ne tsatsonsa ne da a kowane hali bazai taba dana sanin haihuwansa ba da rayuwar da suke akai yanzu, Cikin tsakiyar idanunwan NUAB din yake kalla cikeda Wani irin yanayin dayake tabbatarda alfaharinsa da samun cikar burinsa da NUAB ya rayu a duniyar datake cike da maqiyansa, Ya rayu ya zama tsayayyen da zai iya tsayawa Ayanah ya bata kariya da rayuwarsa batareda shakkar kowa a duniya ba, Babban burinsa ‘dansa jininsa ya tashi ya rayu a duniya batareda shakkar komaiba bare kowa ba Bayan Allah daya haliccesa, A yanda ya tashi ba shakka ba tsoro ba fargaba ba kunya ba wasa babu abinda yake girgiza dan kuwa ko mutuwa baya tsoro koyaushe tazo zai amsa kiranta haka yake burin jininsa ya kasance gashi burinsa ya cika harya zarta sbd Zafin wutar dayake gani a idanuwan NUAB bayajin akwai abinda zai kashesu, Ba qiyayyarsa yake gani a idanuwansa ba zafinsa da fushi me tsananin gaske yake hangowa Wanda yasan da hakan yana ganin hakan tin yana yaro dan haka bai damu ba tinda ya zama Zakin dayake fatar ya zama ko da wannan qiyayyar ta idanuwan NUAB din zai rayu tinda a cikin idanuwansa take baa zuciyarsa ba,hakama indai wannan fushin nasa da nisan dake tsakaninsu zaisa ya tsayu a cikin zarrarsa sa fushi ne yake da qarin karfin riqeta ya shirya rayuwa da hakan har sai ya tabbatarda yahau mulkin da shine zai gama bawa Ayanah cikakkiyar kariyar dayake mata yaqi hakama dashi kansa da ake fatan fizgewa daga tarihin BOYEM dan haka saiya tabbatarda wannan burin nasa Akan NUAB din ya cika kafin ya nemi kusanci da ‘dan nasa dayafi masa duniyarsa gabaki daya. Cikin sautin daya saka fadar sake daukan tsit NUAB ya bude Baki muryansa ta shiga kunnuwan duk Wanda yake gurin kaman saukar Aradu yana juyowa yace ‘Waye yaga ya kamata a aika bayin Amminah kirana??? Rufe idanuwa sultan yayi a hankali Wani radadi na ratsa zuciyarsa na yanda ‘dansa ya zabi kasa masa magana a bainar mutanen fada da suma duk sukai tsit sbd kafe fadar da Yaransa sukai da ido ba ko kyaftawa kamar robot suna jiran Wanda zai motsa bada amsar shine su fasa kansa da bindigar dake hannuwansu ko Jeho masa wuqar da zata tsaga kansa biyu dan haka ganin sultan baice komai ba har lokacin kallan NUAB yake son dayake masa yaci karfin mulkinsa da matsayinsa dan haka sukai shiru babu Wanda ya dago tukuna dan kuwa duk karfin mulkin BOYEM aka fasa kan mutum da bindiga kafin masautar ta dauki mataki ko nuna ikonta da zafinta Akan hakan andai Riga Kai an kasheka a banza da wofi ihu ne kawai ze biyo Bayan hari gashi da alama kafiran samudawan thugs din dake tsaye basu San dokokin masarautarba tukuna dan haka ba wata bata lokaci zasu aikaka ba shiri. ASIM ne ya motsa cikin tsananin mamaki da baqin ciki me girman gaske ya miqe shima ganin NUAB bai durqusaba ya kalli NUAB din ransa na tsananta tafasa da quna mai tsanani ya bude Baki zaiyi magana NUAB din ya sake bude Baki da mahaukaciyar muryan data saka ASIM din ja da baya cikin sauri ‘Waye ya nuna wannan rashin daar ga mahaifiyata???? Aleeyyy………. Cikin karfin murya datake tattare da umarni da iko mai karfi Sultan ya Katsesa sbd hanasa abinda yake niyar yi koma menene yace ‘LEUL NUAB ALMAZZ ka nutsu kasan inda kake, A gaban me BOYEM kake, Nine me mulki a nan ba kaiba, Nine me fada aji anan ba Kai ba Nine Wanda ya isa ya kira kuma dole a amsa, Sake kallan jikinsa sultan yayi cikeda bacin rai kafin yace ‘Nan fadar BOYEM ce ba gurin wankanka ba dan haka umarni ne ka koma Ka sake shiryawa fada zata sake nemanka amma Ka sani hakan da kayi na yanke maka fita Masarautar BOYEM bisa umarni me karfi sai Bayan wata daya zan buqaci ganinka’ Da mamaki me karfi da shakkar dake cikeda zukatan yan fadar kowa ya dago ya kalli sultan sbd zazzafan furuci suke jira daga garesa da hukunci me Zafin gaske amma suma tsananin shock da mamakin da suka kasa fitowa a cikinsa na ganin tantirancin karshe ganin idonsu ya saka suka bazasu iya cewa komai ba ko yin komai sai tinani da nutsuwansu ya dawo daidai jikinsu tukuna dan haka barin fadar a watse meeting din suke buqata yanzu suje su sako tinani, NUAB kuwa juyowa yayi cikin nutsuwa da sabuwar tafasar datake cin ransa zai kalli sultan sai kuma ya fasa ya juya yana barin gurin sbd bayason jijjiga duniya da ikon sultan din a gaban mutanen da ikonsa yafi komai a duniyarsu. Yana Juyawa gabaki daya bayi da securities din fadar suka sake zubewa qasa suna sauke kansu jikin bayi na tsima, Su aleey ma Juyawa sukai suna bin bayansa sultan ya zubawa Bayan NUAB din idanuwansa yana kallan sunan GHAZ din dayake Baro Baro bayyane a tsakiyar bayansa daga sama. Kaman yanda ya taho haka aka daga masa umbrella ta basa kariya daga Zafin rana hakama shades dinsa na rage masa hasken rana ne da zai keto a cikinta, Har suka fice sukai nisa babu Wanda ya motsa saida suka bace wa fadar gabaki daya tukuna aka ringa sauke Numfashi me Zafi da bacin rai me tsanani musamman ASIM daya kasa motsawa daga kallan inda suka wuce din idanuwansa jajir da sbd tsananin ja da bacin rai da baqin cikin dayake ciki har wasu ruwa ruwa suka cike idanuwan fuskarsa tayi jajir hannuwansa na dan rawa ya saukesu yana juyowa ahankali ya fara bin palace officials din wato manyan fada da kallo daya bayan daya yana debe musu albarka a zuciyarsa tareda Jin zazzafar tsanarsu da baqin cikin ganinsu ma a gabansa sbd shiga rudin da sukai har suna kasa cewa komai a fadar da sun isa su yankewa ‘dan mistress kowane irin hukunci, Wasu yawu masu daci na baqin ciki ya Hadiye yana dauke idanuwansa daga kansu ya dawo da kallansa kan sultan Wanda tin kafin ASIM din yayi magana yace ya tada zaman fadar na yau sai kuma wani lokacin. Cikeda girmamawa da son barin fadar su shaqi iskan nutsuwa a waje kowa dake fadar suka zube qasa a hankali suna masa a huta lafiya. Koda ASIM ya zube qasan shima zuciyarsa kaman zata fado yake jinta tsabar baqin cikin sultan da duk Wanda yake fadar dan haka har sultan ya bar fadar ta kofar da shi kadai yake bi ASIM bai dago ba, Sultan na ficewa aka fara ficewa daya bayan daya daga fadar babu Wanda ya samu cewa dan uwansa komai har suka watse, ASIM ne yayi na qarshen fitowa tareda babban yaronsa Salman Wanda shima zuciyarsa taje cikeda baqin cikin dayake kusan na ubangidansa haka suka bar fadar Kai tsaye suna nufar bangaren HAILE. A kofar bangaren da babu me wucewa sai jinin BOYEM da bayinsu mata kadai, Tinda ya tinkaro bayin dake bangaren suka ringa zubewa qasa kansu a qasa suna masa Barka da shigowa amma babu Wanda ya kalla zuciyarsa gap take da bugawa ya isa palon hutawar mahaifiyarsa inda ya tadda su a tsaye dukkaninsu Banda meryam dake Zaune itama tana dafe da goshinta Aslam da HAILE kuwa a tsaye suke qyam kowannensu abinda ya faru a fadar yake son ji dan kuwa suna tsammanin jin zazzafan hukuncin da zai saka NUAB zuciya ya sake barin qasar gabaki daya. Yana shigowa suka zuba masa ido dukkaninsu suna jiran jin bayani a bakinsa amma ganin yana yinsa ya saka jikin meryam da Aslam sanyi suka zauna batareda sun furta komaiba sedai HAILE ne tace ‘Meya faru? Yaya akai a fadar? Wane hukunci sultan ya zartar masa? Zai bar qasar dai ko? Zazzafan fushi me tsananin zafi ne ya taso masa ya saka hannuwansa biyu ya dauki table din dayake gurin cikeda Kayan marmari da Kayan ciye ciye ya daga sama ya buga qasa da karfi komai ya fashe da karfi tareda watsewa da kara me karfi. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 56 HAILE data ga hakan take zuciyarta ta tabbatar mata da basu samu abinda suke so ba kenan, NUAB bai karba kowane hukunci ba daga sultan kenan, Matsalarsu akwai yiyuwar zata fara ne daga yanzu matiqar NUAB yana nan, Kallan ASIM da idanunwansa suka mugun jajir tayi tana bude Baki zatai magana ya Katseta da cewa ‘Ba dan taadda kadai bane mahaukaci ne,haukace da kanta take kwance a cikin jininsa bawai a cikin kansa bama,ya tabbatarda shine bastard son da sultan YASAR me BOYEM yakeda shi a Idon duniya’ Aslam da duka ba wannan take son ji ba dan bata jin kowace hauka ce akansa zai gagaresu su da suke su hudu ga kuma manyan fada a bayansu hakama ASIM ALMAZZ shi BOYEM ta sani a matsayin ‘dan sultan dayake tareda shi kawai ita hukuncin da akaiwa NUAB din takeson ji dan jin hukuncin ne zaisa su sani ko NUAB din zai tafi ne yanzu ko zaman qasar. Meryam kuwa da tsananin quncinta da rufewan Idon son cikar burinta ta samu abinda takeso to ita koma waye se hau mulkin BOYEM yanzu indai zai janye musu hukuncin dake kansu babu abinda ya shafeta muradinta kawai tayi auren kada ta qare a haka ta mutu a hakan tsufa na cimmusu a ba aure bare ‘yaya. HAILE kuwa guri ta nema ta zauna haka shima ASIM din zaunawa yayi yana zayyana musu abinda ya faru a fadar tas. Shiru Aslam da meryam sukai kafin suka dago suka kalli juna meryam na shaqar Wani Numfashi me zafi sbd tabbas ita kam yanzu takai karshe bazata yadda a fara wannan sabon rikicin da zai zama babban al’amariba a lalata Sauran lokacin da suke tinanin suna dashi na samun abinda suke so dan kuwa komai rikice zeyi yaqin Neman mulkin ya dawo sabo duk suna nan suna jiran a gama me hawa ya hau ita kam yayi mata tsayin da tabbas ba lallai ta iya jira ba dan haka duk inda taga alamar nasara da gaggawa wlh can zata koma ba bata lokaci koda kuwa hakan na nufin tabar ‘dan uwanta uwa daya uba daya ta zabi bastard son din. Aslam ma Zurfi tayi a tinanin da babu alkhairi ko daya a cikin ranta dan ita kam ko zata qara shekara nawa batajin zata taba kaunar ko Inuwar Wanda ma yake kaunar Ayanah da NUAB. Shiru sukai dukkaninsu suna tinanin ta inda zasu fara wannan sabon yaqin da suke ganin kaman yana tinkaro su batareda sunyi tsammanin Wanda sukewa kallan baida banbanci da almajirin yan taaddan shine taaddancin ma da kansa, Kuma idan har zai iya tsayuwa a gaban sultan me BOYEM da babu dan Adam din dayake BOYEM da zai ita tsayawa gaban idonsa ya kallesa bama bare tsayuwa ba kaya daga shi zai towel a gaban dukkanin manya fada da suma iya karshen rashin girmamawan rayuwa sun samesa a hakan da yayi musu to tayaya suke expecting akwai abinda zai girgiza sa, Numfashi HAILE ta sake me Zafin gaske kafin ta dago ta kalli ASIM da idanuwanta da sukai jajir itama ta bude Baki tace ‘Ka saka salman yayi kwakwaran binciken qarshe Akan NUAB din ya binciko waye shi da wainda yake tare da huldodinsa da matsayin dayake tinanin yanada shi dan da alama akwai Wanda ya tsaya masa, Hakama ta Dayan bangaren babban abinda zai kawo sassauci a wannan yaqin da zaayi dashi nasarar mu ta zarce tasa shine tabbatarda qiyayyarsa da sultan bame warware wa bace har abada hakama Ka tabbatarda an gano menene abinda yafi so da’ Shiru ASIM yayi baice komaiba sai idanuwansa jajir daya kafe Hailen dasu yana sauraronta dan kuwa ta hakan zai fara tabbas yana buqatan sanin komai Akan NUAB sbd abinda aka fara musu akansa ba shuke idanuwansu suka gane masu akansa ba. ******Sultan kuwa tinda ya bar fadar yake Zaune palon sa cikin nutsuwa Zaune yana jin tinanikansa da burikansa suna gauraraya da warware wa da saqawa sbd duka burinsa Akan NUAB ya zama tsayayyen Zakin BOYEM ne da zai riqe uwa da qasar da Amana amma hakan ya budewa alaqarsu sabuwar babbar alaqar nisanta da juna tareda zama Wanda fushinsa da zafinsa yayi yawan dabai tsammata dan haka ya basa umarnin tsayawa cikin masarautar ne batareda ya fita koina sbd ya samu lokaci isashe me tsayi da nutsuwa tareda mahaifiyarsa kafin ya basa umarnin dayake ransa na shekaru Akan amsar mulkin BOYEM cikin lumana dan kuwa ana fara wannan yaqin bazai samu irin wannan nutsuwan kulawa da mahaifiyarsa ba dan tako Ina fitina ce zata bude kofa musamman ga wainda suke jiran amsar mulkin da manyan fada dan shi koma menene NUAB din ya zama shi shine yake son ya zama mai mulkin BOYEM bayansa kota halin yaya ya shiryawa kowannensu a tsakanin shi NUAB din da bazai karba ta lalama ba da wainda zasu tada hankalin baa basu ba da manyan fada da duka zasu iya kasa Aminta da hakan a shirye yake da kowa. ******a bangaren LEUL kuwa koda suka koma saida ya sake sabon wanka ya shirya cikin ash Rb wears da suka zauna jikinsa a natse qamshinsa me sanyi na tashi ya fito palonsa inda aka kawo abincin rana daga bangaren Amminsa aka cika dining din a Jere babu kalan fruits din da babu Bayan lafiyayyan abinci Kala uku. Zaunawa yayi a natse batareda damuwan komai a ransa ba duk da har lokacin zuciyarsa daukan dumi takeyi idan ya Tina rashin daar da aka nuna ta aiko bayin mahaifiyarsa kiransa, Bai damu da hukuncin sultan akansa ba sbd bayajin akwai dalilin daya isa ya hanasa fita idan ya tashi fitar musamman da Ayau din ya basa umarnin aleey ya fara shirin tafiyarsu da Amminsa barin qasar gabaki daya Wanda da kansa a shirye yake da samun sultan ya fada masa da Amminsa zai tafi Kai tsaye idan shirye shiryen suka kammala kenan. Tareda Yaransa gabaki daya suka ci abinci a dining din Wanda hakan ke qara musu kaunarsa da tsayuwa Akan kowane lamarin sa dan babu kyama ko nuna banbancin matsayi a tsakanin sa dasu, Cikin kulawa da sakewa sukaci abincin aleey na sake koro masa bayanin manyan fada guda nawa ne a tarihin Masarautar hakama guda nawa ne suka Halarta taron yau din da dukkanin yanayinsu daya nuna a fuskarsa tareda sunayensu babu Wanda bai dauko komai akansa ba tsaf dan haka kwakwalwansa take tamkar computer. Bayanin full binciken rayuwar ASIM daya hada da abinda ya qara karanta tattare da yanayi sa na yau din shima ya fara koro bayanin a tsare dalla dalla cikin ilimi da tabbaci tin daga kan karatunsa na primary har zuwa yanxu dayake da har masters da Sauran ilimin wasu abubuwan tas. Dakatar dashi NUAB yayi daidai lokacin da zai zayyana bayanin su Aslam da mahaifiyarsu tas sbd baya buqatan sanin kowa da komai a masarautar tinda baida alaqa dasu bakuma zama zaiyiba bare rayuwa a cikinsu. Sai yamma Bayan magrib ya sake komawa gurin Amminsa wadda take jiransa zuciyarta cikeda ‘doki dan haka tare suka ci abincin dare tana jin kaman zata maidasa ciki sbd tsananin kaina shi kuwa kowane motsinta kashe jikinsa yakeyi sbd yanayinta dake nuna she’s very weak hakama fatarta kaman tanayin pale. Sai dare sosai Bayan ya tabbatarda tayi bacci kafin ya Baro bangaren ya koma nasa, Wanka yayi ya saka Kayan baccin James plebe ya daure gashinsa tsakiyar kansa ya dauki wayar sa ya kunna ya Nemo numbern likitansa dayake Greece ya sanar masa da yana buqatan qwararrin likitan zuciya da kwakwalwa su shirya su hadu a qasa daya ko Greece din dazai kawo mahaifiyarsa a duba masa lafiyarta cikakkiya. Washe gari haka ya dake tafiya gurin mahaifiyarsa ya wuni tareda ita yana bata lokacinsa da rayuwarsa gabaki daya ta wannan lokacin kafin sbd ganin hakan na taimakawa gurin samun kuzarinta. Kaf masarautar haryanxu bame samun damar ganinsa dan kuwa duk lokacinda zai fito daga bangarensa zuwa na mahaifiyarsa watsewa kowa keyi sbd Yaransa dake tare hanyar sbd tsaro, HAILE da ‘yayanta kuwa baqin cikin jiran wata Dayan ta cika ya hanasu kowane irin motsi tinda dole dik shirinsu su jira wata dayan tayi su ji me sultan zai yanke akansa, Fada ma gabaki daya sun kasa sakewa sbd shakka da zullumin me wata Dayan zata haifar idan ta cika, Duk tsawon wannan lokacin NUAB bai taba zuwa gurin sultan ba dan haka basu sake haduwa ba bakuma su da niyar haduwar kowa da abinda yake ransa Akan haduwar tasu sbd NUAB jiran komai ya kammala yakeyi ya samu sultan din ya tsaya a gabansa da kansa ba sako ba ya sanar masa zai tafi da mahaifiyarsa. Shi kuwa sultan ranar yake jira sbd yana sane da dole bazaa rasa dalilin da zai saka NUAB zuwa garesa ba indai Ayanah tana raye dan haka ranar shima yake jira. ********koina masarautar ta fara daukan zafi sbd watan nan daya tafiya yakeyi amma kamar shekaru suke jinsa ganin baya gudu dan kuwa Kai tsaye su HAILE sun gama yankewa da tsayar da sabuwar shawara me karfi Akan NUAB na barin BOYEM zasu kawar da abinda ya rage masa kadai a BOYEM Wanda zai sakasa dawowa koba yanzu ba wato uwarsa dan kuwa tana barin duniya sunsan bazai taba dawowa BOYEM ba, Wannan sabon burin ya kafu ne a ransu sbd zuciyarsu kaf data rasa nutsuwarta sakamakon tarihin LEUL BOYEM tas da suka samu daga kwakwaran bincikensu Wanda ya gigita kwakwalwansu da sanin cewa su idan a boye zasu iya daukan ran mutane shi a tasa duniyar a bayyane sukeyi batareda shakka ko tsoro ba dan haka shi ASIM a yanzu baida muradi Bayan NUAB yabar BOYEM har abada ba dawowa dan ko ya mutu basa kaunar a kawo musu gawarsa BOYEM dan haka idan hakan zai faru to dole saisun kawar da wadda sbd ita kadai yakeda alaqa da BOYEM ayanzu da harma a gaba. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 57 Yanda masarautar ta dauki Zafi kusan haka kan kowa ya dauki Zafi kowa tinaninsa da burika tareda kudirinsa daukan zafi sukeyi babban matsuwar kowa burinsa ya cika ya samu abinda yakeso dan hakanne a wannan lokacin kowa harkarsa ce sa burinsa a gabansa, Aleey shirye shiryen ganin komai na tafiyansu ya kammala yakeyi da Ammi wadda hakanan ta sakawa ranta NUAB ta kwallafa ranta fiyeda tinani akansa bata kaunar ko dare yayi ya tafi ya barta jin takeyi kaman kowane lokaci zai iya tafiya ya barta dan haka ta kasa samun sukuni da nutsuwa idan baya tareda da ita, Hakan ne ya saka gabaki daya zuciyarsa ta sake riquwa da alkawarin tafiya da ita bazai taba sake rabuwa da ita ba har abada, Su kansu Maa tenya yanda Ayanah ta qwallafa ‘dan nata a wannan Karan ya saka zuciyarsu shiga zullumi da faraban komai zai iya faru da lafiyarta me muni idan NUAB din ya tafi dan haka suma suke fata da tsananin adduar NUAB ya zauna a masarautar sbd sun San babu ta yanda zaayi wishmah tabar Masarautar matiqar sultan nata rai a cikinta zata rayu sai koma idan sultan dinne ya fita da ita da kansa zuwa rayuwa Wani gurin. Shirye shiryen tafiyar da akeyi hadda Maa tenya da sakinah akeyi sbd suma full nauyinsu yana kansa kaman yanda na Amminsa yake kansa dan haka shirye shiryen suke samu dan delay sbd tafiya ce ta kwata kwata zaiyi dasu su da BOYEM se labari. Tinda Yazo qasar bai fita koina ba koyaushe yana tareda mahaifiyarsa dan bata lokacinsa kuma baida kowane irin business a qasar kuma baya shaawan kullawa dan haka sun cikin fadar hutu kawai sukeyi suna jiran komai ya hadu. A hakan suka share sauti hudu Ana Sauran kwana biyu wata Dayan da aka yanke masa ta cika komai na tafiyarsu ya kammala tsaf Wanda ya sakasa jin wata irin nutsuwa da sanyin zuciyar cikar burin tafiya da Ammi, Aleey ne yaje har fada shi da securities biyu suna biye dashi ya isarwa da kadir babban hadimin sultan dashi kadaine duniya yakeda sirrin komai na zuci da bayyane na sultan sakon LEUL BOYEM yana buqatar ganawa sa sultan ganawar uba da ‘da bata sultan sa magajinsa ba. Kadir cikin girmamawa ya Karbi sakon da kunnuwa sa zuciyarsa ya isa gurin sultan daga gefensa ya dan ranqwafa cikin girmamawa daya sanar masa batareda duk Wanda yake fadar ba yaji sundaiyi tsit sbd ganin su aleey da securities din NUAB din sunsan sakon daga bangarensa ya taho. Sultan daya gama sauraron sakon bai furta komai Wanda yanayinsa kadai kadir ya kalla ya gane me sultan din yake nufi dan haka ya juya ya koma Inda suke ya isar musu da sakon cewa sarki zai ga LEUL BOYEM anjima Bayan sallar ishai a palon hutawarsa. Da wannan sakon su aleey suka koma ya sanar da NUAB din Wanda yana Jin hakan ya ajiye wayar dake hannunsa gefensa yana nade hannuwansa biyu a kirji fararen idanuwansa na kafe a makekiyar flat screen din dake gabansa. Da kansa ya sanar da mahaifiyarsa tafiyarsu a Washe gari insha Allah hakama su tenya, Su tenya da sakina sanyi jikinsu yayi suka shiga zullumi da tinani Kala Kala zuciyarsu na rasa nutsuwa da sukuni sbd sanin hakan ba abune me yiyiwa ba batareda tashe tashin hankali ba da tsallake karfaffun sharudda daban daban dan haka a tsaye zukata da hankalinsu yake suna jiran abinda goben zata haifar idan har zasu samu barin masarautar kaman yanda NUAB ya kudirta da su kansu yanda suke so indai Zasuje suyi rayuwa da Ayanah da NUAB din sun shirya barin Masarautar BOYEM da basuda kowa a cikinta tinda ita kanta tenya yayanta duka basa nan suna gurare daban daban suna aurensu. Tinda ya sanar dasu suke cikin zullumi da tashin hankalin da baya faduwa kuma baya nunawa musamman tenya data San aka samu matsala akasan dasu ake shirin barin masarautar da wishmah hakan zai iya zama bakin rayuwarsu dan haka suke a rashin nutsuwa da sukuni kwata kwata tareda jiran goben da zasu bar masarautar da qasar gabaki daya shikenan komai ya qare na tashin hankali da damuwa Ayanah zata rayu da ‘danta. Ita kanta Ayanah din Wani irin rashin sukuni da zullumin goben takeyi sbd tabar nan tabi HAYATEEM duk inda yake rayuwa itama tayi rayuwar acan tareda shi da Abaas da shima yayi mata alkawarin a kwanakin nan zai fara Neman kawo mata shi. Gabaki dayansu wunin a cikin zullumi me tsanani suke yinsa kaman yanda bangaren HAILE da yayanta suma suke cikin zullumin watan daya cika hakama manyan fada da suma suke cikin zullumin abinda zai iya faruwa a fada yanzu kuma dan suna ji a jikinsu duk Wanda yayi garajen kasa tsayawa ya duba kalaman sa da kyau zai iya rasa ransa batareda yakai qarshen labari ba dan haka su kawai ma barin NUAB da Yaransa suke so a masarautar ya koma inda ya fito masarautar bata buqatarsa hakama halayensa sun gama bayyanarda babuta yanda zaayi yayi mulkin qasa gabaki daya dan zai iya ringa bayyanarda tsiraicin jikinsa ga duniya ne Bayan yana matsayin sultan dan haka Sam babu ta inda zaa basa mulkin BOYEM. Shi kansa Wani irin yanayi ne me Zafi da radadin kuruciyarsa dayake taso masa yakeji na haduwan da zaiyi da mutumin dayake matsayin ubansa amma yayi watsi dashi tinda qananun shekaru ya jefa sa duniyar da babu kowa da zai rayu dashi a cikinsa, ya kuma rabasa da mahaifiyarsa batareda tausayin halinda take ciki ba har tsawon shekaru…. Numfashi me dumi ya sauke mara sauti a lokacinda yake tsaye gaban mirror din dayake closet dinsa tukuna Kai tsaye ya wuce bathroom dan wanka, Mintina ya dauka gurin wankan kafin ya fito daure da towel gashina na tsiyayar da ruwa a hankali. Wani towel din ya saka a kansa qarami yana goge gashinsa dashi kafin ya iso gaban dresser ya tsaya. Shirin mintin kusan talatin yayi kafin ya gama ya fito a lokacin 10 na dare tana gap da yi dan haka yana fitowa Kai tsaye bangaren sultan ya nufa cikin nutsuwa da Izzarsa. Suna isa tin daga nesa masu tsaran kofar suka wangale masa kofar kansu a qasa cikeda girmawa suna masa Barka da zuwa da zallar ladabi. Shima kadir dayake kofar a tsaye yana gadin isowansa dan tarbansa rissinawa yayi yana masa Barka da zuwa cikin girmamawa me girman gaske kafin ya basa hanya ya wuce shikuma yana gabansa dan yi masa iso har inda sultan yake Zaune cikin palon sa dayake hutawa na alfarma koina qamshinsa da sanyin ac ne ya kame ya riqe. Su aleey a kofar suka tsaya dukkaninsu a natse sha hayaniya, Palo biyu suka wuce kafin suka isa asalin palon dayake din yana Zaune cikin shigarsa ta hutawa tamkar ba dattijin daya manyanta sosai ba yana sanye da ash Riga da wando masu kauri da tsadan gaske da sukaiwa jikinsa kyau kwarjinsa ya cike gurin kaman yanda qamshinsa ya cike gurin. Sako kan NUAB a cikin shigar datake kusan iri daya data sultan nasa qamshin a hankali yana gauraye gurin yana kokarin doke na sultan din sanyin nutsuwa a zuciya, Dagowa sultan yayi yana Dora fararen idanuwansa akansa yana kallansa cikeda nutsuwa da kaunar da ba damar nunawa sbd wutar dayake gani a idanuwan NUAB din ta fushin da ba yanzu zai sauko ba shima baya buqatan ya sauko din yanzu harsai ya tirsasa karban abinda yakeson ya karba, Kwarjini da nutsuwan kyan NUAB cike idanuwan sultan sukai kaman yanda nasa kwarjini yake kokarin shiga lafiyayyun idanuwan LEUL me BOYEM daya daukesu daga kallan mahaifin nasa yana isowa cikeda nutsuwa da izza tareda kamewa ya zauna a kujeran dake facing sultan din ya dago fararen idanunwansa ya kallesa yana yaqar wutar datake cin zuciyarsa ya bude Baki a taqaice da kamewa yace ‘Barka da wannan lokaci me BOYEM’ Numfashi me sanyi da dan murmushi sultan ya sake yana sake kafe idanuwansa Akan NUAB din Wanda shima dagowa yayi da idonsa masu razana maza ya bude Baki cikeda nasa mulkin da izaa yace ‘Barka da isowan magajin me boyem LEUL NUAB ALMAZZ, Batareda bata lokaci ba menene dalilin son ganina?? Qarasa fada yayi yana komawa sultan dinsa sak cikeda ikon mulki ba wata sakin Fuska, Shima NUAB din baida lokacin batawa a maganar ya dago ya kallesa Kai tsaye yace ‘Zan bar BOYEM a karo na biyu kuma wannan Karan tafiya ta har abada Wadda zanyita ne tareda mahaifiyata wadda banajin tanada Sauran amfani a masarautar…’ Qarasa maganar yayi yana dagowa ya zubawa sultan idanunwansa da suka bayyana da kyau fes Akan fuskar sultan din. Cup din hot green tea din dayake hannunsa yana hayaqi sultan yayi yana jingina bayansa a natse hankali kwance kafin ya kalli NUAB din dakyau har lokacin hankalinsa kwance ba alamar ko mamaki a tattare dashi, Bude bakinsa yayi da cikakkiyar nutsuwa da kwanciyar hankali yace ‘Nine datake a qarqashina zan sanar idan ma batada amfanin amma ba Kai da kake baqo ba a masarautar da rayuwarta ba…… Wani irin kallo NUAB yayi masa maganarsa na sukar zuciyarsa baice komaiba idanunwansa na dan sauyawa. Cigaba da magana sultan yayi da cewa ‘NUAB ALMAZZ mahaifiyar Ayanah ghaz ta haramta gareka da kowa ma duniya Bayan ni daga ranar data zama wishmah ko yayanta basada iko da ita saini, Wannan shine abinda Baka gama fahimta ba inaga, Ayanah ghaz har abada kafarta bazata bar Masarautar BOYEM ba sai ranar da bana raye nabar duniya kenan to daga wannan lokacin ne zaka iya samun ikon mahaifiyarka amma Banda ina raye.. Wani irin motsi jijiyoyin NUAB din sukeyi suna fitowa idanuwansa kuwa ja suke rikidewa sunayi me tsananin gaske ya kafe idanuwansa akan sultan din Wanda yake magana hankali kwance, Zafi jininsa yafara yi yana tafarfasa da maganar da sultan ke kokarin fada masa na cewa baida ikon mahaifiyarsa har sai ranar da sultan din yabar duniya Bayan shi bazai iya jiran hakan ba kome zai iyayi dan a basa mahaifiyarsa…. Bude Baki sultan yayi yana sake daukan cup dinsa yakai bakinsa ya dago ya kalli kadir dayake tsaye Wanda take ya juya ya dauko wasu takardu a cikin file biyu me kyau da tsari Yazo ya ajiye gaban NUAB kan table din gabansa ya juya ya koma gefe. Sultan ne ya kalli files din kafin ya dago ya kalli NUAB din ya sake sakin nutsatsen murmushi me kyau yace ‘LEUL NUAB ALMAZZ me boyem kanada zabi guda biyu anan Wanda nasan zaka iya sbd mahaifiyarka, Kallan files din NUAB yayi zuciyarsa na Wani irin tafarfasa da kaunar da har jikinsa ya nuna sbd Wani irin ja fuskarsa da hannuwansa sukeyi, ‘Zabi biyu ne a gabanka, Na hannun dama takarda nada sabon sultan dazai mulki BOYEM ne datake dauke da sunanka kanta saka hannu a cikinta gobe zaa fitarwa da Masarauta da duniya ita a matsayin sabon sultan dazai fara mulki a gobe Wanda hakan zai Baka damar samun cikakken iko Akan mahaifiyarka harma da mahaifinka da baka buqata, Ta hannun Hagun kuwa takarda ce da zata fita a gobe itama idan Ka saka mata hannu cewan har abada kabar BOYEM da mahaifiyarka harsai ranar da Allah ya dauki raina…. Zabi na gareka me BOYEM da Moscow. Idan akwai abinda yafi tafarfasan jini shine yake faruwa da NUAB Wanda dukkanin jikinsa ke wata irin rawa koina nasa nayin ja idanuwansa na kafe Akan sultan Wanda shima shi din yake kalla zuciyarsa a shirye da karban duk zabin da NUAB din zaiyi a cikin biyun. Yanda jikin NUAB din ke wata irin rawa da fizgar wutar dake ci a jini da kansa da kirjinsa ya saka yayi shiru batareda yace komaiba kuma bai dauke idanuwansa daga kan sultan dayake wa Wani irin kallan tsanar datafi duk wadda ya taba yi masa a baya ba ta yau din kokarin buga zuciyarsa takeyi dan miqewa yayi ya juya yabar palon idanuwansa kaman zasu fara feshin wuta sbd fushin da bai taba shigaba rayuwarsa. Yana fitowa su aleey suka sha jinin jikinsu taje suka bi bayansa a qame batareda cewa komaiba. NUAB na ficewa sultan shima take ya aika wa tenya sako a cikin Daren cewan Ayi sanarwar a Daren nan ya maida mata matsayinta na komawa zuwa kwana tiraka daga yau dinnan. Sakon na isarwa tenya mummunan shock ta shiga Wanda y sakata mutuwar tsaye, HAILE data fito a Daren itama cikin shirin zuwa tirakar kwana tama fitowa aka Dakatar da ita da sakon hakan Wanda ya sakata mutuwar tsaye kafafunta na kasa daukanta. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_ Mamuhgee 58 Jiri me karfin gaske ne ya dibi HAILE wadda idanuwanta suke kokarin juyewa sbd dishi dishin da suke gani tsabar mummunan bugawan da kirjinta yayi tareda shock na babu tsammani, Fetto ce tayi saurin riqeta cikeda tashin hankalin da baa saka masa rana ba itama dan kuwa kaman kunnuwansu basu ji musu da kyau Dagowa fetto tayi ta kalli jakadiyar sakon wadda ke tsaye da bayi biyu a bayanta kansu a qasa cikeda girmamawa ta zuba musu ido bakinta na nauyin rasa ta inda zata fara jeho tambayar ta bude Baki a dan rikice tace ‘Maimaita sakon’ Cikin girmamawa bayin suka sake zubewa qasa Banda jakadiyar sakon data sauke kanta qasa cikin tsananin girmamawa ta sake maimaita sakon Wanda ya qarasa wargaza kuzarin HAILE ta Nemi zubewa jikin fetto kowace jijiyar jikinta jinin cikinta na katsewa kanta yayi nauyi sbd wata irin sarawa da yayi. Cikin sauri da kokarin sirrinta yanayin Hailen fetto tace masu kawo sakon su wuce ita kuka Kama Hailen tayi suka juya tareda Sauran bayin dake bayansu kowa kafafunsa a nauyaye sbd jinin uwargidansu dake tafarfasa duniyar bangaren tana daukan zafi gabaki dayanta. Suna isa Kai tsaye har bedroom dinta fetto ta kaita ta kwantar tareda fitowa take ta aika bangaren Aslam Akan a kira likita a turo sa queen haile na buqatarsa. Aslam na samun sakon ta fito ta nufo bangaren mahaifiyar tata sbd ganin meya sameta kokuma idan Wani abin ne ya faru dan kuwa tasan tabarta da shirin tafiya gurin sultan. Tana isowa ta tarar da ko magana Mamee din bata iya yi kirjinta ke tsananin ciwo da zafi sosai idanuwanta sunyi jajir ajiyan zuciya kawai takeyi me Zafi da karfi akai akai bakinta baya iya furta komai. Kallan fetto Aslam din tayi ta tambayeta meya samu mameen Bayanin komai fetto tayi mata Wanda ya saka Aslam din juyowa ta kalli mahaifiyarta itama idanuwanta na sauyawa zuciyarta tayi dum tama rasa abin fada sbd alamu na sake tabbatarda masifu da ranakun baqin cikinsu zasu bude su fara ne matiqar NUAB na nan dan kuwa dasu da bokayen su sun tabbatarda shine matsalar datake tsakaninsu da dukkanin Buri,nutsuwa,kwanciyan hankali da farin cikinsu da suke buqatar kawar wa matiqar suna son rayuwa da wainnan abubuwan. Shekara sama da ashirin rabon sultan da Wishmarsa, Ya rufe ya shafe babinta a rayuwarsa da shimfidarsa kaman yanda kowa da Masarautar suka rufe shafinta a cikin matan sultan, Wace masifar ce take Neman kunno Kai da a cikin Daren nan wannan mummunan sakon zai bayyana? Me sultan yake shirin yi na maida wishmah matsayinta a dare guda batareda tsammanin kowaba, Tayaya macen da suke son ‘dan tawayen ‘danta ya tattarata ya tafi da ita ko su aika masa ita sama zaa ce an maida mata matsayinta dayake tabbatarwa duniya ita din cikakkiyar ikon da mallakar sultan ce. Wani nauyi kirjinta ya ta jefar da wayarta a kujeran dake dakin tana fasa kiran likita ta bude Baki kaman zuciyarta zatai aman wuta tace ‘Yanayin Mamee baa buqatan likita baqin ciki ne da dacin zuciya zata dawo daidai zuwa anjima idan ta samu sassauci’ Tana gama fadar hakan a koma kan kujeran ta zauna tana dafe goshinta dayake mata nauyi sbd ciwon Kai da bacin ran dayake cinta, Shiru sukai dukkaninsu kowa da yanda baqin cikinsa yake cin zuciya da kirjinsa, Meryam da aka aikawa mameen ba lafiya Kai tsaye tana zuwa taji abinda ya faru shiru tayi batareda tace komaiba ta jiya ta koma sbd batada abin fada hakama karfinta da lafiyarta Neman qarewa sukeyi a gurin dawainiya sa dakon baqin ciki da ritirin zuciya kullum Wanda a yanzu kam ta fara gajiya gangar jikinta ta fara gazawa ga daukan wannan baqin cikin da baida ranar qarewa bata fatar ta mutu a cikinsa batareda ta dandana farin ciki da kwanciyan hankalin gidan aure da tara zuria ba. ******Tenya kuwa a tsaye take qyam kan kafafunta tinda wannan sakon ya iso mata Wanda kwakwalwan kanta itama ta kasa dauka sbd babu ta yanda zaayi ace Bayan shekaru masu yawa da yafe wishmah daga zuciya da shimfidarsa rana tsaka dare daya yace ya dawo da ita a Daren da suke kallan Daren karshe na rayuwarsu a masarautar, A Daren da suke jiran gari ya waye masa su bar komai anan suje su shimfida sabuwar rayuwa, Shin sultan ya San da shirin tafiyarsu ne a goben daya yanke wannan hukuncin daya girgiza zukatansu dama duk Wanda zaiji cikakkiyar sanarwar zuwa da safe, A wane Hali NUAB zai tsinci wannan mummunan labarin ga kunnuwa da zuciyarsa sbd hakan da sultan yayi Baro Baro yana nuni da Hana cikar burin NUAB ne yayi ta hanya me sauki se karfi dan kuwa koda NUAB yake ‘danta Wanda yafi kusanci da ikonta Akan kowa zamtowanta wishmah din ubansa kuma maidata cikakken matsayinta ya kere kowace irin dama da ikon da ‘danta yake dashi akanta. Zufa ne a tsiyayo mata ahankali yana gangarowa daga gefen goshinta ta zame ahankali ta zauna gefen sakinah datai mutuwar Zaune itama idanuwanta jajir dan kuwa matiqar wannan mummunan sakon ya isa kunnan NUAB wutar tsanar mahaifinsa datake ransa ce zata sake hauhawa sbd tafiya da mahaifiyarsa bazai taba yiyuwaba gashi a yanzu datake cikin tsananin shauqin danta matiqar ya tafi yabarta batareda ya cika mata alkawarin tafiya da itaba komai zai iya faruwa da ita dan haka akwai tashin hankali a cikin wannan lamarin daya sauka a dare daya tamkar saukar aradu. Kasa isarwa da Ayanah sakon sukai dukkaninsu sbd basusan tayaya kwakwalwanta zata karbi sakon ba hakama basu saniba ko sakon ya isa kunnuwan NUAB shima basusan yaya zai amsa sakonba dan haka tamkar sakon mutuwa sakon ya zamewa kowane ba gangaren harda na maraki wadda itama daga sama taji sakon ya saukar mata kamar tsawa sbd ta Riga ta dauka ta sakawa zuciyarta sultan ya gama da wishmah kenan har karshen rayuwarta, Ko HAILE da zuriarta sun dauka ya gama da ita ya rufe babinta har qarshen rayuwarsa Shiyasa komai Yazo musu a mummunan bazata da gigita. Kowane bangare a cikin bangaren uku na matan nasa tsit ya dauka babu bangaren da ba a cikin dacin zuciya da mutuwar jiki me tsanani suke ba tareda fargaba dan kuwa abu ne dayazo babu shirinda zasu San yaya zasu tarbesa ba. Dare sake nutsuwa yakeyi Wanda ya saka tenya da suke Zaune zasuyi kwanan Zaune miqewa tayi shirin kaiwa sultan ziyara dan isar da rokon alfarmar da zasu buqata. Tareda bayi hudu ta isa bangaren sultan din ta isarwa da kadir roko da sassaucin da wishmah take nema daga sultan Akan zuwanta Ayau Yazo ba shiri sultan yayi mata Afuwan karbanta a gobe ba yau din ba sbd yanzu haka ta jima da bacci sbd yanayin jikinta. Kadir bai jima sosai a ciki ba gurin isar da sakon ya fito da sakon rokonsu ya karbu Ayau sultan ya mata Afuwa zuwa goben ta dawo cikakkiyar macensa wishmah dinsa. Da sanyin jiki tenya tayi godia da girmamawa ta juya ta bar gurin tana komawa bangarensu kowa yayi dakinsa cikin jimamin yanda zasu iya sanar da Ayanah a gobe ta Koma wishmah dinta bazata taba iya bin ‘danta ba sedai shi idan zai zauna Masarautar tareda ita. ********A daidai wannan lokacin NUAB yana tsaye tsakiyar palonsa idanuwansa jajir sunyi Wani irin jan daya saka gabaki daya Yaransa sunkuyar da kansu suna tsaye Jere a kofar palon babu me ikon cewa komai ko tambayar komai sbd fushi da wutar dake ci a idanuwan LEUL dinsu sun tabbatarda mahaifinsa ne kadai a duniyar nan ya isa ya tabasa haka batareda sun shiga ba amma wannan fadan ba gurin shigarsu bane amma dukda mahaifinsa ne yana cewa suyi Wani abin tsaf zasuyi batareda tsayawa komaiba dan haka Ayau da suke ganin fushi da tsananin bacin ran da basu taba ganiba a tattare dashi ba yasa sun tabbatarda akwai Sauran Wani abu koma menene a zuciyar NUAB gameda mahaifinsa dan ba dan hakan ba Ayau sultan YASAR bazai kwana da kansa Akan wuyansa ba batareda sun tabbatarda ya samu ganawa da malaikan daukan rai. Duk wata jijiyar dake jikinsa sun fiffito fuskarsa da kunnuwansa sunyi jajir Wanda ke bayyanarda ba qaramar wuta ce take ci a jini da zuciyarsa ba dan kuwa zuciyarsa gap take da bindiga Akan abinda yake ji, Duk yanda ya rayu cikin fushi da mahaifinsa Akan abinda yayi na rabasa da uwarsa bai taba dauka zuciyarsa takai maqurar matakin karshe na qinsa da mahaifiyarsa ba da har zai iya basa zabi biyu na abinda yasan babu Wanda zai taba yi a cikin biyu ? Bazai taba karban mulkin BOYEM ba sbd qiyayyar BOYEM da duk Wanda yake cikinta dake zuciyarsa, Hakama zabi na biyun bazai taba saka hannun yabar mahaifiyarsa a BOYEM ba bazai taba dawowa ba har karshen rayuwarsa, Tayaya wannan mutumin zaiyi tinanin yabar mahaifiyarsa anan qasar yabar qasar har abada sbd kawai yana son ya karbi mulkin masarautar da bai taba shaawan zama magajinta bare sarkintaba,Masarautar data wulaqanta mahaifiyarsa, Masarautar da bata taba daraja mahaifiyarsa ba. Rintse jajayen idanuwansa yayi yana sake Jin fushin da bai taba Jin irinsa ba yana danne kirjinsa da numfashinsa ya bude bude ido yana dunqule hannuwansa biyu da suke wata irin rawar tsantsar bacin rai da baqin ciki me tsananin gaske. Tsit bangaren nasa ya dauka harma da zagayensa dan kuwa niimar bangarorin duk Wanda yake jinin masarautar dumi ya dauka me karfin gaske sbd masifar da babu shiri data fadowa kowannensu a Daren. A bangaren sultan shima a Zaunen kaman yanda duka iyalansa suke ya kwana zuciyarsa cikeda abubuwa daban daban da suke shirye da karban tsanar kowace iri daga NUAB da kowa ma matiqar zai Kai qure lambar fushi da Zafin kan NUAB ya sakasa karban mulkin Masarautar dayake shirye da sauka ako Yaushe dan kawai ya Dora sa akai Wanda saiyayi hakan zai samu nutsuwa da sukunin dabai samu irinsa ba tinda ya hau mulkin. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 59 Koda safiyar garin ta waye kowa dake cikin ahalin da ciwon Kai masu tsanani suka ringa tashi dashi tareda ciwon rai shima me tsananin gaske ga wainda suka samu rintsa wa baccin kenan ga wainda basu rintsa ba kuwa kaman wainda suka kwana gadin gawa haka suka tashi da idanuwa kaman baqin china. NUAB ALMAZZ da duk Wanda yake bangarensa cikin Yaransa kaf babu Wanda ko gifta masa bacci yayi a ido, Dan haka Koda ya fito sallar asuba sukai sallah a tare daga nan geamin suka shiga dakin da aka tsara masa dan hakan suka fara geamin har lokacin suna iya ganin fushinsa da bacin ransa bai gama sauka ba dan haka a kiyaye da shirye da kowane shirin suke hakama kaman yanda baice komai gameda tafiyarsu datake a ranarba babu Wanda ya tada maganar sbd a shirye suke da qarasa rayuwarsu anan matiqar baice ga ranar da zaa wuce ba su a inda ya zabi rayuwa acan tasu rayuwar take suma dan haka bangaren tsit yake babu wulgawan kowane bawan da baa nan yake aikin hidimar NUAB ba Wanda ko ruwan shansa basu cika barin kowa na basa ba idan ba su din ba sbd tsaro. Tenya da Maa sakinah kuwa tinda garin ya waye suke juya yanda zasu isar da sakon sultan ga Ayanah wadda ta tashi da tsananin kulafucin son ganin NUAB sbd tafiyarsa da zaiyi a ranar ya tafi da ita dasu sakinah dan haka Ayau din ma koda bayinta suka gama hada mata ruwan wanka tana tsaye jiran su gama tayi ta shirya dan kuwa haka take Jin tsananin kewan Abaas Wanda a zuciyarta tana barin masarautar take ganin zata hadu dasu. Karfe tara na safe Ayanah ta gama dukkanin shirinta tana Zaune tana jiran NUAB Wanda ya kasa zuwa inda take dan baisan tayaya zai iya kallanta ba ya sanar mata ya daga tafiyar tasu data saka aranta sosai, Shi kansa tsoron Wani ciwon ya sameta ko jikinta ya rikice ya saka ya rasa ta yaya zai kalleta, A Karan farko rayuwarsa da Wani ya sakasa a matsatsen yanayin da komai nasa ya tsaya cak batareda ya kaddamar da danyen hukuncin akansa ba, Maganar data shafi mahaifiyarsa tafi masa business deal din billions na dollars a rayuwarsa, Akan lamarin da duk ya shafi mahaifiyarsa baya masa garaje hakanne ya saka sultan yakeson ya quntata masa ta hanyar bullo masa ya nuna masa karfin ikonsa dayake kanta shima. Karfe sha daya da rabi ya shirya cikin black fendi wears da black geometric shape glasses na tom ford qamshinsa na tashi a hankali ya fito ya tinkari bangaren mahaifiyarsa Aleey na gefensa yana waya a natse shima Akan Wani business dinsu Yaransa biyu ne a bayansa da umbrella sai bayi kusan goma a can Bayan yaran nasa da suke bayin da aikinsu basa Rakiya da tsaro na cikin masarautar Wanda Sarkin bayi ne ya tanadar masa su masu karfin gaske ya aiko a matsayin bayinsa. Ko kafin ya iso a daidai wannan lokacin Ayanah ta dauko wayarta zata saka kiran NUAB dabai taba kaiwa wannan lokacin bai taho gareta ba hakama a saninta yace da safe zasu wuce amma gashi har rana tayi babushi Wanda hakan ya saka zuciyarta rasa sukuni hankalinta ya fara tashi da shiga firgici. Tana kokarin saka kiran Sakinah ta kalleta tareda saka hannu ta karbi wayar ta ajiye gefe ta kalleta tareda zama kujeran datake kusa da ita ta sauke Numfashi tana kallanta ta bude Baki zatai magana tenya da itace takeda alhakin isar da sakon ta kalli Ayanah data zuba musu ido zuciyarta na Wani irin nauyi tana jiran Jin abinda zasu fada ta katse sakinah da zubewa gaban Ayanah kanta na yin qasa sbd cike al’adar isar da sakon sultan ga wishimah dinsa ta bude Baki da murya me sauti dake yankar zuciyarta ga abinda zata fada tace ‘Allah ya qara miki lafiya da tsawon rai da zaki sheda aure da mulkin LEUL BOYEM NUAB ALMAZZ me BOYEM da Moscow, Allah ya qara miki girma da daraja wishmah uwar NUAB,Zakin BOYEM,Sarkin BOYEM,diamond din BOYEM, Ina fatan Allah ya bakin karfin zuciyar da zata karbi sako me daraja daga me daraja sultan me wishmah da LEUL NUAB ALMAZZ boyem wato sarki YASAR ALMAZ me boyem, A Daren jiyan sakon me daraja ya iso sultan mai boyem yace a miki albishirin ya maida miki martabarki ta wishimarsa ya maida miki karban kwananki a tirakarsa daga Daren jiyan Wanda Ayau zaki far……… Cikin wani irin sauti da basu taba ji ba a muryar NUAB da basu taba tsammanin ganinsa lokacinba kaman saukar aradu sukaji cikin nutsuwa yace ‘What? Maa? Sakinah ce ta dago jiki a matiqar sanyaye ta kalli kofar idanuwanta na sauyawa sbd Wani dandanon zallar daci da bacin rai tareda baqin ciki me tsananin gaske da suka jiyo a muryansa da idanuwansa dayake zarewa glass, Kafe idanuwansa yayi Akan Maa tenya din wadda ta sunkuyar da kanta zuciyarta na ‘daci itama dan basuyi farin ciki ko kadan da hakan ba amma ba yanda zatai dole ta isar da sakon sultan ga wishmah dinsa a darajance. Ayanah data dauke wuta a Zaune sbd kwakwalwanta data kasa digesting komai zuwa hankalinta dataji yana gushewa ta dago ta zubawa NUAB din idanuwanta dake sauyawa suka ja ahankali tareda tahowan wasu hawaye masu tsananin zafi a cikinsu ta miqe tsaye tana girgizata Kai da sauti me karfi tafara cewa ‘HAYATEEM Karka tafi Ka barni, Bazan iya zama idan Ka tafiba.. Kayi mun alkawarin tafiya dani inda zaka mu rayu acan tare, Sultan zai rabani dakai ne, Bazan iya rayuwa babu kaiba a kusa dani Hayateem, Hayateem kada Ka tafi Ka barni kaima, Baa ya tafi ya barni,Ammah ta tafi,Nurat ta tafi Zuhrah ta tafi Abaas ya tafi kaima zaka tafi Ka barni?? Wata irin rawa da fizga jikinta ya fara yi mai tsanani tana ja baya tana maganar da karfi idanuwana jajir bakinta na wata irin rawa. Mummunan tashi hankalin tenya da sakinah yayi suka miqe tsaye dukkaninsu suna kokarin nufarta tayi baya da karfi tana kafe idanuwanta Akan NUAB tana maganganun dake tada tsigar jikinsa gabaki daya idanunwansa na yin jajir sbd kallanta tana ficewa hayyacinta Akan idanuwansa yana gani mafi muni na rayuwarsa gabaki daya. Riqota yayi da sauri yana son bude Baki yayi magana amma Ayau Rauninsa yana Neman bayyana ‘Ya Ammi’ ya furta da Wani irin mataccen sautin daya saka gashin jikinsu tenya tashi suna dakatawa cak jiki mace. Riqota yayi jikinsa yana kokarin rungumeta amma gabaki daya fita takeyi hayyacinta tana ture sa da karfin gaske tana cewa mutuwa zatayi itama bazata iyaba kowa yabarta itama zata tafi batason zaman duniyar. Yanda taje maganganun koina jikinta yana fizga da jijjiga ya saka abinda yakeji yana tsananta a jininsa tareda Wani irin mutuwar jiki sbd bai taba ganin mahaifiyarsa a wannan yanayin ba dan haka ya rungumota jikinsa da karfi yana rungumeta ta fasa wani irin kuka me tsananin karfin gaske da tsima zuciya Wanda ya saka su Sakina sake shiga mummunan Halin tsoron dawowan tinaninta tin daga lokacinda ta fara ambatar sunayen ahalinta data bata taba ambata ba a lokaci daya tinda memory dinta ya samu matsala. Kukanta ya sakasa bude bakinsa da yayi mummunan nauyi shima nasa jikin kakkarwar yakeyi da sautin daya ratsata yace ‘Ammi bazan taba tafiya koina na Barik ba, Zan rayu guri daya dake kaman yanda nayi miki alkawari, Zan tafi dake insha Allah ko ba yanzu ba…… Rufe idanunwata tayi tana fasa sabon kukan dayake gigita nutsuwa da rikita jinin jikinsa tace ‘Idan Ka tafi mutuwa zanyi bazaka sake ganinaba Hayate….. ‘Ammi babu inda zan tafi na miki wannan alkawarin matiqar ba dake ba to Hayateem yana nan babu inda zai tafi wannan alkawarina ne gareki Ammi…… Girgiza Kai takeyi tana sake rikicewa sbd wannan Alkwarin dayake yana sake haukatar da kwakwalwanta ne sbd haka ya fada a farko zai tafi da ita amma yanzu a karo na biyu zai sake tafiya yabarta kaman yanda kowa ya barta dan haka kwakwalwanta tafara kokarin dawo mata da memories dinta sa suke buga kwakwalwan tata gangar jikinta fa lafiyarta na kasa dauka fizga tafara me tsananin gaske tana Wani irin Ihun da batasan tanayiba wasu azababben radadin dayake Dakatar da bugawan zuciyarta suna dawo mata tana tsananta ihunta daya saka NUAB qanqameta a jikinsa wasu irin hawayen da tinda yake duniya basu taba zuwa idanuwansa ba suna taruwa a cikin manyan idanunwansa da sukai mummunan ja yanajin yakushinta da dukanta na sauka jikinsa ya Lumshe idanunwansa yana sake rungumeta da kyau sbd taci gaba da illatasa Akan ta illata kanta. Sakinah ma kuka takeyi sosai Wanda ta manta rabon dataisa sbd clearly memories din Ayanah dinne suke kokarin dawowa baqin ciki da quncin rayuwanta zai dawo kenan Wanda yanzu zuciyarta bazata iya dauka ba sbd girma dayazo gangar jikin batai karfin daukan baqin ciki da quncin rayuwar dasuka dauka ba abaya. Bangaren tsit yayi gabaki daya kowa ya shiga Wani irin sanyi da tsananin tashin tsigar jiki musamman bayinta kaf da suka koma kofar shigowa suka jeru kansu a qasa cikeda dacin zuciya da mutuwar jiki. Cikin wani irin mummunan yanayi NUAB yace Maa tenya ta sanar da Aleey yana buqatan manyan likitocin qasar boyem cikin awa daya zuwa biyu a cikin masarautar. Labarin abinda yake faruwa take ya isa kunnen sultan Wanda zuciyarsa ta sosu da Wani irin daci me kaifi amma bai nuna ba saima kiran likitanta da shi kadai ya yadda dashi akanta kuma shine mai bata kowane irin magani Akan umarnin sultan din. Koda aka kira likitanta labarin zaucewanta da ciwonta ya isa kunnuwan kowa dan haka su HAILE dake cikin jimamin baqin ciki har lokacin suka dan samu sassauci suna dasa sabon zaman jiran labarin cikawarta sbd tsananin gaske jikin nata yayi. Kamar abinda zuciyarsa zata iya jikin nata ya fara sai gashi a lokaci daya cikin mintinan da basu gaza uku ba ta fice hayyacinta tana rasa numfashinta gabaki daya Wanda hakan ya saka kowane motsi ya dauke cak masarautar sbd kokarin ceto ranta da ake Neman likitoci suyi da gaggawa. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 60 Cikin qanqanin lokaci Aleey ya fara zuba kwararren bincikensa na Neman manyan doctors da suke qwararri a qasar boyem din gabaki daya, Wayoyi masu zafi da bincike ta waya da kuma Neman qarin bayanai daga sources masu karfi Aleey ya ringa yi ba ba kakkautawa ba delay ba hutawa har saida ya hada sunayen likitocin guda kusan goma da suke kwararri a qasar tareda informations nasu da komai, Babban farko da shine number shine Dr Amed Sulaim Wanda shine asalin likitan da sultan yakeda cikakken ikonsa ya kuma nadasa likitan Ayanah din tin shekarun da suka gabata kuma shi kadai ke a qasar Sauran kusan duka basa nan a yanzu sunyi tafiya wasu qasashen wainda ke nan kuma qwarewansu batai na Sauran ba dan haka take aleey ya saka shirin taho da doctors dinsu dake wasu qasar dan zuwa boyem idan sun samu ta daidaita kenan idan kuwa komai yaqi tafiya yanda suke so dole ko zaayi yaqi to zasu fita da ita qasar sedai hakan ya bude babin yaqi a tsakanin Masarautar BOYEM Da Moscow. Likitan nata da sultan ya kira tini suma shi suka tinkari gidansa Kai tsaye da securities nasu da motocinsu sbd aleey baida lokacin batawa Akan duk abinda ya shafi abinda NUAB ke so musamman Amminsa da ayanzu uwa ce ga daruruwan ‘yayan da batasan adadinsu ba da ‘danta ya samar mata dan kuwa a Moscow Ana can Ana shirin turo wasu set din securities din mata sbd tsaron lafiyarta a yayin datake jinya babu ruwa su da bayin masarauta gurin tsaron lafiyarta sbd lafiyarta itace lafiyar ubangidansu. Koda kiran sultan ya isa ga Dr Amed Akan zuwan gaggawa ga Ayanaah yana fitowa motocin su GHAZ na tsayawa kofar gate din gidansa me girma dan haka ko dogon bayani bai samu ba tsakiyar motocin su suka saka tasa motar da suka sakasa Wani gudu a cikinsu dan kuwa gabansa da bayansa babu daga qafa gudu sukeyi kaman zasu tashi sama dashi su ajiye sa gaban Wishamar BOYEM. Tin kafin su iso irin yanda suke gudu tafe da motocin ya saka securities wangale musu gates din masarautar tin daga na farko Harna qarshe a lokaci Daya suna shigewa a guje da motar Dr Amed tana tsakiyarsu. Koda suka isa har kofar bangaren shiga NUAB gabaki daya jijiyan jikinsa sun gama fitowa kana kallan idanuwansa gabanka zaiyi mummunan yankewa ya fadi sbd zaka iya rasa hankalinta sbd rikicewa da firgici. Kai tsaye wasu doctors din Dr Amed ya buqata su taho masa da Kayan aiki sbd hatta oxygen tana buqata da gaggawa anan suka rufu akanta. Cikin tashin hankalin duk wani me kaunarta da danta yake jiran ganin sauki ko farfadowanta daga yanayin da ya saka jikin kowa sanyi sbd take ta sauya kamanni kamar ba zata taba tashiba kwata kwata. Zaman fada a ranar gabaki daya ya tsayawa yayi cak sbd Ayau duk Wanda yake masarautar ya sheda tareda tattabarda son Ayanah bai taba fita daga zuciyar sultanba duk tsawon wannan shekarun sbd al’amarim daya bayyana garesu na halinda take ciki da halin da suke iya hango wa qarara sultan ya shiga dukda ya boye hakan tareda danne wa amma a wasu lokutan sirrin zuciya idanuwa ne suke nunawa. Halinda ya bayyana daga idanuwan sultan dayake Neman tona zuciyarsa ya lalata sanyin zuciyar dasu HAILE ke samu ga wannan ciwon lokacin daya dayake Neman kawar musu da Ayanah a cikin sauki. Duk yanda likitoci ke kokarinsu sunyi sun samu daidaita numfashinta dake samuwa da taimakon oxygen amma bata farfado ba Wanda kuma a abida suka gani ba lallai ta iya farfadowa yanzu ba bare dawowa daidai hakama abu biyune zai faru idan ta farka shine zata iya dawowa daidai harma da tinaninta da memories dinta data rasa hakama zata iya tashi kuma ba lafiya ba ta rasa Sauran hankali da memoryn daya rage mata Wanda zata manya komai hatta dan data Haifa da sultan da duk Wanda ta taba sani a rayuwarta dan haka abinda sukafi buqata a yanzu shine kada ta farka kusa kusa hakan zai bawa qwaqwalwarta daman samun ishashen hutun da batai aikin komaiba dan haka tinaninta da nutsuwarta zata fi Saurin dawowa cif cif insha Allah sabanin ta tashi da wuri hakan zai iya harbawa cikin kwakwalwan ta buga gabaki daya dan haka zasu hada da nasu taimakon dazai saka bazata farfado ba sai Bayan kaman wata daya haka indai so samu ne. Wannan bayanin ya karya tareda jijjiga duk wani kuzari da zuciyar NUAB ALMAZZ yake dashi dan kuwa Amminsa duniyarsa ce idan har zata iya tashi ta manta wanene shi da girman kaunar datake tsakanin jininsa da nata zai iya rasa kansa a wannan duniyar. Gabaki daya duniyar su aleey suma sai data jijjiga da wannan bayanin na likitoci dan haka Kai tsaye Aleey ya buqaci tattaunawa a tsakanin nasu likitocin dake qasashe daban daban dasu Dr Amed Wanda suka tattauna tattaunawa me tsayi kafin suka fahimci komai anan doctors dinsu suka tabbatar musu da bayanin su Dr Amed din haka yake a yanda suka fahimci kowane bayanin yanayinta da results nata. Wannan tabbacin da suka samu daga nasu doctors din ya saka suka shiga sabuwar zazzafan yanayi suna jiran abinda Allah zaiyi a farfado wan nata. Su sakinah da tenya duniyar tayi musu tsananin quncin da babu kowace irin walwala a rayuwarsu dan haka suka duqufa fadawa Allah sbd dawowan hankalinta da tinanin wata sabuwar masifar ce a rayuwarta da kowane irin baqin cikin data dandana zai dawo mata sabo fil. Sultan tsananin tsaro ya qarawa bangaren Ayanah din hakama shima NUAB Zafafan securities dinsa mata sun iso daga Moscow sune ciki da wajen bangaren Wanda a yanzu Bayan tenya da sakinah sai likitanta Dr Amed babu me shiga dakin datake idan ba NUAB din. Sultan bai taba zuwa dubata ba al’adar dake kansa matsayin shugaba dan haka zuciyar NUAB take sake tsananta akansa. A bangare daya kuwa Wani tsananin bincike aleey yakeyi me gigitarwa Akan Neman Abaas Wanda NUAB yayi alkawarin Nemowa kafin watan nan daya da ake saka ran tashin Amminsa ya cika dan kuwa a yadda likitocin sa suka basa tabbacin indai aka samu abinda zuciyarta tafi tsananin so ko maitarsa fiyeda komai a memory dinta na baya aka gabatar mata dashi tana farfadowa to hakan zai iya tabbatarda tsayuwar hankalinta da memories dinta. Hakan ya saka Kai tsaye ya bada umarnin duk inda Abaas yake a duniya yanason aleey ya qure lissafin kwakwalwansa Akan inda zaa fara nemansa. Wannan ya saka qwaqwalwan Aleey budewa da kyau ya nutsu ya buqaci ganawa da Wanda yasan Abaas a duniya Bayan Ammin. Kai tsaye Sakinah ce wadda zata basa bayanan dayake so dan haka a lokacinda ya zauna a palon da zai tattauna da Maa sakina dagowa yayi a natse ya kalleta da idanuwansa masu sirkin blue blue na asalin baturen Russia ya bude baki Bayan ya dauki iPad din dake hannunsa dan dauka da tattara duka bayanan da zatai masa ya dago yana nutsar da duka hankalinsa akanta yace ‘Maa’ Kallansa tayi a natse itama batareda ta bude bakiba sbd nauyin da bakin yayi mata na rayuwarsu dake dawo mata, ‘Maa,waye Abaas?? Ina Abaas yake? Bata yayi ko guduwa yayi kokuma korarsa akai? Idan bata yayi daga ina ya bata? Idan guduwa yayi daga ina ne ya gudun? Idan korarsa akai waye ya koresa,me yayi aka koresa? Meye cikakkiyar alaqar Abaas da Ammi? Shekara nawa yanzu da rabuwan Ammi da Abaas?’ Numfashi me nutsuwa ya sauke yana kallan Maa din Wadda idanuwanta sukai jajir ya sake tausasa muryansa yace ‘Maa,Maa duka wannan bayanan shine zai bani daman dawo da Abaas rayuwarku, Da wannan bayanin da zaki mun Maa nayi miki alkawarin Nemo Abaas matiqar yana raye insha Allah dan haka kowane bayaninki Maa ki sani yanada mahimmanci da rawar dazai taka a wannan aikin.’ Numfashi me Zafi da wasu hawaye masu Zafin gaske suka gangarowa Maa sakinah wadda Bayan shekaru masu tarin Yawa Ayau NUAB kila zaiji tarihin mahaifiyarsa da bai taba saniba mai daci da rashin dadin ji. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 61 A hankali cikin tsananin sanyi da mutuwar jikin radadin dayake dawo mata da quncin da harsu mutu bazasu manya dashi ba Maa sakinah tace ‘ABAAS GHAZ shine ‘da na karshe a jinin sarautar GHAZ data shafe a duniya gabaki daya yanzu, Shekaru masu yawan gaske ne da bazan tinaba suka Baro mu da asalin ANJOM GHAZ wato garin da mahaifin Abaas yake mulki, Abaas da Ayanah uwa daya uba daye suke tareda yan uwansu biyu da duka iyaye daya ne suka haifesu, AYANAH GHAZ itace babba sai ZUHRAH GHAZ sai NURAT GHAZ kafin ABAAS GHAZ…….. Ahankali tafara basa mummunan labarin rayuwarsu dayake cikeda baqin cikin da bai taba gogewa ba daga zuciyoyinsu,baqin cikin da dashi zasu mutu,baqin cikin da shine ya kawar da lafiyar kwakwalwa da gangar jikin Ayanaah,baqin cikin da shine zai zama abinda zasu mutu dashi,baqin cikin da har zuriar Bayan baya tasu Ayanah zasuyi baqin cikin jinsa har cikin jininsu,baqin cikin da a yanzu shine yake Neman raba Ayanah da rayuwarta…. Wani irin kuka takeyi mara sautin daya saka aleey daukan tissue ya miqa mata idanuwansa jajir hannuwansa na rawa zuciyarsa kaman zata fado hakama hawaye ne masu Zafin gaske suke Neman cikowa idanuwansa yanajin komai cikin zuciya da kirjinsa, Babban abinda yake sake saka jikinsa rawa shine yanda wannan mummunan tarihin zai isa kunnuwan LEUL, Yaya tarihin nan zai isa ga zuciyar datake shirye da mutuwa Akan wadda wannan mummunan tarihin yayi kaca kaca da rayuwarta? Tayaya zuciyarsa zata riski wannan tarihin kaddarar dayake dabaibaiye da rayuwar Amminsa. Numfashi Aleey ya sake saukewa yana kallan Maa yayi mata alkawarin zai Nemo Abaas a cikin qanqanin lokaci insha Allah hakama wannan tarihin LEUL ba a bakin kowa zaiji Saba insha Allah Sai a bakin Abaas da kansa. Ficewa Aleey yayi daga palon yana danna iPad dinsa sbd fara tattara kan bayanan daya riqe tsaf a cikin kansa na tarihin da abubuwan da zasu taimakawa bincikensa. Bedroom dinsa ya isa ya rufe yana Zaunawa kan sofa da table a gabansa ya bude laptop yana fara bi takan qasashen dake zagaye da BOYEM ta kowane bangare gabas yamma kudi da arewa. ******A Daren ko kadan aleey bai rintsa idanuwansa da kwakwalwansa ba saida ya hada wasu irin fitinannun bincike da bayanai har asuba, Sallar asuba yayi ya cigaba da hada kan bayanan sa da zai gabatarwa LEUL kuma yana saka ran ta hakan insha Allah Abaas kaman yana hannunsu ne. Karfe goma na safe NUAB ya fito a shirye cikin brown gucci wears da takarmin berluti brown suma fuskarsa fresh duk da yana cikin tsananin damuwa a kwanakin amma komai nasa yana nan daukan ido da girgiza zuciya yakeyi, Koda ya fito aleey yana tsaye shirye a palon hannunsa dauke da iPad fuskarsa sanye da farin glass da girmamawa ya yi masa Barka da fitowa yana bin bayansa zuwa dining inda aka cikeda tsaf da breakfast dinsa sbd yanzu da Amminsa take kwance ya Dena cin abinci acan. Zaunawa yayi a daidai lokacin shima aleey din ya zauna Bayan yayi serving nasa. Cikin nutsuwa sukai breakfast din suka kammala suka Baro dining din NUAB ya zauna Akan lafiyayyar 2seater Turkish royal cushion dake palon ya dago fararen idanuwansa masu daukan ido ya sauke Akan Aleey Wanda ya sauke ajiyan zuciya a natse ya matso ya bude iPad dinsa ya kamo bayanin dazai masa ya miqa masa a natse da girmamawa kafin ya dan ja baya kadan yana bude laptop din hannunsa daidai lokacinda NUAB ya bude abinda ya gama hada masa yafara bayani da cewa, ‘ANJOM GHAZ shine asalin garin da su Ammi suka fito, Safarar bayi ce ta fiddosu daga can zuwa nan Wanda a yanda Maa tayi bayani babu sunan qasar da suka sani Bayan anfito dasu zuwa nan din BOYEM, Abinda na tattara a bayaninta shine tace qasa goma sha shida aka wuto dasu ta ruwa kafin suka iso BOYEM, A bayanin nata su qasashe shidan nan bawai ta tabbatar bane amma a iya lissafinta tsayuwa goma Sha shida akai dasu Wanda hakan ya tabbatar mun da qasashe ne suke tsayawa kenan dan babu jirgin ruwa me girman da zai ringa tsayawa koina idan ba bodar wata qasar ya isoba, Zoomin map din daya hada yayi yana cigaba da cewa ‘Batasan sunan qasar da suka rabu da Abaas ba amma qasa biyu suka qara tsayawa Bayan rabuwarsu dashi a ta ukun ce suke isa inda aka saida su maana nan BOYEM kenan, A binciken dana tabbatar bisa ga wannan bayanin nata dama hada shima to qasar LARASIA aka siyar da Abaas Wanda idan muka duba qasa biyu ce tsakaninta da BOYEM dan hakan nake da tabbacin larasia dince inda aka siyar dashi.’ Wani bangaren Aleey ya sake zooming yana cigaba da cewa ‘Idan kuma na aka hada lissafin qasa goma sha shida dake akwai daga nan BOYEM ta gabas to Nahiyar qasar BASSHAH kenan idan kuma daga yamma ne qasa sha shida daga nan qasar ALSIYASH kenan, Idan kuma ta kudu ne qasar BUHARAQS kenan Hakama idan ta arewa ne to qasar ANTARIA kenan. Duka duka wannan bayanin dana hada qasashen nan sune inda zaa fara binciken nemansa amma dole duk qasar da zamu tafi Bayan sauka qasar sai an tafi bakin bodar ruwansu tanan ne dole zaa iya gane garuruwa masu kusa da manyan oceans da zaa iya samun tabbacin samun sa. Dagowa yayi ya kalli LEUL BOYEM da idanuwansa da suke cike da Basira da wata irin kwakwalwa me hasko komai Akan lissafi da nazari, Shima NUAB din gama kallan bayanin da duka suke a rubuce da map din Bayan duk bayanan dayayi masa da baki kuma, Dagowa yayi ya kalli Aleey ya bude baki a natse yace ‘Meye karshen tinani da bayaninka ya hada? Ajiye laptop din hannunsa yayi tareda kallan NUAB din cikeda girmamawa yace ‘Tinda ta ruwa suka iso qasar to dole bangare biyu ne Hagu da dama Wanda yake kudu da arewa kenan dan haka a cikin biyun zaa fara da daya maana a faro binciken daga inda suka fito tin farko ANJOM GHAZ kenan dan kuwa akwai yiyuwar tinda Abaas namijine to tabbas a tsawon shekarun nan indai ya samu yancinsa to tabbas ya koma gida dan sake ginawa da farfado da sunan GHAZ da bazai taba barin ya shafe ba Bayan ya nema yan uwansa be samu ba kenan, Dan haka inaga a fara daga can din Kai tsaye sbd tabbatarwa idan bai komaba Sai a Nemi Sauran qasashen. Kallansa NUAB ya dago a natse yayi cikin yadda da kowane bayanin aleey a koda Yaushe Akan komai sbd baya taba hada lissafin da bai qure kwakwalwansa akansa ba dan haka Numfashi me sanyi ya sake tareda dagowa yace ‘A gobe Inason a shirya tafiya zuwa qasar buharaqs din Wanda a cikinta ANJOM GHAZ take insha Allah. Gyada Kai aleey yayi sbd yanada tabbacin insha Allah haka bayanin yake ba tantanma indai Abaas na raye yana saka ran ya koma dan farfado da GHAZ matiqar shi namijin jinin GHAZ ne dan ‘dan halak ko baida zarra bazai yadda sarautar gidansu ta fadi ta shafe a tarihi ba. Juyawa yayi ya bar gurin yana daga wayar sa dan fara shirin tafiyar tasu da bazata wuce kwana biyu su wuce ba. Bayan barin aleey shiru NUAAB yayi yana Jin Wani irin yanayi na rashin sanin tinanin Kamawa Akan me haduwan mahaifiyarsa da Abaas zata kasance hakama a yanzu da mahaifiyarsa take cikin halin da bazata iya basa labarin cikakken tarihinta ba a bakin Abaas dayake jininta yakeson jin asalin tarihin komai na Amminsa. ******* Cikin kwana biyu aleey bai hutawa ba sbd bai taba wasa da duk abinda yake na LEUL ba dan haka shirin tafiyar ya tsaya tsayin daka saida ya tabbatarda ya hadata a cikin sati guda Bayan ya gama tanadar da komai na tafiyar wadda ya hadata hadda Maa sakinah da zata kaisu har cikin ANJOM GHAZ Bayan sun isa qasar kenan. Tenya batasan da tafiyar ba sai ranar da zaa wuce kai tsaye NUAB ya sanar dasu dan haka jiki a mace da tsananin zullumin daya saka jinin Maa sakinah mummunan hawa sbd komawa inda komai ya faro. Karfe Dayan rana motocinsu a Jere suka fice daga Masarautun zuwa airport Wanda motocinsu na zuwa gate din qarshe daidai nan motocin da suka dauko mai girma YUNAR BOYEM daga airport tareda ‘yarsa LEYLAH YUNAR BOYEM ‘yar amaryarsa ZUHRAH GHAZ BOYEM wadda ya kawo a matsayin tukuicin dawowan MAGAJI LEUL NUAB ALMAZZ BOYEM ya basa aurenta a matsayinta na jinin BOYEM itama. Ficewa motocinsa sukai tareda securities dinsa Bayan motocin mai girma YUNAR din sun shigo sukuma batareda kowannensu yaga junaba musamman LEYLAH YUNAR data gama mutuwa akansa tin kafin ganinsa a zahiri sbd kallo daya datai masa a hoton labarai ta shirya zama ko mistress dinsa ce ba matarsa ba dan haka wannan tukuicin da mahaifinta ya badata na aure shine abu mafi farin ciki da girma na rayuwarta dan haka batada baqin cikin dawowan su Masarauta da zama. Su kuwa suna isa airport Kai tsaye jirginsu ya daga yabar qasar. Tafiyar awanni masu yawa sukai kafin suka isa qasar bhariqs din wadda saida suka kwana a wata qasar kafin suka sake hawan jirgi suka isa. Tinda suka iso daga shi kansa NUAAB din Wanda baisan kaddarar mahaifiyarsa da zai tarar acan ko tasa sbd zuciyarsa dake Jin rashin nutsuwa da sukuni, Maa sakinah ma sosai ta shiga mummunan halin daya sakata fara ciwo me dan karfin da har saida taga likita kafin suka dauki wasu mahaukatan motoci zuwa tafiya me tsananin tsayin da zata kaisu ruwan dake qasar Wanda tacan zasu bi sakinah ta gane dajin garin ANJOM. Kwana daya da wuni sukai suna tafiya kuma saida suka dauko likita ma musamman sbd ciwon Maa dazai iya tashi koyaushe, Sun iso garin dayake bakin ruwa basu tsaya komaiba Aleey ya siya musu jirgin ruwa gabaki daya suka shiga dan barin gurin. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 62 Tafiyar wuni guda da kwana daya sukai suna zagaye ruwan da tafiya ke tsayi kafin Kaman a mafarki sakinah ta daga hannu tana nuna gurin daya saka idanuwanta jajir hannuwanta na rawa. Bakin dajin suka tsaya su aleey da Sauran Yaransa suka fidda drones dan duba duk abinda yake cikin dajin da gari ma idan akwai. Aleey ne yake riqe da iPad din dayake kallan dajin da drones dinsu suka shiga suna yawo a sama, Sauran yaran kuwa a tsaye suke da mahaukatan bindigoginsu a shirye da harbe ko dabba ce tayi motsi a gurin, NUAB yana ciki Zaune yana jiran bayani daga aleey Wanda yake sake kallan iPad din hannunsa da kyau sbd tabbas yaga gari. Wasu mahaukatan bikes dake shiga daji suka fidda daga jirgin ruwan suka hau tareda kutsawa cikin dajin a shirye da bindigoginsu da wasu manyan wuqaqe masu shegen hadari. Tafiya sukeyi suna kutsawa kafin sukai tafi me Nisan gaske basu isa garin ba sai yamma lis wanda ya saka sakinah yanke jiki ta fadi tama Dora kafarta a qasar garin ANJOM GHAZ kenan. Cikin kulawa da bada umarni yace a koma da ita jirgi taga doctor ya dubata abarshi daga shi se aleey su fara ganin lafiyar garin ma tukuna. Sauran yaran da bikes din tareda Maa sakina Juyawa sukai suka koma. Kafarsa ta dama ya fara dorawa a cikin garin ANJOM GHAZ daya saka tsigar jikinsa tashi sbd ganin yanda garin ya zama tamkar ba garin da mutane suke rayuwa a cikinsaba sbd duk tsawon shekarun garin bai dawo daidai ba sun rasa niima da tarin albarkar garin nasu. Akwai mutane sosai da gidaje sosai da kasuwanni a garin amma ba kamar baya ba sbd kusan kowa na garin yasan kowa tinda ba yawa sosai. Ganin baqi a garin ya saka gabaki daya mutane shiga tsoro da tashin hankali dan haka Kowa ya fara silalewa yana komawa gidansa ya shige ya rufe tinda dai shugaban garin nasu baida lafiyar dazai basu kariya, Fiyeda shekaru tara yana kwance yana jinyar da ba lallai ya tashi ba sbd yayi mummunan nisa. Gidan shugaban garin Aleey ya nema a taimaka a nuna musu babu musu kuwa Wani ya kaisu har kofar gidan asalin sarautar GHAZ. Fadawane suke gadin masarautar amma tsirarru Wanda yake nuni da Masarautar batada karfi ko Kwata kwata tinda garinma duka ba Wani karfi bare Ayi mulki me karfi. A fada suka zauna nan Sarkin fada ya shigo yana kallansu tareda zubawa NUAB idanunwata kaman zasu gado sbd ganin kammanninsa da jinin GHAZ dayake Neman shafewa daga Yauma kila sbd jikin Shugaba yau yayi tsananin da sai Allah. Kwarjinin NUAB ya saka shine ya gaidasu yana musu Barka da zuwa maimakon su su gaidasa sbd shine kila me mulkin GHAZ anan gaba. Aleey cikin nutsuwa shima ya dan gaidasa da yarensu Wanda NUAB yakeji sosai sbd mahaifiyarsa dake masa tin yana yaro hakama Maa sakinah shikuwa ya kullafa saida ya iya yaran shikuwa aleey baya wasa saida ya iya shima sbd uban gidan nasa da idan ta Kama. Kaman daga Sam Kai tsaye NUAB yace ‘Menene sunan shugaban jinin GHAZ daya rage a yanzu??? Da mamaki Sarkin fada yace ‘ABAAS GHAZ sai ‘yarsa qwalli daya tak AYANAH BAHAR GHAZ sune suka rage jinin GHAZ a duniya… Wani bawa ne ya fado fadar da sauri yana zubewa qasa yace ‘Sarkin fada jikin Maigirma yana sake tsananta kana buqatan zuwa. Miqewa Sarkin fada yayi yana barin gurin a rikice Wanda ya saka Kai tsaye NUAB miqewa yabi bayansa sbd kowane Hali Abaas din Amminsa yake yanason ganinsa. Sarkin fada na saka Kai dakin NUAB ma yana sakawa idanuwansa suka sauka Akan fuskar datake sak da sak data mahaifiyarsa. Abaas dake aman jini ahankali dagowa yayi idanuwansa na sauka Akan NUAB take ya dauke wuya komai nasa na kokarin tsayawa cak yayi baya zai zube Taku biyu NUAB yayi ta tarosa jikinsa yana Jin dukkanin nauyin dake zuciyarsa yana qaruwa da ganin sanyin idaniyar mahaifiyarsa a wannan halin. Feso Wani jini Abaas yai da karfi cikin azabar dayake kasa riqewa NUAB ya katse azabar ciwonsa da cewa ‘NUAB ALMAZZ ‘da ga AYANAH GHAZ…… Rintse idanuwana Abaas yayi cikin wani azababben yanka daya ratsa zuciyansa data gama yanke kauna da yan uwansa har abada musamman yanzu dayake kan gadon mutuwarsa, Riqosa NUAB yayi cikin rashin bata lokaci sbd kafin komai yana Abaas din na buqatar likita da gaggawa, Girgiza Kai Abaas yayi cikin wani mummunan rashin kuzari da ciwon da baida sassauci ke kadan ya damqi hannun NUAAB din da karfin gaske yana jan Numfashi da qyar yace ‘Ayanah tana raye??? Cikin sauri NUAB din ya Gyada masa Kai tareda bude baki yace ‘Kana buqatan likitan dazai duba lafiyar Ka da gaggawa daga baya duk zamuyi magana amma Ka sani Amminah tana raye, Tana son ganinka itama kafin tabar duniya dan haka kada Ka tafi Kabarta zuciyarta bazata iya daukaba sbd kaine hasken zuciyarta da idaniyar Abaas ghaz. Girgiza Kai Abaas ya sake yi yanajin kaman bazai iya ko minti dayaba a duniya dan haka koma yayane Allah yayi masa rahama ne tinda Sauran ransa daya kawo masa dan Ayanaah zai cika a hannunsa Bayan burinsa na hada jini da Ayanarsa ya cika Akan gadon mutuwarsa. Sake qanqame hannun NUAB yayi yana bude baki daqyar yace ‘Ka cikawa mahaifiyarka Dani burin da muka tashi dashi na hada zuria da juna Ayau cikin Daren yau na mutu da nutsuwar na bada ‘yata daya tak ga jinin Ayanah…… Wani kallan rashin fahimta NUAB yayi masa yaja kallan aleey yace Ayi gaggawar daukansa dan tafiya dashi ga likita. Abaas zamewa yayi yana sake dan girgiza Kai daqyar yace ‘Lokaci na yayi Allah ya yanke ganawata da Ayanah bazan Kai koinaba zan bar duniya, Kokarin daukansa aleey yakeyi amma jikin sake rikicewa yakeyi dan haka ba bata lokaci Aleey ya fita ya fidda wayar sa ya saka kiran Sauran yaran yace a kawo Maa sakinah yanzu. A lokacinda aka iso da Maa sakinah Abaas cikin tsananin ciwo da rashin karfi ya zayyanewa NUAB labarinsu tas Wanda baida dadin ji me tarin qunci da baqin ciki. Nasa labarin yake kokarin Dora masa Maa Sakinah ta shiga kafafunta na Takawa ahankali cikin sanyi da rawar zuciyar dake gap da bugawa. Suna kallan juna Abaas ya fashe da Wani irin kukan daya saka dakin yin tsit gashin jikinsu na tashi. Itama Maa sakinah zubewa tayi qasa tana fasa kuka a gabansa koina jikinta na rawa tana kiran sunansa da sauti me ratsa jiki. Bude baki yakeson yi ya Ambaci sunata da tambayar yan uwansa amma karfinsa yayi qasa sosai dan haka ta rarrafo da sauri tana bude bakinta dayake rawa cikin sautin daya sake saka gurin daukan tsit ta fara fada masa dukkanin halinda suka shiga har zuwa halinda ake ciki yanzu da Ayanah dake tsananin so da buqatarsa a rayuwarta. Magana zeyi harshensa ya fara kokarin karyewa dan haka take aleey yace securities su daukesa Ayi gaggawar tafiya dashi. Riqe hannun sakinah Abaas din yayi da karfin dayake na barin duniya yana kallanta daqyar ya iya furta ‘yata jinina AYANAH BAHAR…. Kasa qarasawa yayi jikinsa na sakewa gabaki daya. Gaggawar fita dashi suke kokarin yi sbd har lokacin akwai Sauran rai a jikinsa Sarkin gida na ganin hakan buga tsalle ya tare kofa tareda kiran fadawa yana cewa kada a Bari su fita koina da Shiguba da yarsa har sai ancika burinsa na auren yarsa Wanda hakan zai basu tabbacin kariyarta Bayan tabar nan sbd igiyoyin auren sa zasu tabbatar musu da zaa iya riqe amanarta matsayinta na ‘yar shugabansu hakama basuda tabbacin Ayanah din da gaske tana raye amma tinda ga ‘danta a gabansu bazaa tafi dasu ba saiya aureta koda Abaas ya rasu kafin akai to ta samu gatan zama Inuwar aure. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 63 Da Wani irin yanayi me ‘dacin gaske da jajayen ido NUAB da aleey suka dago dukkaninsu suka kalli Sarkin fadar Wanda ya sake tsayawa Akan maganarsa ba tsoro sbd wannan shine gatan da adalcin da zasu wa ‘yar shigabansu jinin GHAZ data rage a duniya a idanuwansu, Su dai bazasu bi su ba hakama bazasu Hana a tafi da Sugabansu ba dan nema masa lafiya sbd yana tsananin buqatarta amma kuma basuda tabbacin zai rayu ko bazai rayu ba a yanda sukaga jikin nasa yayi nisa dan haka gwara ‘dan Ayanah kaman yanda ya fada ya auri Bahar ‘Dinsu a gaban idonsu ta yanda koda Allah bai tashi kafafun Abaas ba sunsan zaman aure zatayi a cikinsu ba zaman garari ba dan haka tsoro ya cire a zuciyarsa matiqar ba auren BAHAR zasuyiba gwara abar musu shigabansu ya cika a gabansu su dauki amanar yarsa wannan shine tsayuwarsu matiqar ba hakan ba kuma sedai a kashe su a tafi da Abaas da BAHAR Bayan ransu. Kuka Sosai Maa sakinah takeyi tana Jin zuciyarta kaman zata fashe sbd idan Abaas yabar duniya Zuhrah ce kadai ta ragewa Ayanah wadda tafi tsananin kauna da son Abaas a rayuwarta fiyeda komai, Tayaya Ayanah zata iya jure wannan rashin? Sake qanqame hannun Abaas din sakinah tayi dake cikin hannunta tana rintse ido da sabon kuka me tsananin rasa zuciya. Aleey da ransa ya gama baci gashi ba lokaci da gaggawar gaske suke son tafiya da Wanda shine rayuwar Ammmi, Kallan Securities yayi da idanuwansa jajir yace su kawar da kowa har sai sun fice dashi. Sarkin fada na Jin hakan ya sake tare hanyar tareda fidda wata irin mahaukaciyar wuqa a jikinsa me munin da zata zata aikaka lahira ba bata lokaci. Wuqar sa ba komai bace a gurinsu sbd sunada wainda sukaci uwarta da ubanta a jikinsu Wanda zata katse jijiya take kafin kyaftawar ido kawai banbanci tasa dafin gaske ne a cikinta da shine zai kasheka bama kaifinta ba kila. Bindiga suka daga cikeda rashin tausayi suka seta Sarkin fadar tareda Yaransa da suka taho suka zagaye kofar dakin da makamai masu hadari a hannunsa. NUAB da jikinsa ke wata irin fizga sbd tsananin tsoron rasa Abaas Wanda shi kansa bayajin zai iya Hadiye radadin rashin sa sbd tsananin kaunar da son dayake masa tin kafin ya gansa sbd shine mutum daya da Amminsa tafi so a duniyarta da rayuwarta fiyeda kowa, Ko shi kansa data Haifa baya iya gane tsakanin shi da Abaas wane tafi tsananin so dan haka da kaunar Abaas shima ya tashi a ransa hakama da ita zai mutu dan haka bazai taba iya barin ya mutu sakamakon rashin likita ba indai ba Allah ya Riga yayi anan zai cika din ba lokacinsa yayi kenan ba dan haka dagowa yayi da jajayen idanuwansa da sukai mummunan ja kamar ma hadda hawaye a cikinsu ya kalli Sarkin fada Wanda yaja baya kadan sbd tsananin kwarjini da shakkar NUAB din data dakesa zuciya da kafafu amma duk da hakan bayajin zai iya ja da baya Akan abinda ya fada sedai Ayau ya rasa ransa gurin tabbatarda gyara goben BAHAR. Bude baki NUAB yayi da wata muryan data saka tsigar jikin Sarkin fada tashi gabaki daya yana sake Jin shakkar NUAB na shigarsa yace ‘Ku Bari na ceta rayuwarsa nayi muku alkawarin bawa rayuwarsa data ‘yarsa kariyar da matiqar ina raye sun wuce kowane matsayin da zasu fuskanci kunci ko rashin gata tako ina…….. Girgiza Kai Sarkin gida yayi yana kasa kallan NUAB din Wanda hatta fuskarsa tayi jajir jikinsa rawa yakeyi. Aleey da zufa ke gangarowa umarni me Zafi ya bada Wanda ya saka aka taqa bindigogin zaa fasa kan Sarkin gida NUAB ya daga hannu daidai nan Maa Sakinta ta zube qasa itama tana fasa sabon kukan daya saka kowa juyowa ya kalleta ahankali da jajayen idanuwa Banda NUAB daya rintse ido hannuwansa dake dauke da Abaas suna wata irin rawar dake bayyanarda halinda zuciyarsa take ciki. Cikin tsananin kukan data jima batai irinsa ba sakinah ta bude baki tareda dagowa ta kalli NUAB tace ‘NUAB Ka aureta kodan cika alkawarin daka daukanwa mahaifiyarka zaka kawo mata Abaas, Ka aureta sbd cetan rayuwar Abaas da zuciyoyi da dama bazasu iya jurewaba idan aka rasashi, Alkwari ne da aka dauka anan cikin masarautar GHAZ tin kafin sanin yaya kaddarar zata taho ba a tsakanin mahaifiyarka da Abaas Wanda idan Ka cikasa Ayau anan inda aka dauki alkawarin zaka cike musu burinsu ne da shi kadai ya rage a tsakaninsu sbd ko baka kaiwa Ayanaah Abaas ba Ka Kai mata auren ‘yarsa dake hannunka Ka cike mata gurbin da Abaas zai bar mata sbd ‘yar Abaas tamkar Abaas dinne a gurinta….. Tsit gurin yayi kowa na shiga sabon mummunan yanayi Banda NUAB da already yake cikinsa idanuwansa a rufe danan. Kallansa su aleey sukai dukkaninsu cikin shock da tashin hankali da firgici sbd babu kowane irin tarihin shigowan nace rayuwar LEUL daya tsara, Bai taba son kowace mace ba sbd baima taba sakasu a tsarin rayuwarsa ba,Amminsa ita kadaice wadda yayi Alkwarin ta ishesa rayuwarsa, Mata uku ne a rayuwarsa kuma su kadai ne wainda zaiyi rayuwa dasu baya buqatan kowace irin mace Bayan ukun nan iyayensa dan haka aleey yasan babu ta yanda zaayi mace ta shigo rayuwar LEUL dan haka dagowa yayi ya dawo da kallansa kan Sarkin fada Wanda jikinsa ya mace da maganganun sakinah da shima sune yake tsaye akansa. ‘A daura mun auren da ita ni zan aureta indai hakan ne kadai zai saka ku Bari mu tafi dashi da ita din…….. Kallansa Sarkin fada yayi da sauri cikin tsananin mamaki da fargaba kafin ya maida kallansa kan sakinah wadda ta fasa sabon kuka tukuna ya maida kallansa kan NUAB Wanda ya bude idanuwansa a hankali ya Dora Akan Sarkin fada din batareda ya kalli kowa ba ya saka hannunsa cikin aljihun wandon kakin dake jikinsa na shigowa daji ya ciro Wani kakkauran awarwaron zinari daya me kaurin gaske dayake dauke da sunan mahaifiyarsa da Abaas din Wanda yake nata ne shine ya bata kyautarsa da hannunsa ya qera sa ya saka sunanta dana Abaas din a yanzu dazai taho yaje har dakinta ya dauko sa sbd nunawa Abaas shedan shi dan Ayanah ne ya miqawa aleey dayake mutuwar tsaye cikeda rudewa da mamaki Abaas shima ya miqawa securities yana dawowa gurin NUAB Wanda ya saka hannunsa daya ya kamo hannun Sarkin gida ya saka masa zinarin ya bude baki da sauti me Kai tsaye da tarin tsananin son cikar Buri daya wato tafiya da Abaas dan ganin likitocin gaggawa. ‘Sadakina,a daura auren a yanzu anan a wannan daqiqar bana buqatar qarin mintina ko kadan batareda an daura ba.’ Jikin Sarkin fada rawa ya dauka sbd shakka da firgici amma hakanan ya tattaro karfin Hali da jarumta ya juya da sauri yace a kira masa Sauran masu dan matsayi a fadar da gaggawa. Aleey matsowa yayi zeyi magana sbd sanin NUAB zaiyi auren ne batareda kaunar ko taba shaawar hakan ba dan haka shi a shirye yake da auren koma yaya take yarinyar sbd LEUL kuma zai rayu da ita komai tsananin yanda lamarin zai kasance dan haka bude baki yayi zaiyi magana, Daga masa hannu NUAB yayi a natse cikin yanayinsa da baya son magana ko daya sbd koina fuskarsa yayi jajir hadda hannuwansa ma duka sunyi jajir. Sauran securities ficewa sukai da Abaas cikin gaggawa zuwa jirginsu na bakin ruwa da akwai Dr a cikinsa dan fara basa taimakon gaggawa kafin a gama daura auren. Sakinah barin gurin tayi ta fito kafafunta da tsananin nauyi ta nufi dakin Ayanaah na baya wainda a yanxu yake na BAHAR din kaman yanda aka fada tana kallan koina a hankali zuciyarta na yanka kuka mara sauti na taho mata hawaye na gudu suna tsiyaya a fuskarta kowane memory na rayuwar da sukai a kowane lungu da sako na gidan suna dawo mata. Inda daidai Baa ya shimfide gawar Ammah a lokacinda sukai ido biyu da gawar tata idanuwanta suka sauka ta rintse idanuwanta tana dafe kirjinta dake Wani irin ciwo hawayenta na tsananta gudu. Fara zagayawa dakunan kowa da aka Bari tana fashewa da sabon kukan baqin ciki me tsanani da kewan rayuwar da suka bari anan wadda koda basuyi arzikin da suke dashi a BOYEM ba ko kadan nan din yafi musu farin ciki da nutsuwa tareda kwanciyar hankali. Koina ya mutu ta zama tamkar kango babu komai da aka sauya,babu komai da aka gyara tin asalin yanda gini d tsarin gidan haka yake haryanzu babu cigaba ako ina dan haka koina a mace yake iya inda suke rayuwa a cikin masarautar yake gyare. A kofar bakin dakin Ayanah ta tsaya cak Wanda yake fes a gyare koina asalin qamshin jinin sarautar GHAZ na tashi yana fitowa daga dakin na flowern Ahlighazania Wanda gabaki daya ahalin shine qamshin da suke amfani dashi tin farko dan haka suka kasance kamshinsu daya me shiga rai da sanyi tareda wata irin nutsuwan kwanciyan hankali da kashe jiki. Lumshe idanuwa sakinah tayi tana Jin bugun zuciyarta na tsananta da Wani irin mutuwan jiki da baqin tareda quncin rashin kasancewan su a rayuwa daya koda duka suka Haifa iyalansu, Idan har mahaifiyar BAHAR bata raye yaya Abaas yayi dawainiyar kulawa da tarbiyantar da ita shi kadai babu dan uwansa ko daya a tattare da ita? Idan yanzu Allah ya kaddara ciwonsa bana tashi bane yaya zasu fuskanci BAHAR dik a matsayin dangin mahaifinta daya rasa shekaru? Yaya zata iya rayuwa a cikinsu batareda tasansu ba ko sabo dasu? Tayaya ma zata iya rayuwan nan babu uwa babu ubanta da shine gatanta, Zata dandana ‘daci da quncin da iyayenta suka dandana na rashin iyaye da tafiya Wani guri rayuwan da batama san yaya zatayi ba, Shi kansa auren da ake daura mata a yanzu basusan a mizanin wace kaddara zai hau ba sbd abu ne da babusa a tarihin GHAZ kuma bazai taba zamaba ga asalin jinin Wanda yake kan mulki kuma Wanda yake magaji bazai taba auren wadda ba jinin BOYEM ba haramun ne ma ga jinin da mahaifinsa ya mulki BOYEM kuma shima Ana sakaran ya mulki BOYEM auren wadda ba jinin BOYEM ba. Tayaya zasu fuskanci wannan auren da zaa kulla yanzu a masarautar da Kai tsaye mutuwarsu ce hukuncin wannan auren da akai indai ya isa gaban sultan da Masarautar BOYEM. Bude idanuwanta tayi ahankali jajir dasu sun kumbura ta miqa hannunta a hankali kofar dakin ta tura a natse bakinta na budewa da disashiyar murya tai sallama tana saka Kai daidai nan kunnuwanta suka jiyo mata sautin FATIHAR da aka shafa ta DAURA AUREN NUAB ALMAZZ BOYEM DA AYANAH BAHAR ABAAS GHAZ Wanda ya ratsa kunnuwan duk Wanda yake cikin masarautar GHAZ din Banda BAHAR wadda bacci takeyi a kishingide idanuwanta a rufe sbd kanta dayake tsananin ciwon damuwan dake zagaye da rayuwarta Akan ciwon BAA dinta Wanda shine gatanta,rayuwarta,hasken idaniya da rayuwarta. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 64 Rufe baki da hannuwa Maa sakinah tayi a lokacinda ta tabbatarda auren ya dauru Wanda hadarine zalla a cikinsa da zai iya raba mutane da yawa da rayuwarsu sbd sun aikatawa masarautar BOYEM gagarumin haram din da zai tono sirri Ka da dama amma koma menene ita saina shirye take da bawa Auren kariya da lafiyarta da rayuwarta har karshen rayuwarta da ba lallai tanada yawa a nan gaba ba. BAHAR da motsi ya sakata bude manyan fararen idanuwanta da suke sak na mahaifiyarta asalin balarabiyar SHEMALI masu daukan hankali da saka baki da jikinka mutuwa sbd Wani irin sirrin kwarjini da nitsatsen kyau dayake cikinsu, Akan sakinah dake kofar dakin tana shigowa ta sauke idanuwan a natse tana qarasa budesu gabaki daya akanta tareda tashi Zaune cikin nutsuwa da jinin mulkin GHAZ dake yawo yawo a jikinta batareda ta bude baki ba tayi magana sbd koma wanene shine yakeda damar bude baki ya sanar da ita shi waye meya kawosa dakinta dan haka kafafunta ta ziro a hankali cikin nutsuwa ta saka a cikin Takarmin dayake bakin gadonta tana kafe idanuwanta Akan sakinah dake qarasa shigowa tana bayyana fa hasken dakin na wutar gargajiya dake dakin take ta bayyana a idanuwan BAHAR din wadda Kai tsaye kukane idanuwanta suka fara cin karo dashi matar na yi Wanda ya saka bugun zuciyarta tsayawa cak sbd babu abinda Yazo ranta sai mahaifinta dan haka ahankali cikin wani irin slow ta maida kallanta kan kofar shigowa dakinta tana miqewa tsaye ta nufi kofa mayafin dake rufe da lafiyayyan dogon gashinta na zamewa bata tsaya ba ta rabe Maa sakina jikinta na wata irin rawa ta fice da gudu tana nufar dakinsa idanuwanta na tara ruwan mummunan tashin hankali da tsoron dayake jijjiga rayuwarta dan kuwa bazata iya rayuwar da babu Baa dinta a ciki ba,mutuwa zatayi idan ta rasashi a rayuwarta sbd shine ginshikin rayuwarta da duka rayuwarta take tangale da soyayyarsa. Saka Kai tayi a dakin tana jefa idonta Akan gadonsa dayake kwance taga babu kowa akai, Wani irin sarawa kanta yayi ta juyo da gudu dukkanin jikinta na wata irin rawar data saka kafafunta suka yanke zata fadi sakinah data biyota da sauri tana hawaye tayi saurin tareta jikinta tana kokarin rungumeta amma ta kasa tsayawa ta nufi fada da gudu idanuwanta basa gani sbd tsananin fita hayyacin data fara ta bude baki da Wani irin sautin daya ratsa kunnuwan duk Wanda yake masarautar cikin wani irin tada tsigar jiki tace ‘Baaa’ Tana saka Kai cikin fadar Kai tsaye da wannan sautin daidai nasu sautin ya shiga kunnuwanta na Sarkin fada dayake cewa ‘Auren NUAB ALMAZZ ya dauru da AYANAH BAHAR GHAZ Wanda muna fatar mutuwa ce kadai zata rabaaaa’ Kamar saukar gudu ma a tsakiyar kanta taji saukar zancen Wanda ya saka idanuwanta qarasa rasa ganinsu ta kafesu Akan Sarkin fada tana bude baki kanta na mantawa da komai Bayan son ganin mahaifinta da sautin daya saka Aleey dagowa a cikin wani irin yanayi me sanyin jikin auren da aka daura amma ya kasa kallanta sbd a yanzu da igiyoyin auren ubangidansa suka riga suka hau kanta idanuwansu bazasu iya mata kallan Kai tsaye batareda girmamawa ba koda kuwa aure ne da a yanzu baida suna bare matsayi kwata kwata a rayuwar me BOYEM din dan kuwa bai dauka auren ne shima yayi ba abu daya ya sani koma menene yayi sa ne dan tabbatarda karban Abaas Wanda yake rayuwar Amminsa. ‘Yet niw Abaa,yet niw Esu?’ Ta fada idanuwanta na kafe Akan Sarkin fada Wanda ya sauke Numfashi me tsananin sanyi da mutuwar jikin rabuwar da zeyi dasu a lokaci daya babu shiru babu sani ba tareda tinanin hakan ba dan ya dauka shine zai shafe Abaas da kansa ya kuma zama uban BAHAR din wadda zai aurar da ita ga nasa dan amma ko a hakan baiyi baqin ciki ba sbd shi kansa zaifi farin ciki idan Abaas yaje amma idan har hakan shine zai hada Abaas da Ayanaah to wannan shine gatan karshe da zai masa shi da Bahar wadda batasan kowaba a dangin uwa da ubanta ba. Tasowa yayi ya iso gaban Bahar din zai furta sunanta ta ja da baya cikin wani irin mutuwar jiki da mafi girman tashin hankalin rayuwarta tana girgiza Kai ta sake furta sunan Abaa dinta idanuwanta na yin wani irin ja hawaye masu tsananin zafi na taruwa a cikinsu sbd kadaici ze kasheta idan Abaa yabarta shine kadai ran dayake cikin empty rayuwarta da babu kowa a ciki sai zallan sunayen da babusu maana yan uwan mahaifin nata da iya sunansu ne basu ba a rayuwarta. NUAB da idanuwansa suke rintse tin lokacinda aka shafa fatihar auren dago kansa yayi ahankali yana bude idanuwansa da sukai jajir ya saukesu Akan fararen kafafun dasuke gabansa masu haske sosai na daukan hankali sarkar Farin azurfan dayake kafar duk motsinta daya na ja da Bayan datake Wani sauti me yar qarar dake shiga kunnuwansa yake fitarwa Wanda ya sakasa dauke jajayen idanuwansa zuciyarsa na Wani irin Zafin lokacin daya bata na cetan Abaas a gurin daurin auren da bai dauru ba a zuciya da rayuwarsa dan kuwa aure ne kadai na biyan buqatar wannan lokacin da suke so na tafiya da Abaas dan haka miqewa yayi batareda ya juyo ya kallo kowaba ya nufi kofa a takunsa na natsuwa da jinin mulkin daya dame sarautar GHAZ ya fice batareda ya cewa kowa komaiba. Yana ficewa Aleey ya miqe shima yabi bayansa Bayan ya dan kalli Maa sakinah dake Bayan BAHAR da Sarkin fada yace suna jiransu a waje. NUAB na fito bike din dake nan Sauran daya daya raye shi ya hau Kai tsaye ya wuce aka bar GHAZ din dashi. Su aleey sai Sauran bikes din sun dawo da sukaji kai Abaas dan haka Aleey fidda wayar sa yayi yafara zagaya masarautar yana daukan videos din dayasan buqatan hakan zata iya tasowa daga baya dan haka ya bawa Maa sakinah da Sarkin fada guri da zasuyi magana da Bahar wadda babu abinda take son ji da gani kawai idan ba mahaifinta ba dan mantawa ma kwakwalwanta tayi da abinda taji na maganar auren da kunnuwanta sukaji an daura da sunanta kawai mahaifinta takeso da ganin idan ba tafiya yayi ya barta ba dan haka ta rikice musu gabaki daya Wani irin rawa jikinta keyi tana ambatar sunansa da karfin gasken daya saka a rikice aka fiddota aka tafi da ita zuwa garesa Bayan Sauran bikes din sun dawo. Sbd yanda Bahar din ta fice hayyacinta tana kasa yadda da kowa harma da Maa sakinah ya saka dole da Sarkin fada aka tafi dan rakiya garesu. Koda suka nufo wajen gari idanuwanta tsananta jajir sukeyi cikin wani irin nauyin kirji na zuciya take jinta duniyar na sake mata duhun da tasan itama kila a cikinsa zata rayu ta mutu kaman yanda mahaifinta ya rayu ya tsufa a cikinsa. Koda suka iso an bawa Abaas taimakon gaggawan dayake buqata amma suna buqatan gaggawar isa dashi asibiti Wanda Dr ya bada shawarar bazai iya kaiwa qasar BOYEM a hakan ba dole suna buqatan fita can cikin babban birnin wannan qasar da suke ciki su fara tsayawa anan dashi asibiti saiya samu dan saukin da zai iya qarasawa dashi qasar BOYEM indai anason ya rayu. NUAB baida raayin tsayawa kowace qasa dashi Bayan BOYEM amma kuma ga yanayin jikin nasa dayake gani dole maganar Dr din zasu bi ta tsayawa asibitin qasar kafin daga baya su wuce idan ya dan zama stable sbd mummunan nisa yayi Wanda yake girgiza zuciyar NUAB din yanajin kaman bazai taba iya fuskantar Amminsa ba idan Abaas yabar duniya sbd baisan tayaya har abada zai iya fada mata Abaas dinta ya tafi yabartaba dan hakan shine blow na karshe da rayuwarta zata iya samu dan haka zaiyi iya kokarinsa yaga ya isar mata BOYEM dashi koda ganin karshe ne su yiwa juna. Kai tsaye barin ruwan dajin ANJOM GHAZ sukai Wanda kila shikenan sun barsa a rayuwarsu, Sakinah tsirawa dajin ido tayi bata kyaftawa zuciyarta na narkewa fiyeda a baya ANJOM shine garin da har su mutu bazasu Dena marmarin dawowa su qarasa rayuwa a cikinsa ba. Bahar ma dake Zaune gaban mahaifinta hannunta ta saka ahankali cikin nasa ta Kama tareda hade tafin hannuwansu tana Lumshe idanuwanta da sukai jajir wasu hawaye masu dumin cikinsu suka gangaro mata Sarkin fada ma kusa da ita su kadai a dakin dayake Sarkin fada na fada mata ‘dan Ayanar mahaifinta ne Yazo ga mahaifin nata dan basa lafiya. Babu kowane irin farin ciki ko Jin dadi ko daya daya sauka ga zuciyarta na abinda Sarkin fadan ya fada sbd babu Sauran kowace kauna ko soyayyar datake Jin zuciyarta nada damar yiwa kowa sbd bata tashi da kowa ba a rayuwarta daga ita sai mahaifinta tayi rayuwa, Rayuwa da zuciyarta a kulle take ga rayuwa da kowa a cikinta sbd kadaici da quncin data taso a cikinsa na rayuwa babu uwar data haifeta wadda ta rasu a ranar data kawota duniya hakama tasowa ta rayu a cikin duhun gidan da babu kowa a cikinsa sai ita da mahaifinta Wanda shima tinda ta bude ido duniya take kallansa cikin qunci da tarin baqin cikin daya hanasa lafiya har yau da rayuwarsa take cikin tsakiyar rayuwa ko mutuwa dan haka zuciyarta da rayuwarta a mace suke ta yanda basuda komai ciki da zata iya farin ciki dan haka rufe idanuwanta tayi ahankali wasu Zafafan hawayen na sake gangaro mata tana fadar idan lokacin mahaifinta ne yayi Allah ya dauki ransu a tare subar duniyar a tare. Tafiya me tsayi sukai kafin suka isa bakin bodar qasar babu bata lokaci aka fito dashi zuwa ambulance da already ankira tana jiransu dan haka take ambulance din ta daukesa tareda Bahar din a cikinta da Sarkin fada su kuma Sauran motocin suka shiga a guje akai asibiti dashi. Suna isa aka karbesa da gaggawa akai ciki dashi suka bisu jikin kowa a mace musamman BAHAR wadda zuwa lokacin ko kuka bata iyayi sbd babu alamar sauki ko kadan a lamarin nasa. A inda ake jira suka zazzauna Banda NUAB da aleey wainda aka kaisu guri kebantacce dan jiran dan hakan har lokacin babu Wanda yayi noticing juna a tsakaninsu. Maa sakinah ce Zaune a gefen Bahar din wadda kanta yake qasa ta dunqule hannayenta guri daya idanuwanta jajir. Hannu Maa sakinah ta Dora a hankali kan na Bahar din tareda kallanta cikeda kulawa da kauna me karfin gaske tareda tausayi itama idanuwanta jajir batareda tace komaiba, Itama Bahar din bata dagoba sedai rintse idanuwanta datai hannuwanta na tsananta rawa Maa Sakinta ta riqe su cikin nata gam alaman bata sassauci. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 65 Zaman da kowace daqiqa take tafiya da tsananin bugun zuciyarsu da zullumi tareda tsoro me tsanani da fargaba sukai na kusan wuni guri kafin aka samu numfashinsa ya dan dawo daidai da oxygen hakama jini aka daura masa Wanda yake na NUAB dinne da kansa aka diba Bayan ya hana Yaransa bada nasu nashin yakeson a sakawa Abaas sbd a shirye yake ga bada jininsa gabak daya idan zaa buqata hakan dan Abaas ya rayu sbd kila Amminsa zata iya juriya da karfin zuciyar rashin sa amma bazata iya daurewa rashin Abaas ba. Idanuwan Bahar sunyi munin da suka sauya kamanninta koina nata yayi jajir sbd kuka da damuwan datake gap da buga zuciyarta da babu kowa a ciki sai BAA din, Sakinah dik da tana cikin mummunan tashin hankalin itama amma ta daure ta fidda karfin halinta a matsayi na uwa dake gurin ta bawa BAHAR dukkanin kulawa da kaunar datake buqata a daidai wannan lokacin Wanda hakan ne ya dan rage zarewan da yarinyar ke kokarin yi a Zaune gurin. Shi kansa NUAB babu Wanda ya gansa a cikinsu dan hakane ma basusan jininsa ne aka sakawa Abaas dinba, Aleey kadai suka gani shima abinci lafiyayye kusan Kala biyar ya saka aka kawo musu Wanda babu Wanda suka saka a Bakinsu Duk yanda Maa sakinah tayi Bahar taci Sam ko sakewa babu a tsakaninsu da zata iya ma cusa kanta dole taci ba dan haka bata ci komaiba fatarta mahaifinta ya tashi ya samu lafiyar da zasu koma inda suka fito suci gaba da rayuwarsu su qarasata a tare su biyu kadai. Dare na yi haka aka daukesu aka kaisu masaukin da yanda Bahar taga rana haka taga Daren batareda ta rintsa ba a Zaune take har asuba idanuwanta sunyi mummunan kumburan da kanta ke tsananin ciwon da ko gani sosai batayi amma Sam ba sassaucin datake ji a zuciyarta. Karfe 8 na safe Aleey ya aiko mota aka maidasu asibiti inda ta tarar da mahaifinta yanda ta barsa tamkar babu rai a jikinsa yayi fayau yayi Wani irin haske ya qarasa bushewa sosai babu Sauran kowace albarkar jiki a tattare dashi. A sanyaye babu kuzari ko kadan a jikinta ta zame gefensa ta zauna idanuwanta na cikowa da hawayen da basu gangaroba ta saka hannunta cikin nasa ta sake hadewa ta qanqamesa cikin wani irin sanyi dayake tabbatarda kaunar datake masa a shirye take da mutuwa tareda shi. Haka ta wuni a dakin batareda kowa Yazo ba aka bata damarta sbd jikin nasa a yanda suke gani ba Sauran hope dan haka aka barta ta kasance dashi a lokutan da suka rage. Kwana biyu da zuwansu asibitin bai farfado ba se a ranar na ukun tsakiyar dare kusan karfe biyu da mintina ya farfado dan haka cikin gaggawa asibitin suka kira waya suka sanar da NUAB Wanda a cikin Daren ya sako babbar jacket din fendi Akan Kayan jikinsa ya fito da hular sanyi Akan gashinsa suka nufo asibitin. Suna isowa Kai tsaye dakin suka isa wanda doctors biyu ne da nurses hudu a dakin yana shigowa dukkaninsu suka jiyo suka kallesa cikeda tausayawa. Takowa yakeyi a hankali zuciyarsa na tsinkewa a Karan farko dayake Jin tsananin tsoro na saka kafafunsa rawa da nauyin daya sakasa kafe Abaas din da idanuwansa da sukai ja yana Jin wata irin kauna me karfin gaske da tsananin so da fatar ya tashi daga ciwon sbd ya basa rayuwa me kyau da nutsuwa da kwanciyan hankali da kaunar da batada sirki. Abaas dayake kwancen kamanninsa sun gama sauyawa daga dukkanin lafiyar da babu ko daya a jiki da jininsa bude idanuwansa Yayi ahankali cikin yanayin daya saka kafafun NUAB sake sarewa yaji kirjinsa yayi nauyin daya sakasa qarasowa da kyar, Akan NUAB Abaas ya kafe idanuwansa masu tsananin Laushi yana Jin dukkanin baqin cikinsa da damuwarsa na yayewa a lokutan sa na karshen rayuwa dan haka Lumshe idanuwansa yayi tareda motsawa a tsananin sanyi ya bude tafin hannunsa na dama da NUAB din yake tsaye, Zaunawa NUAB yayi a natse tareda Dora hannunsa ahankali Akan nasa din tareda kamawa ya riqe cikin nasa cikeda kulawa da kauna mara sirki. Numfashi mara karfi Abaas ya sauke cikin rashin karfi ko kadan ya saka hannunsa daya ya zare oxygen dinsa Wanda NUAB yayi saurin riqe hannunsa shi da aleey a lokaci daya amma Abaas din ya girgiza musu Kai tareda bude baki cikin karfin Hali yace ‘Inason Ayanah tasan labarina a bakina kafin barina duniya idan Allah yasa na tashi zan fada mata da bakina idan ban tashi ba Ka gabatar mata da rayuwar da Abaas dinta yayi sbd kada tarihinmu ya zama ba qarasashe ba a tarihin duniya.’ Aleey baya yaja ahankali tareda fidda iPad dinsa da babu inda yake taba zuwa bada ita ba koman emergency kuwa, Recording na video ya saka tareda tahowa ya ajiyeta a setin gadon Abaas din Wanda hannunsa yake cikin na NUAB yana jinsa har ransa sbd Jin yakeyi kaman hannun Ayanarsa ce a cikin hannunsa hade dan haka baida Sauran regret na rayuwa. Juyawa aleey yayi waje inda securities suke yace suje su dauko BAHAR sbd ganawa da mahaifinta. Yana dawowa wayar sa ya fice da ita dan fara hada tafiyar da zasuyi da asubar komai tsanani suna buqatan dagawa da Abaas din tinda ya farfado sbd likitocin su na gaggawa da suka hada suna can suna jiran isowansu. Kafin Abaas ya fara cewa komai sake qanqame hannun NUAB yayi da dan karfin daya rage masa mara kuzari ko kadan dan ya bude baki ahankali ya furta ‘AYANAH BAHAR’ dago jajayen idanuwa NUAB yayi ya kalli Abaas din Wanda tin daga qasan zuciyarsa sunan ‘yar tasa ya fito harya manta da ita sbd aleey ne yake tsaye Akan kulawa dasu. Ajiyan zuciya me sanyi Abaas din ya sauke kafin ya Lumshe idanuwansa a hankali sbd rayuwar komai ta farko data fara dawo masa radadi da baqin cikin na budewa yana famawa Wanda gashinan dashi zai mutu yabar duniya. Asalin tarihinsu da rayuwar da sukai a qarqashin kulawa da kaunar iyayensu ya fara jerowa ahankali cikin nutsuwa da Wani irin ratsa zuciya da yanda kusrawa suka tarwatsa rayuwarsu suka sauya tarihinsu da kaddararsu zuwa mara dadi da kyau, Yanda rayuwarsu ta sauya ne daga ranar da suka bar garinsu zuwa tafiya qangin bauta yafara zayyana wa Dayan bayan daya daki daki batareda ya boye ko kalma daya zuciyarsa na Kina da radadi me tsananin ciwo da baqin ciki, Yana zuwa daidai inda aka lalata rayuwar Nurat wadda akai komai a cikin kunnuwansu qanqame hannun NUAB yayi cikin wani irin mafi zazzafan baqin cikin da har yanzu sautin kukanta bai fita kunnuwansa da zuciyarsa ba shiru ya dan yi jikinsa na rawa idanuwansa na rufewa cikin azaba… Rawa jikin NUAB yakeyi sosai yana wata irin jijjiga a hankali ya qanqame hannun Abaas din da karfin daya saka Abaas bude idanuwansa yana sauke su Akan NUAB din Wanda yake hango Wani irin radadi da baqin ciki me tsananin karfi a cikin idanuwansa, Rintse ido shima ya sake yi yana cigaba da bada labarin mutuwarta da abinda yaci gaba da biyowa Bayan nan har zuwa inda aka rabasa da yan uwansa, Cigaba yayi da cewa, ‘Bayan an rabasa da yan uwansa anan kasuwar kwana yayi a daure a Wani ice tamkar dabba haka ya kuma wuni a rana babu ruwa babu Inuwa har saida karfinsa ya qare ya dunqule guri daya yana fita hayyacinsa sbd azabar rana da kishirwan dayake fatar ta dauki ransa dan kuwa bazai iya rayuwa babu su Ayanah a tareda shi ba dan haka duk duka da azabar da aka ringa gana masa Qin cin komai ko ruwan da aka basa yayi sbd yunwa yake sonta kashe sa ya huta. Ganin taurin kansa ya saka sukuma suka siyarwa wasu marasa imani shi da niyar zasu je dashi su huta a tinaninsu mace ce gashi yaqi cewa komai dan Alkawari ne bazaiyi magana ba da yayiwa Ayanah harsai rayuwarsa ta kubuta dan haka bazai taba karya wannan Alkwarin ba. Akan kudi ba masu yawa ba aka siyar dashi take wainda suka siyesa suka tafi dashi zuwa gurin hutawarsu, Koda suka tafi dashi mummunan abinda suka fara aikata masa shine dukansa suka ringa yi har saida ya Dena motsi yayi mummunan illatar da baida Sauran amfani a duniya tukuna suka yaga Kayan jikinsa gabaki daya Akan zasu masa fyade sai suka tarar dashi namiji ne dan haka baqin cikinsu ya tsananta take suka qarasa kashesa da dukan tsiya suka tattara shi suka Kai bakin ruwan suka yar suka Tafiyarsu. A wannan Daren gap da asuba wasu suka tsincesa suma maimakon su taimaka masa sai suka duba suka ga yanada Sauran rai dan haka suka wankesa tas suka sake saka masa Kayan mata sbd ganinsa da yan kunne a kunne harma da abin hanci, Gari na fara wayewa kafin rana ta fito suka kallaba suka siyarwa Wani matafiyi shi a matsayin baiwa mace sbd anfison bayi mata a Kasuwan yanzu Shiyasa suka fi tsada. Matafiyin raya siya bawan asalin balaraben shemali ne Wanda yayiwa ‘yarsa kwalli daya alkawarin siya mata baiwa mace da zata zama tamkar kawarta sbd debe mata kewan rashin uwa da kawayen datake fama dashi dan haka har zai tafi ya samu baiwar duk da taji jiki tana cikin wani mummunan Hali sosai amma hakanan bai damu ba ya siye sbd jirgin ruwa zaibi zuwa komawa qasar sa bazai jira gari ya waye a fara cin kasuwan bayi ba. Hakanan ya karbi Abaas ya wuce dashi Bayan ya biya kudin jirginsa na ruwa ya biya kudin kayansa da bawansa Wanda zaa saka guri daya da Kayan sbd haka akeyi bayi da kaya guri daya ake sakasa kaman wasu dabbobi dan haka babu komawa jirginsu yabar qasar. Tafiyar wuni da kwana daya sukai suka isa qasar wadda take cikeda nata kalar arzikin, Boukar shine sunansa hakama shi din mai arziki ne sosai a gurin yan uwansa dama garin nasu Wanda yake na qasar larabawan shemali ne, ‘Yarsa tak daya a duniya wadda mahaifiyarta bata jima da rasuwa ba tabarta da kadai cin daya saka ya siyo mata baiwa sbd ta fita daga kewan datake cikinta, Baya tareda yan uwansa sosai sbd akwai Hassada da qyashi sosai a tsakaninsu dashi, Duniyarsa ta tsone musu ido sosai, Tsananin hanyar da zasu rabasa da dukiyar suke nema dan haka basa rabarsa ko kadan sbd rayuwarsa suke dako dan hakanne ma yake tsananin kiyayewa Akan yarsa da ita kadai garesa bai hadata da komai, AYSHAHH ne sunan yar tasa wadda take balarabiya gabanta da bayanta sbd uwa da ubanta duka yan asalin shemali dinne dan haka da kyau da gata da nutsuwa ta taso tareda gatan da kusan a garin babu Wanda ya keda irinsa. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 66 Koda boukar ya kawowa yarsa ayshahh baiwa tayi farin ciki sosai sbd tana tsananin buqatar Abokiyar debe kewa dan haka tayi kaunaci kyautar baiwar musamman ganin kusan kansu daya kila ma ba Wani sosai baiwar ta girmeta ba dan haka taimaka mata sukai sosai da magani da ruwa da Sauran abubuwan da abinci ta samu a cikin kwana biyu ta dawo daidai hayyacinta ya dawo Wanda a hakan bata tana magana ba dan haka ran boukar ya baci ganin Ashe Murna aka siyar masa dan haka yayi alkawarin sake siyo mata wata idan yayi tafiyar kasuwancinsa. Sosai Abaas yayi jinya tukuna ya dawo tsaye a kafafunsa ya fara aikin bautar da aka siyosa yayi batareda har lokacin ya fara magana ba, Bauta yakeyi a gidan da rayuwar masu gidan dan kuwa kaf hidima da wahalar aikin gidan shine yakeyi Bayan hutawa babu abinda sukeyi se idan boukar ya fita ke yake Zaunawa da Ayshaah dan debe mata kewa kuma har lokacin basu taba sanin shi namiji bane a haka a hakan harya dauki kusan shekara bakwai dasu yana bauta sun samu Wani irin sabo dashi sosai gaske sbd kaf rayuwarsu babu kowa a cikinta baya su kadai uba da ‘ya sai maqota da yan uwan mahaifiyarta dake zuwa akai akai dan haka shine mutum na farko da suka sabo dashi fiyeda kowa da komai duk da har lokacin shi din kurma ne hakama bai taba fita daga qunci da tsananin baqin cikin da zuciyarsa take ciki ba amma daidai gwagwado sbd babu mugunta ba azaba ba tozarwa ba hantara ba qyama a tsakaninsu dashi ya saka suka samu matsayi a zuciyarsa musamman ayshaah dayake kallo kaman yar uwarsa sbd sosai take kaunarsa. Shi Kansa boukar sosai yake da nutsuwa da kwanciyan hankali idan yabarsu tare sbd ya yadda da yarsa zata samu samu kulawa tamkar yananan koma fiye a gurin Nurat kaman yanda ya fada musu sunansa kenan a rubuce da larabci. Bayan sabo shekarun suna dake nitsawa shaquwa me karfi ta shigesu sbd a yanzu ya koma tamkar Wani bangare ja rayuwarsu dan haka a yanzu tamkar ahalin mutum uku suke jinsu duk da haryanzu har gobe shi bawan su ne amma akwai kauna da kulawa tsakaninsu sbd tsananin biyayyarsa da rashin hayaniyarsa. Saida yayi shekara kusan goma a hannunsu tukuna sukasan asalin jinsinsa da tintini boukar ya fahimta amma bai nuna masa ba sbd son qure lamarin Wanda baisan ina ze tsaya ba dan haka ya fuskunci hukunci me tsanani a gurinsa kafin kuma daga karshe ya barsa a macensa cewa shine hukuncin sa haka zaici gaba da zama tamkar dan daudu. Baiji ciwo da Zafin hukuncin ba sosai sedai Ka quncin sa daya dawo sabo na rashin yan uwansa a rayuwarsa dayake ganin batada Sauran amfani a gurinsa, Yanayin alaqar sa da ayshaah sauyawa tayi sbd jinsinsu daya bayyana ba daya ba dan haka ta rage shige masa sosai hakama ta Dena bayyanar da inda be kamata ba a jikinta indai suna tare sbd kiyaye dokar addini. A hakan sukaci gaba batareda sun sauya masa tako wace hanya ba ko kadan, Kaf garin sun San Nurat a matsayin bawan ahalin da shine bawan da zai zama na ahalin me zuwa dan kuwa idan har boukar ya mutu Nurat yana cikin gadon da zaa raba maana shi Kansa abinda Wani ze iya gada ne a gurin rabon gadon Wanda yan uwansa keta lissafi sbd arzikinsa yayi wata irin sake habbaka ya tara dukiya ke yawan gaske data saka yarsa taje rayuwa tamkar sarauniya a fada, Da farko Bayan angane Nurat namiji ne ba mace ba mutan gari sun so korarsa sbd jifansa da ihu aka ringa yi masa daga kasuwa da aka aikesa Wanda Koda ya iso gida sun masa mummunan illar data sauya masa kamanni sosai sbd jifar ta fasa Kansa da fuskarsa amma a hakan ya iso gidan baya ko gani sosai sbd jinin daya rufe idanuwansa. Da karfin dukiya boukar yayi amfani ya hana a kori Nurat din amma kuma tin daga wannan lokacin Nurat ya zama abin qyama da hantara tareda jifa a cikin mutane a duk lokacinda zai fita gashi har lokacin shigar mata yakeyi, Tsananin tsana da qyama tareda hantarar dayake fuskanta a rayuwarsa tsawan shekara kusan uku ya saka rayuwarsa gabaki dayanta komawa asalin baqin ciki da qunci dan haka sai abin ya fara taba zuciyarsa da daman bata taba fita tsananin qunci ba. Wasu bayin boukar ya siyo guda biyar masu karfi dan gadin gidansa da ako Yaushe ake kokarin kawo harin Kai karshen rayuwar Nurat din Wanda kaf garin suke ganin mugun abu ne a cikinsu zama da zabgegen namiji a cikin Kayan mata dan haka koda be bar garin ba to zasu kashesa dan zamansa a garin tamkar zunubi ne. Cikin wannan fitinar dake tashi koyaushe yan uwan boukar dake harin rayuwarsa suka shige sbd samun biya da cimma burinsu na shekaru masu yawa akansa sbd a yanda Nurat ta zama rayuwarsa da ‘yarsa bazasu iya rabuwa dashi ba dan haka suna samun ya fara shirye shiryen barin garin da Nurat dan komawa Wani garin suyi rayuwa hankali kwance tinda yanada dukiyarsa me yawan gaske. Ana cikin wannan halin rana tsaka kwatsam cikin dare kawai aka cinnawa bangaren abincin boukar dake gidan wuta inda tarin dukiyar abincin sa take me yawan gaske buhuhuwan hatsin da dukiya ce me tsananin gaske, Fitowa boukar din yayi cikin duhu da hayaqin daya gauraye gidan har Baka ganin komai yana kokarin isa bangaren idanuwansa da kunnuwansa sukai masa mummunan ji da ganin daya tabbatar masa da halin yan uwansa dayake zargi na shekaru masu yawa dan haka da sauri ya juya cikin hayaqin jikinsa na rawa zuciyarsa na Wani irin radadi da firgici sbd lamarin Yazo masa a bazata. Fada ne ya fara kaurewa da hayaniya tareda ihu a gurin kashe wutar wadda duk da tsakiyar dare ne amma take mutane da suka cika gurin da sunan kashe wutar da kuma son qaddamar da nufinsu a cikin hayaniyar kashe gobarar na kashe Nurat su kuma yan uwan boukar kashe sa dan hakanne ma suka fada sun tada wutar yanda zaa hargitse ana ihu da hayaniyar kashe wuta su kuma sukuma su aikata aikinsu tareda sace dukiyarsa dan haka basu taho da shirin barin ko ‘yarsa ta rayu ba bare bawansa. Fada aka fara tareda sare sare Ana fidda jini me yawa sbd bayin dake tsaron gidan da sukaga alamar fitina a tattare da kashe wutar dan haka suka fara hanawa sedai ko gama rufe baki na farkon beyiba suka rufu a Kansa suka sassarashi suna cewa shi bawa ne bai isa ya basa umarni ba sedai su su basa. Jin hayaniya da Ihun kashe karshen daya dauki gari ya saka boukar daya dauko makaminsa dakatawa ya juya ahankali ya kalli kofar dakin ayshahh sai kawai yaji tinaninsa ya sauya ko yayane yanason ‘yarsa ta rayu dan haka ya nufi kofar dakin da Nurat yake kwana yana zuwa Kai tsaye shiga dakin yayi ya tadashi da karfi tareda dagosa daga kwancen batareda yace komaiba ya riqo hannunsa da karfi suka fito tsakar gida yana sake shiga tashin hankalin hayaniyar da Ihun daya qarasa gauraye gari. Abaas na fitowa yanda wutar take ci da Ihun da akeyi ya sakasa jin Kansa na Juyawa zuciyarsa na bugawa da karfin gaske komai na yanda ya faru garinsu yana dawo masa sabo. Wani irin Zafi da tiriri yaji yana tasowa daga zuciyarsa yana gauraya jininsa komai na sake dawo masa tin daga gawar magaifiyarsu da suka fara rasawa. Rawa jikinsa keyi kowane irin radadin daya dandana a baya yana dawowa yana zama kuzari da fushinsa dan haka dagowa yayi idanuwansa jajir da wasu irin hawaye a cikinsu sbd bazai taba yadda ya sake shiga hannun kusrawaba koda zai rasa ransa gurin cetan Kansa da ayshahh da boukar sbd har abada bayason su dandana baqin cikin daya dandana shi da yan uwansa musamman ayshaahh datake mace, A baya rauni da rashin karfi ya sakasa zamowa nace yana kallo baida abin yi Bayan kuka aka tarwatsa rayuwar yan uwansa aka kashe masa Nurat dan haka wannan Karan a yanzu daya zama namiji ya zabi mutuwa Akan tafiya wannnan mummunan rayuwar. Takobi da adda boukar ya basa yana kallan Zafin dayake bayyana a cikin idanuwansa yace ‘Ka tabbatarda Ka bawa Kanka da Ayshaah kariya’ Wucewa gaba boukar yayi da dan gudunsa na fuskantar komai ai kuwa yana fita take fadan ya dawo Kansa amma dayake yanada nasa karfin sosai haka ya ringa fadan dasu. Shima Abaas baisan lokacinda ya fado cikin fadan ba idanuwansa a rufe komai na abinda ya faru dasu kawai yake gani dan haka kusrawa kawai yake gani a idanuwansa ya ringa fadan bayaji baya gani. Fin karfinsu fadan ya fara yi sbd kusan duk bayin biyar an kashesu hakama suma anfara musu rauni dan haka boukar da jini sosai yake fita jikinsa kallan Abaas yayi cikin tsananin galabaitar daya fara yace ‘Ka tafi Ka dauki ayshahh da jaka na nan gefen gadonta na ajiye ku bar nan kuje garin neruji ku tsallaka ruwa zuwa kiyoje ku jirani anan,Ka tafi da sauri…. Kasan Juyawa Abaas din yayi yana kallan boukar din tamkar yanda Abaa dinsu yayi musu hakan ce yake sake faruwa Ayau din dan haka zaiyi musu boukar damqi hannunsa da karfi yace ‘Idan ban taho ba zuwa gobe to bana duniya Ka dauki Ayshaah Ka tafi da ita inda zata samu rayuwa me kyau ita amana ce gareka duniya da lahira, Hakama idan ranar goben ta fadi ban bayyana gareku ba na ‘yantaka Nurat, Ka zama gatan ‘yata ka zama gatanta da dukiyarta’ Cikin tsananin baqin ciki da radadin zuciya a Karan farko Abaas ya bude bakinsa Bayan shekaru ya furta ‘ABAAS GHAZ’ Kallansa boukar yayi da Wani irin yanayin karyewan zuciya batareda yaddarsa akansa ta girgiza ba ya bude baki idanuwansa na yin jajir yace ‘Abaas ghaz ina fatar Ka zamo gatan ‘yata da bata kariya da rayuwarka har karshen rayuwarta ko taka’ Tura Abaas din yayi da karfi zuwa cikin gida shikuma yana sake bude kofar fita daga bangarensu zuwa bangaren da hatsin zuwa da kuma zuwa kofar ficewa da tini suka shigo. Da sauri Abaas ya juya yana jin zuciyarsa na yanka da Wani irin yanayin da yake sakasa jin kaman bazai iya tafiya yabar boukar ba amma kuma matiqar zasu bawa ayshahh kariya su tseratar da rayuwarta dole ya tafi. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 11:19 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 67 Kai tsaye dakinta ya isa da gudun gaske ya banka kofar bai tsaya komaiba ya dauki jakar da boukar yace ya miqa hannu ya damqi hannunta datake tsaye ta miqe cikin tsananin tsoro da fargaba. Janta yayi da karfi suka fito tsakar gidan Wanda yake hayaqi da ci da wuta take ta riqe hannunsa da karfi cikin tsananin tsoro da tashin hankali tace ‘Meya ke faruwa, Ina Abbu?? Baice mata komaiba ya jata da saurin suka bi ta kofar baya da babu Wanda ya sani sai iya su zasu fice ta qwace hannunta zata koma da gudu tana kwala kiran sunan mahaifinta. Riqota Abaas din yayi da karfin gaske yana kokarin sake tafiya da ita ta fara fizgewa tana Ihun daya sakasa rufe mata baki da karfi yana kallanta cikin duhun hanyar ya sanar da ita abinda yake faruwa da kuma abinda mahaifinta ya ce akan zuwansu su jirasa. Kasa iya barin mahaifinta tayi ta fara Wani irin kuka da rawar jiki tana kokarin kwacewa sbd tasan mahaifinta bazai tsiraba kashesa zasuyi batada kowa bazata iya rayuwa ba mahaifinta ba,bazata iya shiga duniyar da tasan bazata taba sake dawowa ba anan ko kabarin mahaifinta ta ziyarta ba dan haka gwara ta mutu a guri daya da mahaifinta. Rufe mata baki gabaki daya Abaas yayi zuciyarsa na jin abinda take ji sbd shima ya shiga irin wannan mummunan yanayin harma nasa ya zarce nata nesa ba kusa ba dan haka daukanta yayi cak yabar gurin da ita yana sake rufe mata baki da duka karfinsa. Gudu yakeyi da ita a cikin tsananin duhu da shukokin da sun kusa finsu tsayi dan haka cikinsu kawai yake jefa Kafafunsa da ko takarmi babu yanaji qayoyi manya da qananu suna sukarsa da abubuwa masu laifin da harma sun fasa kafafunsa jini suke fiddawa amma bai tsayaba gudun yakeyi sosai sbd yana jiyo hayaniyar biyosu da akai Wanda hakan ya tabbatar musu su duka biyun da boukar ya fadi. Kuka Ayshaah takeyi sosai dukkinanin jikinta na sakewa a jikinsa tanajin duniyarta ta gama kifewa da lalacewa kenan har abada dan haka bazata taba dawowa daidaiba. Shi Kansa jin yakeyi jikinsa na Neman mutuwa da wannan mummunan baqin cikin na rasa Wanda yakeda mahimmanci a rayuwarsa datake a rube Bayan rasa iyaye da yan uwansa amma ganin a yanzu shine gatan ayshahh da kuma zai samu yancin zuwa Neman yan uwansa da sune kadai rayuwarsa ya saka yake sake tattaro karfinsa yana cigaba da Wani irin gudun da kafafunsa ke fidda jini sosai amma bai tsayaba dan basu tsira ba. Gudu sukeyi har kusan asuba hakama karfinsa ya kare daqyar yake iya daga kafa sbd galabaita da jininsa daya fara qasa da kuma wata irin azababbiyar ciwon kirji amma hakanan yake dagewa yana daga kafa. Koda suka isa wani garin dayake daga shi sai inda boukar din tace suje anan suka samu suka tsare wa wainda suka biyosu amma duk da hakan bai tsayaba dauketa kawai yayi ya Kama hannunta tamkar wadda bata gani haka ya ringa Janta ba karfi a jikinta ko kadan. Tafiya me tsayi suka kuma yi kafin suka isa garin dayake bakin ruwan da zasu tsallaka Anan dinma basu tsaya ba cikin wata gona suka boye yayi sallah a galabaice kafin suka fada jirgi suka bar nahiyar kwata kwata. Tafiyar wuni guda sukai kafin suka isa inda zasu din suka fito jirgin tareda barin bodar bakin ruwan wadda sai anan ne Abaas ya gane garin da aka siyosa ne dan haka ya sake riqe hannunta gam suna kutsa mutane suna shiga cikin garin sosai Wanda yake a cike tamkar kasuwa koina hidima akeyi. Wani qaramin gidan baqi da yan gudun hijira ya isa dasu suka zauna Bayan ya tsaya a hanya ya siya mata gasashiyar fulawa da zuma. Suna Zaunawa ta cusa kanta cikin kafafunta tareda qanqame jikinta tana fasa wani irin kuka mai tsima zuciya koina na jikinta na jijjiga da tsananin quncin da batasan haka radadi da zafinsa yake ba. Shiru Abaas yayi a gefenta idanuwansa jajir yana Kurawa ruwan dake mamaye da bakin bodar ido zuciyarsa na yanka shima sbd anan ne aka rabasa da tasa rayuwar, Anan ne ya rabu da wainda suke rayuwarsa, Anan ne komai na rayuwarsa ya qarasa Juyawa harzuwa matakin dayake yau akai na rayuwa da bulayi cikin duniya shi kadai babu kowa acikinta. Radadin azaba me tsanani kafafunsa keyi Wanda ya ke sakar masa da zazzabi me Zafi amma bai damuba shiru yayi ido jajir Akan ruwan. Kuka tayi Wanda saida ya qarasa cinye karfinta kafin tayi shiru tana Kurawa hanyar ido itama batareda ta iya cin abinda ya bata dinba. A gurin suka kwana Zaune cikin mummunan halin daya tsananta yanayinsa dama nata datake wata rawar sanyi dan haka ya cire rigar jikinsa ya rufa mata Akan nata Kayan da babu ko kallabi a kanta gashinta a bude yake a sake sbd yanayin da suka fito. Koda gari ya waye daqyar sukai sallah a gurin suka tashi Zaune suna sake gadin hanyar da duk masu isowa, Duk yanda yayi da ita taci Wani abin qi tayi gashi tayi Laushi sosai ta fita hayyacinta kawai mahaifinta take son ganin ya taho din. Haka suka wuni har rana ta Kuma faduwa babu boukar ba labarinsa, Zuwa lokacin dagashi har ita daqyar suke Numfashi dan haka Akan dole sukaci abinci sbd suna Neman karfin cigaba da jiransa har ranar daya taho. Wani wunin suka kuma yi ba labarinsa haka suka kuma kwana, Ahankali ahankali kwanakin suka ringa tafiya ba boukar ba labarinsa su kuma sun kasa cire tsammani dan haka basu iya tafiya koina ba haka su kaita zaman jira a bakin bodar wadda tin baa Ankara dasu ba har aka fara ankarewa dasu Ana musu kallan mata da miji marasa hankali sbd yunwa da wahalar data Kama jikinsu take fara bayyana dan kuwa basa Wani iya cin abinci suna cikin tsananin damuwa da baqin ciki tareda rashin sanin inda zasu. Ganin an fara saka musu ido ya saka suna cika sati shida a gurin Abaas ya tattarata suka bar qasar sbd Wani jirgin na tahowa Wanda zaiyi gaba binsa sukai sbd a yanzu tafiya Neman yan uwansa zai tafi dan haka a qasar datake gaban wannan zai fara tinda daga nan gaba akai dasu Ayanaah. Tafiya sukai ta kwanaki a jirgin kafin suka isa qasar dake gaban wadda suka Baro, Isarsu qasar dole anan bakin boda ya samu aikin wahala Wanda zaa ringa biyansa dan yana buqatar kudin dazai nema yan uwansa bazai taba dukiyar Ayshaah ba a gurin nemansu, Gida suka samu Wanda ake biyan hayar daki daya ya biya hayar ya saka ayshan a ciki shi kuma yana kwana a kofar dakin. Rayuwa a qasar qunci tafara yi musu sbd yanda ake qyamarsa ganinsa namiji da Kayan maza amma yan kunnen mata ne a kunnensa wainda ya kasa cirewa sbd Ayanah ce ta saka masa su da hannunta bazai iya cirewaba. Ita kanta ayshahh tsangwamarta mutane suka fara yi sbd tana tareda shi babu aure a tsakaninsu dan haka rayuwa tayi mata qunci da nauyi bata cikin kowace irin walwala bare farin ciki dan haka suka bar garin suka koma can quryar qasar Wani garin suka fara rayuwa shima ahankali ahankali zaman yakasa dadi sbd qabilanci na qasar sam basason baqi dan haka dole suka tattara suka sake sauya guri Wanda duk inda sukaje kaman mahaukaci haka Abaas ke Neman yan uwansa. Shekara kusan guda da rabi sukai a qasar suka barta gabaki daya zuwa qasa ta gaba Wanda itama aikin wahalar gaske yakeyi wanda yake cin lafiyarsa sosai sbd duk wannan lokacin aikin wahalar gaske yake a rayuwarsa dan rufa musu asiri kuma har lokacin dukiyarta na nan wadda tace ta basa halak malak amma ya kasa tabawa sbd yanason ya Nemi inda zai ajiyeta dan bata rayuwar kwanciyan hankali da nutsuwa amma abin ya gagara. Ahankali suka fara Gagarin rayuwa a qasashe gurin Neman su Ayanah Wanda zuwa yanzu rayuwarsa ta qarasa macewa gabaki daya sbd ciwon wahala da azabar rayuwa da qunci da suka taru suka rufar masa dan haka ya samu qasa me dan nutsuwa yace zai siya mata gida y ajiyeta tayi rayuwarta ta huta da binsa gararin duniya kada ta qare rayuwarta kamar tasa ta mutu a banza. Kasa yadda da hakan Ayshaah tayi sbd bazata taba iya rayuwa ita kadai babu sa ba sbd a yanzu shine t Rabin jikinta rayuwarta, Shine kadai hasken dayake rayuwarta shi kadaine Wanda rayuwarta take dashi dan haka ta shirya mutuwa a gurin Gagarin duniya tareda shi, Ta shirya rayuwa da mutuwa tareda shi ko an inane ko awa ce qasane zata iya zama dashi. Da wannan suka fada qasar BOYEM Wanda Sam babu ta yanda zaa barsu su shigeta kusan watan su uku anan babu damar shiga qasar dan haka suka juya suka bar qasar. A border ta farko da baa shiga qasar BOYEM aka daura musu aure sbd hanasu gurin zama da akai koina garin sbd basada aure dan haka suka daura aure Wanda har cikin zuciya da ransu suna tsananin son junansu hakama sun shirya rayuwa da mutuwa a tare, Aurensu ne ya kawo wata yar nutsuwar rayuwa a rayuwarsu data cikin tsananin duhu da qunci tareda kadaici, Kusanci da sabuwar shaquwa da kauna tareda so me tsananin gaske sukewa juna suna sake Jin karfin gwiwan fuskantar rayuwa. Bayan wata uku suka bar BOYEM sakamakon cikin daya bayyana a jikin Ayshaah, Cikin ya taho mata da rashin lafiya sosai dan haka tafara wata irin rama taba kofewa alaman jininta yana yin qasa dan haka Abaas ya sadaukar da rayuwarsa da kudirin sa dan bata nutsuwan rayuwan daya kamata kodan abinda zasu haifa kafa suyita yawon duniya dashi dan haka suka juya inda suka fito, Shima kirgen garuruwan da suka Baro a baya tsawon shekaru lokacin da aka dauko su daga garinsu ya fara yi dan komawa qasar sa garinsa gidansu da iyalinsa sbd matiqar Ayanah tana raye to tabbas yasan zata je nemansa a cikin duniya kokuma anan gidan mafarinsu dan haka zai jirata daga yanzu har ranar da Allah zai dauki rayuwarsa. *****tafiyar watanni sukai nai cikeda wahala da ukuba da tsinkewan zuciya ga yanayin ayshahh kafin Allah ya iso dasu dajin garinsu daya sha matiqar wuyar gaske kafin ya gane hakama dukiyarsu tayi qasa dan haka Koda suka iso ANJOM GHAZ cikin Ayshaah ya tsufa yakai wata takwas. A garin ANJOM babu mutane sosai sbd garin ya Riga ya mutu dan haka babu wata daula da tatttalin arziki kaman baya amma akwai kwanciyan hankali dan haka babu wahala ko tashin hankali aka karbesu tinda ansan waye shi hakama duk da shekaru sunja kamanninsa basu sauyaba. Babu kowa a fadar mahaifinsa dan haka Sauran dukiyar daya taho da ita ya bayar aka dan yi gyaran dazai yiyu suka shiga batareda tsoro ba suka zauna tareda kokarin daga ANJOM. Kokarin dayazo dashi da qwazo ya saka jamaar garin samun kuzari da qwazonsu suma ya dawo take garin ya fara komawa ANJOM dinsa na baya a bisa mulkin ABAAS GHAZ din. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali [09/12, 11:19 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 68 ANJOM GHAZ ta dawo ANJOM dinta duk bazata taba komawa ANJOM din baya ba amma Abaas yayi iya kokarinsa ya sake kafata da dukiyarsa da karfinsa da lafiyarsa datake qasa sosai amma ya tsayu ya kasa barin ciwon kirji da zuciyar dake damunsa yakai sa qasa, Ayshaah ma ta samu rayuwar kwanciyan hankali da nutsuwar da Abaas ke fatan ya bata sedai yanayinta itama sai ahankali lafiyarta tayi qasa sosai musamman da cikinta harya wuce watannin haihuwa bata haihuba dan haka aka ringa kawo mata addua da maganin al’adarsu tana sha, Kauna da soyayya me girma tareda wata irin tsafta da nutsuwa take tsakanin Ayshahh da Abaas Wanda kusan duk ANJOM ansan irin son dayake mata da irin yanda ita kuma ya kere mata komai da duniyarta harma da rayuwarta dan haka yanayin jikinta ya saka duk Wanda yake garin mutuwar jikin halinda Abaas yake ciki Akan rashin lafiyarta. Cikinta na cika wata goma sha daya cif ta Wanda yayi daidai da wata su uku cikin na hudu da dawowa ANJOM da samun rayuwa me nutsuwa Bayan shekarun gararin duniya da gwagwarmaya a qasashe cikin rashin gata hakama shekaru biyar cif da rasuwarta mahaifinta ta haifi ‘yarta,yar Abaas,jinin ghaz,hasken idaniyar mahaifinta a duniya wadda tana haihuwarta a idanuwanta kadai ta kalleta ko a hannunta Allah bai bata ikon daukanta ba tabar duniyar ta tafiyarta tabi mahaifinta Wanda bata taba Dena kewa da radadin rashinsa ba a rayuwarta tabar masoyinta da ‘yarta a duniyar da basuda kowa sai junansu a yanzu. ABAAS GHAZ wannan shine farkon bude dukkanin kofofin karfin ciwon dayake cin tasa zuciyar wadda ta kasa dauka da jure rashin matarsa wadda itace take riqe da zuciyarsa dake a zube tin acan baya ta rashin yan uwansa a rayuwarsa dan haka mutuwar Ayshaah ta karya duk wani karfin hali da jarumtar dayake da ita ya fadi ciwon da bai taba samun waraka daga garesa ba, A haka ya rungumi ‘yarsa da sabuwar kaddararsa a cikin qunci da ciwo, Ya zama uwa kuma uba ga yarsa Ya zamo aboki da dangin uwa da dangin uba ga yarsa wadda ta taso itama a rayuwarta batasan kowaba Bayan mahaifin nata sai tarin sunayen da kunnuwanta da zuciyarta sun riqesu, Duhu ne a rayuwarsu da babu ranar shigowan haske a cikinsa, Qunci ne a rayuwarsu da babu ranar saukar sa sbd duk wani daci da qunci da baqin ciki tareda duhun rayuwar mahaifinta ta dabaibaye tata rayuwar ta shigo ciki tayi zaman da bata taba sanin menene farin ciki ba bare dandanon yanda yake, Bata taba sanin haske a rayuwa ba bare sanin yaya yake a ruhi, Bata taba sanin walwala ba bare sanin ya murmushi yake ba a zuci da Fuska dan haka a haka ta taso tin mahaifinta nada karfi da kuzarin kulawa da ita har karfinsa ya qare shima ciwo ya kaisa qasa yana jiyo qamshin mutuwarsa datake gap da iskoshi dan haka tinda ya kwanta ciwo ya sadaukar da Sauran numfashinsa gurin rokon Allah a kowace daqiqa Akan Allah ya kawo masa Ayanah kafin ransa yabar jikinsa sbd yarsa Ayanaah, Ya roki Allah a kowane Hali Ayanaah take Allah a kawota garesa kafi mutuwarsa sbd goben yarsa ta inganta, Ya roki Allah ya tsaya Akan rayuwa da duk wani lamarin BAHAR, BAHAR itace rayuwa da sanyin idaniyarsa da ayanzu yake rokon Allah ya zama gatanta ya tsaya a lamarinta ya bata kariya da tsari daga kowace irin sharri na rayuwa da zata fuskanta. Tinanin rayuwarsa na sake zuwa gangara babu haske ko daya a rayuwar dazai bar BAHAR dinsa ya saka ya roki Allah dauki ransa tareda ‘yarsa subar duniyar tare sbd zuciyarsa ta kasa riqe tsananin daci da radadin dayake ji na tinanin barinta a duniyar da babu komai a cikinta Bayan zalinci da son zuciya ita kadai ba uwa ba uba ba dangi ko daya sai tarin duhu da qunci.’’ ****Wani wahalallen Numfashi ya sauke ahankali daqyar numfashin yana sarqe wa ya dago jajayen idanuwansa Akan NUAB ya sauke yanason bude baki yayi magana amma karfinsa yayi qasa sosai baya iya jan Numfashi da kyau hannuwansa na dan rawa yanason dagawa ya sake Kama hannun NUAB din amma karfin ya qare, Da sauri Aleey ya da idanuwansa ke zubda ruwa ya qaraso ya mayar masa da oxygen sbd NUAB ganinsa ya dauke tsaf sbd yanayin mummunan Jan tashin hankali da jijjigar zuciya daya shiga hannuwansa rawa sukeyi yana riqe da hannun Abaas din daya gam, BAHAR da tinda mahaifinta ya fara bada labarin suka iso amma bata shigoba itada sakinah suna tsaye kofar sakinah na Wani irin kuka mara sauti jikinta da kafafunta na rawa, Ita kuwa jikin bangon gurin ta jingina tana rintse idanuwanta dake Wani irin silili da yajin azabar radadin dayake cikin zuciya da jininta da suka zama rayuwarta datake tamkar fanko, Shigowa tayi kafafunta na wata irin rawa hawaye masu tsananin zafi da radadin dayake Neman fasa zuciyarta ta iso gurinsa tana zubewa qasa kan kafafunta ta Kama hannunsa daya da hannuwanta biyu dake wata irin rawa ta Dora kanta Akan tafin hannunsa ta fasa wani irin kukan da bata taba fasawa ba a rayuwarta me tsananin tsima zuciya da tafa tsigar jiki tana kasa cewa komai Bayan sake hannunta da nasa datai kanta na kai batasan me takeji ba a yanzu Bayan gajiya da rayuwa, Bata taba shaawa ko so daya taci gaba da rayuwa ba idan mahaifinta yabar duniya sbd babu abinda zata tsaya ta samu a duniyar, Mahaifinta shine kadai hasken dayake rayuwarta idan ya tafi rayuwar batada Sauran amfani sbd duhun dake cikinta kasheta zaiyi dan haka bata taba sauya adduarta daga Allah ya dauki ran mahaifinta tareda ita ba. Ahankali ya bude idanuwansa dake rufewa ya Ambaci sunanta daga Wani irin sautin daya saka kukanta tsananta tana dukan kirjinta dake tsananin ciwon da tinda ta tashi itama dashi ta tashi sbd baqin ciki da qunci kawai. Aleey ne daya fita ya dawo ciki da sauri tareda isa gefen NUAB cikin nutsuwa da qasa qasa ya sanar dashi komai na tafiya da Abaas din ya zama ready. Gyada kai NUAB din yayi a hankali yana kallan Abaas da idanuwansa dake cikeda tsananin kaunarsa yana sake riqe hannunsa daya a cikin nasa yace a kira doctors. Babu bata lokaci doctors suka taho tare akai masa wata allura a cikin drip tareda Sauran abubuwan da suka kamata aka bada umarnin kowa a fice. BAHAR da NUAB ne kadai basu fice ba hakama babu Wanda ya iya sakin hannunsa a cikinsu saima Wani irin kukanta sanyayyan sauti dake tashi tana sake cusa fuskarta cikin tafin hannunsa daya sake baya motsi ko kadan. Fitowa akai dashi aka saka ambulance suka fada motoci suma kai tsaye aka wuce airport dashi inda komai yake a shirye. Private jet suka shiga Bayan dan dogon shirye shiryen dabai dauki lokaci ba Wanda akaiwa kowa tinda suka iso da Abaas din dan haka kai tsaye jirginsu ya daga gabaki dayansu. #MAMUH 09033181070 [09/12, 11:22 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_* Mamuhgee 69 Bayan doguwar tafiya Greece suka isa inda suna sauka jirgin sultan me BOYEM na isa qasar tareda Ayanah wadda jikin yake buqatar ganin likitocin nan da NUAB din ya tanadar mata tini amma basu taho ba dan haka doctors din su buqaci a kawota sbd ta farfado a kusa dasu dan su tabbatar sun bata treatment din dazai hanata rasa hankalinta. Hakan ya saka NUAB shima kai tsaye tahowa da Abaas din nan dan ganin likitocin, Manyan motocin ghaz dake qasar ne suka taho har airport suka daukesu shikuma Abaas ambulance ta asibitin ce ta taho dan haka kai tsaye asibiti suka dunguma gabaki dayansu. Koda aka isa asibiti da Abaas ya farfado sedai zuwa lokacin gabaki dayansu jikinsu yafara mutuwa me tsananin gaske ta yanayinsa dan haka Koda suka iso abinda NUAB ya saka akai musu shine hade Abaas din da Ayanaah a daki daya. Koda suka iso asibitin babu kowa sbd baa barin relatives shiga kai tsaye dan haka sultan Bayan an kammala komai na admitting Ayanah dashi da tenya tareda securities dinsa da fadawansa barin asibitin sukai zuwa masaukinsu sai kuma idan an nemesu dan haka Sam basuma San isowan su NUAB ba. Duk wani taimakon gaggawa da doctors zasuyi wa Abaas dayake fidda jini a bakinsa a duk ya yunqura da tarin da bayama fitowa sbd rashin karfi ko kadan daya rage a jikinsa sunyi sunga ma sunbarwa Allah dan haka NUAB shigowa yayi dakin a sanyaye kafafunsa da Wani irin mugun nauyi ya tako ya iso inda yake. Tsayawa yayi ahankali bakin gadonsa tareda miqa hannunsa a tsananin sanyaye ya Dora Akan na Abaas din Wanda ya fara bude nasa idanuwan da ganinsu ya fara ragewa ya saukesu Akan NUAB din. Wani irin Numfashi me tattare da sanyin jiki NUAB ya sake tareda daga hannun Abaas din ahankali ya Dora Akan na Amminsa dake kwance har lokacin bata farfado ba ya hada hannuwansu guri daya ya matse musu su da nasa hannuwan biyu yana sunkuyar da Kansa qasa wasu hawaye masu tsananin Zafin gaske suna ciko idanuwansa ya kasa cewa komai…. Kokarin tsayawa Numfashi da bugawan zuciyar Abaas sukeyi sbd abinda ya dirar masa zuciya ya Lumshe idanuwansa ya bude ahankali da qurawa fuskar NUAB dake sunkuye ido batareda ya juyoba yaga fuskar hannun dayake hade da nasaba sbd bazai iyaba. Aleey ne dayake Bayan NUAB din ya tako a sanyaye shima nasa idanuwan na cike da hawaye masu zafi ya Kama kan Abaas din cikin kulawa da ya juyo dashi setin fuskan Ayanaah dake gefensa Akan nata gadon daban idanuwanta a rufe fuskarta fayau asalin kamanninta babu abinda ya sauya sai manyanta datai…. Wasu hawaye ne masu tsananin dumi suka gangaro daga cikin idanuwan Abaas daya kasa kyaftawa daga kafe idanuwansa dayayi Akan fuskar Ayanah hawayensa na tsanananta gangarowa da Wani irin dumi, Bude bakinsa yakeson yi ya Ambaci sunanta amma Allah bai basa damar hakan ba dan haka hannunsa ya dan iya motsawa ahankali ya Kama hannunta cikin nasa tareda sauke ajiyan zuciya me sanyi ya rufe idanuwansa ahankali wasu hawayen suka gangarowa ahankali idanuwan na rufe. Shiru gurin ya sake dauka me tsananin gaske Wanda ya saka NUAB sauke ajiyan zuciyar daya sauka tareda wasu irin hawaye masu Zafin gaske daga idanuwansa da suka kasa riqe dukkanin jarumtarsa. Aleey ma Juyawa yayi ahankali yana saka hannunsa daya ya rufe idanuwansa dake fidda hawaye sosai har hannuwansa rawa sukeyi kaman yanda na NUAB ke wata irin rawa sbd tabbatarda Ran ABAAS GHAZ ayau yabar jikinsa ya amsa kiran ubangiji. Sakinah dake bakin kofa rawa jikinta itama ya dauka me tsananin gaske ta saka hannu da karfi ta rufe bakinta tana fasa wani irin kuka Mara sauti zuciyarta na tsananin ciwon me Zafi. BAHAR da bata fahimci meya ke faruwa ba tana tsaye daga waje idanuwanta jajir ganin irin yanda sakinah ke Wani irin kuka jikinta na jijjiga ya sakata fara takowa ahankali ta sako kai cikin dakin kafafunta na rawa. Gap da isowa ga mahaifinta data kafe da ido takeyi Aleey ya sake fasa wani irin kuka me sautin daya sakata fahimtar Abaa dinta ya bar duniya yabarta. Duhu ne ya rufe zuciya da idanuwanta ahankali Wanda ya sakata kafafunta gazawa ta yanke jiki a gurin ta zube jikin NUAB Wanda ya tarota da hannu daya har lokacin Sauran hannunsa daya yana riqe da hannun Abaas da Ayanah. Doctor shigowa sukai suka fara kashe naurorin dake manne da Abaas din bayan sun rubuta time of death nasa. Daganan ficewa sukai sukabar fmly da jimamin rashin. Kuka sosai sakinah takeyi kaman rayuwanta tazo karshe sbd wannan itace kaddarar karshe data qarasa yanke farin cikin dasuke sakaran yi a gaba, Ayau Abaas ya tafi yabar duniya kaman yanda Nurat da Ayshaah suka tafi sun barsu da tabo da gurbin da bazai taba cikewaba har abada. NUAB daukan Bahar yayi yakaita Dayan dakin da doctors zasu dubata kafin aleey ma da yasha kuka sosai ya fara shirin komawansu da gawar da bazaa rufeta a nan ba dole zasu koma dashi ghaz acan zaa rufesa. Zaman qunci da damuwa tareda zullumi me tsanani sukai kafin cikin saa suka samu jirgin dawowa da gawar wadda Washe gari tinda safe suka Juya kuma har lokacin Bahar bata farfado ba haka suka dawo da ita. Haka suka kuma doguwar tafiya kafin suka sauka kai tsaye suka sake daukan manyan motocin da suka kaisu har cikin ANJOM ghaz da gawar Abaas GHAZ Wanda a lokacinda Bahar ta farfado rungume gawar tayi ta kasa cewa komai hatta kukan ya kasa zuwar mata idanuwanta ne kadai sukai Wani irin ja. A haka babu bata lokaci akai janaizarsa aka rufesa a cikin masarautar gefen kabarin mahaifinsa da mahaifiyarsa da Ayshaah da akai a cikin masarautar duka dan haka Ana gama janaizarsa suka tattaro suka juyowa tareda Bahar wadda gabaki daya baa San ma Wani halin rayuwarta take ciki ba sbd ko kyaftawa kaman batayi komai nata ya tsaya cak tana rungume a jikin sakinah wadda take jinta har cikin jinin jikinta. Suna isa qasar inda zasubi jirgi anan NUAB ya bada umarnin Maa sakinah da Bahar a wuce BOYEM dasu shikuma zai koma ga Amminsa. Zasu wuce Bayan kowa ya fice kallan Maa sakinah NUAB yayi da manyan idanuwansa da sukai tsananin Laushi ya tattaro dukkanin nutsuwansa ya bude baki yace ‘Maa ina Neman wata alfarma da nakeson kimun alkawarinta a yanzu, Inason kimun alkawarin idan Ammi ta farfado bazaki taba fadawa mata Abaas yabar duniyaba sbd bazata iya dauka ba a yanzu da muke kokarin Neman lafiyanta, Kimun Alkwarin bazata taba sani ba Bazata zan komai ba har sai ranar dana fada mata hakan da kaina, Zuwanmu ghaz da duka abinda ya faru Inason ya zama sirrin da bazai taba fita ba sbd lafiyarta da bazata iya dauka ba, Ki riqe ‘yarsa Amanace ya bar miki amma kada Amminah tasan wace ce ita sbd sanin ita waye din zai saka dole tasan anga Abaas ankuma rasashi dan haka ita din batada kowa sai ke sbd auren da aka daura ba aure ne dazaa tinaba bare qararwa, Maa Inason kiyimin wannan alkawarin’ Numfashi mai tsananin dumi sakinah ta sauke tareda dagowa ta kalli NUAB tukuna ta Gyada kanta alaman tayi wannan Alkwarin har karshen rayuwarta matiqar ba shine ya tado zancenba ta rufesa kenan har ranta ya fita. Numfashi me nutsuwa ya sauke kafin yayi sallama da ita aka wuce dasu airport ba bata lokaci jirginsu ya daga zuwa BOYEM. Suna wucewa da awa hudu suka nasu jirgin yayi daga zuwa ga Amminsa wadda bazai taba dawowa da ita ba matiqar lafiyarta bata daidaitaba. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laoualir *_HAYATEEM_* Mamuhgee 70 A jirgi kwance jikin Maa sakinah Bahar ke kwance idanuwanta da sukai ciki ciki jajir da galabaitar rayuwa da zuciya tareda sarewa da fidda rahama ga rayuwa gabaki daya, Rungumeta cikeda wata irin kulawa da kauna me tsananin gaske da Jinta har jininta Maa sakinah tayi sbd BAHAR itace Abaas da suka rasa har abada sai kuma Aljannah idan Allah yayi sunada rabon haduwa, BAHAR itace jini daya tak ta Abaas dinsu a duniya da idan basu jita har cikin jininsu ba me zasuyi? BAHAR itace jinin Abaas da duniya Ayanah batada kamarsa, Ayanah Allah baiyi tanada rabon sake Dora idanuwanta Akan ‘dan uwanta ba rabin jikinta ba sedai tanada rabon rayuwa da ‘yarsa a matsayin matar ‘danta da bazata saniba sbd ita kanta koda NUAB bai sakata alkawarin kada ta fada mata Abaas ya tafi yabar duniya ya barta ba itama kanta bazata taba iya fada mata mutuwar Abaas ba Wanda Ayanah bazata iya dauka ba dan haka wannan Alkawari ne ta daukanwa kanta itama bazata iya fada matan ba sedai shi NUAB din duk ranar dayaga ya kamatan, BAHAR Amanarta ce a yanzu da zata riqe da rai da rayuwarta tareda bata kariya da dukkanin kauna da kulawan tareda tattalin data rasa tin tasowanta, Insha Allah indai kulawa da nuna kauna da soyayya me tsanani sune suke kawo haske a rayuwar datake cikin duhun kadaici to tabbas zata cikewa Bahar duhun rayuwarta da haske koda kuwa zasu qare a cikin wannan sirrin su mutu matiqar hakan na nufin kariya da samun tsaronta. Numfashi ta sauke ahankali me sanyi da mutuwar jiki tana tina rayuwarsu ta baya da yanda suka Baro ANJOM GHAZ da kuruciyarsu dukkaninsu amma ayau gasu sun manyanta wasu sun rasu sun bar duniya wasu kuma basa tareda su ita kuma gatanan ayau da ‘yar Abaas a hannunta batareda dukansu sunsan hakan kaddara ta tanadar musu ba. Wasu hawaye ne suka ciko idanuwanta tana kallan tata rayuwar da babu komai a cikinta face kaunar jinin GHAZ da bauta musu har qarshen tata rayuwar da batasan Yaushe ne ba amma koma Yaushe ne tana fatar Allah ya dauki rayuwarta itama a cikin aminci da kauna. Shafa fuskar BAHAR data rufe jajayen idanuwanta a hankali tayi tanajin kaunar Bahar din na sake ratsata sbd rayuwarsu a wannan matakin da suke kai yanzu iri daya ce, kaddararsu iri daya ce, Basuda uwa basuda uba basuda Wanda kai tsaye zasu kira nasu Bayan Ayanah dake kwance basu San yaya tata kaddarar zata kasance ba sai NUAB Wanda ayau idan ya rasa Amminsa kila shikenan yabar BOYEM da duk Wanda yake cikinta har abada su kuwa kila duniyar zasu bi sbd rashin Ayanah a BOYEM zamansu a BOYEM din ya qare sbd ita sakinah ba baiwa bace a yanzu hakama Bahar din duk da a yanzu basuda zabin daya wuce a shiga da ita masarautar a matsayin baiwa tinda babu Wanda yasan ita wace ce hakama babu damar fadar ita din waye Wanda sakinah batada zabin daya wuce ta tafi da ita a baiwa matiqar tanason kasancewa da ita batareda Ayanah tasan komai Akanta ba bare mutuwar Abaas. Tausayin Bahar din ya sake cike zuciyarta sbd batasan tayaya zata fara fuskantar rayuwar da zasu tarar din a BOYEM ba musamman da suke ba kowa ba basuda kowane karfin kansu, Hannun Bahar din na hagu dayake ajiye Akan kafafunta ta zubawa ido Akan lambar 99 dake zane a hannunta Baro Baro tayi baqi sosai Akan farin hannunta daya keda fari sosai sbd zamanta bata Baro komai na mahaifiyarta ba, Wasu hawaye masu tsananin zafi ne suka gangaro daga idanuwan sakinah dake Haba kukanta zuwa sbd da wuta aka rubuta lambar 99 din wadda take lambar Abaas ta Shedan zama cikakken bawa da kusrawa sukai musu, Lambar mahaifinta Abaas ce a jikinta zeti da inda akai masa tasa shima a gefen hannu daga sama gurin gwiwan hannun, Rufe baki da hannunta daya sakinah tayi tana kukanta bayyana sbd Bahar dake shiru a jikinta, Nata hannun ta kalla inda tata lambar take Baro Baro a jiki 96, Zuhrah ce 97 sai Nurat 98 tukuna Abaas dinne 99 Ayanaah 100 Wanda haka akai musu su a Jere babu Wanda a cikinsu haryanzu wannan lambar bata jikinsa Wanda da ita zasu mutu, NUAAB tin da ya tashi yaga mahaifiyarsa da wannan lambar a jikinta da hannunsa ya zanawa Kansa lambar a jikinsa da wuta sbd itace lambar dazai tabbatarwa Abaas shi din ‘dan Ayanah ne dan haka da lambar mahaifiyarsa ya tashi a jikinsa bata taba dauka Abaas shima yayiwa tasa yar lambar sa ba sbd koda baya raye da lambar sa zasu yadda da Bahar ‘yarsa ce. Kuka sosai Maa sakinah din tafasa tana kasa riqe kanta sbd har abada sunyi rashin da bazasu taba manta radadin sa ba, Sunyi rashin da shine mafi ciwon rashin da sukai a baya Bayan nan. BAHAR dake kwance shiru zuciyarta bata iya komai Bayan bugawa ahankali sbd komai ya tsaya mata cak tana jin sautin kukan Maa sakinah yana shiga kunnuwanta a hankali yana ratsata sbd tasan kukan rashin Abaa dinta ne akeyi. Bude idanuwanta tayi wasu hawaye masu zafi suka gangaro daga cikinsu a sanyaye tana sake Numfashi me sanyi Mara sauti batareda ta motsa daga kwancen datake a jikin matar da bata taba saniba a zahiri Sai a tarihi amma ayanzu da ita kadai zatai rayuwa. Tafiyar kusan wuni guda sukai kafin jirginsu ya sauka a qasar BOYEM suka fito tareda securities din NUAB din duka da aka hado su dasu shikuma daga shi sai aleey suka koma. Motocin alfarmar GHAZ ne suka daukesu daga airport zuwa Masarautar BOYEM me tarin abubuwa da tarihi dama Wani tarihin da zaa kafa. Ko a cikin mota hannun BAHAR din yana cikin na Maa ta riqe cikin nata tana bata dumin dazai Haba gangar jikinta qarasa rasa kanta. Duk duniya da Aljannar duniyar dake tin daga babbar gate din farko ta masarautar bai shiga idanuwan Bahar ba bare zuciyarta sbd komai na rayuwarta a yanzu rufe yake gap babu kowane irin Sauran shaawa ko burgewa a rayuwa da zai shigeta dan haka idanuwanta a kafe suke kawai a waje tana kallan wajen amma kwata kwata tinaninta baya jikinta ko daya tayi nisa a tinanin rayuwar datai a baya da mahaifinta Wanda a yanzu yana kwance cikin qasa, Tafiya sukai suka sake wuce gate na biyu har zuwa gate na uku suka shige akai parking motocin bakin hanyar da zata kaisu bangaren cikin gida kai tsaye aka bude musu motocin dukansu su biyun a lokaci daya. Maa ce ta fara fitowa a natse cikin sanyin jiki ta sauke ajiyan zuciya da Numfashi kafin ta zagayo ta miqa hannu cikin motar ta Kama hannun BAHAR wadda bata motsaba tinda aka bude mata motar ta janyota a hankali cikin kulawa ta fito motar, batareda ta saki hannunta ba ta jata a natse zuwa ciki suna tafiya babu me karfin jiki. Duk Taku daya da Bahar ke yi Wani siririn sautin sarkar kafarta ta mahaifiyarta data gada ne yake tashi tareda Wani irin sakar da nutsuwa da saka son juyowa ga duk Wanda sautin ya shiga kunnensa dan hakane duk tayi Taku daya bayin dake jere a hanyar sai sun sauke kansu qasa cikeda girmamawa ga Maa sakinah wadda kowa yasan matsayinta na shaqiqiyar Wishmah kuma jakadiyar bangaren wishmah ta biyu. Kai tsaye hanyar bangarensu Maa ta nufa da BAHAR wadda har lokacin duk inda Maa ta jata saka kafa kawai takeyi ba Wani kuzari a jikinta. Isowarsu gap da hanyar data raba bangaren Queen HAILE da bangaren Wishmah Ayanah a daidai wannan lokacin Li’uli ASIM ALMAZZ ya fito bangaren mahaifiyarsa cikin shigar sky blue cashmere mai fitinanniyar tsada qamshinsa yana sauya niimar gurin take dukkanin bayin dake hanyar suka sauke kansu qasa suna tsayawa cak inda suke har saiya wuce. Maa sakinah dake gap da shigewa da Bahar bata juyowa tayi a natse dan basa girmamawa itama a natse Banda Bahar da batasan me takeyiba daga kafarta tayi tana cigaba da Takawa ba karfi a gangar jikinta ko kadan. Sautin takunta ne da sarkar kafarta ke fiddawa a natse a gurin daya dauki tsit tamkar babu rai ko daya a gurin sbd bada girmamawa garesa ya sakasa tsayawa da takunsa cak yana dakatawa. Sake ratsa kunnuwansa sautin yayi Wanda ya sakasa juyowa da Wani irin nutsuwa da mamaki yabi inda sautin ke fitowa da kallo a daidai lokacin Maa Sakinta ta riqota cikin nutsuwa da juyo da ita a hankali sbd inda yake dosa ba can zasu nufa ba. Kafafunta dake rufe cikin doguwar rigar dake jikinta ash Kala wadda batada adon komai sedai daidai jikinta take ta sauka qasa sosai harma tana dan ja da kasa kadan mayafin rigar ne kadai yakeda adon dayake qawata rigar da fuskar da zata saka kayan ya tsayar da idanuwansa yana kalla amma babu ta inda kafarta ta fito se sautin. Dagowa yayi a natse ya maida kallansa kan fuskarta zuciyarsa na dauka Wani irin Zafin mamaki da jin abinda bai taba ji ba a bayi sedai yayan sarautar ne kadai sukeda iko da wannan damar dan haka mamakinsa ya dan qaru yana bude idanuwansa da kyau a kanta. Fuskarta dake bayyane ya zubawa idanuwansa yana kasa daukesu daga kanta mamakinsa na sauka ahankali tamkar wutar da aka zubawa ruwa, Bin fuskarta yake sakeyi da kallan dayake sake saka zuciyarsa mamaki da jin Wani irin yanayin daya sakasa kasa dauke kallansa akanta. Shiru gurin ya sake dauka musamman da Bahar din bata sake ko motsawa ba har tsawon mintina kafin ya dauke idanuwansa daga kan kyakkyawar fuskarta ta jinin GHAZ ya juya a natse batareda yace komaiba ya wuce zuciyarsa na riqe kamanninta da kai tsaye suka isa gareta. Yana barin gurin Maa sakinah ta Kama hannunta suka nufi kofar da take aka bude musu ita gabaki sbd girmamawa suka shige aka rufe. Babban palon dayake na farkon isa suka shiga Maa sakinah ta sake ajiyan zuciyar samun isowa gida cikin Amintci. Dakinta kai tsaye ta wuce da Bahar, Komai na dakin a gyare yake sbd babu ranar da baa Shara so biyu a kunna qamshi, Ac ne kadai baa kunne ba sai wuta dan haka kai tsaye remote ta dauka ta kunna komai Wanda take haske ya haske dakin gabaki daya tamkar fitowan rana, Makeken bedroom ne dayake dauke da royalbed me kyau da girma sosai sai Sauran set din royalbed din su wardrobe da dresser tareda bedside da wata lallausan Turkish carpet da table sai couch masu Laushi da tsari, Duk wani jin dadi da tsarin dayake bayyanarda Hutu da kwanciyan hankali shine a dakin komai a tsaf ga sanyin ac din ya fara ratso wa yana kokarin Kama dakin. Zaunar da ita Maa sakinah tayi tareda zare mata rufar kanta a hankali gashinta dayake rufe ya zubo a hankali yana bayyana Maa ta sake sauke ajiyan zuciya tana kallan baiwar data shigo dakin dauke da babban tray da kayan sanyi da fruits masu sanyi ta bude baki tace ‘Ki hada ruwan wanka masu dumi’ Gyada kai baiwar da ake da Salmah tayi tana ajiye tray din ta juya kanta a qasa ta nufi toilet din dayake dakin na Maa ta shige dan hada ruwan wankan. #MAMUH HAYATEEM by Mamuhgee 700 0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi 09033181070 Yan Nijar kuma 89825722 Depot my nita Nissaiba laouali End of part 1