1- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* _"Ƙungiyar Marubuta masu tasawa, Rubutunmu shi ne tafiyar da ke wuce lokaci, mu ne masu ɗaukar harshen gobe a yau. Marubuci ba ya zana kalma kawai, sai dai ya zana mafarki a zuciya, ya maida shi haske ga al'umma. Wannan shi ne alwashinmu a matsayin mu na matasan marubuta. Taken mu shine ɗaga darajar Marubuta masu tasawa."_ 🌻🌻🌻 *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* Hasashen soyayya free book ne,amma ga masu bukatar complete #500 ne, zaku iya magana ta wanan lambar 08129553971. _Page 01_ Labarin rayuwar Bhatool Senate,Soyayya mai ɗauke da salon burgewa, rayuwar aure mai cike da hargitsi da ruɗani. Matashiyar buduruwa ce wacce aƙalla zata kai shekara 22 zaune a backseat na motar ƙirar GLK, tana sanye cikin atamfa Super holland mai adon ja da touch din green, fara ce kyakkyawa tagani tafaɗa, tana da tsayi amma ba doguwa can ba, dara-daran idanunta masu matukar kyau, haka ƙananan pink lips dinta masu ɗaukar hankali, green veil ta yafa sai kuma ƙaramar handbag da takalmi golden cloud, wuyanta yasha manya sarƙoƙin gold haka yatsunta. Yau ne fitar ta farko tun bikinta da aka yi, sati uku da ya wuce, bikin wata coursemate ɗinta akeyi wacce sukayi amarci a lokacin bikinsu, hakan ya sa ta fito. Tunda driver yayi parking motar tasu wacce a wajen rubuta lamba aka rubuta *Senate* gaba ɗaya hankalin yan matan yayo kan motar, driver ne ya fito daga wajen da yake tare da buɗe mota ƙofar inda take zaune, hill sheo ɗinta ne ya fara fitowa kafin kuma ita ta fito, ai tuni wajen ya ruɗe da faɗin. “Fatima senate! Fatima senate!!.” ~ Asalin labari ~ Fatima Ahmad Ishaq shine asalin sunanta, haifaffiyar garin Yobe state cikin unguwar Nyan’ya, Mahaifinta Malam Ahmad dan kasuwane mai rufin asiri yayi aure tare da matarsa Habiba da yara guda uku. Karima itace babba, sai kuma Fatima da ƙaninta Abdulwahab wanda tsiran shekara ɗaya ne tsakaninsu,hakan yasa suka zama abokan tsama na gaske. Cikin yaran Malam Ahmad Allah ya jarabceshi da son Fatima, tun baya iya bayyanawa har ya fara, Habiba tayi duk ƙoƙarinta wajen kar ya bayyana hakan domin zai’iya kawo saɓani cikin yaran nasu. Sunanta Fatima amma ana kiranta da Bhatool, Bhatool ta taso yarinya mai rawar kai, gayu da kuma iyayi, ko magana Bhatool take abun tsayawa a kallane, bare kuma tafiya da yanayin rayuwarta. Wanan rawar kai ta Bhatool taja mata rashin so daga ɓangaren mahaifinta, waƴanda dama basa wani ƙaunar mahaifiyarta tun farko, saɓanin Karima wacce take shiru-shiru bata da wata damuwa, tana da haƙuri. Haka shima Abdulwahab, bashi da wata damuwa, idan kaga damuwarshi ko hayaniyarshi to da Bhatool ne, domin shi a yanayin rayuwarshi ma bashi da hayaniya, shiru yafi yawan maganarshi, Bhatool ce kaɗai kansashi magana harda faɗa da hayaniya. Karima nada shekara sha takwas, Bhatool sha shida, Abdulwahab kuma nada sha biyar. Allah yayiwa mahaifinsu rasuwa sakamakon hawan jini daya dameshi. Lokacin da rashin lafiya taci ƙarfinshi, yahaɗa amininshi Alhaji Aminu da Abdulwahab man yanuna masa harkokin kasuwanci, domin yasan yana mutuwa ƴaƴansa da matarsa sun rasa gata, yasan halin ƴan-uwanshi ciki da bai, haka bayan ya haɗa Abdulwahab da Alhaji Aminu yanemi Alhaji Aminu daya raba dukiyarsa gida uku, ya ajiye gida biyu zuwa sanda ƴan uwansa zasuyi rabon gadonsu na son zuciya, sai yaɗora Abdulwahab akai yasan zaikula da kanshi da ƴan-uwanshi. Haka kuma acikin gida bashida magana sai dai. “Habiba ki kulamun da yarana, ki tsaya kai da ƙafa su samu ilimi da rayuwa mai kyau.” A cikin ƴaƴansa kuma bashi da magana sai. “Ku haɗe kanku, kuzama tsintsiya ɗaya maɗauri ɗaya, kuso junanku, ga kuma amanar ƴar-uwarku nan Bhatool ku kula da ita, takasance mai rauni, Abdul Allah ne gatanku, kaine gatansu, kazama gatanta,kar kabari ko sau ɗaya tayi kukan rashin mahaifi.” Sai yajuyo ga Karima itama ya fara. “Karima kizama babba, komai ki ɗauka Bhatool ƙanwarki ce mai kuma rauni, ki zama yayata ƙwarai a gareta, karki bari ko sau daya tayi kukan rashi na.” Da irin waƴanan kalaman yake kwana yake tashi, kowa yasa ba dasu a cikin gidannan, ranar da zaiyi magana ta ƙarshe dasu ya tarasu baki ɗaya, ya fara magana. “Karima, Kamar yadda nasha faɗamiki ke ce babba,Allah ne gatanku kece na ƙannenki, Allah zai buɗamiki, domin ki kula da ƙannenki, ga Bhatool nan ako yaushe ina faɗamiki, dan Allah dan Annabi karki bari koda sau ɗaya tayi kukan rashin mahaifi.” “Fatima! Karima yayarki ce, Abdulwahab ƙaninki ne, inaso ki haɗa kiyimusu biyayya kai ɗaya shida yayarki, ki maidashi yayanki, Bhatool koda sau ɗaya karki bijire musu, nasan bazasu taɓa barinki kiyi kukan rashi na ba.” “Abdulwahab! Kaine ƙarami amma Allah ya baka girman, kazama uba a garesu, kazama bango a garesu, kubi umarnin mahaifiyarku sau da ƙafa, Abdul ko sau ɗaya karka bar ko ɗaya tayi kukan rashi na.” “Karima banida abinda zance miki, kiyi tarbiya a wajen yaranmu, amma ako yaushe ina faɗamiki amanar Bhatool.” Shuru sukayi baki ɗaya, sun saba jin irin wannan maganar awajenshi, amma na yau sai yayi musu daban, harta Bhatool dake jindaɗi idan yayi irin wanan maganar amma yau sai abun yazo mata wani kala. A daren ranar Alhamis wayewar garin juma’a Allah yayi mai rasuwa, wacce ta kiɗima iyalanshi haka kuma ƴan-uwanshi sukazo sukayi ta ihu, bayan kwana uku sukace sunaso araba gado. Malaminsu na bogi suka ɗakko yazo yayi rabon ha’inci da son zuciya, ya kwashe rabi da kwata na dukiyar yabasu, ƙarshe dai gidan da suke ciki suka tsira dashi. Bayan ƴan-watanni da rasuwarshi Alhaji Aminu, ya buɗewa Abdulwahab babban shago a kasuwa, bayan yayi mai tsallake-tsallake a makaranta ya tsira da takardar gama secondary. Abdulwahab ya fara kasuwanci, kuma Allah ya dafa mai aciki, Karima da fatima sun cigaba da makaranta, suna rayuwa cike da nutsuwa abubbuwa daya ba sufi ƙarfinsu ba. Ana wannan matakin ne kuma ƴan-uwan mahaifinsu waƴanda basu sake bibiyarsu ba, tun mutuwar mahaifinsu suka zo da buƙatar sunason aurar da Karima da Bhatool, a lokacin Karima nada shekara sha-tara zuwa Ashirin ita kuma Bhatool tana da sha bakwai. A lokacin akwai wani mutumi da suka haɗu da Karima lokacin tana aji na farko a makarantar kwaleji ta, Shehu Sule collage of Health science shiyasa da sukazo da maganar, Maman tace musu Karima nada wanda takeso amma Bhatool ba yanzu zatayi mata sure ba, domin ko secondary school bata gama ba, sanan shekarunta basu kaina wacce zata yi zaman aure ba, ga kuma halinta na rawar kai ba kowanni namiji bane zai zauna da ita. Wanan kalami na Mama ya tayar da tashin hankali babba ba ƙarami ba, a cikin ahalinsu domin su akwai wanda ma sukesu subawa yaran a cikin ƴaƴansu dasuka lalace, sanan kuma sunsami labarin yanda kasuwancin Abdulwahab ke haɓaka a kasuwa, amma Mama ta d’age ta tsaya sosai domin tasan aure shine cikon rayuwar ƴa mace, to baza taso akai su inda aure zai wahalal dasu ba, bata taɓa magana akan hukuncin da suka yanke akan yarantaba sai yanzu. Badan ransu yaso ba, Bashir ya gabatar da kansa a matsayin wanda yake son Karima, aka saka lokacin aurensu wata shida. Su da suka zaƙe akan sai an aurar da yaran baka ƙarajin bakinsu ba, sun koma gefe sai Mama suka bari da ƴan-uwanta, daman kuma Maman mai tanadace. A haka bikin Karima yazo da mijinta Bashir wanda yake ma’aikacin NNPC, a lokacin wannan bikin ne Bhatool taja magana mai tsayi cikin ƴan-uwanta domin abunda tayi, tayi ɗinkuna irin waƴanda ake gani a jikin ƴan film da kuma mutanen da akewa kallon ƴan-iska su *Zuge darling*, *Show me your back* da sauran ɗinkuna, hakama eyelashes (gashin ido) a wanan lokacin a iya idanun ƴan film ake ganinshi sai kuma waƴanda ba musulmai ba, ga kuma karin gashi na brazil mai-jar kala. Wannan abu ya jawa Bhatool magana sosai da sosai, wasu nacewa tazama ƴar iska, wasu na cewa zata zama,haka akayi biki aka tashi kowa da magana a bakinsa. Haka rayuwarsu Bhatool taita tafiya, tana samun duk wata kulawa a wajen ƴan-uwanta baki ɗaya, barima yanzu da Karima ta yi aure kuma mijinta irin mazajen nan da’ake kira *mijin marainiya ne*, domin duk wata buƙatar data ƴan gidansu ya ɗauke mata, ya tsaya mata akan karatunta harta kammala, yanzu haka yana ciku cikun buɗemata clinic ne. Haka shima Abdulwahab yazama babban ɗan-kasuwa mai nasibi, gashi yaro amma da manyan ƴan-kasuwa yake mu’amala, ya koma karatu part-time a yanzu haka akwai shagona guda biyu bayan na farko da akabuɗe musu. A ɓangaren Bhatool ma, yanzu ta girma kyawunta ya ƙara fitowa, gayu da iyayi sunƙaro amma yanzu sun haɗu da ilimi da wayewa, komai nata classy ne. A yanzu tana first year a jami’ar Yobe State University (YSU), tana karanta Entrepreneurship. A yanzu haka suna first semester ne sababbun ɗalibai, ƙawayenta guda uku ne waƴanda suma gani sukayi halinsu yazo ɗaya kuma tana burgesu yasa suka nemi ƙwance da ita, domin Bhatool akwai farin jini. ~~~~~Unguwar Red Bricks Makeken gida ne iya ganinka, ya gaji da haɗuwa tundaga girman shi, yanayin tsaruwar shi da kuma adon shi. Gida ne irin flat house amma mai girma sosai da sosai, part ɗaya ne mai girma da kuma tsaruwa. A cikin gidan wani ƙaramin part wanda a ƙalla shima yayi girman wani gidan, kyawawan samari ne guda biyu, ɗaya fari ɗayan kuma baƙi. Farin baya kama da mutanen Nigeria gaba ɗaya, yafi kama da mutanen ƙasashen larabawa,amma yanayin sumar shi yana akwance kuma ya zubo har zuwa wajen giransa kamar na ƴan Korea. Lips dinsa pink ne sosai da sosai kamar baitaɓa kai wani abu bakinsa ba, girarsa a cike take da gashi kuma baƙi ne huluk, ɗayan kuma baƙine, kuma mai kyau amma kuma baikai ko rabin kyan farin ba, baƙin ne yake ta magana amma farin ya yi shiru. “Senate magana nake fa.” Shiru yaƙarayi amma idanunsa nakanshi, ko ƙiftawa bayayi. “Idan bazakayi magana ba I will leave..” Girgiza masa kai yayi alamun “A’ah” “To talk.” A hankali yafara magana yana buɗe karamin bakin kamar mai koyan magana. “Bud-die.” Wata iriyar murya mai mugun sanyi da sanyaya zuciya. “Basan ta’ina zanfara ba.” “Fara ta ko’ina, Senate.” “Idan naganta zuciyata canja bugu take, tanayi da ƙarfi kaman zata fito, and I'm scared.” Yaƙara faɗa cikin sassanyar muryarsa, kallon shi ya yi sannan ya ce: “Wace?.” “Idan bangantaba bana jindaɗi, zanjini empty, Idan nayi nesa da ita zanji kamar I'm leaving what I love the most.” “Senate who is she?.” Girgiza kai Senate ɗin ya yi sannan ya ce: “Actually I don't even know her name.” “A ina kake ganinta?.” “School.” “Which school?.” “ ( YSU).” “What take you to Yobe state university, Senate?.” Girgiza kai yafarayi kamar ƙaramin yaron dayayi laifi aka kamashi, sannan ya ce. “ Naje wajen wani secondary school mate ɗinane da mamansu ta mutu, time ɗin ina Cyprus, shine naje yimai gaisuwa ya ce muhaɗu school ɗinsu.” “Kafaɗawa Momy?.” “Nope naso faɗamata amma nakasa Anas, shiyasa nakiraka inajin tsoro.” Murmushi Anas yayi domin yasan tabbas dagaske Senate ɗin najin tsoro, domin haka allah yayi sanyi kamar ƙaramin yaro, magana ahankali sanan babu abinda take tsoro kamar mata, amma fa yanada zafi sosai idan yatashi ɗaukan zafin, he is cool but difficult to handle. “You know you have to tell her ko?, dan bazan yi advising naka ba daga baya kaje kace nina hanaka faɗamata.” “I will okay, but please Anas what do you thinks is this?.” Dariya Anas ɗin yayi sanan ya ce. “Might be you fall in love.” “Love.” Senate ya faɗa aɗan tsorace. “Yes.” Anas ya faɗa tare da ficewa, kwantawa yayi kan gadonsa tare da rufen idonsa, amma itaɗin yagani ɗazu cikin ƙawayenta suna hira tana ta dariya amma cike da yanga da kuma gayu, bude idon yayi sannan kuma ya sake rufeshi. ~~~~~~ Yobe State University (YSU) Bhatool da team ɗin ƙawayenta zaune wajen da suka saba zama suna hira, ɗaya cikin ƙawayen nasu mai suna Jannah ce ta ce: “So yanzu ankon yakama 78thousand kenan, Kuma payment ɗin cikin satinan za’ay.” Daga kai sukayi sannan ɗaya maisuna Amrah ta ce. “Nan da 2weeks bikin, amma gaskiyya Suhaima baki kyauta mana ba, aiko engagement ɗin kyafaɗamana muzama cikin shiri, yanzu ina zamuje mu samu dubu ɗari da motsi.” Dariya wacce aka kira da Suhaima tayi sanan ta ce. “Time ɗin da muka shigo school ɗinan ai anyi engagement ɗin, kuma nasan ku big girls ne sannan kuna da rich-boyfriend's they can afford anything for you.” Sai a lokacin Bhatool ta bud’e baki ta yi magan. “Amma Suhaima kinci kai, kina tunanin samarinmu kemana wannan sutturar, to ni wallahi Yaya Karima da Abdulwahab ne, kuma nakaisu bango banji zasuyimun naki.” “Nima dai nakai Anty bango, banjin zatayi mun.”Amrah ta faɗa tanakai hannunta kan cinyar Bhatool tana taɓota da alamun gulma. “What?.”Bhatool ta faɗa tana dukan hannun Amrah. “Have you girls notice this guy.” Amrah ta faɗa tana nuna musu Senate da baki wanda ke zaune ɗan nesa dasu yana danna wayarsa, amma hankalinsa nakansu kuma zuciyarshi na bugawa da saurin data saba. “Yes.” Jannah ta faɗa sannan taƙara cewa. “Kusan 3weeks kenan.” “Nikam bantaɓa kula dashi ba.” Cewar Bhatool cikin ranta, domin da gaske bata taɓa kula dashi ba. “Gaskiyya yadaɗe yana bibiyarmu, namayi tunanin ɗaya cikinmu yakeso.” Suhaima ta faɗa, tana kallonsu shiru Bhatool tayi na ƴan-mintina saikuma ta ce. “Ku barshi Allah yasa gobe yazo.” Daganam suka tashi sukabar wajen, shi kuma yayi shiru na cankuma ya ce. “ I have to tell my Mother.” Daga haka ya tashi ya nufi motarsa ya wuce gida, su Bhatool kam wata lectures ɗinsuka shiga, sannan su a tsarinsu koda sungama lectures basa tafiya gida sai shida, kullum fitar takwas komawar shida. ~~~~~Red bricks A makeken main falo ɗinta ya sameta, wanda yasha ado da tsadaddun royal chairs, datijuwar mata wacce kuɗi da ilimi suka ɓoye shekarantu, domin a kallon farko zaka iya cewa batafi shekara 30 ba wanda a zahiri takai shekara 45, farace itama mai kamanni da larabawa, tana sanye cikin wani ɗan ubansu lace maroon clour. Shigowa yayi ba tare da yace da ita ko ƙala ba, zama ya yi nan kujera tare da haɗe hannayensa biyu ya zuba tagumi. Matsowa ta yi kusa dashi tare da sa hannu ta cire mai tagumin da ya yi. “My prince, what is going on?.” Kallonta yayi idanunshi cike da ƙwalla, a hankali ya buɗe baki ya ce. “Mom! I'm scared.” “What happen, and what are you scarring for?.” “Mom the girl.” “Which girl?.” “Mom Idan na zauna kusa da ita, zuciyata na bugawa da ƙarfi kamar zata fito, idanta tashi zata fice zanji kamar ina nesa da abinda nakeso, idan banje naganta ba banajin daɗi, I don't know what to do Mom.” “Nutsu kaji! Faamun komai from the beginning.” Legends pen 08129553971 2- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ _Page 02_ “Mom Idan na zauna kusa da ita, zuciyata na bugawa da ƙarfi kamar zata fito, idan ta tashi zata fice zanji kamar ina nesa da abinda nake so, idan banje naganta ba banajin daɗi, I don't know what to do Mom.” “Nutsu kaji! Fa’amun komai from the beginning.” Shiru yasa ke yi sai kuma bakinsa dake karkarwa, jawo shi tayi tare da ɗaura kanshi akan cinyarta ta fara shafa masa gashi. A hankali ya fara sauke ajiyar zuciya, sai da yaɗau kusan minti goma sannan ta fara magana. ~~~~~Usman Yunusa Ahmad Shine asalin sunansa, haifaffen garin Yobe state Damaturu kamar yadda mahaifinsa yake. Saɓanin mahaifiyarsa dake yar asalin garin kano. Alhaji Yunusa babban mai kuɗi ne wanda akaf garin Yobe asandashi da kuɗinsa. Babban ɗan kasuwa ne wanda yake kasuwanci har kasashen ƙetare. A lokacin da yaje Kano gudanar da wani harkar kasuwanci ya haɗu da Zainab wacce yaji ta kwanta masa arai kuma ya yi magana da iyayensa da ƴan-uwansa sukayiwa nata magana akasaka lokacin aurensu. Bayan anyi auren suka fara gudanar da rayuwar aure mai kyau da tsafta, Yunusa na bata lokacinta a matsayinta na iyalinsa, haka itama tanayi masa biyayya iyakacin yinta, sukan ware lokaci sufita ƙasashen ƙetare. A wani lokaci da sukaje ƙasar Dubai suka daɗe wajen wata shida, a lokacin ne Zainab tasamu ciki. Yunusa yayi murna sosai da sosai hakama ƴan-uwansa da kowa da kowa. Sai da cikin yakai wata bakwai sannan sukabar Dubai, suka tafi Korea inda ananne kuma ta haihu, yaron yaɗakko kammanin mahaifinsa amma yana yanayi da larabawa kodan a ƙasarsu akasami cikinsa, haka kuma gashin kasan ya yi kama dana ƴan korea. Bayan yaron yayi wata ɗaya suka huce Saudi Arabia alokacin aikin hajji suka gudanar da Hajjinsu, sannan suka dawo gida. Usman ya taso cikin gata- gata na gaske domin Usman ko zaman sati biyu cikakke bayayi a Nigeria, Nursery School kawai yayi anan amma ko primary school ɗinshi acan south korea yayi, lokacin dasuka tafi tare da Mahaifiyarsa. Wacce bata dawo ba sai da yashiga Junior secondary school. Sai da Usman ya gama Secondary school kuma yatafi Madina ya had’e haddarshi daganan kuma yakoma Cyprus ya cigaba da karatunshi. Usman ya dauko sanyin hali dana mu’amala irin naƴan South Korea, idan yana magana kamar mai koya, tafiyarshi dai yanayinta cike da ƙasaita, bashida fushi ko kaɗan amma idan yayi fushi tashin hankaline domin bai iyaba. Usman yanas on wasa, ya iya wasa da yara sosai sannan kuma yanason yara, ko dan shikaɗai ne wajen iyayensa, sannan yaransa yasa ko da yaushe gidansu yake cike da ƴaƴan-ƴan uwa. Tun a south korea Usman yasamu sunnan “Senate” sunnan da ya karɓa yakuma ɗorawa kansa, duk da wani wanda yasanshi to da wannan sunan ya sanshi. “Senate” Anas cousin Brother ɗin shi ne, ɗan wajen ƙanwar Momy wanda Usman take matuƙar ƙauna, yayarda dashi sama da kowa, Usman baya iya doguwar magana da mutane, Daga Momy saikuma Abba domin idan yana tare da Mahaifinsa yakan zama serious cikakken mutum, kowanan sanyin maganar bayayi,saikuma Anas yana magana da Anas sosai da sosai domin gani yake bashida wani ɗan-uwa kamar Anas. Tsiran shekara biyu ne tsakaninsu, shiyasa Usman yake gani kamar Anas ɗin ƙaninshi ne. Senate yana da abokai guda biyu, Salman da Juraij, sukam sun iya rayuwa dashi a yanda yake, sun haɗu da Juraij a south Korea ne a primary school, shi kuma Salman abokin Juraij ne na gaske, hakan yasa suka zama abokai. Senate bai taba jin rashin daɗin zama dasu ba, domin suna fahimtarshi akan komai, abokaine na ƙwarai, yana Cyprus mamansu Salman ta rasu, hakan yasa ranar da ya dawo yaje gidansu, anan yafaɗa masa yana school. Kai tsaye Senate yatafi School ɗin. Shigar shi makarantar ya kira Salman waya, Salman dake lectures yayi text. “Wait me at the Garden” Okay kawai ya ce, Sanan ya nufi Garden ɗin. Tun shigowarshi makarantar yaji bugun zuciyarshi ya canja, yaƙaro amma ya alaƙanta hakan da yawan mutanen dake ciki, wani saurayi yagani yana tafiya, da sauri yace masa. “Assalamu alaikum, Garden please?.” Hannu gayen ya ɗaga masa tare da nuna masa Garden ɗin, godiya yayi masa sannan ya wuce. Shigarshi Garden ɗin ƙarin bugun zuciyarshi. “ Yasalam.” Yafurta dai-dai lokacin da yashiga Garden ɗin, sakamakon wani irin bugun da zuciyarsa tayi da mugun ƙarfi. Guri yasamu ya zauna bugun zuciyarna daɗa tsananta, runtse idonsa yayi tare da fara sauke ajiyar zuciya, sautin da ya fara jine yafara rage bugun zuciyar, a hankali sassanyar muryarta ta shiga cikin kunnensa, ƙwaƙwalwarsa ta yi masa record and save ɗinta a lokaci ɗaya. “Wani yaron zai cewa bazaiban ba, aikuwa na kwanta a ƙasa na ƙwalla ihu ina faɗin, Abba yau nayi kukan rashinka, kafin naƙarasa yayi sauri yatoshemun baki yana faɗin yi haƙuri Yaya nawa zan baki.” Dariya ƙawayenta suka saki sannan Suhaima ta ce. “ Gaskiyya baki da kirki, duk ƙoƙarin da mutanen nan suke akanki gun mutuwar mahaifinku amma sai kince kinyi kukan rashinshi.” “Aikin ga ko Abdulwahab ko Yaya Karima, ke har Umma ma idan inason anko sai na kwanta a ƙasa nace nayi kukan rashin uba, last time Umma cewa tayi naita kukan rashin uban, amma nace mata nayi mafarki Abba yace bazaiyafe musu ba, ai Wallahi bayan anko Abdulwahab harda kaini Shopping.” Dariyar suka ƙarayi sanan Amrah ta ce. “Nikam wallahi Yaya Sulaiman yafi ɗanyen kashi ɗoyi, ai ban isaba.” “Ke waya faɗamiki Abdulwahab ɗin Yayanane, ƙaninane fa shiyake bini amma shine mai kuɗin.” Dariya suka sake wanda ko da yaushe idan suka zauna a wannan seat ɗin basu da aiki sai hira kala kala, daganan kuma ajuye gulma. Kalmar rashin Mahaifi ta Bhatool tashiga cikin zuciyar Senate tasamu waje ta zauna gamgam, wanna hirar tasu itace ta dinga saukarmai da yawan bugum zuciyar harta yi dai-dai, hankalinshi nakan Bhatool da ƙawayenta, hankalin yan mata Yobe State Universtity nakan Senate. Wayarsa ce tahau ƙara da sauri ya ɗaga yana faɗin: “Man how far.” “Kana ta ina acikin Garden ɗin?.” “Ina daga wani gefe.” “okay naganka.” Yana Zaune Salman yazo yana faɗin. “Man how far.” Murmushi yayi sanan yace: “Nml Man ya ƙarin haƙurin Momi kuma?.” “Haƙuri sai ma’aiki broo.” “Yasu Haliman kuma.” Murmushi Salman yayi tabbas Senate yanada matuƙar damuwa da kula akan ƴan-uwan abokansa. “Suna lafiya, kasan ayu engagement ɗinsu dukansu to yanzu kawai ansakko da bikin nasu nan da 3weeks.” “Masha Allah hakan yayi sosai da sosai, Abban yadawo ne?.” Girgizakai Salman yayi batareda yace wani abu. “Ayyah to yanzu aina ka tsaya.” “Akwai wani gida na Mama shi akayanke za’asiyar harma antayashi 10million, za’ayi hidiman biki ragowar kuma a gyara shi wannan gidan damuke ciki zuwa ko hayane sai asa, nikuma zankoma gidansu juraij.” “Wannam shawarar tayi amma banajin yakanata asiyar da gidan man, sabida gaba zanbada tawa gudumawar insha Allah koda basu isa duka ba za’ayi wani abu.” Senate ya faɗa yana danna wayarshi, Transfer ɗin kuɗi yayiwa Salman ₦10’000’000 kuɗin daka taya gidan sanan yace: “Wanam gidan abarshi Salman gaba zaiyi muku amfani and insha Allah zanyi magana da Uncle za’anema wane acikin company dinsu kafin ka ƙarasa degree ɗin, sai mubuɗe namun.” Hawaye ne sukafara fitowa daga idanun Salman, gun tasowarsu Senate da Juraij ke ƙoƙari akansu, yanzu haka Juraij ɗin shima yabashi 5million. “Bani da bakin da zanyi muku godiya kunyimun komai a rayuwa.” “Shut off bro, mene haka dan Allah. Menene amfanin abotar da ba’a taimaki juna ba?.” Shiru Senate yayi domin jiyayi zuciyarshi na tsinkewa kamar yanarasa abinda yafi ƙauna, rufe idonshi yayi yasoma faɗin. “Inna’illahi wa’inna illahir raji’un.” Da sauri Salman yariƙeshi da faɗin. “Senate lafiya, meyafaru?.” Shiru Senate ɗin yayi kusan minti biyar kuma bugun zuciyarshi yafara dai-daituwa, a hankali yabuɗe idonshi ya kalli Salman sai kuma ya kalli inda ƴan-matannan suke amma babusu. “Meyafaru?.” Salman yaƙara tambayarshi. “ I don't know wallahi, kawai naji bugun zuciyata yasauya.” “Yasalam yakamata kaga likita.” kai kawai yaɗaga sanan yace: “Yanzu zakatafi ko kana school ɗin.” “No ina school.” “Okay Sai anjima.” Senate yafaɗa tare da tafiya, bin bayanshi Salman yayi yana faɗin. “Ka tsaya naraka kamana.” Buɗe baki yayi daniyar yin magana amma yaji zuciyarshi tabuga da wani irin ƙarfi. “Wallahi bazan shiga class ɗinnan ba, jifa yanda ajin yacika ko attendance bayi zaiba.” Ya jiyo sansanyar muryata na magana, da sauri ya juyar dakai idanunsa suka sauka akan kyakyawar fuskarta, da ɗankaramin bakinta dake magana. Dum yaji Zuciyarshi tabuga da wani mugun ƙarfi sakuma bugin yadaidaita. Ƙuramata idanu yayi yana kallonta, yanayin yanda take magana ya haifar masa da wata kasala ta mussaman,bai taɓa kallon mace yaji wani yanayi bayan na tsoro sai wanan, wani irin abu yake gani a ciki Idanunta masu kamada taurari. “Man mekake kallo?.” Da sauri yajuyo ya kalleshi yana faɗin. “Na’am, muje” Tafiya sukayi amma baidaina waigen taba, haka yadawo gida yanajinshi empty kamar yabar rabin rayuwarshi kowani babban ɓangare na rayuwarshi a wani waje. Gaba ɗaya yakasa mantawa da fuskarta ko yanayin maganarta, haka yayini yana faman tunani, babban abinda ya tsoratashi shine yanda yakasa bacci daya rufe idonshi ita yake gani. Haka washe gari yatashi da tunaninta, yakasayin komai. Haka kawai yaji zuciyarshi na azalzalallashi akan yatafi school ɗinsu, a dai-dai lokacin dayaje jiya kuma wajen da yasamesu jiya, wanan ganin dayayi mata shi yarage masa duk wani yanayi dayakeji a zuciyarsa. Abu kamar wasa yazama kullum idan yatashi da wannan yanayi yake tashi, jinshi yake empty kamar bai cikaba har sai yaje yaganta, har zuwa yau daya fuskanci ƙawayenta sunfara noticing nasa. ~~~~~ Kallonshi take har yagama bata labari tundaga zuwanshi wajenshi wajen Salman har zuwan dayayi yau dakuma abinda ƙawayenta suka faɗa. “Tsoranta kake itama?.” Girgiza kai yayi daga kwancen dayake akan cinyarta. “Is different acikin zuciyata nakejin maganarta, idan nayi nesa da ita inajina empty kamar fankon ashana baby ƴaƴan ashanar aciki.” “Do you believe you're in love?.” “No mom, ta ina zansota bansantaba sai ranar kuma haka akeyinso daga ranar dakaga mutum?.” “Tashi nabaka labari.” Tashi yayi ya zauna yana kallonta, itakuma tafara magana. “Kasan Dad ɗinka ɗan Yobe state ne ko?.” “Yes Mom.” Yafaɗa tare da daga kai. “Good! kuma kasani yar kano state ce ko?.” “Yes Mom.” “Bakayi mamaki ta inda muka haɗu ba?, zuwan Dad ɗinka kano nafarko yahaɗu dani,kuma a lokacin yafara sona, kuma yabbayanamun and nayi accepting ɗinshi, to kaima haka ne.” “Mom bangane ba?.” “Senate kafaɗa soyayyar yarinyanan a lokacin farko dakaganta wanan shi ake kira “Love at first sight”.” Shiru yayi alamun yatafi tunani, itakam tana tunani take ɗanta yafaɗa soyayya mai zafi da kuma nauyi, gashi ɗanta tasan yanda take itadai fatanta Allah yasa yarinyar ƴar mutunci ce, wacce zata kula da rayuwar ɗanta. “Mom mene solution?.” Ta tsinkayi muryarshi, kallonshi tayi sannan tace: “Kaje kasameta.” “Mom I can't.” “Kaifa namiji ne zaka iya.” Girgiza kai yayi idanunsa suka ciko da ƙwalla kamar zaiyi kuka. “A haka zakace kanason yarinya, zakaje mata kana hawaye salan ta raina ka… Legends pen 08129553971. 3- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ _Page 03_ ~~~~~ Unguwar Nyan’ya “Kaga Abdulwahab ka tsaya muyi magana a nutse ta fahimta.” Bhatool dake zaune cikin ɗakinsh bayan tagama yi mai shara da mopping, hardasu turaren huta ta saka masa. Kallonta yayi yasan dole akwai abinda take buƙata kuma babbane tunda ta kai ga yi masa shara harda mopping sannan kayansa da’aka kawo daga wanki ta jera mai a cikin sif. Mama na kallonta tana yi ta ce mata. “Fati mai kuma ake buƙata!.” “Haba Mama shikenan ni bazanyi abu dan Allah ba.” “To ai Fati ansan halinki ne?.” “Ni ba abinda nake buƙata kuma idan akwai abinda nake buƙata ai munfi kusa wajen ɗan-uwanah.” Shiru Mama ta yi, dan tasan dai dole akwai abinda take ɓukata hakan yasa yanzu dataji tanayiwa Abdul daɗin baki yasa tayi murmushi. “Yaya kaci abincin kona daƙƙo maka ruwa ne?.” “A.a barshi kawai ki faɗi abinda zaki faɗa.” “Yaya kaga wallahi ina wannan ƙawartawa Suhaima?.” “Suhaima!.” Ya maimaita sannan kuma ya ce: “Ni ban santa ba gaskiyya.” “Baka gane ta ba, wacce muke makaranta tare to bikinta za’ayi nan da sati biyu, wani mai kuɗine yazo zaiyi wuff da ita, shi ne ankon nata da kuɗin kwalliya da komai da komai zai kai dubu ɗari.” “Dubu ɗari Bhatool?.” “Eyh Yaya!, wai nace yama sunan buduruwarnan taka, ai ranan mun hadu da ita har ƙasa na tsugunna na gaisheta, tana da mutunci sosai gaskiya kayi dance.” Dariya ce ta kwace masa amma ya riƙeta. “Bhatool yaushe kika bani atamfofi na siyomiki, kikace bikin ƙawayenki za’ayi.” Marairaice fuska tayi sannan ta ce: “Yaya kasanni da farin jini.” Haɗe rai yayi sannan ya ce: “Farin jinin nake ne yasa har yanzu baki da tsayayyen saurayin dazai aureki.” “Haba wannan ai gori ne, kuma Allah bai manta dani ba, wallahi natashi kawo mijina duk sai kunyi mamaki, ni yanzu kabani kuɗinnan na wuce.” Ta ƙarashe maganar cikin asalin yanayinta da take mai magana dashi na isa da izzah. “Bazasu samu ba.” Miƙewa tsaye tayi sannan ta ce: “Wallahi sai kabiyani sharar da mopping ɗin danayi maka.” “Aibani nasaki ba.” Tsaki taja sannan ta fice zuwa dakinta, mayafi ta ɗauka da jaka ta fice. Mama tana faɗin: “Ina za ki?.” “Police station.” “Bhatool wallahi karki fita.” Dawowa tayi ta ajiye jakar da mayafin nata takwanta akan gado. ~~~~~Washe gari Tun 7:30 tagama shirinta, fitowa tayi Mama da Abdulwahab na falon tahucesu tana shirin ficewa. “Ina za ki?.” “Makaranta.” Ta faɗa a dakile. “Bazaki karya ba.” Mama ta tambayeta, shikuma Abdulwahab ya ce: “Kuɗin makarantar fa.” “Naƙoshi. Zanje a ƙafa.” Duka tabasu amsa a haɗa tare da ficewa, bakin titi ta nufa tasami napep tahau, bama makarantar ta nufa ba Gidan Yaya Karima ta nufa dake unguwar. Red bricks. Itama gidan nata babbane amma bai kai ko rabin nasu Senate ba, amma suna thesame line ne, su Yaya karima sune gida na biyu, a ɓarin hannun hago, sukuma su Senate suna gida na biyar a ɓarin hannun dama. Yana zaune man kujera a parking space yaji zuciyarshi tafara bugu da sauri da sauri, bugun yana ƙaruwa akai-akai, runtse idonsa yayi saikuma yaji kamar Abinda yakeso na tunkaro dashi. Da sauri ya sauka daga kan kujerar ya nufi gate, hannu yasa ya buɗe ƙaramar ƙofar jikin gate ɗin ya fito. Dai-dai lokacin da ita kuma ta tsaya ƙofar gate ɗin gidan Yaya Karima. Kallonta yake kamar wata sabuwar hallita yanajin bugun zuciyarshi yana daidaita sannan shi kanshi yanajin shi very full, kamar yagama cika cikakken mutum. Ƙofar gate ɗin aka buɗe mata tashige ba tare da tasan da tsayuwarshi a wajen ba. Kasa komawa ciki yayi yasamu waje ya tsaya yanabin ƙofar data shiga da kallo, itakam tana shiga cikin gidan main falo ɗinta tafara faɗin. “Anty! Anty!!.” Yaya karima dake cikin ɗaki ta fito tana faɗin. “Inna’illahi lafiya?.” Tsayawa tayi turus ganin Bhatool, ita kam Bhatool naganinta ta kwanta a ƙasa tare da fara birgema tana faɗin. “Anty Abba yace karku barni nayi kukan maraici, karku barni nayi kukan rashinshi. Amma kun rantse sai nayi.” Barrister Bashir ne yafito yana faɗin. “Autar Abba, me ya faru kuma me akayi miki?.” Kukan ta cigaba tana faɗin. “Sunkasa riƙe amanar da akabasu, sunkasa cika alƙawarin da suka ɗauka.” Kallon Karima yayi yana tambayarta me sukayi mata, girgiza mai kai tai alamun bata sani ba. “Kiyi haƙuri kidaina kukan-nan haka, kar yaranki sufito suganki haka.” Tashi tayi tare da fara goge hawayen nata. “Yawwa, yanzu faɗamana abinda ya faru?.” Goge hawayen tafarayi sannan tace: “Kafin Abba yarasu saida yabasu amanata ita da yaron can, sannan yace nayimusu biyayya sabida haka nayarda nabarmasa girman, amma su sunkasa riƙe amanar sunbarni sai garari da shan wahala nake: Kallonta sukayi baki ɗaya, Yaya Karima kuwa ta ƙufula hae wuya jitake kamar takamata tafara dukanta har sai taga banta numfashi. “Me kuma sukayi miki?.” “Yaron canne nace yabani kuɗi nayi ankon bikin Suhaima amma yaƙi.” “Ubanki ke da Suhaiman.” Yaya Karima ta faɗa a fusace sannan taɗora da ce wa: “Ke rayuwarki baki da aiki sai anko da biki, a haka rayuwarki zata ƙare, Bhatool kinayiwa kanki faɗa?.” “Kiyi shiru Karima, ai lokaci ne idan tayi aure bayi zata yi ba.” “To yanzu waye zai aureta a haka, tasawa ranta masifar girman kai, bata kulakowa sai yawon biki biki, duk kayanta anko ne baki ɗaya.” “Kiyi shiru dai na faɗa miki.” Barrister Bashir ya faɗa, yana maida hankalinsa kan Bhatool. “Ki daina kuka Bhatool ai hardani Abba yabawa amanarki, dan haka idansu sunƙi riƙe amanar ni kizo zanriƙe, nawane kuɗin ankon?.” Goge hawayenta tayi sannan ta ce: “Shi ankon 65 thousand saikuma kuɗin ɗinki da make-up.” “Bhatool wallahi sainaci ubanki, kuma karki ƙara zuwarmun gida.” Yaya Karima ta faɗa a fusace tare da tashi tabarmusu wajen, tasan kome zata faɗa Bashir sai yabata kuɗin nan. “Shikenan bari nakawo miki zaikijeki siye ankon, Allah yasanya Alheri.” ~~~~~ “Meyasa zaka bawa yarinyarnan kuɗin-nan, kullum ita bazatayi hankali ba? Yar waye ita da zata dinga yin irin waƴanan anko ɗin?.” “ita ɗin ƙanwar matar barrister Bashir ce, ko laifine idan tayi?.” “Bazaka gane ba, tunda Abdulwahab ya hanta kuɗinan yakamata kaima ka hanata, last zuwan danayi gida atamfofi guda biyar yakawo mata, waita bashi ƙyallen kuma duka na ankon bikin ƙawayenta ne, sannan yanzu tazo tana maganar bikin wata Suhaima, yarinyar da anan Makarantar da suke suka haɗo.” “Inaso kigane komai lokaci ne, yanzu nanda wani ɗan lokaci bazatayi ba.” Shiru Yaya Karima tayi amma itadai tagaji da wanan halin na Bhatool, zama yayi kusa da ita tare da dafamata kafaɗa. “Kiyi haƙuri kuma ku cigaba dayimata addu’a.” “Shikenan Allah ubangiji ya shiryata.” “Amin ya Allah, sannan dan Allah banaso kinuna mata ɓancin rai kinji.”, Ya ƙarashe maganar kamar mai naiman alfarma. Tashi ta yi tadawo falon tasame Bhatool data zauna ɗai-ɗai tana faman danna waya. “Bazaki makarantar bane?.”, ɗagowa tayi ta kalleta sannan ta ce. “Hutawa zanyi yau nagaji da wahalal makarantar nan.” “Bhatool muyi magana dake mana, idan kinada time?.” “To Yaya inajinki.” Ta faɗa tana kashe wayar alamun tabata hankalinta baki ɗaya. “Bhatool kinsanfa kin girma, sannan ƴan-uwan Baba sunsa ido akanki, meneyasa bazaki nutsu kifitar da miji ba kiyi aure.” Kallonta Bhatool tayi sosai cikin yanayin nutsuwa sannan tace: “Yaya wai idan mijinan baizo ba, ni zanjanyo shi ne?.” Kallonta Yaya Karima tayi ido cikin ido sannan ta ce: “Kinaso kicemun duk cikin samarinki babu wanda kikeso?.” “Gaskiya ni bakowann irin namiji zan aura ba.” “Wane iri kikeso?.” Gyara zama Bhatool ta yi kamar wacce zatayi karatu ko dogon jawabi sannan ta ce: “Yaya inason namiji wanda zai bani ƴancina, wanda zaibani soyayya, yabani damar da zanyi duk wani abu da name buƙata.” Dariya Yaya Karima ta yi sannan ta ce: “Bhatool kina *Hasashen soyayya* a rayuwarki, kina tunanin akwai sakaran mijin da zai ɗauki duk wani shirmenki ne?.” “Kamar ya ina *Hasashen soyayya*, *Yaya nasan Mace bata canja Namiji, yana canjawa ne sabida yana sonta* to nima zannemi maisona wanda zai canja.” “To Allah yabaki sa’a akan wanan *Hasashen soyayyar*” Legends pen 08129553971. 4- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ _Page 04_ “Kamar ya ina *Hasashen soyayya*, *Yaya nasan Mace bata canja Namiji, yana canjawa ne sabida yana sonta* to nima zannemi maisona wanda zai canja.” “To Allah yabaki sa’a akan wannan *Hasashen soyayyar*” ~~~~~ Yana tsaye jikin bango tun shigarta gidan, ya rufe idonsa yana sauraron bugun zuciyarsa. “Bud-die what are you doing outside?.” Buɗe idonsa yayi ya sauke su akan Anas,sannan ya sake rufesu. “Senate magana fa nake?.” “The Girl!.” Kallon shi Anas yayi sannan yace: Which Girl?.” Sai kuma ya ce. ”Unnamed?.” Ɗaga kai Senate yayi sannan yace:” I just saw her right now?.” Dariya Anas yayi sannan ya ce: Harta fara maka gizo ne?.” “Ba wasa nake ba Anas, wancan gidan naga tashiga.” ya faɗa yana nuna masa gidan da hannu, kallom gidan Anas yayi sanan yace: “Gidan Barrister?.” “Bansan gidan ba nima.” “Kuma ka tabbatar ita ce?.” “Wai maika ɗaukeni ne, idanba itace ba zance itace?.” “To yanzu mene zakayi?.” “I will wait naga tafiyarta.” Senate yafaɗa babu alamun ko damuwa da tsayuwar da zaiyi. “You know this isn't the solution?.” “Ka ƙyaleni.” Wucewa ciki Anas yayi ya barshi a wajen tsaye. A falo ya haɗu da Momi wacce fitowarta kenan daga ɓangaren Senate, Kallon Anas tayi sannan tace: “Where have you been?.” “Morning joking, ina kwana Momi?.” Anas yafaɗa tareda durƙusawa. Amsawa tayi sanan tace: “Ina Senate ɗin?.”, Amsa yabata dacewa “Yana waje Momi?.” Kallonshi tayi sosai sannan tace: “Waje kuma meyakeyi?.” Zama Anas yayi sannan yace: “Yayi miki maganar wata yarinya da yakeso, duk da shima baison yana sonta ba?.” “Yes yayimun daman neman danayi maka jiya, inaso nace kaje YSU ɗin kaganta.” “To wai yanzu ita yaga tashiga gidan Barrister.” “Inanema Gidan Barrister?.” Taƙarashe maganar da alamun son tunawa. “Matar da tazo ranar nan kika ce tanada tarbiya.” “Oh oh Gidan Karima zakace, toshi nan yaga tashiga?.” “Haka dai yace Momi, ninafi tunaninma gizo tayi mishi, it seems yafaɗa soyayya mai ƙarfi.” “Yes I understand too, Allah yasa yarinyar tazama ƙanwar Karima ɗinma. Yanzo go and call him.” Kallonta yayi sanan yace: “Momi sa masu aiki dan yanzu zai sauke mun kwandon masifa.” Tashi tayi da kanta tana dariya tasan tabbas yanzu zaizo yana bubbuɗe baki, waishinan masifa yake Maigadi tasa yakiramata shi, wanda shima sai dayace masa Momi ɗin tana compound. Shigowa yayi yana turu baki gaba yana haɗe gira kamar ƙaramin yaro yana shirin fara rigima. Momi kam naganin yashigo tashige ciki, bin bayanta yasakeyi har zuwa falo, wato uwar harara yamakawa Anas wacce tasa Anas tuntsirewa da dariya. “Momi kinganshi ko?.”, “Meyayi maka?.”, “Dariya.”, “To sannu.” Dariya Anas ɗin yasakeyi ganin yanayin dasukayi maganar kamar masu gasar maida martani sannan kuma a ƙarshe ta gwaleshi. Senate kam zama yayi kan kujera ba tare da yace ko uffan ba. “Katabbatar ita kagani tashiga gidan Barrister ɗin?.” kallonta yayi da mamaki sannan yace: “Allah ita ce.” “Okay have your breakfast, ina zuwa.” Daga haka ta tashi tashige ɗaki, shikuma yanufi dining Anas ta tsokanarshi amma yayi masa banza. Sunanan zaune Momi tafito, kallonta sukayi gaba ɗaya itakam tasa kai ta wuce. Yau ce rana ta farko da Momi tataka ƙafa tashiga gidan wata mata a unguwar, bayan wani gida data taɓa shiga sabida mutuwar maigidan. Maigadin gidan naganinta yabuɗe mata yana faɗin. “Barka da safiya Hajiya.” “Barka masu gidan na nan.” “Sunanan mai gidan ne kawai yafita.” “Okay.” kawai ta faɗa tare da shigewa, A fall tasami Yaya Karima wacce ke zaune tana danna waya. Baƙaramin mamaki Yaya Karima tayi ba ganin Momi acikin gidan nata, baki buɗe ta tashi tana faɗin. “Momi ina kwana?”. Murmushi Momi tayi tana amsaww da faɗin. “Lafiya kalau ƴar-momi ya maigidan.” “Alhamdulillah Momi, ga waje zauna dan Allah.” Zama Momi tayi tana yaba karamci irin na, Karima tana kuma addu’ar Allah yasa yarinyar da tilon ɗanta yafaɗa soyayya da ita takasance ƙanwarta. Fitowar Bhatool kenan daga kitchen hannunta rike sa plate wanda ta Soya plaintain tana faɗin. “Yaya gashinan nasan zakiji daɗinshi.” Tsayarda maganar tayi ganin baƙuwa mai cike da kwarjini. Ajiye plate ɗin Bhatool tayi tareda durkusawa sannan tace: “Ina kwana.” Murmushi Momi tayi sannan ta amsa da faɗin. “Lafiya Ƙlau ɗiyata.” “Momi ga Plaitain.” Yaya Karima ta faɗa tana ɗakko plate ɗin tare da miƙamata, Murmushi Momi tayi sannan tace: “A,ah ɗiyata, wanan ƙanwarkice?.” “Eyh Wallahi Momi, itace ke bina.” “Allah sarki, Allah itakuma yaushe ne bikinnata?.” Murmushi Yaya Karima tayi itakuma Bhatool takoma kitchen. “Munafata dai.” “To Allah yakawo nagari, daman yau kawai nace zanzo gidan Ƴar Momi mugaisa.” “Naji daɗi sosai Momi, Allah yaƙara lafiya.” “Amin-amin , bari na wuce.” “To Momi nagode sosai da sosai.” “Yasunan ƙanwartaki, tabiyoni ta ƙarbi turare.” “Sunan Fatima Bhatool.” Yaya Karima tabawa Momi amsa sanan ta ƙara cewa:”Angode sosai Allah yaƙara arziki.” “Amin.”Momi ta faɗa itakuma Yaya Karima tashiga Kitchen ɗin. “Ke zoki bita gidanta ki amsa saqo, sanan kuzuba plantain ɗin a bowl mai kyau kibita dashi.” “To.” kawai tace sanan, tazuba plantain ɗin a bowl mai murfi tarufe tafito, Momi na tsaye taɗauki mayafinta tayafa tareda bin Momin suka fice. Kallon Bhatool Momi tayi sanan tace: “Ɗiyata ya makaranta.” murmushi tayi sanan tace: “Makaranta Alhamdulillah Momi.” “Masha Allah, shekarunki nawa kuwa?.” Bhatool bataji komaiba dangan da tambayoyin Momi tace: “20 amma zanshiga 21 nanda 5months.” “Ah masha Allah angirma Saura kuma aure.” Shiru Bhatool tayi batare da tace komai ba suka tunkari gidan. ~~~~~Suna zaune kan dining ɗin. Anas namasa hira shikuma hankalinshi nakan wayaa. “Dum Dum” yaji bugun zuciyarshi naƙaruwa da sauri-sauri, hannu yasa yadafe ƙirjin tareda rufe ido. Da sauri Anas ya ce: “Senate are you okay?.” Bai kaiga bashi amsa ba Muryar Momi tayi sallama. Legends pen. 08129553971 Masu bukatar complete kofa abude ta ke. ‎5- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ _Page 05_ “Dum Dum” yaji bugun zuciyarshi na ƙaruwa da sauri-sauri, hannu yasa ya dafe ƙirji tare da rufe ido. Da sauri Anas ya ce: “Senate are you okay?.” Bai kai ga bashi amsa ba Muryar Momi tayi sallama suka shigo cikin falon Batool na biye da ita. Da sauri ya mike yana kallon ta yayin da yaji bugun zuciyarsa ya samu nutsu, wani sanyayyen murmushi ne ya kufce masa. Momi ta dubi Bhatool da take tsaye ta ce. “ Daughter ki zauna mana.” Murmushi ta mata tana zama a k’asa. “ Ah haba ki zauna a sama mana k’asan akwai sanyi ai.” Tashi tayi tana zama a kan kujera mai zaman mutum uku dan shine kusa da ita. Anas ya dube inda yake yaga ita yake kallo, taba shi yayi ya buge masa hannu, murya k’asa k’asa kamar wanda ya buya baya son a gan shi ya furta. “ Anas leave me Abeg!.” Momi na fadin. “ Ina zuwa.” Gurin su ta iso tana kallon shi cike da so da kauna, kafin ta ce. “ Son kaje ku gaisa.” Girgiza kai yayi. “ Ina tsoro gaskiya.” “ Har yaushe tsoron zai tsaya? Anas ka raka shi.” “ Ok Momi.” Ya kama hannu Senate yaja zuwa tsakiyar falon. Tana zaune ta aro nutsuwar dole ta sawa kanta, jin kamar tsayuwar mutane yasa ta dago kanta a hankali ta zuba masa sexy eyes dinta, ji tayi kamar ta taba ganin fuskar nan a wani guri. Da sauri ya janye idanunsa daga gareta yana matse hannu da karfi, Anas na sakar mata murmushi. “ Sannu fa.” “ Yawwa ina wunin ku.” “ lafiya, ya gida?.” “ Alhamdulillah.” Zama suka yi a kujera mai facing nata, duk motsin da zata yi akan idanunsa, sai ta jita duk a takure, can Anas ya katsai shurun da fadin. “ Ya sunanki Sis?.” “ Bhatool.” “Wow” ya fada a ransa yana lumshe ido kafin ya bude ya zuba mata, karaf suka had’a ido, wani kwarjini ta gani a tattare dashi hakan yasa ta sunkuyar da kai. “ Wani school kike ne?.” “ YSU.” Ta fad’a a dakile dan ta fara gajiya da tambayar. “ Ya ban sanki ba a school din? Wani department?.” “ ENT.” “ Ok bana daukar ku shiyasa, iya yan Anatomy nake dauka.” “ Ayya.” “ Ni baki sanni bane?.” Daga kai tayi ta gan shi ta girgiza kai alamu bata gane shi ba. Hararansa Senate yayi jin yana zakewa dayawa, dariya kawai yayi bai sake cewa komai ba. Momi ta fito hannunta rike da leda fari. “ Daughter kinyi shuru, ga yayunki bakwa hira dasu.” Sunkuyar da kai kawai tayi tana wasa da yatsun hannunta tana murmushi da iyakacinsa fuska. Mika mata ledan Momi tayi ta karba tana mikewa ta ajiye bowl din hannunta ta ce. “ Mun gode sai anjima.” Ta juya zata fita. Da sauri Senate ya dubi Momi kamar zai yi kuka yana girgiza mata kai, ya mike da wuri yana kallonta har ta fita a falon, zuciyarsa ce ta harba da karfi yasa hannun yana dafewa, Momi tayi saurin isa gurin shi. “ Ka ajiye tsoron nan ka fuskanci soyayyarka, if not you’ll loose her.” “ A.a Momi, ki ce ta dawo.” ~~~~~Bayan ta fito daga gidan ne ta shiga gidan Yaya Karima tana mita. “ Yaya Karima ni fa bana son takura, haba.” Fitowa Yaya Karima tayi daga d’aki. “ Yanzu kuma me aka miki?.” “ Tun dazu kawai jiran sak’o, ta kawo da wuri shine ta ajiye ni ta tafi ciki, tabarni da yaronta mai surutu, amma Yaya naga wani kyakkyawa fa.” Zama Yaya Karima tayi tana ganin yanda take wani lumshe ido tana juyawa. “ Ke!! Kina lafiya kuwa?.” “ Hmm Yaya kenan bazaki gane ba, guy din ya hadu over, sai dai har na tafi ko magana bai yi ba, sai na gefensa da yake over sabi ya dame ni da surutu.” Zuba mata ido kawai Yaya Karima tayi tana ganinta. “ Yaya ina miki magana ma kin mantar dani! Uhm to nikam nama tafi zanje na siya anko, dan yanzu ko bazaku min ba Uncle zai min.” Ta dauki jakarta ta fice daga gidan. A waje takira wayar Suhaima tasa taturamata ankon dan so take taje kasuwa da kanta. Ta dade tsaye a bakin titin amma ba machine, dan dama unguwar ba machine ake samu ba saboda yayi nisa da gari. Tana tsaye wata baƙar mota ta tsaya a gabanta, sauke glass ɗin motar akayi, Anas ne da kuma Senate, ɗan haɗe rai tayi kafin Anas ɗin yayi magana. “ Ah Bhatool ina zuwa haka?.” “ Bayan tasha zanje.” “ Ok shiga mu kai ki ko?.” “ Dama kun bari ai zan samu machine.” Bata rai Senate yayi yana mintsinin Anas. “ Ah ah baza ‘ ayi haka ba, shiga muje.” Madadin ta shiga ta gurin Anas sai ta zagaya ta shiga ta bayan Senate, wani sanyi yaji ya mamaye shi lokacin da ta shiga, sanan yaji bugun zuciyarshi yadaidaita tsaf. jan mota yayi suka nufi hanyar bayan tasha. “ Yau ba makaranta ne?.” “ Bazan je bane, yau zan huta.” Ta fada a dakile dan haushin Anas ta fara ji. Bakin Senate na rawa ya furta. “ Kahh-rage music ɗinn.. nan.” ‘ Dama yana magana kenan? Na dauka ai kurma ne.’ tafaɗa aranta afili kuma murmushi kawai tayi domin muryarshi kaɗai abunso ce. Daganan babu wanda yaƙara cewa komai harsuka isa bayan tasha. Anas ne yace: “ A ina za ki sauk’a?.” “ A shagon Alhaji Mala.” “ Ok.” Yayi parking kusa da shagon, ta bud’e ƙofa tayi tafice Senate ne yabi bayanta ya fita, da mamaki Ansa ya fito yana kallon Senate. “ Senate where?.” Ɗame fuska yayi yana kallon Anas ɗin, nufan shagon tayi yana biye da ita Anas ma ya mara musu baya. Ankon Suhaima tanuna hoton,Nan aka ciro mata su guda uku. “ Nawa ne?.” “ Ya kama 76k.” Bud’e jakarta tayi da niyar bada kudin Senate ya miƙa ATM dinsa da sauri, bin hannunsa da ido tayi. Cire kudinsu suka yi suka mata package nashi a leda, ya dauka mata, murmushi ta sakar masa tare da fadin. “ Thanks.” “ You’re welcome.” ‘ Dai-dai ne, ai kuwa shagon takalma zamu wuce da gyelle idan yaso har da jaka ni ai gaba takaini gobarar titi.’ Ta fada a ranta a fili kuwa sai murmushi take masa. Bud’e baya yayi ya saka mata, Anas da ya zama dan kallo ya ce. “ Saura ina?.” “ Ina ta baku wahala fa da kun barshi ma kun tafi sabida daganan inaso naje wani shago ne.” Ta karashe tana dan sosa kai. “ Don’t take it some bother.” Anas ɗin yasake faɗa, shidai Senate sai binta abaya amma baya cewa ko ƙala. “ Thanks.” Tafaɗa. Kafin ta nufi shagon Alhaji Nuhu Tata suna biye da ita, duk da yana tsoro amma hakan bai hana binta ba sai dai baya bari su hada ido. “ Veils nakeso da shoes and handbag.” “ Wani colours?.” Juyawa tayi ta kalle shi. “ Please key din motar zan dauko kayan.” Mikawa Anas yayi bai yi magana ba kuma kansa a sunkuye, fita Anas yayi dan dauko kayan, yayin da shi kuma ya isa kusa da ita dan ganin wani yana mata magana hakan kuma ba karamin taba zuciyarsa yayi ba. Ganin ya tsaya kusa da ita ne yasa ta kalle shi. Y’an matan shagon sai ganinsa suke dan duk inda Senate ya shiga abun kallo ne, namiji iya namiji ga kyau ga hali ga k’asaita uwa uba farin jini. Dawowa Anas yayi yana bata kayan, cirowa tayi tana kallon colour kafin ta kalli pink din jaka da takalmi ta ce a kawo, haka ma taga maroon da brown, gyalle kuma ta dauki shentili baki da brown. Lissafa kudin kayan suka yi aka ce. “ 64k.” Nan ma kafin ta ciro kudi Senate ya bada ATM an cire. Tsaya kallon shi tayi a ranta tana fadin. ‘ Akwai Capacity ba laifi, shima kila Abba ya basa amanar nawa ne, amma shi sai yanzu ya bayyana.’ Hada kayan suka yi daya daga cikin yaran shagon ya dauko musu, fita suka yi suna jerawa tana ta danne-dannen waya, aka saka kayan a baya. “ Nagode sosai fa Allah ya biya.” Kallam da ya fara shiga zuciyarsa kenan ya zauna. “ Bansan ina zaku yi ba na katsai muku tafiya.” “ Don’t worry, yanzu ke ina za kiyi?.” “ Gida zan tafi.” “ Ok shiga mu kai ki.” Shiga tayi kafin suma suka shiga. “ Wani unguwa?.” “ Nyan’ya.” Hanyar suka nufa tana musu kwatance har suka isa. Fitowa tayi tana bud’e bayan ta fito da kayanta, Senate ya fito yana jin zuciyarsa na harbawa tamkar abun da yake buk’ata yana nisa da shi. Jin an zuba mata ido yasa ta ce. “ Nagode sosai sai anjima.” “ Uhmm yaushe za ki dawo gidan Barrister?.” “ Bani da lokaci kawai duk sanda naji inason zuwa nake.” “ Ok sai anjima.” “ Nagode.” Da haka ta shige ciki. “ Senate shiga muje.” “ A nan zan zauna.” “ Lover boy, muje gobe ma zaka ganta ai.” Numfashi ya sauke kafin ya shigo motar. ~~~~~~ Tana shiga Main falon ta tarar da Abdulwahab da Mama suna zaune. “ Rayuwa dadi, dadi! Rayuwa dadi! Wayyo dadi! Wayyo dadi! I’m so happy! I’m so happy, dama haka rayuwa take idan wani yakika wani zai sonka, y’an uwana sun kasa rike amanar da Abbana ya basu yayin da wasu bare suke rike amanar hannun biyu.” “ Ke! Waya baki kudi kika siya kayakin nan.” “ Mama kenan! Kyautata wacce ba’a tsammani tana zuwa daga masoyi ne wanda yassan soyayya kuma ya damu da mai son shi.” “ Tambayar ki fa ake?.” “ Abdulwahab ka min shuru a nan, wait tukun ni sa’arka ce ma.” “ Lallai yau Bhatool ta samu duniya.” “ Ai da kaki bani kudin Allah ya turo wanda ya bani.” Ta fada a asalin yanayinta na isa da izza. “ To waye ya baki?.” Cewar Mama tana zuba mata ido. “ Mijin Yaya Karima da kuma wani Kyakkyawan saurayi.” “ Waye ne shi din?.” “ Bazaku gane ba.” Daga haka ta tattare kayakinta ta nufi daki. “ Ni yanzu ba mutumiyar banza bace da kudina a aljuhu….. Legends pen 08129553971. Masu bukatar complete kofa a bude ta ke. 6- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ _Page 06_ “ Bazaku gane ba.” Daga haka ta tattare kayakinta ta nufi daki. “ Ni yanzu ba mutumiyar banza bace da kudina a aljuhu.” “ Abdul yarinyar nan fa sai an dakatar da ita, rawan kanta ya fara yawa.” “ Hmmm Mama yanzu kana magana zata kwanta ta fara burgima tana fadin ita sam ba’a kyauta mata, daga karshe ma ta ce amanar da abbana ya baku baku rike ba.” “ Haka za’a zuba mata ido?.” “ Mama zata daina fa, komai lokaci ne.” Ya daura da fadin. “ Sai dai wani abun da yake burgeni da ita bata kula maza bare har ta bari a bata mata suna, iya iskanci ta dai a gida ne da kuma gurin kawayenta, sai Yaya Karima kuma.” “ To! Allah ya shiryar da ita.” “ Ameen.” Akan gado ta zuba kayan tana video din su, WhatsApp group nasu na iya yen Team nasu ta shiga tayi posting tana caption da *bayan ni sai wacce? Saura dinki kawai ya rage min guys* Nan da nan Amrah ta gani. “ Kina wuta ina binki da fetur, yarinyar nan akwai capacity ba laifi.” Jannah da itama yanzu ta hau online tagani, voice ta danna da wuri. “ This gurl Wallahi kina bamu a jikinmu, da nayi calculation over a 150k fa.” “ Dey play yara, remain dinki shi ma zai kai 50 ko?.” Ta tura tana danna musu emojin dariya. Suhaima ta danna Video call, nan kowa ta shiga aka fara hira, sai hura mata kai suke chan da hiran nasu yayi nisa ne ta furta. “ Ina zamu kai dinki ne? Coz inaso a cire ni sosai a samu a fitar da shape kamar zasu fito a kayan.” “ Ke!!! Ki bari kawai gobe a school muyi maganar.” Cewar Suhaima tana kashe kiran. “Dama naje wajen ɗinki, sunbiya kudin. Kokuma karson zuciyata yayi yawa.” Tafada a ranta bayan sun kashe wayar.Cilli tayi da wayar ta nufi toilet. ~~~~~~~~~~ Red Bricks Yana kwance a kan gadonsa ya rungumi filo idanunsa a rufe, yayin da Anas ke zaune kusa da shi yana fama magana. “ Senate yanzu ko maganar kirki ka gagara yiwa yarinyar nan, haka za’a yi soyayyar.” Mantar dashi yayi ya sake rungume filon a kirjinsa yana lumshe ido. “ Senate are you okay kuwa?.” “ Anas barni, ka hanani kallonta me kyau sai damuna kake.” “ Wait a ina kake kallonta?, don’t tell me that you’re imagining her?.” Bar masa kan gadon yayi ya dawo kan kujera dake tsakin ya dunkulu a ciki yana rufe ido, dariya Anas ya saka yana kallon shi tare da ficewa daga dakin. Momi da fitowarta daga kitchen ta kalle shi ta ce. “ Are you okay? Laughing for?.” “ Momi Senate mana! He’s gone crazy, wai fa imagination nata yake tun da muka dawo.” “ To why not yaje ya same ta.” “ Momi yanzu zai fara I’m scared.” Ya karashe yana kwaikwayon yanda Senate yake. Dariya kawai Momi tayi ta nufi dakin nasa, Anas kuma ya tafi gida dan dare yayi. ~~~~~~~Washe gari Tun 7:35 ta gama shirinta dan zuwa makaranta, fitowa tayi hannunta rike da wayanta ta rataya handbag dinta. Wajen daining ta nufa tana kallon su kafin taja kujera ta zauna. “ Mama ina kwana?.” “ Lafiya! har kin shirya?.” Gyada mata kai tayi. “ Kai baka iya gaisuwa bane? Ko baka san akwai manya a nan ba?.” “ Bhatool da alamu daga jiya zuwa yau akwai kwayar da kike hambuda ko?.” “ Bana son raini irin naku na yaran zamani, yanzu kai Abdulwahab zaka dubi cikin idona ka fadamin zancen banzan nan tsabar raini da fitsara.” “ Yau din kuma Fati? Da alamu bakya buk’atar komai a gurin shi ko?.” Mama tafaɗa ganin yanda ta zaƙe sai rufe ido take wai ita babba. Tashi ma tayi ta dauko wayarta da jakarta ta fice bata kula su ba, murmushi kawai Abdulwahab yayi Mama ta bita da addu’a. Tana fita ta samu machine ta hau, boss stop ya kaita ta bashi kudinta kafin ta hau wani machine zuwa Makaranta. Direct gurin garden ta isa ta zauna akan resting bench, wayanta ya fara ruri ta dauka. “ Rich kid ban ganki ba.” “ Ina resting bench.” Tafaɗa tare da kashe wayar. Isowa gurin ta su Amrah sukayi suna fadin. “ Sai da ke yar kuna bakin wake, tamu ba irin tasu bane.” Dariya suka kwashe da shi kafin ko wacce ta samu guri ta zauna sannan Suhaima na fadin. “ I can’t believe wai har kin gama siyan komai na auren, remain dinki fa.” Gyara zama tayi tana kallon su daya bayan daya. “ Ba abun surprise bane fa, kudi ne zai yi magana.” Shigowa haraban Makarantar yayi tare da yin parking ya nufi gurin garden, bugun zuciyarsa ne ta fara sauyawa ta soma bugu da sauri sauri a hankali ya furta. “Bata shiga ajin ba kenan.” Inda ya saba zama ya zauna yana ciro wayansa ya soma dannawa. “ Ni fa yanzu bani da damuwar komai, yau kuma sai 2-4 muke da shi, so ina gamawa zan ware gida kawai, dan wannan yaron sai ya bani kudin dinki ban isa ba bazan kashe kudina ba kuma.” Dariya suka yi Jannah na cewa.“ Kina son kudinsa kuma kina ce masa yaro Bhatool ke fa sai shiriyar Allah.” “ To ai Yaron ne tun da kam na girme shi, a kudi ne kawai ya girme ni, kuma idan bai bani kudin nan ba yau sai Hizba.” Taba ta Amrah ta soma, buge hannunta tayi. “ What dalla kina mintsini na.” “ Dalla ke baki iya gulma ba, ga can Guy din nan fa yau ma ya sake zuwa.” Idan ta nuna musu suka kallo Jannah na dariya k’asa-k’asa. “ I think guy din nan yana son daya daga cikin mu ne.” “ Idan ma daya daga cikin ku yake so ai is not forbidden ko?.” Shiru ita dai Bhatool ta yi tana zuba masa ido ko giftawa bata yi Jannah na dariya da fadin. “ Wata fa ta fola.” “ No ba falawa nayi ba fadawa nayi gaba daya.” Murmushi ya yi yana gyara zaman shi tare da kiran Salman. “ How far?.” “ I’m waiting for you fa.” Sanyayyar muryansa ya daki dodan kunnen ta. Tashi tayi tsaye ta kalle su. “ Guy din nan ya kamata yau na tambaye shi me yake zuwa yi.” “ Bhatool dawo ki zauna ko kin manta school ne? Kowa kan iya zuwa yayi harkan gaban shi, mu da kullum muke zama a nan an taba yi mana magana ne, let him.” “ Maybe ta fada love ne.” Jannah tafaɗa tana dariya ƙasa ƙasa. “Jannah daily talk naki kenan Love.” Cigaba da hiran su suka yi amma hankalinta ya dawo kansa, duk ta gagara nutsuwa kawai so take taje taji dalilin bibiyar ta din da yake, dan ta fara ganewa bibiyarta yakeh. “Ke ban iya barin bala’i yayi sleep ba, ko barni naje.” Bata jira amsarsu ba tatashi. Jiyayi zuciyar ta buga da wani mugun ƙarfi, da sauri ya juyo idanunsa suka faɗa cikin nata. “Hey.” Tafaɗa tana zama, jikinshi ne yafara rawa ƙafafunshi na ƙakaɗawa, amma ya ƙureta da idanu. “Senate!!.” tafaɗa sakamakon jiya taji ankira shi da haka, wani sanyi yaji acikin zuciyarshi gaba ɗaya a rayuwarshi baitaɓa jin wani yakira sunanshi dai-dai ba kamar haka ba. “Yeyes.” Yafaɗa tare da sauke ajiyar zuciya kamar yau yafara magana a rayuwarshi. “Kaine kenan, anan school ɗin make?.” Girgiza kai yayi alamun “A’ah”, sai a lokacin ta tuna cewar baya magana. “Ko Anas kake jira?.” “A’ah, Eh.” Yafaɗa duka da sauri, murmushi tayi sanan tace. “Okay nagode faa.” “Dame?.” yafaɗa yana kallonta ciki da mamakin yanda yakejin shi complete kaman yasamu duk abinda yakeso a rayuwa. “Jiya mana ko kamanta?.” “A’ah wanan baby komai.” “Tom zantafi.” Tafaɗa tare da tashi ta koma cikin ƙawayenta. Dai dai lokacin da Salman yazauna yana faɗin. “So my man is now fall in love.” Girgiza kai Senate yayi sanan yace “No.” Karfe goma cif ya tashi ya bar Makarantar. Juyawa tayi dan ganin ko yana nan taga wayam, numfashi ta sauke kafin ta ce. “ Muje capteria.” Legends pen 08129553971,masu bukatar complete kofa a bude take. 7- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ _Page 07_ A Hanyar Cafeteria ne Amrah tace “Wancan gayen mai kyau ne.” “Wane gaye kuma?.” Suhaima ta tambaya its dai Bhatool ba face ko ƙala ba amma tabbas ta yarda Senate mai kyau ne. Sai ƙarfe 06:00 na yamma suka bar YSU daman su kullum shigar 08:00 fitar 06;00 ne ko sun gama classes ɗin su haka zasu zauna suyi ta surutu. Alla Alla take ta koma gida domin ta karɓi kuɗi wajen Abdul, wani ɓari na zuciyarta ma cewa take taje can kasuwar suyi ta ta watse, a haka ta samu ta ƙaraso gida. Da sallama a bakin ta kamar abun arziƙi ta ajiye jakarta ta ɗauki tsintsiya tana faman shara. “A’ah Bhatool sharan me like?.” Murmushi tayi ta cigaba da sharar tana faɗin. “Yanzu idan ban gyara gidan nan ba wa zai gyara, idan ban taya uwata aiki ba wa zai taya ta.” Kallonta sosai Mama tayi sanan face “ Banbu ƙaci aikin ba Bhatool balle nan da ƴan mintina kizo kina cemun ban riƙe amana ba nasaki aiki, idan wani abun kikeso kawai faɗi.” A jiye abun sharar tayi tana faɗin “Wallahi Mama so nake kisa yaron can Abdul yaban kuɗin ɗinki.” “Ke yanzu fisabillahi Bhatool baki da wata magana sai abaki abaki, ke ko tanadi baki iya ba?.” “Ta nadin mene, naga dai haƙƙin kune ki ciyar da ni, ku tufatantar dani sanan ku ilmantar dani haka zalika ko kaini ɗakin Miji, sanan kuma gashi Allah yabani ƙani mai mai kuɗi, Sister na tana auren mai kuɗi sabida nice Nan banza zan zauna na yi tanadi.” Baki Mama ta riƙe sanan tace “Uhm ke ba bamza bace.” daga haka ta koma ɗaki, itama Bhatool ta ɗau jakarta ta shige ɗaki. ~~~~~~~Red bricks “Mom please introduce me to her.” Kallon Senate Mom tayi, wani kululin takaici kamar ta kwaɗe shi, wanan sanyi halin nashi yayi yawa. “Senate wane introducing yarinyar da na kawo maka har gida, akwai wani introducing da make ɓukata?.” “Mom yau tayi mun magana, amma ba a soyayya ba, I want you to introduce me to her as lover.” “Senate idan nayi introducing dinka as her love, sai na dinga raka ka zance ina yi maka hira ko?,bayan kunyi aure sai na koma gidan ko?.” Girgiza kai yayi sanan yace ”Ba haka ba Mom, ina so ne tace mun tana so na” “Sabida ita ta rako mata duniya ko, kaine yaka mata kayi proposing da kanka, and please ka nemi Anas ya taya ka ka barni na huta.” Shiru yayi kamar zaiyi kuka, idon sa ya ciko da ƙwalla, bakin shi ya fara rawa. “Ya Allahu.” Momi ta faɗa tare da tashi ta matso inda take, hannu tasa akan ka faɗar shi sanan tace “Senate what?.”. “Mom I so much loved her, I'm always going far.” “I know kana sonta but yaka mata ka nemo soyyarta da kanka, shine zata so ka ta ga girman ka as her Husband.” “Mom taya zanyi hakan?.” “Kabani two days kaji.” Gyaɗa mata kai yayi daga man ya tashi ya nufi ɗakinshi, Anas yaje gidan su kasancewar Maman shi ta dawo daga Kano. ~~~~~Nyanya Zaune take kan ƙaramar kujera a tsakar gida, Mama kuma na daga gefe kan abun sallah, hankali Bhatool na kan waya tana chatting tare da zaman jiran Abdul ya dawo ta karɓi haƙƙinta, ita ko acikin gadonta ne. Sallama yayi ya shigo hannunsa riƙe da ledar da ya siyo fruit wanda wanan abu ne wanda kullum sai ya siyo, Tashi tayi tana faɗin “Yaya Abdul sannu da dawo wa.” Kallon ta yayi sanan yace “Yawwa sannu Yaya Bhatool ya makaranta ya gida.” “Ai kune manya , ya kasuwa kawo na riƙe ma.” ta faɗa tana karɓar ledar, kamar abun arziƙi ta shiga kitchen ta ɗakko plate ta zuba, suna zaune ta kawo musu ta ajiye tana faɗin. “Yaya ya kasuwa?.” “Kasuwa mungode Allah, ya makaranta.” Murmushi tayi sanan tace “WallaHi Alhamdulilah, Yaya.” Shiru ne ya biyo baya Kafin Abdul yace “Yawwa Mama ɗazu ake faɗamun Goggo Larai ba ta ji daɗi ba, ina ga yanzu zanje na duba ta ko?.” Dariya Bhatool tayi sanan face “Abdul kanada shishigi a rayuwar ka, mene haɗin ka da wanan matar?.” “Ubanki Bhatool yayar mahaifin naku, uwa ɗaya uba ɗaya zaki ce mene haɗin ku da ita, to kisani har ke za’aje dubiyar nima gobe zanje.” “Ai shikenan, da shi wanda ya bada amanar, da amanar da ya bayar aka hada aka zage, Abbana ka mutu ka barni inda ba’aso na, ina da ba ƙauna ta ko ƙaunad farin ciki na, Abbana ka mutu ka barni wajem waƴanda basa sauke hakkinka akaina, Abba ba samun sutura abinci kawai suke banI.” Kuka take sosai kamar gaske, gaba ɗaya jikin Abdul yayi sanyi, tashi yayi yadawo kusa da ita. “Bhatool kiyi haƙuri yanzu me aka yi miki.” Kuka take yi sanan tace “Yanzu nazo da anko aka kasayimun aka barni, yanzu kuɗin dinki ma an hanani so ake naje titi nayi bara.” “Waye ya hanaki, kin tambaye ni ne?”. Girgiza kai tayi sanan tacee “Nasani Yaya Baza ka bani ba.” “Yanzu tashi ki shirya muje gidan Goggo Lami ɗin sai mu biya wajen mai ɗinkin na bashi kudin. Miƙewa tsaye tayi tare da kar ka ɗe jikinta ta shige ɗaki, Girgiza kai kawai Mama tayi sanan tace “Allah ya kyauta.” Bayan mintina kaɗan ta fito cikin wata doguwar ta wani lace, irin ɗinkin nab da amare keyi sai zuba uban kyalli take, ankon bikin wata ƙawarta ne shima da tashin hankali akayi mata shi wajen dubu saba’in amma tun da akayi bikin ta watsar ba ta ƙara ɗaukan shi ba sai yau. “Bhatool ina zaki da wanan kayan?.” Takalmin ta mai tsini ta ajiye ƙasa tana faɗin “Zani gidan maƙiyana ai gwanda nasa ka ka ya masu kyau, yanda baƙin ciki zai ƙarasa Goggo Lami ta mutu har lahira.” “Innullahi wa inna illahir rajiun, ni Habiba wanan yarnya Allah yakawo mata sauƙi da nutsuwa da kuma hankali, walallahi ko da wasa wani yazo neman auren ki sai na bashi kuje can ku ƙara ta.” Dariya Abdul yayi yana faɗin “Mama da ƴar ta.” “Faɗi ka ƙara Mama da Ƴar ta, ƴan bakin ciki.” Ficewa yayi itama tabi bayanshi tana faɗin “wallahi kafin mu ƙarasa sai na siya sabon cover ɗin waya mai kyalli dan wallahi so name bakin ciki ya ƙarasa munafu kar matar naman ~~~~~~ Red bricks Senate ne zaune cikin ɗakinshi tare da wani kyakyawan saurayi wanda take sanye cikin ƙanan kaya, saurayin ne ke magana yana cewa. “Senate you're so annoying wallahi, na dawo daga Cyprus ba ka barni na samu isashen hutu ba kace kana da magana kuma nazo kasani a gaba.” “Am sorry Juraij, Na faɗa soyayya.” kallon shi Juraij, sabida Juraij ya nada baiwar Fahimatar Senate ssosai da sosai. “Who is the lucky girl.” Murmushi Senate yayi sanan yace “Sunan ta Bhatool I mate her last three months but ba mu taɓa magana da ita ba sai yau, I mean yau da kanta tayimun magana.” “Hahaha.” Juraij ya faɗa sanan yace “Muga hotonta kuma yanzu me make tunanin yi.” “I don't know.” Ya faɗa yana nuna mai hoton ta dake kan screen ɗin wayarsa wanda ya dauke ta a makaranta ba ta ma sani ba. “This Girl?.” Juraij ya faɗa cike da mamaki. Legend's pen 08129553971 8- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ _Page 08_ “This Girl?.” Juraij ya faɗa cike da mamaki, ”Kasanta.” ɗaga kai Juraij yayi yana dariya “Uwar ƴan rigima kenan yayanta abokina nane, ina siyan shadda wajensa daga nan muka fara mutanci dashi, wanan yarinyar ƙanwar sa ce the stubborn girl I ever meet in my entire life.” “Juraij she is my future wife stop addressing her like that.” Senate yafaɗa Kamar zaiyi kuka. “Okay nadaina but kana ganin haɗin ku zaiyi?.” “Why not?.” Senate ya faɗa tare da ta shi ya shiga toilet, shima Juraij ɗin tashi yayi ya fice. ~~~~~Suna cikin mota tana baza ido inda zata hango masu fruit ko provision store, dan tayi alƙawarin sai ta ƙunsa musu takaici sanan kuma tana son canja case ɗin waya, cikin ikon Allah ta hango wani kusa da shi kuma masu fruit ne sai kuma provision store. “Abduk wai haka zamuje gidan nan hannu mu na dukan cinya?.” Tsayar da tuƙin yayi ya kalleta sanan yace “Bangane ba?.” Girgiza kai tayi sai kuma tace “ Ai daman ba zaka ganw ba, zaka je gidan maƙiyan ka shine zaka tafi a tsiyace ƙarshen asara babu ko leda.” Kallon ta kawai Yake shi tsoron sa ma kar taje tace musu maƙiyan ta. “Kinga nutsu yanzu me kikeso ayi?.” “Kaga mu sauka muje wancan provison ɗin kasiya mata ƙwai, madara, suger sanan muje wajen mai fruit shima kasiya ma ta dayawa ma, yanda baƙin ciki da takaici zai ƙarasa ta.” Da mamaki yace ”Ke Bhatool!.” Rufe ido tayi tana faɗin “Abdul umarni na baka ba shawara ba.” Shi dai mamaki ya kusa kashe shi yanda ta rufe ido tana faɗa wai ita umarni ta bayar. “Abdul wallahi idan naƙara maimaita kaina baza kaji daɗi ba.” Parking yayi zuwa gefen titi suka fito, wajen mai fruit su ka fara zuwa “Mai fruit inaso kabani lemo na dubu biyu, kankana ta dubu biyu? Abar ba ta dubu biyu, ko kuma kabani kowanne na dubu uku uku, sai ƙabani ayaba ta dubu daya kaga yakama dubu goma.” Mamaki kam zai iya kashe Abdul a wanan lokacin, dan yanda take abu kamar itace Mama. “Bashi dubu goma.” Abdul yaji ta faɗa, hannu yasa a aljihu ya ciro kudin gaba ɗaya ya bata. Lissafa wa tayi tabawa mai fruit ɗin 10k sanan ta shiga provison store ɗin, man madara tasa aka ɗakko mata babban gwangwani da kuma milo shima babban gwangwani sai ƙwai kiras biyu, akayi mata lissafi taba su kuɗin aka biyo ta dasu. A wajen mai fruit ɗin ta ga Abdul Yana tsaye,”Amso fruit ɗin ka haɗa da kayan Nan kasa a bayan mota, sanan mai fruit ka ware mun banana ɗin daban, dan bazan ba taba tunda ba kuɗin ubanta ne, wanan ɗin ma Allah ya isa.” Daga haka tashiga shagon masu cover ta siya wata mai ƙyalli sosai sanan ta dawo mota suka nufi hanya. Babu wanda yayi magana a cikin motar sai Bhatool da take cin ayaban ta hankali kwance, har suka ƙarasa ƙofar gidan Abdul yayi parking. Saida ta gama gyara jikinta sanan tafito daga cikin motar, hannun ta riƙe da Wayarta wacce cover ɗin ke ƙyalli da sheƙi, a yangance take tafiya Abdul riƙe da ledoji kamar wani ɗan aikinta a haka suka shiga cikin gidan. Kasancewar gidan family house ne, duk ƴan uwan Abbansu na cikin gidan, ɗai-ɗai ku ne basa gidan, cike yake da hayaniyar yara kamar ba farkon magariba, duk inda sukayi binsu ake da kallo. Abdul ne ke tsugunnawa yana gaidasu, itakam daga tsaye take cewa “Ina wunin ku.” su bama ta gaisuwar ta suke ba, kayan jikinta dake ƙyalli suke kallo. A haka har suka ƙarasa ɓangaren Goggo larai wanda shima cike yake da mutane, Sallama sukayi aka fara gyara musu wahe da faɗin. “Bisimillah ku shigo.” Shiga sukayi Abdul na ta washewa ƴan uwa baki, Bhatool kam ta haɗe rai a zuci kam cewa take “Kai Abdul anyi asararre waƴanan kake washe baki haka wallahi sai kaci gidanku.” “Goggo ina wuni, ya ƙarfin jikin.” Abdul ya faɗa bayan sun zauna, “Lafiya ƙlau Abdul bawan Allah.” Goggo larai ta faɗa murya ƙasa ƙasa. “Ai kings leda munafuka done kice bawan Allah.” Bhatool ta faɗa a ranta, a fili kuma cewa tayi “Ina wuni ya jiki naki, Allah yasa kaffara ne.” “Batula jiki Alhamdulillahi, ya maman taku.” wata uwar harara Bhatool ta maka mata “Wai Batula.” Abdul ne yace tana lafiya, itama gobe zata shigo.” “To Allah ya kawo ta lafiya.” Goggo Larai ta faɗa zuciyarta cike da mamakin yanda ‘ya’yan Ahmad suka samu cigaba a rayuwa, yaran da suke kira ‘ya’yan mace, gashi sun sami cigaba sama da ‘ya’yansu. “To Goggo ga wanan ba yawa.” Bhatool ta faɗa ta miƙo ledojin sanan ta buɗe jakarta ta ciro canjin kuɗin ta miƙawa Goggo tana faɗin “Ga wanan ma Goggo.” Hannu na rawa Goggo larai ta amshi damin kuɗin tana faɗin. “Allah ya yi muku albarka yaran nan, Allah ya yi wa mahaifinku rahama.” Miƙewa Bhatool tayi tana faɗin “Ameen.” Haka Abdul ma yatashi ya fito yana mamakin wanan Abu na Bhaool, su kam su Goggo larai mamaki ya kusan kashe su yanda yaran suka canja baki ɗaya, kana ganin su kasan suna cikin huti da jindaɗi, Furai ce tace “Ni kam kunga kayan jikin yarinyar nan kuwa?.” Habi ce tace “Furai nagani wallahi, ke mijin karima ke mata suttura dan ubanta basu da kuɗin da za suyi wanan suttura.”. “Ba kiga wayar hannunta ba, har wani sheƙi take.” Furai ta sake faɗa. “Uhm kwaji da shi nidai na samu abun duniya cansu ƙarata, idan na gama ci na tufa abinda ke bakina.” Goggo Larai ta faɗa tana buɗe ledojin. “Ni Balaraba wacce aka haifa tabawa ranar sa’a, wanan kayan duka?.”Goggo larai ta faɗa tana duba kayan duka. “Aike Goggo waɗan nan yara sun gwangwaje ki.” Habi ta faɗa tana kallon kayan “Ni wallahi waƴanan kayan a banza bazan daina tsanar yaran nan ba, da uwarsu gashi yanzu sunyi arziƙi sun bar namu yaran.” Furai ce face “A’a Goggo likita yace karki saka damuwa a ranki.” Tsaki Goggo larai taja tana shan lemo tana faɗin “Banso rayuwar ‘ya’yan Ahamadu tayi kyau haka ba.”. “Wai kinga wani banza kallo da wanan mara kunyar yarinyar take mana.” Jumala dake gefe tun ɗazu ta faɗa, “Nagani wai its yar iska,Wallahi Goggo ki ta da bori sai anhaɗa ta aure ko da kamisu ɗan wajen Baffa ne.” Jumala ta faɗa sabida ita tana mugun bakin ciki Karima ma shekara ɗaya ta bata amma gashi ita tayi sure gidan hutu amma ita auren ta biyu duk sun rabu sai yara guda uku, amma gashi wanan yarinyar ma tana cikin kuɗi. “Nikam maganarki da gaskiyya Jumala.” Furai ta faɗa tana kwance sauran kaya, ita dai Goggo ba tace komai ba. ~~~~~~Parking ya yi dai dai ƙofar gidansu bayan sun biya ta wajen mai ɗinki an bashi kuɗin, kallon Abduk Bhatool ta yi sanan face “Allah ya isa kuɗin mu, nasan suna can suna ta zagin mu amma ko ba komai mun barsu da kayan bakin ciki.” “Ke dai kika sani, fitar mun daga mota.” Abdul ya faɗa yana koƙarin buewa ya fita “Mara kunya.” ta faɗa tana fita, a haka suka shiga cikin gidan tana gaba yana baya. Kai tsaye ɗakin ta huge tana faɗin “Wanan kayan kamar huta haka nake jinsu.” “Ke dai kika sani da wani yace ki saka su.” Mama dake cikin ɗaki ta faɗa, Abdul dai ɗakin Mama ya shiga yana faɗin wanan ‘yar taki halinta sai ita, yau idan ki kaga abinda tayi sai kinsha mamaki.” “Ai wallahi Bhatool bazata taɓa hankali ba, ina tausayin Wanda zai aure ta.” Bhatool daga cikin ɗaki face “In Allah yayarda miji nane zai fara kaiki aikin hajji tunda wanan yaron kaiki Umara.”. Washe gari ~~~~~~Red bricks Ganin hae ƙarfe 08:00 babu Senate babu alamun shi yasa Mom tafiya ɗakinsho domin ganin mai ya hana shi tashi, kwance yake yana bacci fuskarshi ɗauke da murmushi da alama mafarki take mai daɗi, juyawa Mom tayi zata fita taji yana cewa “Bhatool I so much love you,please karki taɓa barina.” Kallonshi Mom tayi sosai its tana mamakin yadda Senatr yafa ɗa soyayya mai zurfi da Yarinyar da ba ta masan yana sonta ba. Komawa ɗakinta tayi ta ɗau mayafin ta ta fice zuwa gidan Karima, Yaya Karima na Zaune ta ji sallamar Momi, tashi tayi tana faɗin “Ina kwana Momi.” murmushi Momi tayi tana faɗin. “Lafiya ƙlau daughter ya mai gidan naki?.” “Alhamdulillah Momi.” Yaya Karima ta faɗa tana ta mamakin zuwa Momi ɗin, Zama Momi ta gyara sanan tace “Karima na tambaye ki wani abu mana?.” “To Momi Allah yasa na sani.” Kana jin yanda tayi maganar kasan tana cike da ruɗu da mamaki. “Wanan yarinyar da kika ce ƙanwarki ce mene alaƙarku da ita?.” Legendspen 08129553971. 9- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 09_ *Not editing* “Wanan yarinyar da kika ce ƙanwarki ce mene alaƙarku da ita?.” Kallon Momi tayi da mamaki sosai sanan tace ”Bhatool!?.” Ɗaga kai Momi tayi alamar “Eyh” Zama Yaya Karima ta gyara sanan tace “Ƙanwata ce, itace ke bina amma kuma sakamakon amanarta da mahaifin mu yabamu kafin rasuwar shi,yasa muka mayar da ita kamar itace last born ɗin, shi Abdul ne ƙarami amma kasnacewar shi namiji ne kuma duk kasuwnaci Abban mu a wajen shi yake yasa muka bashi girman, ni kaina ganin shi nake kamar shine sama dani sai ita muka bata kankantar.” “Kunyi mata miji ne?.” Momi ta tambaya, Girgiza kai Yaya Karima tayi sanan tace “Banjin ta fara kula samari yanzu fa tana 18 duk da nima bankai 20 nayi aure ba.” A jiyar Zuciya Momi ta sauke sananface “I can't hide anything for you, impact ma abun ya shafe ki, Senate ne yafa ɗa soyayya da ita tun wata rana da yaje school ɗinsu, kuma soyayyar da ya faɗa wata kalal soyayya ce ni tsoro ma take ban, yanzu haka tun dazu yakasa tashi kawai murmushi yake yana kiran sunanta, gashi kuma da tsoron mata kamar masifa bana jin zai iya tunkararta ma” Itama ajiyar zuciya yaya Karima ta sake sanan tace ”Momi Bhatool wata iriyar yarnya ce mai muguwar rigima, ta kwanta a kasa taita burgima bawani abu bane a wajenta, haka zatazo nan tai tamun ihu, last time ma da tazo kukan tayi mun kuma ga Sebate very silent anya tafiyarsu xatayi dai-dai kuwa?.” “Daughter shi yaji yagani yace yanaso, to zai iya yanzu wata alfarma nake nema wajenki.” “wace alfarma ce momi?.” Dafa kafaɗar Yaya Karima Momi tayi sanan tace “Kinsan ba’a taɓayin aure sai duka ɓangare biyu sunso juna, inaso ki taimaka ki zamo tsani wanda Senate zai taka ya samu soyayyar Ummi dukda nasan abu ne mai wahala.” “Momi me kenan zanyi?.” Yaya Karima ta tambaya “Daughter ki kawo Bhatool gidanki ta zama kusa da Senate.” Shiru yayi Karima tayi Rigimar Bhatool ba’abunda zata iya ɗauka bane, amma kuma tabbas a karamci irin na Momi ta cancanci Karima tayi mata sama da haka, sanan Mama da Abdul zasu ɗan samu bakim su ya huta na kwana biyu, kuma tabbas Bhatool za tayi dacen sirika. “Daughter!.” Momi ta faɗa ganin tayi nisa cikim tunani “Ki yarda dani ba zan taɓa cutar da ƙanwarki ba, ko wani ma sanan bawai ina nuna son nawa ɗan bane, nasan matsalal shi sanan ko ke a ɗan shiga gidana da kikayi kinsan yana da matsala tsoron mata kuma indai har baiyi nasarar saka soyayyar a zuciyarta ba, dole ya haƙura.” “Shikenan Momi insha Allah zanyi.” Murmushi Momi tayi sanan tace “ Tabba gidan ku yasamu kyakyawar shaida, mahaifiyarku tayi ƙoƙari akanku bayan rasuwar mahaifin ku, a ɗan karamin binciken da nasa akayi mun, Allah yajikanshi da rahama.” “Ameen yah Allah.” Yaya karima ta faɗa, ba tayi mamakin binciken da Momi tasa akayi mata ba domin dama ya dace duk wanda zai nemi aure yayi. ~~~~~ YSU Tun wajen 10 Bhatool ke baza ido a cikin garden ko za ta hango Senate, amma babu shi babu alamun shi gaba ɗaya hirar da suke hankalin ta baya kai, Jannah ce tace “Yanzu ke Amarya ina zaki Make-up?.” “Teemarhs glow zanje, ina ga ma ta 150k za’ayi mun.” Dariya sukayi sanan Amrah tace “Sai dake Suhaima Amarya, Bhatool ke fa.” Sai a lolacin hankalin ta ya dawo kansu, Murmushi tayi sanan tace “Me?.” kallon ta su kayi baki ɗaya “Do you mean you're not with us?.” Girgiza kai tayi sanan tace “Ban dai ji mai kuka ce last ba.”.“Muna magana ne akan wajen kwalliya.” . “Uhm ina zamu.” Bhatool ta tambaya alamun dai ba taji mai suka ce ɗazu ba. Jannah ce tace “Ita dai amarya wajen Teemahs glow zata, ayi mata ta 150k.” Kallon Suhaima Bhatool tayi sanan tace “Sai dake capaciteted ko ina zaku.” ta ma yarda hankalin ta gasu Jannah da Amrah “Ni wallahi sister na ta iya kwalliya wajenta zani.” Amrah ta faɗa alamun dai tayi broke. “Uhm nima da kaina zanzi zara abata jiya haka kawai naje nasa yaron nan yayi asarar kuɗi sanan kuma ya biya mun kuɗin ɗinki, ko bani da imani bazan ƙara amsar kwabo ba a wajen sa.” Dukkanin su sunsan idan tace yaro to Abdul take nufi, haka sukayi ta hira kowa yana faɗin abinda yake bakinsa, kamar ko yaushe dai sai shida suka bar makaranta kowacce ta nufi gidan su. A cikin gidan ta tarar da Yaya Karima, wani tsalle tayi taje ta rungume ta tana faɗin “Yaya Karimancy.”. Neman faɗuwa su ka fara daga ita har Yaya Kariman da ƙyar Yaya Karima ta dafa bango tana faɗin “Ke wai mai yasa baki da kwakwalwa ne?.” Cuno baki tayi gaba tana faɗin “Ke kuma mai yasa ba’a yi miki abun arziki ne?.” Kallonta Yaya karima tayi sanan tace “Bhatool indai wanan ne abun arziƙi to riƙe abunki bana buƙata.” Kallonta ta mayar ga Mama sanan tace “Mama nadawo.”. “Naganki.” Mama ta faɗa tana mayar da kallonta ga Karima, sai bayan Bhatool ta shiga Mama tace “Anya Karima yarinyar nan tabiki kuwa, ke da kike da ƙaramin ciki.” Ajiyar zuciya Karima ta sauke sanan tace “To Mama ya za’ayi su likitocin ne suka ce ina buƙatar mai ta yani aiki, kuma idan ba ita ba wa nake da ita, haka dai zanyi hakuri da ita.” “Shikenan bari nayi mata magana.” Mama ta faɗa tana shiga ɗakin da Bhatool ke ciki,Zaune ta sameta tana danna waya. Zama Mama tayi kusa da ita tare da kiran sunanta “Bhatool!.” Ɗagowa tayi ta kalleta “Na’am Mama.”. “Inaso ki buɗe kunanki kijini, Yayarki Karima bata da Lafiya a asibiti ance ta naimi mai ta yata aiki hakan yasa zaki bita gidanta na kwana biyu kafin ta samu ƙwarin jiki.” Kallon Mama tayi sanan tace “Gidan Yaya Karima zanje na kwana biyu?.” tayi maganar kamar mai tambaya. “Eyh can zaki.” Mama ta bata amsa, shiru tayi sai can tace “To yaushe zandawo.” “Bayan ta samu sauƙi.” Shiru Bhatool tayi tana son tace bazata ba, sai kuma ta tuna dole zata ga Senate Mutumin da kyansa da sautin muryarsa ya tsaya mata arai. “Shikenan bari na haɗa kayana.” ta faɗa tare da tashi. Cikin ƙanƙani lokaci ta haɗa kayanta da kuma jakar makarantar ta, fitowa tayi tsakar gidan ta tarar da Mama da Yaya karima, Mamace ta kalleta sanan tace “Bhatool kinga bata da lafiya ki nutsu dan Allah.” Cikin sanyi murya tace “Insha Allah Mama, ki gaishe mun da Abdul ɗina.” Daman haka Bhatool take tana da rigima amma tabbas bata son nisa da Mama ko Abdul, Kasancewar Yaya Karima na da mota kuma a ita tazo ba mijinta bane zaizo ya ɗauke ta kuma ga Yamma yara sun kusa dawowa daga school, daman tun safw tazo sunje duba Goggo Larai ita da Mama. Ko a mota ma Bhatool ba tace uffan ba, har suka ƙarasa Gida tayi nisa a cikin tunani taji Yaya karima tace “Dan Allah je gidan Momi kice mata nadawo ta aiko da saqon.” Tabbas Bhatool taji dadi sosai domin tunanin da takeyi kenan tinda suka tawo har tazo, “Tom Yaya.” ta faɗa tare da nufar hanyar gidan. ~~~~~Yana zaune cikin gidan Yau bai samu ko yaje makarantarsu Bhatool ba sabida gaba ɗaya ita yake gani da ya rufe idonshi, bama yaso yayi tafiyar da zaiyi nisa har yakasa rufen idon, kuma abunda ke sa mai jindadi shine idan ya ganta murmushi take masa, kuma Salman ne da juraij sunzo a gidan suka yini, sun tattauna kan bikin ƙannen Salman da kuma company da zasu buɗe, Rabin kuɗin da za’a bude company ɗin Abban Senate ne ya bashi sanan shima ya haɗa da nashi, shi ke da kaso 75 cikin ɗari na campanin sai Kuma juraij da yasa kaso 25 wanda yasawa Salman ne domin Juraij Dad ɗinshi ya bashi company shi dake Cyprus shiya ba cika zama nigeria ba. Sunyi ja’inja sosai wajen saka sunan kamfanin inda Senate yadage sai dai asa Bhatool, Shi Salman bai cika hayaniya ba Juraij ne dai yayi ta ja dashi,shima kuma wasa yake mai sabida yana so yaga Senate na doguwar hira kuma a rayuwar Senate dasu kaɗai yake iya hirar sakamakon sanin halinsa da Juraij yayi hakan yasa yake janshi da doguwar hirar, ƙarshe dai suka amince a haka. Bayan tafiyarsu ne yadawo falo, su na zaune tare da Mom suna hira sama-sama,sai kuma Anas da bai daɗe da daowa ba, Anas ɗin ne ke tsokanar Senate yana cewa”Ango mijin Amarya.” Wani kallo senate ya watsa mai ba tare da yace komai ba. “Angon Batula.” kallonshi ya ƙarayi sanan yace “Stop.” cikin sasanyar muryarshi. “Na batula.” Anas ya sake faɗa yana dariya, kallon Mom senate yayi wacce take zaune kamad ba ta jinsu. “Mom! kiyi masa magana.” Harara ta makawa Senate ɗin sanan tace “Komai ni zan maka ko?.” Hannu yasa ya fara sosa ƙeya shi kuma Anas ya ƙara cewa “Senate Bhatool.”. “Mene yasa ba zaka kira ta da Anty ba.”Daga Mom har Anas juyowa sukayi suka kalleshi, jin yanayin da yayi magana kamar bashi ba,Murya cike da ƙarfi da ƙwarin gwiwa da kuma kwar jini,son ƙara tabbatarwa ne yasa Anas ƙara cewa “Bhatool senate.”. “Anas ba kai naiwa magana ba?.” Tabbas shi yayi maganar wallahi,Mom ce tace “Senate, daman ka iya magana haka?.” cikin fushi yace “Mom mai yasa bazai kirata Anty ba,ai na girmeshi dan haka mata ta ta girmeshi.” kallon ikon Allah Mom ta tsaya yi, kenan idan yana cikin ɓacin rai shine yake magana haka lallai ne. “I'm sorry.” Anas ya faɗa”Sorry for your self.” Senate ya faɗa tare da tashi. Rufe idonshi yayi da ƙarfi tare da riƙe ƙirjinshi.. Legend's pen 08129553971. 10- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 10_ Rufe idonshi yayi da ƙarfi tare da riƙe ƙirjinsa, dai-dai lokacin da tayi sallama ta shigo falon, da sauri ya bud’e manyan idanunsa yana sauke su akanta. Momi ta mike tsaye tana murmushi ta amsa sallaman tare da cewa. “ Daughter k’araso mana.” Murmushi tayi tana shigowa cikin falon, har yanzu idanunsa na kanta ya gagara daukewa. Har k’asa ta durkusa tana fadin. “ Momi ina kwana?.” “ Lafiya Daughter ya gida? Kin zo lafiya? Tashi ki zauna a sama.” Momi ta fad’a tana murmushi. Da lafiya ta amsa tana zama a kan kujeran kafin ta kalli Anas ta furta. “ Ina kwana?.” Washe mata baki yayi yana cewa. “ Lafiya kalau Bhatool ya Makaranta? Yasu Mama da kowa da kowa an same ku lafiya? Ya…” Hararan da Senate ya masa ne yasa yayi dif bai ce komai ba sai dariyar da yake yi ƙasa-ƙasa, kallon Senate din tayi ta ce. “ Yaya ina kwana?.” Sanyayyen murmushin nan nasa ya yi ya ce. “ Lafiya.” Yana komawa ya zauna yana facing nata. Momi ce ta nufi fridge ta dauko mata ruwa da juice ta ajiye a gabanta tana fadin. “ Daughter ki sha ruwa ko.” Murmushi tayi bata ce komai ba, Senate sai murmushi yake yi kamar wanda ya zauce, kafin ya ce. “ Bhatool ruwan gidanmu ne bazaki sha ba?.” Da sauri ta kalle shi dan batayi tunanin zai sake yin magana ba har taji zazzakar muryansa mai kwantar mata da hankali, wani sanyi taji a zuciyarta kafin ta ce. “ A koshe fa nake.” “ Haba daughter dan ban dibo miki abinci bama ko?.” Cewan Momi tana bata fuska. “ Momi Wallahi na koshi yanzu nasha ruwa, dama Yaya Karima ce tace nazo za ki ban sako.” Ta karashe suna hada ido da Senate. “ Ok to ina zuwa bari na dauko miki.” Cewan Momi ta nufi dakinta. Tashi Senate yayi ya dawo gujeran da take kai yana fadin. “ Za ki dade a nan ko?.” “ Eh nazo taya Yaya karima zama ne bata da lafiya.” Hannunsa ya saka a cikin sumarsa yana shafawa kafin ya kalli Anas ta gefen ido yana sakar masa murmushi, girgiza kai kawai Anas yayi bai ce komai ba. Momi ce ta dawo hannunta dauke da bakin leda, mikawa Bhatool tayi tare da fadin. “ Gashi nan Daughter.” Karba tayi tana mai tashi tare da cewa. “ Momi sai anjima.” “ To Daughter ki gaishe da Karima.” Da sauri Senate ya mike yana mara mata baya da fadin. “ Momi bari na taka mata zuwa gidan.” Ya fita da sauri dan ya isa gurinta. Momi ta dubi Anas tana fadin. “ Naga Senate ya canja ne lokaci kadan, daga yanayin maganar zaka gane yana magana tamkar zaki, ina nufin muryansa da kausashi.” Momi ta karashe da dan mamaki, dan Senate idan zai yi magana duk a cikin sanyi yake sai dai daga dazu ya canja ya zama cikekken na miji, amon muryansa ma ya isa ya sa jikin mutum ya dau rawa. Anas ya ce. “ Momi kila dan ya fara soyayya ne ya chanzu.” “ Maybe.” Kafin ta nufi kitchen. Bayan ya iso inda take suka jera suna tafiya, fuskarta dauke da murmushi haka ma nasa, kamar ba zaiyi magana ba kuma sai ya ce. “ Bhatool.” Ya kira sunan a wani irin voice. Ji tayi babu wanda ya kai shi iya kiran sunan ta, a wani irin yanayi ta kalle shi ta furta. “ Na’am Senate.” Tsayawa cak suka yi babu wanda ya motsa, kafin ya ce. “ Kina da wanda kike so ne?.” Girgiza kai tayi, wani naunauyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya saki murmushi ya ce. “ Muje ko.” Suka cigaba da tafiya babu wanda ya cewa wani kala. A bakin get ya tsaya ta shiga, ganin ya tsaya yasa ta ce. “ Ka shigo ku gaisa da Yaya mana.” Girgiza mata kai yayi ya ce. “ A’a yanzu kunyar ta nakeji, akwai lokacin da zan shigo har mu gaisa muyi hira da ita.” “ Ok nagode ka gaishe min da Momi.” Ta fada tana masa bye bye ta shiga falon. Har sai da ta bace kafin ya sauke numfashi yana furzar da iska ya ce. “ Yau na mata magana, yesss God kasa kar tayi wani saurayi har ta gane inason ta.” Ya fada yana tsalle da murmushi kafin ya koma gida. Tana shiga falon ta fara ihu wanda ya tsorata Yaya Karima ta fito da gudu daga kitchen. “ Wallahi sona yake, yess na kamu da soyayyar Kyakkyawan saurayi fari ajin farko irin na fita cikin kawaye da shi, na kece raini.” Cike da haushi Yaya Karima ta ce. “ Shi ne zaki shigo da ihu?.” “ What the fuck, Yaya Karima ki barni kawai.” Ta fada tana fadawa akan three seater ta lumshe ido. Filo Yaya Karima ta dauka tana buga mata, da sauri ta tashi tana dariya ta nufi dakin da ta sauka ta ce. “ Sai hakuri idan zaki iya, kisan wanda ya fada soyayya baya jin shawara.” Yana komawa gida ya shigo falon da gudu yazo ya rungume Momi. “ Babana Lafiya? What’s wrong?.” “ Momi babu wanda ya kai ki sona a duniya, ina kaunar ki Momi.” Dariya Anas yayi yana ciro waya ya fara musu video yana fadin. “ Cigaba mana da maganar, irin yau kaga bugun zuciyarka, ai har yaran ku sai sun ga video nan In Sha Allah.” Turo baki gaba Senate yayi yana hade fuska ya nuna Anas yana kallon Momi ya ce. “ Momi ki ce ya daina bana so.” “ Anas ka daina baya so.” Cewan Momi tana dariya. “ Ke ma dariya kike min Momi?.” “ A’a kuka nake.” Juyawa yayi ya tafi dakinsa yana guna-guni kamar yaro karami. *Bhatool* Tun bayan da ta shiga dakinta bacci ya dauke ta, sai kusan mangarib ta fito tana bata fuska. Yaya Karima ce da Barrister a falon yaran sun tafi wasa, kallon ta Barrister yayi yana cewa. “ Yar dakina nazo kina bacci.” Sakin fuska ta yi tana cewa. “ Uncle ina wuni?.” “ Lafiya ya gajiya.” “ Alhamdulillah.” Tashi yayi yana cewa. “ Ni kam na wuce masallaci kar na makara.” “ A dawo lafiya.” Yaya Karima ta fada tana masa murmushi, da haka ya fice. Duban Yaya Karima tayi tana yamutse fuska ta ce. “ Yaya abinci.” “ Ni zan kawo miki kenan?.” “ Ni bance haka ba, naga bakon ka Annabin ka.” Da mamaki Yaya Karima ta ce. “ Ke ce bakuwar kenan?.” “ Eh mana.” Jinjina kai tayi tana danna wayanta, zama Bhatool tayi a kasan tana fadin. “ Nikam gurin Abbana zan tafi, duk babu wanda yake so na sai shi, abinci ma ana ma mutum yanga, abun duniya da za’a mutu a barshi ana hana ni.” Ta fashe da kuka. Jikin Yaya Karima ce yayi sanyi ta tashi tazo gurin ta tana durkusawa ta jawo ta jikinta, tana bubbuga bayanta ta ce. “ Bhatool kiyi hakuri mana, ba fa hanaki abincin nayi ba, amma ai kema ba bakuwa bace.” “ Babu wani nan, kawai bakya sona ne, amanan da Abba ya baku kukeson ku ci.” Ta kuka take maganar. “ Wallahi Bhatool ba haka bane, bari na dibo miki abincin kiyi hakuri.” Ta mike ta nufi kitchen din. Bata dade ba ta dawo hannunta rike da tray da abinci a ciki. Mikewa Bhatool tayi tana karba ta nufi daining table, zama tayi ta fara cin tuwo miyan egusin tana mita wai yaji yayi yawa, Yaya Karima bata kula ta ba ta nufi dakinta tana cewan Momi ta kawo mata masifa. Tana gama ci ta tashi ta dauki ruwa a fridge ta koma dakinta, salla tayi kafin ta dauki waya ta fara charting da friend’s nata kuma duk hiran akan auren da suke dashi ne, tana zaune aka kira Isha ta tashi tayi, sai kusan goma kafin tayi bacci. *Yaya Karima* Kallon mijin nata tayi tana cewa. “ Barrister sai ina ganin kamar Senate zai sha wahala a hannun yarinyar nan, dan ko mu da muke yayunta muna shan wahala bare kuma mijinta da zasuyi zama na har abada.” “ Karima bana jin zaman Bhatool dashi akwai matsala, Bhatool tana da hakuri sannan kuma tana da tsoro, kuma miji ai ba wasa ba, ni a ganina a musu fatan alkhairi idan har auren nasu alkhairi ne.” “ Hmmm! Barrister Bhatool fa….” Dakatar da ita yayi yana cewa. “ Karima kar baki yayi yawa a ciki, Allah ya tabbatar.” Ajiyar zuciya ta sauke tana cewa. “ Amen.” Kasan zuciyarta kuma yana raya mata cewa akwai matsala. ✍�Legends pen 08129553971. 11- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 11_ Ajiyar zuciya ta sauƙe tana cewa. “ Amen.” Ƙasan zuciyarta kuma yana raya mata cewa akwai matsala. Murmushi yayi ganin ta tafi duniyar tunani ya ce. “ Mar’atussaliha!.” Juyowa tayi tana kallon shi ta ce. “ Na’am Hayati.” “ Kar ku saka damuwa a ranki kinsan ciki ne dake, yanzu ba lokacin tunani bane, yanzun lokacina ne.” Ya daga mata gira. Dariya tayi tana fadawa kirjinsa. *Senate* Yana zaune a tsakiyar gadonsa shi da Anas suna video call da Juraij da Salman. Salman ya ce. “ Senate soyayyar yarinyar nan ya saka baka gane komai.” Anas ya ce. “ Hmm!! Ku da bakwa tare dashi kenan amma har kun gane, idan zaku bawa yaron nan shawara tun wuri ku bashi, bayi da magana sai na Bhatool.” Rai a bace ya kalli Anas yana cewa. “ Na fada maka ka daina kiran sunanta tsirara kana cewa Anuty Bhatool.” Dariyar rainin hankali Salman yayi yana cewa. “ To kaji dai ko Anas, saboda haka take note.” “ Ni fa bazan ce mata Anuty ba, after all na girme ta.” “ Wallahi da Anuty zakana kiranta.” Senate yayi maganar yana hararan shi. Dariya kawai yayi yana kallon Juraij ya ce. “ Ya kayi shuru fa?.” “ Hmm!! Ba shuru nayi ba, lamarin Senate ke ban tsoro, nifa nasan yarinyar kuma akwai rawan kai, ga rigima, kaga Senate kuma bai iya ba, shine nake tunanin soyayyar nasu.” A tsawace ya yi maganar wanda yasa dukan su yin shuru. “ Ina ruwanku idan tana da rigima, ko ku zaku zauna da ita ne? For the last time idan daya daga cikin ku ya sake embarrassing din matata ban yafe ba, kuma sai mun rabu dashi.” “ Gaskiya ne baka so kuma dole sai mun fada maka.” Cewan Juraij a fusace yana disconnecting din nasa, Salma ya ce. “ Mun ji ayi hakuri.” Shima ya kashe. Anas ya tashi ya nufi kofa yana fadin. “ A dakin k’asa zan kwana sai da safe.” “ Ku kuka sani kuma.” Ya fada yana jan bargo ya rufe fuskarsa. ~~~~~~~Washe gari Tana tashi da safe ta shirya dan yau suna da lecture na karfe takwas kuma tana so tayi attendance, shiryawa tayi cikin abaya blue mai ratsin fari, sai sheki da daukar ido yake, tayi roiling din veil dinsa. Handbag dinta ta dauka ta saka perfume nata da lips glow ta jefa biro a ciki, kafin ta dauki wayanta tana bud’e wardrobe ta dauki kudi ta zuba. Sauri sauri ta fito, a daining ta hangi Yaya Karima da mijinta suna breakfast, isa gurin su tayi ta gaishe su tana cewa. “ Na tafi muna da class eight.” Barrister ya bata kudin machine, ta karba tana godiya ta fito waje. Tana tsaye machine yazo ta hau, a bus stop ya ajiye ta ta bashi kudinsa ta hau wani machine zuwa Makarantar. Tana shiga Makarantar ta kira number Amrah, bugu daya ta dauka tana cewa. “ Billahil lazi kiyi sauri wai test zai yi.” Kashe wayan tayi tana sauri ta isa department nasu. “ Excuse.” Ta fada cikin sanyin murya. Kusan duka ajin sai da suka juyo da hankalin su zuwa gare ta, a hankali Lecturer ya sauke glass din idanunsa ya zuba mata ido. Magana class din ya dauka wasu na fadin bazai barta ta shiga ba wasu na cewa ya fada soyayya da ita. Muryansa taji yana cewa. “ Ki shiga test zanyi.” Da mamaki team nasu suka kalli juna, Jannah ta ce. “ Kun ga kallon da ya mata kuwa?.” Amrah ta rage murya tana murmushi ta ce. “ Ni kuwa na gani.” Suhaima na fadin. “ Ku bari sai mun fita kafin muyi magana, yanzu any slice of mistake zai fitar damu.” Shuru suka yi suna zubawa Bhatool ido. Duk taji wani iri, a sanyaye ta soma tafiya zuwa gurin su ta zauna, paper ta ciro ta rubuta reg no ta, kafin ta fara rubuta question din, question biyar ya rubuta ya ce a amsa duka kuma 30 minute, sannan ko wanne da a and b. A hankali ya soma zagaye class din yana kallon su daya bayan daya, dai-dai bayanta ya tsaya yana zubawa yatsunta kallo ganin yanda take rubutu a natse. Ji tayi kamar an tsaya a kanta hakan yasa ta juya ba shiri, karaf suka had’a ido, da sauri ta janye idanunta tana kallon Amrah ta gefen ido, murmushi kawai suka yi wanda iya sune suka gane abun su. Sai da ya tabbata ta gama kafin ya ce. “ Submit, before I count 1 to 5.” Kafin ka ce me har kowa yayi submitting. Suna fitowa daga ajin Amrah ta ce. “ Guys I don’t get rite, me hakan ke nufi?.” Tafiya suka cigaba da yi zuwa wajen garden Jannah na cewa. “ Maybe kawai ya taimake ta ne.” “ Wannan ba taimako bane, ko kin manta waye Dr Hashim? Ranar fa bani da lafiya nazo amma ya hanani shiga lecture dinsa, yau kuma Bhatool tazo kuma tayi letting amma ya bar ta ta shiga.” Suhaima ta fada tana zama a kujera bayan sun iso garden din. Kallon su kawai Bhatool tayi kafin ta gyara murya ta ce. “ I don’t think that so, maybe kawai ya taimake ni ne kamar yanda Jannah ta ce.” Tabe baki suka yi suna chanja hira, a cikin hiran ne Amrah ke cewa. “ Yau ban ga wannan kyakkyawan saurayin yazo ba.” Lokaci daya Bhatool ta hade rai tana cewa. “ Ina ruwan ki dashi?.” “ No kawai tambaya nayi fa, naga ya saba zuwa ne, kin ga dole na tambaya ko lafiya.” Ba ta bata amsa ba suka wani yazo gurin su yana cewa. “ Bhatool tazo inji Dr Hashim nan da minti biyar.” Ya karashe yana juyawa ya tafi. A tare suka hada baki gurin furta. “ Whatttt!!!!.” Amrah ta ce. “ Wallahi na fada muku dama kallon da ya mata ba’a banza ba akwai dalili, ya fola.” Ta karashe suna tafawa ita da Suhaima. “ Kai dalla shut up, ku fa kun zare I swear, kun san me nayi ne?.” Tayi maganar tana duba gefe da gefe kafin ta cigaba da cewa. “ Amma idan ya nuna alamun soyayya, to idan mun kara yin karatun shi make i bend, ai na banza ya samu.” Ta mike da wuri tana cewa. “ Bari naje kar na makara.” “ Bhatool idan kin ga ruwan sanyi ki kawo mana.” Cewan Jannah suna dariya. *Senate* Ko da suka hadu da Anas a daining babu wanda ya yi wa wani magana, har sai da Momi ta lura da haka ta ce. “ Naga yau baku yiwa junan ku magana ba, is that any problem?.” Girgiza kai Anas yayi yana cigaba da cin abinci, mikewa Senate yayi ya koma perlo ya zauna yana kallo amma rabi da kwatan hankalin shi yana gurin Bhatool. Sallaman abokanan shi yaji, da sauri ya juyo dan tabbatar da su din ne. Salman ne da Juraij kowa rai a hade, suna kallon shi suka dauke ido, gurin Momi da Anas suka nufa suna murmushi. Da mamaki Senate ya mike yana kallon su, kamar zai yi kuka ya ce. “ Ni kuke sharewa? Then sai me idan kun ki yimin magana, Mtsw.” Ya dauki key din motansa ya fice daga falon Momi na cewa ya tsaya bai saurare ta ba. Salman yayi murmushi yana cewa. “ Momi zafin soyayya ke rudar shi, yanzu ba’a isa a fada masa gaskiya ba inde akan Bhatool ce.” Fuskar Momi da damuwa ta ce. “ Me ya faru ne?.” Juraij ya ce. “ Hmm! Momi dan kawai mun ce yarinyar tana da rigima shine yayi fushi damu, shi ne muma muka yi fushi da shi.” Bata ce komai ba ta nufi dakinta dan dauko wayanta ta kira shi. *Bhatool* Da sallama a bakinta ta shiga office din nasa, yana zaune akan gujera mai juyi yana facing din kofar shigowa. Bayan ya amsa sallaman ne ya nuna mata kujera yana cewa. “ Have a seat.” Zama tayi tana sunkuyar da kai, bata ankara ba taji maganar da ya kusa toshe mata kunne da ganin ta…. ✍🏼 Legend's pen 08129553971. 12- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 12_ Bayan ya amsa sallaman ne ya nuna mata kujera yana cewa. “ Have a seat.” Zama tayi tana sunkuyar da kai, bata ankara ba taji maganar da ya kusa toshe mata kunne da ganin ta. “ Za ki aure ni?.” Da sauri ta dago da manyan idanunta ta zuba masa, kamar wacce aka ce an aikowa da sak’on mutuwa, muryanta har rawa yake gurin cewan. “ Sir Ina da wanda nake so.” “ I don’t care 🤷‍♂️, ba shawaran ki nake nema ba umarni na baki.” Ya fada yana nuna ta da yatsa, kafin ya cigaba da cewa. “ If not duk abunda kika gani ke kika jawowa kan ki, na baki nan da gobe kadai.” Wani yawu mai kauri ta hadiye, tun da take ba’a taba yi mata barazana ba sai yau, hakan kuma ba karamin tasiri yayi ba a kanta. “ You can go.” Ya fada yana juyawa akan kujera. Da sauri ta tashi ta fita daga office din har tana k’ok’arin fadi. Gudu yake tsulawa akan titin, horn kawai yake yi sai motoci su matsa, da gudu ya shigo YSU yana parking a tsakiyar Makarantar. Ya dade a ciki kafin ya fito yana bata fuska saboda zafin ranar yau din daban ce, gurin garden ya fara nufa amma sai yaji zuciyarsa bata canja bugu ba, da mamaki ya furta. “ Bata nan kenan..” Bai karasa ba ya hango ta tana nufo garden din duk a burkice. Duk da ya ganta a burkice amma sai da murmushi ta kufce masa, cike da k’asaita ya fara nufo inda take yana murmushi, wanda ita ko lura dashi bata yi ba. Tana shirin shiga garden ne tayi tuntube za ta fadi, cikin zafin nama ya taro ta ta fada kirjinsa, yana furta. “ Subhanallah tunanin me kike yi haka.” Sai da ta runtse ido kafin ta bude tana zuba masa, duk a tunanin ta zata fadi, janye jikinta tayi tana dan yin baya kafin ta ce. “ Thanks.” “ Tunanin me kike yi?.” Senate ya fada yana duban fuskarta. Girgiza kai tayi tana cewa. “ Babu.” Bai ce mata komai ba har ta isa gurin su kawayen ta ta zauna. Dukan su ita suke kallo, kafin Suhaima tayi magana a sanyaye. “ Me ya faru Bhatool?.” Shuru ta musu bata ce komai ba, ganin kamar bata tare dasu ne yasa Amrah taba ta tana fadin. “ Bhatool!!!.” A furgice ta juyo tana kallon su. Jannah na fadin. “ Me ya fada miki?.” Girgiza kai ta shiga yi tana kallon inda Senate yake tsaye ya zuba mata ido, duk kuma maganar da suke yi yana jin su. Kamar baza tayi magana ba sai kuma ta ce. “ Babu abunda ya faru, just kawai gaisawa muka yi.” Dariyar rainin hankali Jannah tayi tana cewan. “ Wallahi karya kike Bhatool, tun yaushe muke tare da ke, mun sanki ciki da bai fa.” Hararan ta Amrah tayi tana cewan. “ Barta ta raina mana hankali ne, idan bata yarda damu bane ai shikenan damuwar ki.” Amrah ta mike a fusace zata tafi. Tashi tayi kamar zata yi kuka ta rike ta tana fadin. “ Ba wai ban yarda da ku bane, after all kun fi kawaye a gurina kun koma jinina ne.” Suhaima ta girgiza kai ta ce. “ Idan har kin dauke mu jininki ai zaki fada mana ba wai kice ba komai ba.” Wani yawu ta hadiye mai kauri, kafin ta juya ta dubi Senate da ya hade hannun a kirji ya zuba mata ido yana jiran yaji me zata ce, kafin ta sunkuyar da kai ta ce. “ Wai sona yake yi, dana ce masa ina da wanda nakeso shi ne ya ce ya bani daga yau zuwa gobe wai na yarda, ko kuma duk abunda ya faru ni na jawo.” Maganar da ya kusa hargitsa zuciyar Senate kenan, bai san sanda ya bar gurin a furgice ba. Kusan a tare suka furta. “ Whatt!!!.” Jinjina musu kai tayi tana cewa. “ Bansan me yake nufi ba, and….” Ta juya taga baya gurin hakan yasa tayi shuru tana tunanin ina yayi. Amrah ta ce. “ Dama kwarto ne, ai na dade da fada muku kune baku yarda ba.” “ Yanzu ya zamu yi Bhatool?.” Cewan Suhaima a dan tsorace. Numfashi ta sauke ta ce. “ Duk abun da zai yi yayi, karshe dai ya ce bazan yi passing din course na shi ba ko.” “ Ni fa ba wannan ba ne tsoro na.” Cewan Jannah tana cigaba da cewa. “ Kin san duk yarinyar da ya ce yana so sai ya same ta, idan kuma bai same ta ba to ya saka ayi raping na ta.” Dukan su shuru suka yi kowa da abun da yake tunanin a zuciyarsa, kafin ta kalli agogon hannunta tana fadin. “ Ni zan koma gida.” Suhaima tayi magana a sanyaye cike da damuwa. “ Ki bari mu gama lecture mana.” “ A’a akwai abun da zanyi ne.” Ta karashe tana daukar handbag din ta. Har bakin get suka raka ta ta hau machine kafin suka dawo cikin Makarantar ita kuma ta nufi gida. *Senate* Bai san sanda ya isa gurin motarsa ba ya shiga ya mata key ya fice a 360, idanunsa yayi ja ga wani ruwan da ya kwanta a ciki, fuskarsa tayi ja abunka da fari, jijiyoyin kansa sun fito rad’a-rad’a. Gudu kawai yake zubawa akan titin kalamanta yana masa yawo a kwakwalwa. < Wai sona yake, ni kuma na ce masa ina da wanda nake so.> Bai lura ba da machine din da yake gabansa har ya kusa bugawa, wani burki ya danna da karfi ji kake chusssss, buga kansa ya soma da stirring yana fadin. “ Why? Why!!!! Waye wanda take son? Dama tana da wanda take so ban sani ba? Ba zai yu ba, ni zan aure ta ba kowa ba! Ni neeeee!!!.” Ya karashe da karfi. Wayansa ce ta soma ruri ya duba, Momi ce hakan yasa ya ki dauka dan yana kusa da gida, tada motan yayi ya karasa gida yana horn da karfi wanda ya saka mai gadi lekowa dan yasa waye ne. Yana kallon motan yasan Senate ne hakan yasa ya bude da sauri, cilla hancin motar yayi ba tare da yayi parking dai dai ba ya fito ya nufi ciki. Duk suna tsaye a parlon Momi na fadin. “ Yaki picking fa, me ya…..” Bata k’arasa ba ya shigo falon. “ Subhanallah.” Kusan a tare suka fad’a, kafin Momi ta nufi gun sa da gudu tana kama shi ta soma furta. “ Me ya faru da kai? Hatsari kayi ne? Kai da waye?.” Ido kawai ya zuba musu, kafin ya janye jikinsa zai haura sama ya ce. “ Duk wanda zata aura ni ne ajalin shi, idan kuma ban aure ta ba to ni zan kashe kaina.” Ya karashe yana shiga dakinsa ya rufe da key. Duk sakin baki suka yi Juraij na cewa. “ Ta haukata shi, saboda yarinyar nan Senate ya zare, idan ba’a aura masa ita ba Wallahi zamu rasa shi kamar yanda ya fada din.” Ya karashe yana kallon su. A hankali Momi ta tako ta zauna tana had’a tagumi, ta rasa ta ina zata fara duk kanta ya dau zafi. Anas ya zauna kusa da ita yana dafata ya ce. “ Momi the best solution shine a kai kudin auren yarinyar nan.” Salman ya ce. “ Ita ta ce muku tana son shi ne?.” Ajiyar zuciya Momi ta sauke kafin ta ce. “ Ita fa bata ma san yana wannan shirmen ba….” Bata k’arasa fad’a ba suka ji karar fashe-fashe a dakinsa. A guje suka haura upstairs har Juraij na buge Momi dan sauri, buga k’ofan suka shiga yi Momi na kuka tana fadin. “ Senate kar ka kashe kan ka dan Allah.” Legend's pen 08129553971 13- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 13_ A guje suka haura upstairs har Juraij na buge Momi dan sauri, buga k’ofan suka shiga yi Momi na kuka tana fadin. “ Senate kar ka kashe kan ka dan Allah.” Magana ya soma musu yana kuka. “ Kun ce HASASHEN SOYAYYA na ke, gashi ina ji ina gani za’a kwace min ita, dukan ku babu wanda zai iya kwato min ita.” “ Senate ka bud’e kofan nan, ka daina fashe-fashen nan, ka kasa zuwa ka tunkare yarinya ka fada mata kana sonta, wai kai tsoro.” Cewan Anas kamar yayi kuka dan haushi. Bai kula su ba ya cigaba da buge-bugen da yake yi. Salman ya dube su ya ce suyi baya, suka matsa da karfi ya buga kofar sai gashi ya fadi, inda yake tsaye suka nufa duk dakin kwalba ga hannunsa din da yake digar jini alamun ya tsage. Cikume rigarsa Juraij ya yi yana cewa. “ Mad kawai, akan mace kana k’ok’arin halak’a kanka da rayuwarka.” Kafin ya sake shi yana shafa gashin kansa ya ce. “ Ka je ka same ta kace kana sonta mana.” Bai bari yaji me zai ce ba ya kama hannunsa suka fito daga dakin, suma suna mara musu baya. Idanunsa yayi ja har da hawaye a ciki ga hannunsa dake zubar da jini, ganin zasu fita daga falon ne yasa ya ce. “ Where?.” “ Gurinta.” Cewan Juraij yana jan shi. Turjewa yayi yaki tafiya ya ce. “ Me zan ce mata?.” “ Kana son ta.” “ Tana Makaranta ai.” “ Muje gidan idan bata nan sai muje school din.” Juyawa yayi yaga Momi da su Anas yana cewa. “ Bazan iya ba, I can’t Momi.” Momi ta gyada masa kai ta ce. “ Zaka iya, kuje zaka iya.” Jan hannunsa Juraij yayi suka nufi get masu aiki na kallon su, ta karamin kofa suka fita, tafiya kadan suka yi suna tsayawa a bakin get din gidan, kwankwasawa Juraij yayi mai gadi ya bude musu, ganin Senate ne ya saka shi cewa. “ Alhaji da kansa.” Murmushi ya kwakulo ya masa Juraij na tambayan shi. “ Bhatool tana nan?.” “ Eh Yallabai yanzu ta shigo tana masifa.” Basu kula shi ba suka nufi cikin falon. *Bhatool* Mai machine yana ajiye ta ta bashi kudinsa ta nufi get, bugawa ta shiga yi tana fadin. “ Zaka bude ko sai na balla get din.” Da gudu mai gadi ya bud’e yana cewa. “ Ina band’aki ne ayi hakuri Hajiya.” Hararan shi tayi tana cewa. “ Yanzu zaka matsamin ne ko sai na buge ka?.” Da sauri ya matsa mata ta shige tana masifa, a falo ta wurgar da handbag dinta tana kwalawa Yaya Karima kira. “ Yaya Karima!!.” Yaya Karima tana daki ta kwanta kenan taji kiran, da sauri ta fito tana cewa. “ Bhatool lafiya?.” Fashewa tayi da kuka tana zama a k’asa, da mamaki Yaya Karima ta iso gurin ta tana dafata ta zauna ta ce. “ Me ya faru?.” Kasa tsayar da kukan nata tayi tana fadin. “ Yaya ni na hakura da Makarantan nan.” Cike da mamaki ta ce. “ Me kuma ya faru? Me aka miki?.” Nan ta bata labarin komai bata boye mata ko daya ba, ta karashe tana kuka. Shuru Yaya Karima tayi, gefe guda na zuciyarta na tuna mata da Senate, kafin ta sauke ajiyar zuciya ta ce. “ Dago fuskarki ki kalle ni Bhatool.” Da idanunta da suka danyi ja ta dago tana kallon ta. Yaya Karima ta ce. “ To ke waye kike so?.” “ Yaya burgeni kawai yake yi.” “ Waye ne shi din?.” Shuru tayi kafin tayi magana suka ji sallaman Juraij da Senate, lokaci daya zuciyarta ya tsinke ta kalli Yaya Karima wacce ke sakin murmushi tana fadin. “ Yau Senate ne a gidan.” Murmushi ya mata suna k’arasowa cikin falon, gaishe da ita suka yi ta amsa tana tambayar su Momi suka ce tana lafiya. Idanunsa na kan Bhatool da taki juyowa dan kukan da tayi ya saka idanunta ja. Yaya Karima ta ce. “ Bari na dauko muku ruwa ko.” Ta fada tana nufan fridge. Juraij yayi saurin dakatar da ita ta hanyar cewa. “ Anuty da kin bari daga gida muke fa, dama gurin Bhatool muka zo.” ‘Dum-dum’ haka taji zuciyarta na bugu, yayin da Senate yayi saurin dafe saitin zuciyarsa yana karanto addu’a duba da yanda lokaci daya ya harba masa. Yaya Karima ta ce. “ Laifi ta muku ko?.” Ta fada tana dariya. “ A’a mun isa ta mana laifi.” Dubanta Yaya Karima tayi tare da cewa. “ Bhatool baki ji ance anzo gurin ki ba.” Jinjina kai tayi tana cewa. “ Naji Yaya.” Kafin ta mike ta ce. “ Ina zuwa bari na shiga daki na fito.” Tayi sauri ta yanda kar a ce ta tsaya. Yaya Karima ta zauna tana duban su ta ce. “ Me ya faru?.” Kallon Senate Juraij yayi kafin ya ce. “ Anuty wannan na rako fa.” Ya nuna Senate kafin ya cigaba da cewa. “ Wai Bhatool…..” Saurin katsai shi yayi ta hanyar buge k’afarsa yana marairaya ido. Tsaki Juraij yayi yana cigaba da cewa. “ Wallahi Anuty hauka ya fara yi akan Bhatool.” Runtse ido Senate yayi saboda kunyan da yaji lokaci daya ya kama shi, Yaya Karima ta ce. “ Ikon Allah, wai Senate har yanzu tsoron ne da kai? Tsoron ma na Bhatool?.” Juraij ya ce. “ Hmmm!!! Shi ne yau na jawo shi nace yazo ya fada mata ko zamu samu sauki.” Yaya Karima ta dubi Senate da kyau ta ce. “ To idan kana tsoron ta taya zakuyi zaman aure kenan? Ko ka taba ganin inda miji ke tsoron mata?.” Girgiza mata kai yayi, ta cigaba da cewa. “ Ka cire tsoro ka ajiye shi a gefe ka tunkare ta da zancen.” Gyada mata kai yayi kafin ta mike ta ce. “ Bari na kira ta.” Ta nufi dakin da Bhatool ke ciki. Da sauri ya dubi Juraij zai yi magana ya ga ya ciro waya yana tashi da alama kiransa aka yi. ‘ Inna’illahi!! ‘ Ya furta a zuciyarsa kafin yaji wani bangare na zuciyarsa na ce masa. ‘ Zaka iya, idan baka fada mata ba wani ya rigaka fa kamar yanda wancan ya rigaka’ Ji yayi wani kishi ya tokare masa makoshi lokacin da yaji ta ce. < Ce masa nayi ina da wanda nakeso>. Ko da Yaya Karima ta shiga dakin ta same ta zaune da waya a hannu tana dannawa, kusa da ita taje ta zauna tana cewa. “ Bhatool!!!.” Ta kira sunanta. Mayar da hankalinta tayi zuwa gareta baki daya tana amsawa. “ Bhatool baki fadamin wanda kikeso ba?.” “ Yaya burgeni kawai yake yi.” “ Waye ne shi din?.” “ Dan Momi ne.” Ta fada tana turo baki gaba ta dauke kai. “ Ke bana son shirmen kin nan fa, dan Momin bashi da suna ne.” “ Yaya Karima Senate ne fa.” Sakin baki tayi tana kallon ta. ‘ Shi sonta yake, ita kuma burge ta yake, me hakan ke nufi?.’ Sanin babu mai bata amsa ne ya saka ta dubi Bhatool me kyau ta ce. “ Ke ko dai son shi kike?.” Da sauri ta juyo tana girgiza kai. Yaya Karima ta yi murmushi tana rike hannunta ta ce. “ Bhatool kin san Senate baya surutu, kuma baya kula mata ko?.” “ Yoo to ni Yaya taya zan sani.” “ Ungo naki🖐 ai fada miki nake yanzun ba wai kin sani ba.” “ To ina ji.” Ta ajiye wayanta ta zuba mata ido. Tsaki Yaya Karima tayi tana tashi ta ce. “ Ki je falo yana neman ki.” Dariya tayi tana cewa. “ Allah yasa outing zamu fita ya kashe min zuciya da kudi.” Kallon ta Yaya Karima tayi tana tsaki ta fita. Mayafin Abayan jikinta ta yafa ta fito falon. Yana zaune yayi shuru kamar maraya, kamar mutuniyar kwarai ta iso da sallama a bakinta. Amsawa yayi ba tare da ya dago ya ganta ba, a kujeran dake kusa da nashi ta zauna bayan ta gaishe shi ya amsa. Shuru ne ya biyo baya babu wanda yayi magana tsawon mintuna, kafin da kyar ya dago da kai ya kalle ta yana fadin. Legend's pen 08129553971 14- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 14_ Da sauri ta d’aga kai ta kalle shi, jinjina mata kai yayi yana cigaba da cewa. “ Za ki iya aure na?“ “ Uhm…. Uhm…. Ni wai?.” Ta nuna kanta tana kallon shi. Gyada mata kai yayi yana mikewa tsaye ya zuba hannunsa a aljuhun wandonsa ya ce. “ Kiyi shawara kafin ki yanke amsa, na baki daga yau har zuwa lokacin da kika ji kin amince.” Ya ajiye mata kudi da bai san nawa ba ya tafi. Da ido tabi bayansa har ya fita kafin ta kalli kudin, dariya kawai tayi dai-dai lokacin da Yaya Karima ta fito. “ Yaya wai fa tambaya na yake zan iya auren shi, can’t believe it wai wannan handsome guy din ke cewa zan iya auren shi, to ai ko baya gani ne sai na aure shi balle kuma yana kallo.” Ta karashe da wani murna a tattare da ita. Dariya ita ma Yaya Karima tayi tana fadin. “ To ke me kika ce masa?.” “ Yaya me zance masa kuwa, barshi na dan wainasa a tunkunyar masa tukun, na ja masa aji sosai kafin nayi accepting.” Murmushi kawai Yaya Karima tayi ta ce. “ Kar ajin dai ya tsinke.” Tashi tayi ta nufi dakinta bayan ta bawa Yaya Karima kudin ta ce ta ajiye mata. *Senate* Yana fitowa a falon ya sauke wani lafiyayyar ajiyar zuciya yana dafe saitin zuciyarsa, lumshe ido yayi yana jin wani karfin guiwa. Dafa sa da akayi ne ya saka shi bude ido ba shiri yana sauke su akan Juraij, dariya Juraij ya fara masa yana cewa. “ Wani irin tsoro ne haka Senate.” Hararan shi yayi yana nufan hanyar fita, shi ma ya mara masa baya yana tsokanan sa amma ya mantar dashi har suka shiga gidan su. A falo suka tarar da Momi, Anas da Salman sun zuba tagumi suna jiran me zai je ya dawo. Momi na ganinsa ta mike ta iso gurin shi tana zuba masa ido alamun tanaso taji karin bayani. Dariyan da Juraij ke yi ne ya saka Anas cewa. “ Ya kwafsa ko?.” “ No bai kwafsa ba.” Ya fada yana dariya kafin ya ce. “ At last ya fada mata yana sonta.” Lokaci daya suka saki murmushi, Momi bata san sanda ta rungume shi ba tana cewa. “ Babana ya zama jarumi.” Murmushi kawai yayi yana fadin. “ Momi dama jarumin ne tun a baya, kuma In Sha Allah ta sanadiyarta na canza, na zama jarumi.” Sakin shi Momi tayi tana jan kumatunsa ta ce. “ Better.” Salman yayi murmushi ya ce. “ Shikenan ai yanzu sai kar ka kashe kanka ko.” Rarumo filon kujera yayi yana wurga masa, da sauri ya matsa yana dariya da fadin. “ Senate na Bhatool.” Dariyan da ya dade bai yi ba yayi yana shafa sumarsa ya ce. “ Fadi da k’ara Senate na Bhatool kuma Bhatool na Senate.” Dariya falon suka saka kafin aka zauna ana hira ana zolayan shi, har su Salman da Juraij suka tafi *Washe gari* Rawar kai, ya mantar da Bhatool tashin hankalin dake makaranta. Hakan yasa ta shirya tun wajen ƙarfe bakwai, so take taje ta kaiwa ƙawayenta gist ɗinan. Ƙarfe 7:45 a bakin gate ɗin YSU tayiwa Bhatool, tana tafe tana danna wayarta. So take takira wata cikin ƙawayenta taji ko sun ƙaraso cikin school. Horn din taji anayi mata a baya, hakan yasata waigawa a fusace, wa zata gani?. Dr Hashim. “Ya Allahu.” ta furta kaman tayi kuka, a hankali ya kawo motar kusa da ita. “Bhatool. Ya maganar mu.” Murmushin dole ta jawo tayi sanan tace. “Nayi shawara, zanzo office ɗinka anjima.” “Okay.” kawai yace yaja motarsa, da harara tabi motar tasa. Wayarta ce tayi ƙara alamun kira. “Wai Suhaima ina kikasa wayarki ne.” “Ina kan mashin. sai yanzu na sauka, Kinzo school din ne?.” “Da banzo ba, zan kiraku?.” “Okay gani nn shigowa.” Kashe wayar tayi ta nufi wajen da suke zama kafin su shiga hall. A wajen ta tarar da su Janah suna zaune, dan su tsarin su sai sun hadu baki daya zasu shiga class tare, yanzu ma takirasu sabida tayi tunanin ko sun shiga. Sabuda bata ce dasu zata zo ba. Ƙarasawa tayi ta zauna, tare da fadin. “Amarya wace zatayi miki make-up?.” Da kallo suka bita, su sunanan cikin tashin hankali da fargaba, ita tana nan tana musu zancen make-up. “Kikace bazakiyi make-up?.” Wata uwar dariya Bhatool tayi, sanan tace. “Ai yanzu banza ta faɗi, arziƙi yazo, gayu sai yaci uban na daa.” Legends pen 08129553971 15- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 15_ Da ido suke kallonta, ita kuwa sai zuba take. “Yanzu ba wannan Bhatool da kuka sani bace, ƙanwar Abdul, yanzu yayar Abdul ce. Ko yaya karima ma sama nake da ita.” “Bhatool. Bamu labari me ya faru?.” Suhaima da bata dade da ƙarasowa ba ta faɗa, gyara zama Bhatool tayi sannan ta ce. “Ashe Abba, ba iya Yaran can yabawa amana ta ba?, can you girls remember that cold, giant, handsome and classy guy dake zama inda muke a garden?.” Ɗaga kai suka yi duka, tare da faɗin.”Yes!.” cike da mamaki. “To shima Abba ya bashi amanata, jiya nan ya ajiyemun kudi. Ban dubasu ba sai yau naga 150k.” “150k!.” suka fada gaba dayan su cike da mamaki. “Yes, 150K.” Bhatool ta maimaita. “Bhatool, kina cikin Alheri dumu-dumu.” “Wallahi faa, and guest what?”. “What?!.” Suka sake fada. “Wai yana sona.” “Ayirrrrr, Bhatool tayi goshi.” Jannah ta fada kamar tayi rawa. “Amma kema kince kina sonsa ko?.” Suhaima ta tambayeta. “Haba mana gurls, atleast ai ya kamata naja Class ko yane.” “Eyh.. Amma kija a hankali.” Jannah ta fada, sai kuma tace. “Dr Haisam fa?.” Dariya Bhatool tayi sannan tace. “Wasa zanyi dashi, zance mai na aminci, amma ya jira mugama 100lvl mushiga 200. Sai ayi engagement da munje 300 sai ayi auren. Nasan shi wanan bazai fi six months ba, za’ayi komai a gama.” “Har bikin!?.” Cewar Suhaima cike da mamaki. “To mai zanjira Allah yakawo mun miji.” Dariya sukayi baki daya, daga nan suka shiga class. *Senate* 07:45 yaƙaraso ƙofar gidan Yaya Karima, sai dai mai gadi yace mai tun 07 Ta fita. Komawa gida yayi rai babu dadi kwata-kwata. Har yanzu bai samu amsa daga wajenta ba, sannan yanaso yaji jiya akan wa take magana. Domin kasa bacci yayi gaba ɗaya, da tunanin maganar ya kwana. Bai san yana da kishi har haka ba. “Good morning Momy nah.” ya faɗa bayan ya shigo falon. “Morning, angon Bhatool.” Murmushi yayi sannan yace. “Momi har da ke.” “Ni dai yanzu zo ka zauna anan.” zuwa yayi ya zauna, Momi ta kalleshi. “Yanzu zuwa yaushe kakeso, a saka bikin nan. Sabida nima na matsu, duk ƙawayena sun fara aurar da yaransu. Har da masu jikoki.” Dariya Senate yayi, sannan yace.”Momi nima bansani ba.” “Zan fara zuwa nayi magana da yayarta, sai asamu iyayenta.” *Bhatool* “Haba Abdul, tunda nace kazo ina son ganinka ai kasan ganinka nakesonyi. Nifa yayarka ce.” bhatool dake waya ta faɗa, shiru tayi Sannan ta ƙara cewa. “Idan kuɗi ne zance sai kazo, ai fada maka zanyi, ni yanzu turumun account number dinka na sama ko 10k ce dan kasan ni yanzu kuɗi basu bane matsala ta.” “Shikenan sai kazo.” daga haka ta kashe wayar ta juyo ta kalli su Suhima tace. “Shi kadai ne Hope dina, sanan bani da wani wanda zai tsayamun daya wuce shi.” “Hakane Bhatool, sanan zai baki mafita sosai. Domin tabbas Dr Haisam ba karamin makirin mutum bane.” “Nasani wallahi Suhaima, kinaji yadda mukaji ‘yan accounting dazu suna magana, kamar damu suke.” “Wallahi kiga dai yace zaki aureshi, to itama ƙawarsu yace zata aureshi. Mai hakan ke nufi.” Jannah kuma ta faɗa. “Alllah ya tsare mu baki daya, ni Abdul din ma idan yazo tare zamu tafi.” “Gwanda ki bishi Bhatool, wallahi banason ganinki a makarantar nan.” “Ke kuma da tsoro kike Jannah.” Ba’afi minti goma ba Abdul yazo makatantar, kiranta yayi a waya ya sanar da ita yazo. “jirani bakin gate.” ta fada tare da kashe wayar. “Ladies yazo, sai munyi waya.” .”Wait baki amshi cards dinki ba, banjin zan sake shigowa school.” Suhaima ta fada tana bude jakarta. “Ɗibi.” ta fada tana miƙamata jakar. “Kala nawa ne.” ta tambayeta. “Dinner, kamu, mothers eve. Su kadaine masu card, bridal babu, henna ma babu card.” “Okay, kowanne ban biyar, zanbawa senate da abokinsa, nabawa Yaya karima da mijinta sai abdul.” “Okay.” Suhaima ta fada tana lissafa mata.”Ga six nan ma ko zaki kara wani, ku nawa-nawa zan baku.” ta tambayesu Jannah. Bhatool dai amsa taita huce, sauri-sauri ta karasa bakim gate. Motar Abdul ta gani da sauri ta nufi motar tare da budewa ta shige a kan idon Senate da zuwansa kenan zai shiga Makarantar. Ji yayi zuciyarsa ta harba da karfi, da sauri ya fara karanto addu’a yana Astagfirullah a zuciyarsa, yana gani ta shiga motar tana murmushi, gashi baya ganin ko waye ne dan tinted glass ne. Numfashi ya sauke ganin motar ya bar gurin kafin a fili ya furta. “ Bhatool!!.” Yana dafe saitin zuciyarsa dake masa zafi. Ta da motan yayi ya bar gurin a 360 ransa a bace, yana isowa get din unguwarsu yaga motar tana fita alamun ya ajiye ta ta shiga gidan Yaya Karima. Har zai tare shi sai kuma ya fasa ya wuce ya nufi get din su, horn ya danna mai gadi ya bud’e masa, ya cinna hancin motar ciki yana parking, ya dade a ciki kafin ya furzar da iska yana fitowa ya nufi dakinsa direct. ~~~~~~~~ Ko da Abdul ya ajiye ta a kofar gidan Yaya Karima sai ta ce. “ Abdul ga card na event din Suhaima, na Dinner, Kamu, nasan baza kazo Mothers eve ba.” “ Abun naku har da mu ne?.” Ya tambaya yana amsa tare da ajiyewa. Hararansa tayi tana cewa. “ Kai ka sani kuma, sannan idan zaka zo Hilis ka shigo da kudi na kari.” “ Uhm naji fita zan koma kasuwa.” Ya fada yana yiwa motar key. Tabe baki tayi ta fita daga motan ta shiga gidan Yaya Karima shi kuma yaja motarsa ya wuce. Da sallama ta shiga falon, Yaya Karima na amsawa dan tun dazu zaman jiranta take ta dawo taji ya suka kare da Lecturer din. “ Yaya Karima ya gida?.” Bhatool ta fada zata wuce d’aki. “ Ke, tun dazu fa ke nake jira amma kinzo zaki wuce.” Cewan Yaya Karima tana jin kamar ta kai mata duka. Reverse tayi tana cewa. “ Sorry Yayata ta kaina, me ya faru? Me kike jira?.” Hararanta tayi tare da fadin. “ Ya kuka kare da Lecturer din naku?.” Dariya tayi tana fadin. “ Ohh wai Dr Hashim? Ai wasan buya muka tayi dashi har na fito, nace zan same shi a office anjima shine na kira Abdul nace yazo ya dawo dani.” Ajiyar zuciya Yaya Karima ta sauke ta ce. “ Alhamdulillah!!! Yanzu ina Abdul din?.” “ Ya koma kasuwa abin shi.” “ Baku da kirki dukan ku, tunda yazo har get ina laifin ya shigo mu gaisa yaci abinci.” Ta fada ranta a bace. Tabe baki Bhatool tayi ta nufi daki tana cewa. “ To ki kirasa ki masa fada mana, amma kin wani sakani a gaba kinamin fada da rungumeman cikin naki… Legends pen 08129553971✍🏼 16- *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_ _Stroy and written_ By Sayyid (Legend's pen)✍️ *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚* *The Fearless Writers Team* _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 16_ Taɓe baki Bhatool tayi ta nufi ɗaki tana cewa. “ To ki kirasa ki masa faɗa mana, amma kin wani sakani a gaba kinamin faɗa da rungumeman cikin naki.” Yaya Karima ta ce. “ Allah ya shirye ki idan mai shiriyar ce, amma ke kam Bhatool halinki sai ke, mijinki ya shiga uku.” Dariya Bhatool ta mata tana bud’e kofar ta lek’o ta ce. “ Cewa za kiyi Senate ya shiga uku dan shine Nurul Hayat dina, kuma Zauj dina.” Ta rufe kofar tana cigaba da dariya. Girgiza kai kawai Yaya Karima tayi sannan ta wuce d’akinta. *SENATE POV* Tun da ya shiga d’akinsa bai fito ba sai guraren sallan Mangrib, dan sallan Azahar ma a d’aki yayi, haka kuma bai kula kowa ba ciki kuma har da Mom, dan yau jinsa yake wani iri duk a burkice. Sauk’owa ya fara yi daga upstairs yana jin hayaniya, sake tamke fuska yayi lokacin da ya lura da su Juraij ne da Salman da Anas, sun tusa Mom a gaba suna hira kuma duk akan yanda za’ayi bikin Senate din ne. Kallo daya ya musu yana tura baki a ransa ya ce. ‘ Gaibu kenan, ko accepting dina fa bata yi ba amma sun zage sai shirye-shirye suke.’ Mom ce tayi murmushi tana tasowa tazo gurin shi tana kama shi ta ce. “ Son kazo mu zab’a wani event da wani event zamu yi.” “ Mom kuje ku zaɓa.” Ya faɗa yana wucewa ya fita daga parlon. Baki a sake suka bisa da ido kafin Juraij ya ce. “ Idan kun ga haka to shi da Bhatool ne.” “ Kai da kasani kuma, kila ko bata masa magana bane yasa yau ransa duk a bace, kamar wanda aka masa bushara da wutan jahannama.” Cewan Anas. Salman yayi murmushi ya ce. “ Ku dai gulma ne naku, ai gwara shi ya nemo wacce yakeso duk da tana bashi headache, amma ku fa? Ko ince mu fa? Kamar wanda basu da farin jini ko haske a rayuwar su.” Dariya Anas yayi yana cewa. “ Cewa zakayi kamar wanda bakin iyaye ya bisu, ni fa tunda nake babu macen da ta taɓa cewa tana sona, anya ma ba aljana bace ta aure ni?.” Juraij ya daura da cewa. “ Ko dai ta aure mu dai, dan nima haka ne lakamtu summa lakamtu.” Mom ta zauna tana fadin. “ Ku tashi ku tafi masallaci, ku fake da cewa aljana ta aure ku, ku dai kuka auri aljanun tunda kune kuka ki auren.” Da haka suka tashi suka tafi masallaci. Ana idar da salla ya fito ya nufi hanyar gidan Yaya Karima, Juraij na cewa ya jira shi amma yayi banza dashi. Ƙwanƙwasawa yayi mai gadi ya buɗe, ya tambaye shi. “ Bhatool na nan?.” Ya ce. “ Tana nan, dazu ta dawo daga Makaranta.” “ Ban tambaye ka ba Malam.” Senate ya fad’a yana nufan hanyar falon, dan shi fa jinsa yake dai-dai da kowa yanzu, duk haushin biyu ya taru masa ya masa yawa, ya rasa waye ne na Makarantar ga wanda ya kawo ta dazu. A bakin kofar ya tsaya yana sallama. Fitowan ta kenan taji sallaman shi, da mamaki ta ce. “ Kamar Senate nake ji.” Yaya Karima da itama fitowarta daga kitchen ta ce. “ Shi ne ma ba kama ba.” Tabe baki tayi tana komawa d’aki dan dauko mayafi. Yaya Karima ta amsa masa tana cewa. “ Haba Senate gidan ne sai kace bak’on ka, ka wani tsaya daga waje.” Dan sosa keya yayi kafin ya shigo kansa a k’asa, ya durkusa yana cewa. “ Ina wuni?.” “ Lafiya ka tashi ka zauna.” Tashi yayi ya zauna yana ta kwakulo murmushin dole, Yaya Karima ta danyi murmushi kafin ta ce. “ Bari na kira maka mutuniyar taka, yanzu ta shiga ciki.” “ To Nagode.” Ya fad’a dan dama ya rasa ta ya zai fara tambayar ta ina Bhatool. Yaya Karima na k’ok’arin shiga dakin, Bhatool ta fito sanye da Hijab har k’asa Maroon color dinkin jalbab, matsawa gefe Yaya Karima tayi tana binta da ido, dan rabon da taga Bhatool da hijab har ta manta idan ba Sallah zatayi ba. Kamshin turarenta ne ya fara masa sallama kafin tayi sallama tana zama nesa dashi. Amsawa yayi yana d’aga kai ya kalle ta, murmushi ta sakar masa wanda ya ratsa zuciyarsa da gangar jikinsa gabaki daya, lokaci daya ya nemi fushi da bacin ran da yake yi ya rasa, yaji zuciyarsa tayi haske furannin cikin sun samu ruwa. Lokaci daya ya tsinci kansa da furta mata. “ Kinyi kyau sosai.” Murmushi ta masa tana sunkuyar da kai kamar munafuka kafin ta ce. “ Nagode.” “ Ba godiya a tsakaninmu ai.” Jinjina kai tayi tana tashi ta mika masa card guda hudu, dan ta kaiwa Yaya Karima guda biyun tace baza su je ba, karba yayi yana kallo kafin ya ce. “ Na mene ne?.” “ Na auren Suhaima ce, da Dinner da Kamu, ko zaka bawa friends naka coz you’re also invited.” Ta karashe tana komawa gurin da ta tashi ta zauna. Murmushi yayi yana cewa. “ In Sha Allah I will be there.” Shuru ne ya biyo baya babu wanda ya sake cewa komai, can ya dago kai ya kalle ta yana cewa. “ Kina da matsala da wani ne a school naji kuna hira? Sannan waye ya kawo ki dazu?.” Da sauri ta dago manyan idanunta ta sauke masa tana cewa. “ Kenan ranar kaji komai?.” Shuru yayi dan shi kawai yaji ta ce akwai wanda takeso ne, amma ga dukkan alamu da ya tambaye ta yaga tsoro kenan akwai bayani, hakan yasa ya ce. “ Eh naji komai.” Marairaice fuska tayi ta fara cewa. “ Wai fa Dr Hashim ne yake sona.” Kalman da ya caki zuciyarsa kenan *SO NA!!!*, ta cigaba da cewa. “ Shi ne nace masa ina da wanda nakeso, wai yace bai damu ba ya bani nan da kwana daya nayi tunani ko kuma duk abunda na gani ni na jawowa kaina.” Ta karashe tana kallon yanda yanayin fuskarsa ya canja lokaci daya, daga fara’a ya dawo bacin rai zalla, amma sai ya dake ya ce. “ Shi ne kawai?.” Gyada kai tayi tana turo baki gaba ta ce. “ Eh.” Murmushi ya mata ya ce. “ Solve, idan dai wannan ne angama da shafin shi.” “ Thanks.” “ Dm.” Sannan ya daura da cewa. “ Wanda ya kawo ki fa?.” “ Abdul ne fa, kanina ne uwa daya uba daya.” “ Ohh 😲.” Ya fada yana sosa keya a ransa ya ce.’ Ina kishi da kaninta kenan.’ Kafin a fili ya ce. “ Akwai wani abu ne?.” Girgiza kai tayi ta ce. “ Bakomai kuma, kawai so nake kuzo events din duka biyu.” “ Idan shi ne baki da matsala an gama.” Kafin ya mike tsaye yana cewa.” Nikam bari na tafi.” Tashi tayi tana rakasa, a bakin get ta tsaya tana ciki shi kuma yana waje. “ Ba ki bani amsa ba.” Sunkuyar da kai tayi ta ce. “ Accepted.” Ta koma ciki da sauri tana dariya. “ Yessss!!!.” Yana sakin dariya, juyawa yayi sukayi ido hudu da su Anas sun zuba masa ido. Saurin tamke fuska yayi dan yanzu zasu mayar dashi karamin mahaukaci, ai kuwa bai gama ba suka fashe da ihu Anas na cewa. “ Senate na Bhatool.” “ Bhatool na Senate.” Cewan Juraij suna sake sakin ihu. Kamar yayi kuka ya ce. “ Ku dena kiranta da sunanta ai wannan raini ne.” Dariya suka sake yi Salman na cewa. “ To Zahra na Senate.” Bai kulasu ba ya shiga gida yana kwalawa Mom kira, da sauri Mom ta fito daga daki tana cewa. “ Lafiya wannan kiran Senate.” Nuna mata su Anas yayi wad’an da har yanzu suna dariya ya ce. “ Mom ki ce su daina kiran sunanta haka raini ne.” Da mamaki Mom ta ce. “ Ban gane ba, sunan waye za’a daina kira haka?.” “ Sunan Bhatool suke kira fa babu cewa Anuty.” “ Ikon Allah.” Kafin Mom ta dube su tana cewa. “ To dai kunji Anuty Bhatool zamuna kiranta dashi.” “ Mom ban da ke, su kadai.” Bata kula shi ba ta koma dakinta dan dama gyara kayanta take. Ya juya ya kalle su ya ce. “ Kuka kara ce mata Bhatool duk sai na kaiku kara police station.” Ya karashe yana nufan d’akinsa. Juraij ya ce. “ Prison za’a kaimu kawai yafi ai.” Nan ma dariya suka masa, yayi kwafa ya shiga daki ya danna sakata. Bhatool kam, tun fitar Senate ta koma ɗaki tana famam xancen zuci. “Tabbas Senate mai kyau ne, ɗan gayu, mijin nuna wa sa’a, mijin shiga taro, idan har nayi sa’a na aure Senate mai zai dame ni a duniyar nan?.”  Ta yi wa kan ta wanan tambayar. “Babu fa.” Ta sake bawa kan ta amsa, tana cikin wanan tunanin wayarta ta hau ƙara alamun kira na shigowa, hannu ta kai ta ɗauka tare da ɗagawa bayan ta ga Sunan Amrah a kai. “Hello Amrah.” Ta faɗa bayan ɗaga wayar. “Bhatool ya garin?.”  “Normal Amrah is everything okay, na jiki wani kala?.” “Not Okay, wallahi Bhatool kuɗi nake nema urgently dan Allah ki aramun ko 30thousand ne.” “Haba Amrah, ai kinfi ƙarfin haka ki bani account ɗin zansa miki.”  “Na gode sosai Bhatool, bari na samiki.” “Okay.” Bhatool ta faɗa tare da kashe wayar, yanzu hankalinta ya koma kan na ta bikin dan ta san dai Senate son ta yake, Abinda ya rage kawai ya yi proposing asha biki, .”Kai zan ta shi kan munafukan ‘yan uwan Abbanah, har na hango Goggo larai ta ga Mijinah, su Fure da hari sun suma, ƙila ma baƙin ciki ya kashe su, wallahi ba za a fasa bikina ba ko sun mutu.” Bhatool ta faɗa tana miƙewa zuwa Toilet.  Wayarta ta ɗauka ta yi wa Senate Sallama ta whatsapp, yana kwance kan gado tun da ta shigo tunanin ta yanda zai yi proposing, sanan shi bai son Auren ya wani daɗe ayi a huce wajen kawai, ga kuma matsalal wanan malamin na su da ta ce. “Ƙila fa neil Abuja zan mai da ta kawai.” Ya faɗa dai-dai lokacin da ya kai hannu zai ɗauke wayarsa, sakamakon ƙarar shigowar saƙƙoni da ta ishe shi. Idonsa ne ya sauka a kan message ɗinta da ta ce. “Salam Yaya Senate.” Da sauri ya shiga yi ma ta Reply da faɗin. “Wa’alaikussalam Bhatool.”  “Na’am Yaya senate, barka da dare.” “Barka Bhatool ya su Yayan?.” “Suna lafiya ƙalau, ya su Mom?.” “Alhamdulillah Bhatool.” “Daman Yaya Senate dan Allah Account ɗin Amrah ƙawata xan baka ka tura ma ta 30k, da safe sai na baka Cash, banda kuɗi a account kuma Yaya ta hanani fita Pos🥹🙏.” “🤩Okay badamuwa turu.” “Na gode🙏❤️22xxxxxxx42.”  *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_     _Stroy and written_              By    Sayyid (Legend's pen)✍️    *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚*     *The Fearless Writers Team*   _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 17_ Tun a farkon littafina na sanar daku cewa Hasashen soyayya Free book ne, ku bar ni na rubuta shi a nutse amma hakan ya garara, a kullum kuna cemum kuna son complt, ayi agama da huri. Tom Allah ya amsa addu’arku, Hasashen soyayya ya zama paidbook amma Vip Paidbook page uku kullum, sabida mu gama shi da huri kafin January. Payment via. 8129553971 Opay Sani Muhammad lawan. Shaidar biya 08129553971 Daga page 22 zamu gama posting Free pages  Ngde. *Bayan kwana biyu* ~~~~Red bricks “Tom yanzu Hajiya daga ganin yarinya sai ku yankw hukuncin gidan da ta fito?.” Dad dake zaune kan kujera ya faɗa yana kallon Mom dake yan ka masa fruit. “Yarinyar fa ƙanwar matar barrister ce, kuma kasan matar barrister ai.”  “Duk da haka fa Hajiya, kawai dan dai kina son yarinyar ne shi yasa haka.” “Tabbas kam, yarinyar ta na da shiga rai kuma ɗan lalena ne ya kawo ta.” Dariya Dad ya yi sanan ya ce. “Shikenan zan sa a yi binciken da ya ka ma ta.” “Amma fa ni cikin ƙan-ƙanin lokaci nake so ayi komai a gama.” Mom ta faɗa sabida ta fuskanci kamar bai shirya aurar da Senate ba, wata dariyar ya sake yi saman ya ce. “Komai saurin ki dai, sai kin jira lokaci ko?.” “Eeyh!.” Ta faɗa kawai tare da ci gaba da haɗa masa fruit ɗin. Senate ne ya fito cikin shiri, ya sha ado cikin milk clour na shadda wacca ta yi matuƙar amsar jikinsa, fuskarsa mai kama da ta larabawa ta fio fes cikin browm clour ɗin hulal da ya saka, tsintsiyar hannunsa ɗaure da golden clour Rolex watch, turaren jikinshi ya ƙarade gidan baki ɗaya, a hankali ya tako zuwa falon. Da kallon soyayya Mom ta bi shi, a ranta tana yi masa addu’ar kariya da neman sa’a an kan komai. “Dad barka da hutawa.” “Barka dai Amgo, sai ina?.” Murmushi ya yi, tare da yin ƙasa da kan sa. “Zanje dinner ne.”  “Tom Allah ya tsare.” “Amin Dad.” Ya faɗa tare da miƙewa xuwa inda Mom take, bai ƙarasa ba Dad ya ce. “Akwai kuɗi a wajen ka ko?.”  “Eyh Dad akwai.” Gyaɗa kai Dad ya yi, ya ci gaba da shan fruit ɗin sa, shi kuma ya ƙarasa inda Mom take. “Mom zan huce.” shafa kan shi ta yi sanan ta ce. “Allah yatsare, a kula mun da Bhatool.”  “In sha Allah Mom.” Daga haka ya fice, motarshi ya hau ya nufi address ɗin da ta ba shi na wajen kwalliya. ~~~~~~Bhatool. “Amrah, banga gold ɗina ba.” Bhatool ta faɗa tana bincike jakarta. “Innullahi wa’inna illahir raji’un, Bhatool sake dubawa dai.” Amrah ra faɗa ana ci gaba da mata kwalliayar. “Wallahi Amrah banganshi ba; Allah yasa gida na bar shi.”  “Amin dai kam.” Amrah ta faɗa dai-dai lokacin sa Jannah ta shigo,wacce daman angama yi mata ta kwalliyar ita da Bhatool. “Suhaima ke ce mun wai sun kusa ƙarasawa.” jannah da ta shigo ta faɗa. “Chaii, Amrah ayi a gama miki ɗaurin nan.”  “Bhatool ya baki sa ɗan kunne ba?.” Jannah ra tambaye Bhatool. “Na bar shi gida wallahi.”  “Ya salam!, yansu ya za’ayi?.” “Ɗaurin na wa za a sakko mun da shi har kunne.” “Eyh kam hakan zai yi ma.” Mai kwalliayar ta faɗa bayan ta gama yiwa Amrah ɗauri, dai-dai lokacin da kiran Senate ya shigo wayar Bhatool. “Laa kunga yazo.”  “Waye?.” Amrah ta tambayeta. “Senate.” Ta bata amsa. “To mu yi sauri kar mu ɓata mai lokaci, kun san manyan mutane ba sa son jira.” Amrah ta faɗa tana haɗe kayanta. “To ko mu fara fita ne.” Amrah dan ta ƙara faɗa. “Ke matsalata da ke hutar ciki.” Jannah ta bawa Amrah amsa. “Duk hutar cikin ta dai nima angama mun.” Bhatool ta faɗa tana sauka daga kujerar kwalliyan, daga nan suka ka ɗai su ka fice.  Haka kwai Senate ya ji kwalliyar Bhatool ta yi yawa, gaba ɗaya ya ji shi wani kala duk ya damu, “Dama ba ta yi ba.” Ya faɗa a zuciyarsa, a fili kuma ya sakar ma ta murmushi. “Ina yini.” Amrah ta faɗa tare da Jannah. “Lafiya kalau, ya taro?.”  “Taro gashi ana ta sha, ya gajiyar jiya?.”Amrah ta ba shi amsa, ita dai Jannah tana ƙoƙarin shiga mota. “Alhmdlh.” Ya faɗa a daƙile tare da shigewa mota, su ka huce hall ɗin. Ko a hall ɗin Senate ya hana Bhatool sakewa, ko ina suna tare yana binta a baya, yan maza na ta kallonta haka shima yan mata na ta kallonsa, zallan kishi kawau ke ɗawainiya da shi, ya yu kicin-kicin ya haɗe rai, Bhatool kam da ta fuskancin haka sai ta yi banza da shi, ko ina ya yi ta bin na ta.  ~~~~~~Hausari “Toh Isiyaku bari ka ji mun isa har mun yi yawa mu aurar da ‘ya’yan Ahmad, ko da ran Ahmad ko babu ran sa; domin ni ce babba cikin ku.” Goggo larai da ke zaune kan kujera yar tsugunno ta faɗa, kawu Isiyaku ne ya ce. “To ai Larai wanan zancen banza ne zancen wofi, idan ba mu aurar da ita ga na gida ba wa zamu bawa? duk lalacewa Saddiku ɗan mu ne, kuma shi da kan sa ya ce idan an aurar mai Bhatool yar gidan Yaya Ahmad zai nutsu, zai daina shaye-shaye, da wanan yawon tafiya legas ɗin.”  “To ko ba zai daina ba tun da ya ce yana son aurenta ai sai an ba shi;dan haka na gama magana, kawai ku haɗa kayan nagani ina so ku kaiwa uwarta.” Goggo larai ta faɗa tare da mikewa tana dafa bango. Furai ce ta kalli Habi su ka kwashe da wata shegiyar dariya, sanan Habi ta ce. “Ina baƙin cikin ganin su Bhatool sun ci gaba.”  “Wallahi Habi nima haka, ke da ina da dama Karimar ma sai na kaso na ta auren.”  “Bari muje fa Bhatool gidan Yaya Sadik, ita ma sai ta fito.”  “Ai wallahi nasan da zarar an aurar da Bhatool ga Yaya Sadik, ta ta taƙare, sai ta hulaƙanta ta sha wahala, ta gane Allah ɗaya ne.” Dariyar su ka ƙara fashwewa da ita. ~~~~~Senate & Bhatool. “Wai bazaka zauna ka ci Abinci ba?.”  Bhatool ta faɗa, dan ta fara gajiya da wanan bin bayanta da Senate ke yi. “Naƙoshi.” Ya faɗa murya kamar zai yi kuka, kujera ta samu ta zauna shima ya zauna kusa da ita, sanan ta ce. “Senate mene matsalal wai?.” Turo baki ya yi gaba sanan ya ce. “Duk kin yi wani kyau, yan mazan sai kallonki su ke.”  “To ai kai ma ka yi kyau ko?; kuma ‘yan mata sai kallonka suke.” “Mu ta fi gida.”  Legendspen 08129553971 Page 18 *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_     _Stroy and written_              By    Sayyid (Legend's pen)✍️    *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚*     *The Fearless Writers Team*   _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 18_ “Mu ta fi gida kuma?.” Bhatool faɗa tana kallonsa, shi kuma ya gyaɗa ma ta kai. “Ni dai A’ah, yaushe mu ka zo haba.”  “Ni zan tafi to.” Tsaki ta ja ta dau jakarta ta fice, shikuma ya bi ta baya gwanda ta yi ta fushin amma bazai jure ganin yadda samarin wajen ke ta kallonta ba, a ƙafa ta fara tafiya. Motar ya shiga ya biyo bayanra, ta na ji yana mata hon amma ta yi banza kamar ba ta ji ba, sauka ya yi daga motar ya nufu ta yana faɗin. “Bhatool, ki tsaya mana.”  “Me zan ma?.” “Ki tsaya mu tafi gida.” Ci gaba ta yi da tafiyarta hankalinta kwance ba ta ko kula shi ba, sai da ta yi tafiya mai nisa sanan ta juyo, ga mamakinta sai ganin Senate ta yi zaune a kan wani tudu yana kallonta, fuskarshi kamar zai yi kuka. “Oh ni Bhatool, mai na kwasowa kai na haka?, shi da zai lallaɓani amma shike fushi.” Ta faɗa a cikin ranta, a fili kam cewa tayi. “Idan bazaka tawo ba zan koma wajen bikina.” “To a ƙafa zamu tafi?.” Harara ta maka mai sanan ta ce. “A me muka zo?.”  “To ai kin ƙi shiga motar.” “Ɗakko mu tafi.” Juyawa ya yi ya nufi motar ita kuma ta bishi da kallo. “Ga mutum har mutum amma sai shashanci kamar wani ƙaramin yaro.” Motar yakawo inda take sanan ya buɗe ma ta ta shiga, haɗe rai ta yi ba ta ce ko ƙala ba dan haushin senete ne fal a ranta, dan wallahi gobe ma ba zata bashi katin dinner ba. “Oh wa ma ya aike ni.” Ta faɗa a ranta. “Bazaki kulani ba?.”  “Wai wane irin abu kakemun haka, kamar ƙaramin yaron, ni banajin yin magana.”  “Ki yi hakuri.” Ya faɗa yana cuno baki gaba. “Me ka yi mun?.” “Na baro ki daga wajen biki, Bhatool wallahi ina son ki, so mai tsananim gaske mai kuma nauyi, Bhatool bazan iya jure ganin maza na kallonki ba, Bhatool a kowanne dare kafin na kwwnta sai na yi kukan rashinki kusa da ni. Bhatool ban san so ba sai lokacin da na sanki, ban san zan iya tunkarar mace ba sai a kan ki, Bhatool ban san zan zama sakarai a kan mace ba sai a kan ki. Bhatool ban san zan iya kuka a kan mace ba sai a kan ki, Bhatool son ki ya shige ni a lokacin farko, ya mamaye rayuwata ta yadda banajin zan iya rayuwa ba tare da sautin bugun zuciyarki ba.”  Shiru Bhatool ta yi, duk kalaman Senate suna shiga sassan jikinta, suna ratsa ƙashi da ɓargonta, wani irin san yi yana mamayw rayuwarta. Tabbas Senate abun a so ne, Senate mai son ta ne, ita kan ta ba ta tuna lokacin da son Senate ya shige ta, sai da tasan ya yi wa zuciyarta kamun da cire shi zai zama babbar wahala.  “Bhatool bana jin akwai abinda zai gagari sadaukarwa sabida ga soyayyarki.” Kalaman da suka dawo da ita daga tunanin da take. “Bhatool nu dake haɗin Allah ne, ki yarda da ni, zan baki gata, zan baki kula, zan baki soyayya, zan zame miki bango da zaki jingina da shi a rayuwa, zan zame miki tsananin da zaki taka ki samu nasara a rayuwa, zan zame miki matattakalal da zaki taka ki samu al-jannah, Bhatool zan zame miki abokin rayuwa na har abada,  Bhatool” ya kira sunata a ƙarshen maganar. Ɗagowa ta yi amma ta kasa kallonsa. “Ɗago ki kalli idona dan Allah.” A hankali ta ɗaga idanunta ta sauke su a kan na sa. “Bhatool..”  “Na’aam.”  “Bhatool ki so ni dan Allah, Bhatool na miki alƙwarin soyayya mai tsafa fa iganci, na miki alƙwarin sadaukar da komai nawa domin siya miki farin ciki Bhatool.” Ƙasa ta yi da kan ta, ta fara wasa da yatsunta. “Ina sonka Senate.” Ta faɗa a cikik ranta, a fili kam shiru ta yi, amma kalaman senate suna amsa kuwa a cikin kunnuwanta, tabbas ta cika mai sa’a da samun senate.  “Kin yi shiru Bhatool.”  “Na’am.” Ta faɗa a ɗan tsorace. “Ba ki ce komai ba.”  “Na ce mana.”  “Banji ba sake faɗa.” “Allah ka ji.” Dariya ya yi sanan ya ce. “Banji ba fa.”  “Na ce Eyh.” “Eyh, me?.” Shiru ta yi tare da yin ƙasa da kai. “Ba zaki ce komai ba?.”  “Ina son ka nima.” Wani sanyi Senate ya ji a cikin zucoyarsa, daman kuma amsar da yake sa ran ji kenan, godia ya yi wa Allah a fili sanan ya ce. “Bhatool na yi miki alƙwarin ba zan taɓa bari ki yi kuka ba, bazan ta ɓa bari ki ji babu daɗi ba, zan fara ta miki da komai nawa, in Allah ya yarda Bhatool.” (Uhm, ni kam na ce Team senate and Bhatool ku yi screemshot ɗin wanan alkwari na senate ku ajiye shi, dan wata rana ku dinga tuna mai😂😂) ~~~Red bricks. Mom ce ta kalli Dad dake zaune yana danna waya, sanan ta ce. “Nifa bangane inda wanan zancen nala ya dosa ba, me kake nufi?.” “Wai mene baki gane ba, tun ɗazu muna ta maimaita zance ɗaya.”  “Shi Justice audun mai ya ce, har da zaka ce baka amince da auren Senate ba, wane abu ya binciko a game da yarinyar?.” Miƙewa Dad ya yi sanan ya ce. “Nima ban san me ya gano ba, amma tun da ya ce mun akwai matsala to kin san dole akwai, dan haka ba zan taɓa yarda ɗana ɗaya tak ya yi aure waje mai matsala ba.”  Yana faɗin haka ya shige ciki, ta shi ta yi ta bi bayan sa ta na faɗin. “To mene yasa bazai faɗi matsalal ba sai dai ya ce akwai matsala, sanan justice Audu ai ba shi yake da ikon yin bincike a kan matar da Senate zai aura ba ko?.”  “Ban san lokacin da kika fara mayar mun da magana irin haka ba, kin sani, na sani justice Audu abokin kwarai ne, tun kafin na sanki na san Audu kuma yakasance abokin shwara a kowanne lokaci, kuma kema a haka kika ta so.” Daga page 20 zamu gama free pages, ranar littinin in sha Allahu zamu shiga paids page, kuma 3 pages za a dinga posting kullum. 8129553971 Opay sani Muhammad lawan Shaidar biya tanan  08129553971 Legendspen. *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_     _Stroy and written_              By    Sayyid (Legend's pen)✍️    *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚*     *The Fearless Writers Team*   _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 19_ “To amma ko da yake abokin kwarai kawai sai ya ce yaro ba zai auri yarinya ba, kuma babu wani ƙwaƙwarran dalili.” Mom ta faɗa bayan ta shigo ɗakin da Dad yake. “Kina so mu ci gaba da maganar kenan, to nima ban san dalilinsa ba, kuma shi nake jira nan yanzu zai zo.”  Ta shi ta yi ta fice ba tare da ta ce ko ƙala ba, sai dai Senate da ta gani tsaye ya yi matuƙar ba ta tsoro.  “Har ka dawo?.” Ta tambaye shi. “Eyh Mom, wace yarinya ce ba za a aura ba?.” “Wai Bhatool.” Da sauri ya matso kusa da ita sanan ya ce. “Me yasa Mom, Bhatool fa ta ce mun tana sona.”  “Nima Senate ban sani ba, wai Justice ne ya ce masa da matsala.” “Ba dai tare da Bhatool ba ko?, Bhatool ba ta da matsala Mom.” “Ka nutsu ka kwantar da hankalinka, sanan ka yi addu’a ka ji.”  “Thom Mom.” Ya faɗa tare da shigewa ɓangarensa, zama ya yi gefen gado yana faman tunani. “Yanzu idan aka ce bazan aure Bhatool ba, na yi ya da rayuwata, na yi farin ciki a kan me?.” Hawaye ne su ka fara gangarowa ta kuncin sa, sanan ya fara addu’a.  “Allah Ka sani ina son Bhatool, kai ne ka samun soyayyarta, Allah ka malakamun ita, Allah ka ba ni Bhatool a matsayin mata, ka ba ta ikon yi mun biyayya ka ba ni ikon kyautata ma ta, Allah ina son Bhatool, Allah ka so ta, Allah ka kula da Bhatool, ka mallakamun ita har ƙarshen numfashi na ya Allah.”  ~~~~~~Bhatool. Tun da Senate ya ajiye ta a gida ta shigo kai tsaye ɗakinta ta nufa, ba ta ko bi takan Yaya Karima da mijinta ba, kalamansa sai yawo suke mata a kwanyar kanta, wani farin ciki na ratsa zuciyarta, ta na ji kamar tafi kowa sa’a a duniya domin samun Senate abu ne mai girma, wayarta ta ɗauka ta shiga groups ɗinsu. Ta tara da saƙƙonin da yawa sa tarin hotona, Jannah sai tsiya take ma ta wai Baby Senate ya sa ta a gaba sun tafi, Suhaima ce ma ta tanka, amma Amrah bata ce komai ba, sallama ta yi musu sanan ta ce. “Yan uwama ku ta ya ni murna, Senate ya furta mun kalmar so tare da aure.” Cikin yan mintuna suka bibiyeta da congratulation, Amrah ce ta fara kiranta a waya cike da farin ciki take magana. “Congratulation ƙawata kece akwai wani shagalin nan gaba.” Dariya Bhatool ta yi sanan ta ce. “Bai fi wata ɗaya ba fa.”  “Ke dan Allah, muna cikin Alheri.”  “Tsamo-tsamo ma.” Bhatool ta faɗa tana dariya, daga nan sula shiga hira da sauran ƙawayen na su har zuwa 12 na dare sanan su ka yi sallama.”  A Ɓanagaren Dad kam ya kasa zaune ya kasa tsaye kalmar “Akwai Matsala.” Da justice ya faɗa masa kaɗai ta ka ɗa masa hanjin cikin sa. Waya ya ɗauka ya ƙara kiran justice Audu amma bai ɗaga ba, sai dai ƙarar warn da ya ji  ya sa shi tabbatar da cewa Audun ya ƙaraso, ta shi ya yi ya yare shi acan su ka yi wancan part ɗin. Bayan sun zauna Dad ya ce. “Audu mene matsalal?.” Kallon Dad Justice Audu ya yi sanan ya ce. “Yunusa kasan me?.”  “Faɗi mana.” “Yarinyar nan yar gidan Habiba ce.” “Wacece Habiba kuma?.” “Habiba dai da ka sani, Habiba ta ka.” Justice Audu ya faɗa yana kallon yanayin Dad. “Ni fa bangane ba Habiba wacce.” Ta shi ya yi ya matso kusa da Dad sanan ya ce. “Habiba wacce kasani guda ɗaya, matar da ka so kamar ranka, matar da ka so kamar ka yi hauka.”  “Innullahi wa’inna illahir raji’un! Justice kama nufin Habiba ce ta haifi yarinyar da Usman ke neman aurenta?.”  “Tabbas ita ce, ita ta haife ta har da wasu ma guda biyu.” Mikewa Dad ya yi ya fara tuna lokutan baya da suka huce, irin soyayyar da suka shimfiɗa da Habiba, irin ƙaunar da ya nuna ma ta, yana tunanin ko Senate a yanzu bai yiwa Bhatool irin son da ya yi wa Habiba mahaifiyar Bhatool ba. ~~~~~~Years Back. A lokacin kallo ɗaya zaka yi wa Dad ka ga kammanin Senate Sak a tare da shi, sai dai Senate ya fi shi jikim hutu da gayu, A lokacin Dad yana tsaka da neman kuɗi a kasuwa, kasuwanci shi bai yi wani nisa ba amma a hakan ma yana samu dai-dai gwargwado. Ranar wata juma’a, bayan sun dawo daga Sallar juma’a shi da Abokinsa Audu su ka yanke shawarar shiga cikin unguwa neman abinda zasu ci, sakamakon gajiya da abincin cikin kasuwa.  Wani gidan da ake siyar da abinci su ka tsaya, ganin samari ƙofar gidan suna tsai-tsaye, a lokacin ne Habiba ta zo shiga gidan tare da ƙawarta, tun a kallon Farko ya ji wani Abu ya ratsa shi, wani baƙon yanayi ya ziyarce shi. Audu ne ya yi magana da su domin shi kam Yunusa ya yi nisa cikin Habiba. “Yan mata dan Allah me da me ake siyarwa gidannan?.” Habiba ce ta  tsaya ita kuma ƙawarta ta shige ciki, domin irin matan nan ne masu jin kai. “Taliya da wake, sai kuma gurasa da miya.” “Yawwa dan Allah, za ki iya amso mun taliya da waken?.” Audun ya ƙara tambaya. “Kawo.” Kuɗin ya miƙa ma ta sanan ya ce. “Mai za’a siya maka?.” “Koma mene ta siyo.” Ido ta ɗago ta kalleshi, ita ma take a lokacin ta ji wani abu ya ratsa zuciyarta, irin kallon da yake ma ta ya shige ta. “A’a ka faɗa me za’a siyo ma ka.”  Ta ba shi amsa. “Si yo gurasa to.” Ba ta ce komai ba ta shige gidan. Bayan ta shige gidan ne, ya kalli Audu ya ce. “Abokina wallahi na sami matar aure.” Dariya Audu ya yi sanan ya ce. “Ai tun kallon da kake ma ta na fahimci haka, Abokina kar ka yi wasa ita dama sau ɗaya take zuwa a rayuwa.”  “To ta ina xan fara?.”  “Ya kake Abu kamar ba ka san yadda xaka fara ba?.”  “Audu kasan ban ta ɓa kula mace ba ko?.” “Amma ai kana da ‘yan matan.” Tsaki ya ja sanan ya ce. “Kamar ba ka san sune ke kawo kan su ba.” “Yanzu dai ka fara tambayar sunanta, da gidansu, daga nan zaka san yadda zaka bi da ita.” “Angama abokina.” Suna tsaye ta fito riƙe da ledar, ta miƙa mu su. “Mun gode.” Audu ta faɗa, shikuma Yunusa ya ce. “Yan mata anan gidan kike?.” Girgixa kai ta yi sanan ta ce. “ A’a, nan baya na ke.”  “Ina ne nan baya kuma?.” Murmushi ta yi mai sanyi sanan ta ce. “Layin dake bayan wanan.” “Ohky, nagane toh amma ai baki fadan sunanki ba,  kuma ni na faɗa miki nawa.”  “Bala fadamun ba Allah.” Ta ba shi amsa cike da shagwaɓar da ta ƙara burgesa. “Anya kuwa bam fadamiki ba.” Ya faɗa cike da wasa. “Allah dagaske.”  “Toh, sunan Yunusa.”  “Ni kuma Habiba.” Daga nan suka fara yar hirar, wacca ta jawo shakuwa sosai a tsakaninsu, tun daga wanan lokaci Yunusa ya dawo siyen Abinci a wana unguwar, hakan nan zasu tsaya su yi ta hira shida Habiba, a hankali shaƙuwa ta na ginuwa tsakaninsu, soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakanin su, wacce shi Yunusa ya sa ni amma ita Habiba ba ta san ta yi nisa cikin kogin ƙaunarsa ba.  A haka shekaru su ka fara tafiya, har ta kai ga Yunusa yana zuwa takanas wajen Habiba, duk da ba ta ba shi damar tsayawa ƙofar gidansu ba, domin tasan a tsarin mahaifinsu da zarar yarinya ta tsaya da saurayi a ƙofar gida to daga wanan lokacin zata fara ƙirgan raguwar kwanakin da zasu rage ma fa a cikin wanan gidan, kuma dukkanin yayyunta mata da suka yi aure mahaifinsu ne ke xaɓa musu miji, wasu ma ba sa sanim waye mijin sai bayan an kai su gidan mazajen su, Amma habiba ta kasance mai fatan cewa mahaifinsu ya canja tsari akan ta.  A haka aka ɗauke shekaru biyu suna tare, har ta kai ga Yunusa ya yi wa Habiba maganar cewa yana son ya tura iyayensa, sai dai ba ta ba shi dama ba sai cewa ta yi ya ɗan ba ta lokaci kaɗan, ko da ta zo gida ta yi magana da yayarta sai cewa ta yi. “Ki gwada sa’ar ki, ki ba shi dama yazo tun da sauran dai ba su ta ɓa tura maneman na su ba.” Haka Habiba ta ɗauki shwarar Yayarta ta sanar da Yunusa cewa ya gwada tura iyayensa.  Ranar da Yunusa ya tura iyayensa, ranar mahaifin Habiba ya sanar da su cewa ya daɗe da fitarwa da Habiba miji, da wanan su ka dawo gida suka sanar da Yunusa, ta shin farko Yunusa ya faɗi ƙasa sumamme. Hakan ma ɓangaren Habiba a ranar mahaifinta ya sanar da ita cewa ya fitar ma ta da miji kuma nan da makwanni biyu za’a ɗaura ma ta aure, ta fara lissafa kwanakin da suka rage, Habiba ta kaɗo matuƙa da jin wanan lamarin, ta yi kuka ta yi kuka kamar ranta zai fita, ganin ta na neman har gitsa musu gidan ya sa mahaifinta haramta ma ta fita har zuwa ranar da za’a ɗaura aurenta, tun daga wana lokacin Habiba ta shiga damuwa, kullum kuka babu ci babu sha, cikin yan kwanaki ta rame ta fige ta fita hayyacinta. Haka ɓanagaren Yunusa ma, kullum sai yazo unguwarsu Habiba, kullum nan yake yini ko zai samu ganin ko giftarwa Habiba ba ya gani, daga baya ya yanke shawarar tun karar ƙawarta, sai dai ta tabbatar mai da halin da Habiba ke ciki, tun daga hukuncin sa mahaifin ta ya yanke na ɗaura ma ta aure cikin yan kwanaki ƙalilan, da kuma hukuncin hana ta fita gaba ɗaya, sanan ta gaya masa halin da take ciki na ƙunci da damuwa.  Daga page 20 za mu gama Free pages, in sha Allahu ranar monday xamu fara paids page, a kan kuɗi Naira 500 ta wanan asusun. 8129553971 Opay sani Muhammad lawan. Gobe da safe zan sako muku last free page, shafi na Ashirin.  *HASASHEN SOYAYYA*❤️‍🔥🥹 _Imagination of love_     _Stroy and written_              By    Sayyid (Legend's pen)✍️    *FUTURE WRITERS ASSOCIATION* *(FUWA)🖋️📚*     *The Fearless Writers Team*   _Marubuta masu tsage gaskiyya_ *BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫* _Page 20_ Last of Free pages….. A cikin kwanaki ƙalilan Habiba ta fita a hayyacinta, ta rame ta canja gaba ɗaya, kuma hakan bai dakatar da mahafinta kan ƙudirinsa na aurar da ita ga mutumin da ba ta san shi ba. Ranar da makwannu biyu suka cika, ranar aka ɗaura auren Habiba da Ahmad mutumin da ba ta san shi ba, ba ta san ko sunan sa ba sai ranar, Habiba ta gigice bayan ɗaurin auren, amma ganin an ɗaura auren ya sa ta haƙura ta fawwalawa Allah komai, tasan hakan ya zaɓa ma ta, ta koma tausayin Yunusa da halin da yake ciki, ta dai na tausayin kan ta gaba ɗaya.  Yunusa kam yana lisaafe da kwanakin auren Habiba, domin ranar ɗaurin auren har ƙofar gidansu yazo domin tabbatarwa da kan sa, ya matuƙar kaɗuwa shima, ya koma tausayin Habiba da halin da zata shiga, ya bar tausayin kansa. Bayan dawowarsa gida ne ya ga babu amfanin zaman shi cikin garin Yobe, hakan yasa ya tarkata ya bar garin Yobe zuwa Kano, ya sha matukar wahala a kano kafin ya mance da tunanin Habiba, ya fuskanci sabuwar rayuwa da sabon sauyi. Habiba kam sai da ta ƙara sati guda a gidansu kafin a kai ta na ta gidan, sakamakon doguwar jinya sa ta yi, Ahmad mijinta mutum ne mai zurfin tunani da hakuri, yasan Habiba ba ta son shi shima kuma hakan, domin umarnin mahaifinsa ya bi, hakan ya sa ya yi amfani da iliminsa da tunaninsa ya dinga bin Habiba sannu a hankali yana hakuri da halayenta, har zuwa wasu shekaru da ta yarda ta karɓe shi a matsayin mijinta, ta man ta da Yunusa.  Haka shima ya ɗauke shekaru da son ta a ran sa, domin har san da ya haɗu da matarsa ya aura bayan ya samu abin hannu ya dawo Yobe state, ko da ya dawo tunanin Habiba ya sake dawo wa sabo cikin rayuwarsa, da ƙyar ya dinga yaƙi da zuciyarsa a kan ta. Wanan shine labarin Mahaifin Senate da Mahaifiyar Bhatool.  Ci gaba. “To Amma Justice aina kasamu wanan tabbacin?.” “A binciken da na yi a kan lamarin auren mana.” “Amma Justice idan haka ne ai bai kamata na hana auren Senate da ‘yar wajen ta ba, ina ganin kamar Allah ne ya tsara kasancewar su tare.”  “Yanzu zaka iya zuba ido ɗan ka ya auri ‘yar Habiba.” “Justice kenan, mai Habiba ta yi mun a rayuwa ban da alheri, sanan shi kan shi mijin Habiban ai ba shi da laifi.” “To ai mijin ma ya rasu, shekaru da dama.”  “Allah ya yi masa rahama, amma akan wanan dalilin bazan hana auren su ba.” Daga haka Dad ya shige ciki ya bar justice. Ɗakin Mom ya shiga, tana zaune gefen gado tana faman tunanin halin da ɗan ta zai shiga idan ya rasa auren Bhatool. Da sallama Dad ya shigo, amsawa ta yi ba tare da ta ɗaga ido takalleshi ba, zama ya yi gefenta sanan ya ce. “Fushi kike da ni?.” Girgiza kai ta yi kawai. “Justice ya zo mun yi magana da shi, kuma ya faɗamun dalilansa.”  “Tom yanzu me ka yanke?.” “Na yanke shawarar nema masa aurenta, domin dalilin da ya ba ni ba wanda zai hana aure ba ne.” Da murmushi a fuskar mom ta juyo sanan ta ce. “To ko kai fa, amma da ka ɗaga hankalina ka ɗaga na ɗana.”  “To yanzu sai ku sauke shi ko, domin gobe sa safe ma zan tura aje gidansu yarinyar, kuma har da ni za a je.” “Alhamdulillah ya rabbi.”  ~~~~~Bhatool…. Ƙarar da wayarta ke yi ne ya tashi daga baccin da ta koma bayan ta yi sallar asuba, hannu ta kai ta ɗauke tana jan tsaki, ba tare da ta kula da mai kiran ba. “Hello.” Ta faɗa murya cike da magagin bacci. “Bhatool.” A zabure ta miƙe jin muryar Dr Hisham. “Na’am.” Ta faɗa a tsorace. “Bhatool aure zaki yi?.”  “Innullahi wa’ina illahir raji’un.” Ta furta a zuciyarta, a fili kuma sai ƙara cewa ta yi. “Waye?.”  “Dr Haisam ne.” “Ina kwana?.”  “Bhatool tambayar ki nake fa.” “Ni ba auren da zan yi, bikin Suhaima fa a ke yi.”  “Nasan ai bikin Suhaiman ake yi, amma ke ma ai aure zaki yi ko?.”  Shiru ta yi ba ta iya cewa komai ba, sai zallan mamakin yadda a ka yi yasan da maganar. “Toh Bhatool, ki je ki yi auren kin ji, zaki ga ni a idonki.” Daga haka ya kashe wayar, shiru Bhatool ta yi “wanan wace irin masifa ce, waye yasan ma zan yi aure?.” Ta tambaye kan ta, amma sanin babu mai ba ta amsa ya sa ta yi shiru, ƙofar ɗakin aka buga sanan a ka ce. “Wai yau ba zaki fito ba?.”  “Gani nan Yaya.” Ta faɗa tana mikewa, a falo ta sami Yaya Karima da mijinta suna zaune, ƙarasawa ta yi inda suke sanan ta ce. “Ina kwana?.”  “Lafiya kalau Bhatool, kin ta shi lafiya?.” “A’a Yaya da matsala Babba.”  “Wace irin matsala kuma, ke fa mahaukaciya ce.” yaya Karima ta faɗa. “Ba irin wanan matsalal ba ce, kuma ni bake nake wa magana ba, Yaya Ka na ji?.”  “Ina jinki Bhatool.” “Akwai wani malami a makarantar mu Dr Haisam, ya ce yana sona, kuma ɗan iska ne kowa ya san shi a makaranta, ranan ya yi mun baraxana na zo na faɗawa Yaya Karima, yau kuma ya ƙara kirana yanzu wai aure zan yi ko?.”  “Ai ina ya samu labarin zaki yi aure to?.” “Nima Yaya bansani ba wallahi.”  “Yanzu da safe nan mahaifin senate ya kira ni, bayan na je ya sanar da ni yana so zai ce ya samu su kawu yau shi da yan uwan sa, a sanya lokacin aurenku na yi tunanin ke ma bakisan maganar ba?.” “Yanzu dai nasan magnar da kafaɗamun.” Bhatool ta faɗa sabida ita gaba ɗaya ta tsorata da lamarin Dr. “To amma shi ina ya sa ni?.” Yaya Karima ta sake tambayarta. “Wallahi bansani ba Yaya.”  “Ba ni lambarsa kawai.” Miƙa masa wayar ta yi yaɗauki lambar. “Ki ta shi ki je ki yi breakfast.” Yaya Karima ta faɗa ma ta. “Tom.” Ta faɗa tana miƙewa zuwa dinning, gaba ɗaya jikin ta ya mutu.  ~~~~~~Hausari….. Gaba ɗaya yan uwan Mahafinsu Bhatool ne zaune a ɗakin Goggo Larai, cike har da Furai da Habi wayanda suka kawo gulmar, wacce suma ƙarya suka shirgo abun su.  “Ku maimaita abinds ku ka faɗa.” Isiyaku ya faɗa, wanda shine mahaifin Habi kuma yayan wanda suke son bawa Bhatool Saddiƙu, Furai ce ta fara magana. “Daman mun sami labarin cewa Bhatool tana shirin barim gari ne, ita da Yayarta da mijin yayarta, sanan Abdul za su tafi ƙasar waje shi da mahaifiyarsa da yarinyar da yake son aura har da iyayenta.”  “Kutumar b***a u**a.” Ɗan ladi ya mako wata ƙatuwar ashariya, sanan ya ɗora da cewa. “Lallai yaranan ‘yan iska ne, mun sun mayar da mu banzaye kenan ko me, Shi Abdul ɗin har ya yi kuɗin da zai tafi ƙasar waje da iyayen yarinyar da zai aura, mu gamu anan shashashai.”  “Ai yaron da manyan yan kasuwa yake mu’amala dole ya yi kuɗi, amma sabida baƙat zuciya irin ta uwarsa ba zata ba shi umarnin xuwa nan cikin dangin ubansa ya nemi aure ba shine ta tura shi duniya.” Isiyaku ya faɗa rai a ɓace.  “To ni yanzu so  nake mu yi musu dirar wuri, a yau ɗinan a ɗaura auren Bhatool da Saddiƙu, sanan shima Abdul a ɗaura masa aure da Sajida yar wajen ka Ɗan ladi, shikenan a raba komai.”  “Tabbas Larai kin yi basira kin yi tunani, kuma kin cika babba.” Auwala ya faɗa wanda shine ɗan autan su. “Yanzu yaushe zamu samesu?.” Isiyaku ya faɗa. “Ai yanzunan zamu je, ayi komai da a kan lokaci. Zasu san girman dangin uba.”  GIRMAN DANGIN UBA😂😂 1 Dangin mahaifin su Bhatool zasu ɗaura ma ta aure yau? 2 Idan mahaifiyar senate ta san asali alaƙar dake tsakanin mahaifin senate da mahaifiyar Bhatool zata bari ayi auren? 3 Mahafin senate zai je nema masa auren Bhatool,amma dangin mahaifinta sun neman riga shi, shin wane zai auri Bhatool? 4 Aina Dr Haisam yake samun bayanai, zai iya haƙura da rashin Bhatool? 5 Idan Senate ya samu auren Bhatool zai iya cika alƙwarin da ya ɗauka, ita ma Bhatool za ta yi biyayya ga Senate? Mu haɗu a cikin paids page na Hasashen soyayya, wanda zai fara zuwa ranar littinin idan Allah yakaimu, ba jira sunan jirgin namu.  Naira ɗari biyar kuɗim tikiti. 8129553971 Opay Sani Muhammad lawan Shaidar biya 08129553971 Legendspen