Showing 18001 words to 21000 words out of 51634 words

Chapter 7 - TATTALIN SO Complete Hausa Novels by Surayya.txt

Surayya   

08 Nov 2025

1404

amare addu'ar Allah basu zaman
lafiya. Amaren suka rinka zagaye tebir-tebir suna
gaisawa da kawayensu, suna yi musu godiya da
damar da suka samu ta hallartar bikinsu.
Aunty sadiya tana ta raba manyan bokitai da
farantai, da kofunan shayi na tangaram. Sun so
yin kalanda, Aliyu ya hana wai baza aje a lika
masa hoton matarsa a wani waje ba, wani gardin
ya kalleta yayi sha'awarta ba.
Da mangariba daddyn zainab ya kira Aliyu ya
tambayeshi ya maganar mansura? Aliyu ya gaya
masa yanda sukayi, yace randa ta gaji da zaman
gidan nasu saita dawo.
Daddy yace, "ashsha haba Aliyu yaushe zaka
daka shirme na mata, ai hakuri zakayi ka
rarrasheta tunda kai ka tabota, kayi mata laifi
babba, don su mata wannan shine babban laifi da
zakayi wa matarka."
don haka ni yanzu zanje wajen babanta mu
tattauna na bashi hakuri kai kuma da daddare
saika je ka tafi da matarka."
Aliyu ya rissina ya amsa masa tare da yi masa
godiya.
Daddy yayi sallama gidan Alh haruna, alh ya fito
da fara'arsa, ya bude dakin saukar bakinsa suka
shiga, bayan su gaisa daddy yake cewa, "nazo
bikon mansura ne, na tambaya dazu aka cemin ai
har yanzu tana gida bata koma dakinta ba."
Alh haruna mutumin arziki, yace kasan halin mata
sai hakuri, hauka tayi masa yace tayi zamanta a
gidansu. To in banda rashin hankali ma ya za'ayi
da hukuncin ubangiji. Allah ya kaddara hakan tun
fil azal, towa ya isa yaja da hukuncin ubangiji?
Daddy yace"hakane fa don wallahi naso na sa shi
ya hakura da auren zainab ya rinka yi min
magiya dana hakura na kyaleshi, to ya za ayi da
hukuncin ubangiji. Don Allah kuyi hakuri Alh, in
ajima Aliyu zai zo ya duketa su tafi gida." Alh ya
washe baki yace, wallahi bakomai saiya zo din."
da Aliyu yazo Alh ya hadasu da mansura yayi
musu fada. Ya dauko mansura suka taho gida.
Tunda suka taho take yi masa kuka, yace "haba
mansura, kin san bana son kuka, laifi ne kince
nayi kuma na baki hakuri ba sai ki yafe minba."

LAIFI ne kince nayi kuma na baki hakuri basai ki yafeni ba."
niba wani wallhi, ai kasan ka zalinceni, haka kawai saikoyo
aure bakamin kayan fadar kishiya
ba, kuma baka canjamin kayan daki ba." yace kiyi hakuri,
idan nagama ginina wanda zan
hadeku waje daya saina canja miki, kayan fadar
kishiya kuwa ga akwatuna biyu can da kudi dubu
dari suna dakinki na ajiye miki."
sannan tayi shiru tana Allah-Allah suje gida taga
irin kayan da yake cikin akwatunan. Suna zuwa
gida shiya bubbude mata akwatunan ta gani,
kaya masu kyau da daraja da tsada, kala goma,
super, holland,leshi, shadda,ingila, diamond,
takalma uku, mayamayai da turaruka da
sauransu.
Ta zumburi baki tace ita kala nawa kayi mata?
Yace, "ba abinda ya shafeki bane wannan, tace
dama mana kace haka, kaci amanata na rike
yarinya ta gama sanin sirrina ka aureta." ya daga
mata hannu yace, "ki rinka yiwa bakinki linzami,
tun kafin nasan zan hadu dake nake son zainab,
tanada shekara daya aduniya mamanta ta bani
ita. Shiyasa lokacin da mamanta ta rasu na dawo
da ita gidana gabana don nasa ido sosai akanta
kada wani ya hure mata kunne. Yayi ficewarsa ya
barta ta dora hannunta aka tana zunduma ihu.
Ranar lahadi akayi wuni ni'ima taci kwalliyarta,
tna cikin kawayenta sunata hotuna da bidiyo.
Zainab kuwa tana cikin dakin hajiya tana
kudundune tanata aikin kukanta, sadiya ta shiga
ta dagota, "haba zainab wai miye hakane, yanzu
du kaunarku da yaya don an aura miki shi kike
kuka irin haka?
Tace, yaya sadiya aunty mansura fa marikiyata
ce, kuma saina juye na zama kishiyarta."
to meye ba haka Allah ya shirya ba. Ta lallabata
tayi wanka, ita ta shiryata ta dandasa kwalliya
cikin wata dakakkiyar galila da akayi mata dinkin
bubu, ta aikatu da surfani ta nada mata dan
kwalin shaddar kamar nadin gwaggwaro.
Tasha gwal tanata sheki, ta fito da ita zuwa
babban falo, mutane sai guda suke suna binta,
maroka kuwa sai wasata sukeyi. Sadiya ta fito da
kudi tana watsa musu, ta zaunar da ita. Ni'ima
tazo ta rungumota tana cewa, "haba my sister ko
kefe. Kawayenta du sunzo sun zagayeta ana yi
mata shekiyanci, bata iya cewa komai sai
hawaye.
Jikinta kuwa ya dumame da zazzabi, aunty
sadiya ta bugawa Aliyu waya, yana dauka tace,
"hello yaya, dama cewa nayi zainab ce ba lafiya
take fama da zazzabi, shine nace ko zaka bari a
barta a gida inta samu sauki akwota? Yace dan
Allah gafara can, inkun ajiyeta a gidan me zakuyi
mata inbanda ku dameta da sannu-sannu. Kunga
ku kawo min matata na bata kyakyawan kulawa."
tace "a yaya haka za'ayi?
Yace ku bata waje ta kwanta ta huta kada kusa
mata ciwon kai, bana so kudameta da hayaniya."
'yan wajen suka sa ihu da dariya.
Zainab kuwa ta dafe kai data ji yana sara mata.
Da daddare akayi jerin gwanon motoci, sai aka
raba jama'ar biyu, rabi zasu kai zainab da
kawayenta rabi kuma zasu kai ni'ima da
kawayenta.
Ankai ni'ima janbulo kabuga, gidanta babba mai
kyau ita kadai abunta, zainab an kaita nasarawa
G.R.A gidanta mai kyau zaman mutum daya,
fadan kyaun gidan bata lokacine. 'yan kawo
amarya sun zagaye ko ina kowa sai santin gidan
yake. Da yanda aka tsara komai, gashi ba wani
babba bane tsarin turai ne komai, 'yan kawo
amarya zasu tafi zainab ta kankame aunty sadiya
tana kuka.
Sadiya ta rasa yanda zatayi mata saboda yanda
taga jikinta yana karkarwa, yayi zafi zau, zazzabi
ne mai zafi. Sadiya tayi mata dabara tace "zauna
anan na samo miki magani da ruwa a kicin.
Ta zaunar da ita a bakin gado ta fice da sauri
tana kuka, bata ankara ba taji gidan shiru alamar
kowa ya fashe kenan. Ta dora kanta kan filo taci
gaba da zubar da hawaye, kanta yanata sara
mata, ta dora hannunta akanta ta dafe shi.
Aliyu yayi sallama cikin sanyi muryarshi, du da
tasan muhimmacin sallama amma saita kasa
amsawa, saboda wani irin rudani data shiga, itace
yau da yaya Aliyu a daki daya, daga ita saishi a
matsayin matarsa ta aure. Ko ina auntyn nata?
Yanda dai taji anata zugugun gidan tasan ba
gidan da auntyn take ya kaita ba. Yazo ya zauna
a bakin gadon, ta zame kasa tace, yaya ina wuni?
Ya dagota "lafiya lau zainab ya taro? Tayi shiru
tana sheshshekar kukanta. Yace zainab kiyi
hakuri nasan bakya sona, kada kiga na takuraki.
Zainab tsananin kaunar da nake miki bazan iya
bawa wani aurenki ba, saina ga kaman zai cutar
min dake. Kiyi hakuri zainab kidaina yawan kuka,
bana so ki jawowa kanki matsala, a sannu a
hankali wata rana zaki soni, kinki zeeyta?
Ni jininki ne dan'uwanki ne, ki daina damuwa
akaina kinji babyna."
yana dan bubbuga bayanta na rarrashi, ya shafa
cikinta, "kinga cikinki kwalam kina zama da
yunwa, bana son zamanki da yunwa kada olsa ta
kama minke.
Ya jaeo ledar kusa dashi yana zaro katon nadin
takarda, gasassun kaji ne guda uku, sai robobin
youghot da ice-cream, ya yago naman zaisa
mata abaki ta kauda kai, cikin sigar rarrashi yace
kinga, "kinsan bana son gaddama, ki karba kici."
ya rinka bata tana ci, a zuciyarta kuwa tunani
take yi, wai dama yaya Aliyu zai iya rarrashin
mutum da lallabashi haka? Yau babu wannan
fadan da hargagi na yaya,..

YAu babu fada da hargagi irin na yaya, sai wani ji
yake da ita. Lallai namiji kenan.
Ta kifa kanta a jikin gadon saboda yanda taji
yana sara mata kamar zai rabe biyu, yace zeeyta
mene ne? Ya dagota yaji jikinta zafi zau, yace, ya
ilahi. Yanzu zeeyta bazaki daina sama kanki
damuwa akaina bako? Ta rinka lumshe idonta
yana kokarin rufewa, saboda azabar ciwon da
kanta yake yi, Aliyu hankalinshi ya tashi, ya
kwantar da ita ya mike ya shiga kicin ya debo
ruwa awata a silba, ya taho da hankicif.
Ya kwantar da ita a cinyarsa ya cire mata rigar,
sai farar shimi mai kyau a jikinta, ya rinka tsoma
hankicin a ruwa yana goga mata jikinta. Sannu a
hankalin zafin jikin nata ya fara raguwa, ya bata
magani tasha, ya barta daga ita sai bes da siket,
ya shimfideta a gado ya mike ya koma kicin don
ya mayar da kayayyakin ciki, ya jere ice-cream
din da youghot din a firij, ya shiga dakinsa ya
fada toilet yayi brush, ya saka kayan bacci ya
koma dakin bayan ya rufe ko ina, ya tofe ko ina
da addu'o'i ya hawo gadon. Tuni ta dade da fara
bacci, ya dagota ya dorata akan kirjinsa ya
rungumeta, a zuciyarsa ya ringa jin wata irin
nishadi, wai yau shine rungume da zainab dinshi,
ashe zaiga wannan rana? Ashe wannan lokaci
yana nan zuwa gareshi? Yaso suyi sallah raka'a
goma sha biyu don nuna godiyarsu ga Allah, to
matsalar rashin lafiyar zeey dinshi hankalinshi ba
akwance yake ba.
Zainab ta dan motsa, ya rinka jijjiga ta yana
lallabta kamar yarinyar goye, da yake zazzabi ya
sauka baccinta take yi sosai.
Sai wajen asuba ta farka, tana jinta rungume
ajikin yayanta Aliyu du kunya ta dame ta, tana
kokarin zame jikinta daka nasa sai ji tayi ya sake
kankameta, dole ta hakura amma du kunya ta
isheta, ta kasa wani kwakkwaran numfashi.
Saida akayi assalatu sannan ya shimfideta a
gadon, ya rada mata akunnanta, "ki tashi kiyi
sallah ni zan tafi masallaci.
Ita kunyarsa take ji sosai, bata iya amsa masa
ba, ya fita ya nufi dakinsa ya shiga toilet ya
daura alwala, ya fita masallaci.
Ta mike tana mamakin yaya Aliyu, daman haka
yake? Tayi alwala tayi raka'atul fijir, ta tashi tayi
sallar asuba, ta gama laziminta ta daga hannu
sama tana addu'a, Allah ya basu zaman lafiya,
Allah ya hada kanta da kishiyarta yaya Aliyu Allah
ya kara buda masa, Allah ya bashi ikon yin adalci
a tsakaninsu. Ita kuma Allah ya bata ikon yin
biyayya ga mijinta.
Tana cikin yin addu'a yaya Aliyu ya shigo, sai ya
huce dakinsa. Tayi sauri ta shafa addu'ar ta
koma dakinta saita rufe kure kofofi, don ita a
tunaninta da wani ido zata kalli yayanta.
Daya taba kofar tata yaji ta rufe, sai yayi
murmushi kawai ya koma dayan dakin ya kwanta,
sai sannan ya samu bacci mai karfi ya daukeshi.
Karfe takwas ta tashi ta shiga wanka, ta shirya
cikin riga da siket na shadda ruwan goro dinkin
stayil ne, anyi mishi hawa-hawa kamar asabari,
an zuba dutsuna aciki yana ta walwali. Farar
fatarta tayi das aciki, ta hade kananan kalabar
kanta tasa ribon ruwan goro ta daure, ta feshe
jikinta da turare tana ta zuba kamshi.
Ta rinka jin ana kwankwasa kofar falon, taje ta
bude. 'yan gidansu ne hamza da sadik suka kawo
musu abun karyawa. Ta basu hanya suka shige.
Hamza ya kama tsokanarta, "amarya kinsha
kamshi, don Allah du kukan da kika sha jiya harda
su zazzabi amma kalleki yanzu shar dake kinsha
kwalliya.
Yace kin hakura kenan? Tace "ban hakura ba,
yanzu zan biku mu tafi tunda ku kuka fara zuwa."
sadik yace kibi su wa?
Na biku mana." hamza yace rabu da ita fade
take, ina zata iya zuwa, data sha bulalan Yaya.
Sadik yayi dariya, yace irin wacce tasha data yi
zance ba. Gaba daya suka sa mata dariya.
Tace to ya isa, tunda kun kawo aiken da akayi
muku kuzo ku tafi. Sadik yace zamu tafi bamu
gaisa da yaya ba? Tace to bacci yakeyi.
To ki taso mana shi mana.
Ya zan taso shi yana bacci aiba haka akeyi ba.
Hamza yace, "wati har kin fara rowarsa ko? Tace,
"kai ka sani.
Suka fice suna mata dariya. Ta bude taga
shiryayyun break din da akayo musu ta girgiza
kai tasan iyayensu mata ne zasu yi ba
'yan aiki ba.
Ta shirya komai a tebir, tuni ta gyara falon tasa
turaren wuta mai dadin kamshi. Daga bayanta taji
motsi, tasan Aliyu ne, saita kasa juyawa, a haka
ta durkusa tace, yaya ina kwana?
Sai shima ya durkusa ya dora kansa a bayanta
yace, "haka akeyin gaisuwa a juyawa miji baya?
Yace "zeeyta ya jikin, meyasa kika rufe min kofa
da asuba?
Du ya saukar mata kasala ta kasa wani katabus,
wai shi yaya baisan kunyarsa take ba, meyasa
yake yi mata hakane? Ya kama shafa
wuyantayana cewa "zeeyta zazzabi ya sauka ko?
Ta rasa yanda zatayi, du ya kanainayeta,
kunyarsa da nauyinsa ya isheta, gashi ta gaji da
tsugunan.
Ta zame zata zauna ya tallafota jikinsa a hankali
yana shakar ni'imtaccen kamshin jikinta,
muryanta can kasa cikin marairaita tace "don
Allah yaya ka bari, kunyarka nake ji.
Cikin kunnanta ya rada mata, kidaina jin kunya ta
nifa mijinki ne, kin taba jin inda mata take jin
kunyar mijinta? Kefa malama ce kinsan hakkin
miji akanki, kada kunyata tasa ki sabi dokokin
ubangiji, ki saki ranki ki saki jikinki.
[9:16AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**11, 2**12 & 2**13

ALLAH NE ya shirya aurenmu, kodai akwai haramci aciki?
Ta girgiza kai alamar a'a ya dagota, taso muje muyi break,
dura zan ringa yi miki bana son
zamanki da yunwa."
ya riko hannunta zuwa kan tebir din, yana bude abincin
yana shirin zuba musu, ta rike hannunsa,
ka bari yaya na zuba mana.
Yace, yauwa ko kefa, ai gwanda ki fara aikin lada." ta zuba
masa farfesun da soyayyen dankali
da kwai, ta hada masa tea mai kauri, ta tura masa
gabanshi.
Yace to sannu, muci." ta girgiza kai tace, bana jin yunwa."
yace, "kinfi so na miki dura kenan?
Ta hada tea kadan tana sha a hankali. Ya zuba
mata ido, shi yarinyar sha'awa take bashi, komai
nata a nutse cikin hankali da nutsuwa. Suna
gamawa ta kwashe kayan ta kai kicin. Shikuma
ya zauna akan doguwar kujera. Tazo zata huce
ta shiga daki, ya jawota ta fada jikinshi, yace
mata a kunnenta in zaki je kibar mijinki? Zo muyi
hirar soyayya, nine fa haidar dinki kin manta da
hirarmu da mukeyi mai dadi? Ta boye fuskarta.
Yayi murmushi wayarshi tayi kara, ya dauka da
sauri ya kara a kunnensa, ya rissina tare da cewa
hello, umma ina kwana?
Lafiya lau, ya jikin zainab din?
Yace, dasauki umma gata nan ma
ya nana mata wayar a kunnenta, ga umma zata
yi miki ya jiki.
Ta noke um-um, nidai kunyarta nake ji. Yace au
yau kunyar umman taki kike ji, bazaki amsa mata
wayarta ba?
Cikin sanyinta tace, hello, umma ina kwana?
Lafiya lau zainab ya jikin naki? Da sauki umma.
"kiyi hakuri zainab kinji, yanda nasanki da hakuri
da biyayya ki kara akan da, kada kisa kunya a
harkar aure, saita jawo miki halaka kinji zainab?
Cikin sanyita tace to umma, nagode, don Allah
umma ku daina wahalar da kanku wajen girki don
Allah umma kada asake kawowa zan girka da
kaina.
Anya zainab, ki bari ki kara hutawa mana ba zaki
iyaba akwai wahala. Tace bakomai umma zan
iya. To shikenan zainab Allah yayi miki albarka."
amin umma.
Ta kashe sannan Aliyu ya cire mata wayar daga
kunnenta, yace, "nifa kada kije ki kone ko ki
yanke, zaki ce zaki iya girki da kanki.
Tace yaya niba mace bace, ai dole nayi girki, zan
bar iyayenmu suna wahala ne? Ai saidai mu muyi
musu don su huta mu kuma samu lada ko? Ya
daga mata kai kawai saboda shi yana yabawa da
hankalin zeey din tashi.
Tace, yaya kaje ka gano aunty da Ahmad kaga
yasuka kwana? Au har korata kikeyi?
Tace ba haka bane yaya, gwanda kaje kaga yanda
suka kwana.
Ya gyada kanshi zanje, daganan zan wuce office
din daddy da Abba na gaishesu.
Sha biyu dai-dai ya fita ya nufi gidansa, yayi
sallama falon mansura tana zaune bata amsa ba.
Ya shiga ya zauna bata juyo ta kalleshi ba.
Yace yau bakisa su talatuwa sunyi shara da
wanke wanke ko ina kaca kaca haka? Tace, tunda
kazo ai saikai kasa suyi.
Ina Ahmad kinsa ankaishi makaranta daiko?
Tace nidai kada ka dameni, ka damu da
rayuwarsa meyasa baka tafi dashi can gidan naka
ba? Wai don Allah ko kunya baka ji ka riki yarinya
ka aureta yau ka kwana gado daya da ita har
wani abu ya faru a tsakaninku? Wannan abun
kunya da yawa yake, wallahi idona idon yarinyar
nan saina raunanata.
Ya daka mata wata irin tsawa data firgitata, yace,
wallahi ki kiyaye, du ranar da kika sake kika dora
hannunki akan matata saikin gane kurenki wallahi
sainayi maganinki. Bissimillah kije ki tabata.
Abunda yasa kenan nakasa bawa kowa auren
zainab, don kada wani ya cuceta, shiyasa na
aureta don nabata kulawa, sannan ke kuma kice
zaki daketa. Wallahi da sai kin raina kanki." ya
mike ya fice ya bar mata gidan, yayi office din
iyayensa.
Zainab kicin ta shiga, inda duk aka jere mata
kayan amfanin kicin kamar a turai, du wata
na'ura da zata dafa abu kota gasa abu cikin
sauki an sa mata aciki.(nan yanda za ayi
abincine nasan basai na rubuta ba)
Ta gama abinci ta shiga wanka ta dauro alwala,
tayi sallah tashafa mai, ta shafa farar hoda du da
ba wata kwalliya tayi ba saida ta kara kyau tasa
atamfa holan baka, dinkin karamine yayi das
ajikinta, ta fesa turaruka tanata kamshi.
Ta jona abun turaren wuta, mintuna kadan gidan
nata ya dumame da kamshi. Tana so taji
mutuniyar tata yayarta ni'ima, to bata tunda yaya
ya fasa mata wayarta batayi wata ba. Koda yake
bawa zai ba tunda shine me sayen?
Yaya Aliyu yayi parking motarsa ya fito a harabar
gidan, daddan kamshi daya ji yana tashi shiya
shaka ya ratsa masa zuciyarsa, saiya ji ya
sanyaya masa rai. Yayi murmushi ya shige ciki,
ya tura kofar falon ya shiga da sallama. Tana
zaune akan kujera ta amsa sallamar kanta a
sunkuye.
Yazo ya zauna kusa da ita, saita zame kasa ta
durkusa, "yaya sannu da zuwa." ya dagota ya
karata ajikinsa yace, "zeeyta meyasa baki taso
kin tareni ba kina oyoyo sannu da zuwa yaya?
Tace, "a da girmaba?
Wane girma kike dashi? Kefa babyna ce. Ta rufe
idonta, yaya kana sani jin kunya.
Zanyi kokari na cire miki kunyar nan dai ta daina
takura mana." don Allah yaya ka bari, ga
abincinka can a tebir." a lallai yau zanci girkin
amaryata, to taho muje ki bani. Ya riko hannunta
suka jere harkan tebir din, ta jawo masa kujera ya
zauna, tana bude abincin kamshi ya bugesa ya
lumshe ido.....

TA loda masa abincin ta rinka tura masagabansa, tasa
masa cokali, ta zuba masa hadinlemo data yi masa. Tace
yaya kaci mana." yazaunar da ita kusa dashi, ya debo a
cokalin yanufo bakinta, tace dn Allah yaya kaci, nasan
fabaka ci komai ba tunda safe. Nikuwa nasha ice-
cream."inbanda ke wa yake maida ice-cream abinci. Yabata
ta karba cikin kunya taci, shima yaci yceum-um carkwai,
waya koya miki girki haka?Tayi murmushi ta sunkuyar
dakai, ya rinka cinabinci yana santi, saigashi yaci dayawa.
Ta rinkamamaki ashe yaya yana cin abinci? Ita saita gaidan
aunty ta ajiye masa, idan yazo kokarinsayayi cokali biyu ya
ajiye.Intayi magana yace yakoshi. Saidai suyi ta ciye-ciye,
da yamma kuwa ya tafi gida yaci acan.Kodai daman rashin
dadi ne yake hanashi ci?Yana tafiya sallar isha ta rufe
dakinta ta kwanta,daya dawo ya taba kyauren yaji shi a
rufe, saiyakoma dayan dakin yayi kwanciyarsa.Da asuba
daya fito sallah ya buga mata, saidayaji motsin tashinta
sannan ya tafi masallaci.Yana dawowa dakinsa ya shige ya
koma bacci.Itama baccin ta koma, sai karfe takwas ta
miketa shiga kicin, tana gamawa ta kwashe komai tajera a
tebir, ta gyara kicin din ta share ko ina, taturare shi da
turaren wuta.Ta koma dakinta ta shiga wanka, tana fitowa
tashirya cikin wani jan les riga da siket, dinkinkaramine yayi
das ajikinta, sai kamshi take.Tana jera kayan kwalliyarta
akan madubi yashigo, ta durkusa da sauri tace yaya ina
kwana?Yace bazan amsa." ta marairaice, haba yayasaboda
me bazaka amsa min gaisuwata ba?Kinyi min laifi jiya kin
rufe min kofa." kayi hakuriyaya kunyarka nakeji.To zeeyta
me zanyi miki, na sani ke yarinya ce,nima ina tausayinki, ki
saki jikinki ba abundazanyi miki, rainonki zan tayi har sai
kinyi wayo,kada ki kuma rufe min kofa ina tsoro kada
waniabu ya sameki a daki ke kadai, gwanda munatare a
waje daya.Saiki yi kwanciyarki a gado, ni saina
kwantaakasa. Kinji zeeyta? Ta daga kai, kayi hakuriyaya
bazan kuma ba.To shikenan na hakura.Yaya ga break
can.Zeeyta harkin gyara waje haka kinyi wanka?Zainab aiki
yayi miki yawa, kodai asa umma tasamo miki mai aiki?
Haba yaya zan iya komai, wallahi malaminmu yagaya mana
du abunda kayi a gidan mijinka ladane, idan ka bawa wani
yayi maka, to shi yake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login