Showing 21001 words to 24000 words out of 51634 words
daladan ba kai ba. Nikuwa yaushe
zan yardalahirata mu rinka rabawa da wasu?Ya gyada kai,
haka akeso zeeyta, mutum ya rinkaamfani da abunda yake
karanta.Akan tebir inda ta shirya masa break ya rinka
ciyana santi yana sa mata albarka. Saida yacidayawa ya
koshi yayi hamdala, yace zeeyta zokigaya min waya koya
miki girki ne? Naga a gidanauntyn naki bata fiya yi ba bare
nace gani kika yitana yi kka koya.Yaya a makaranta mana
ai har fanni koyon girkiakwai, shiyasa in mun tafi tun safe
sai shidda nayamma za a tashi. Yaya Aliyu yace ai
makarantartana da kyau, daddy baya wasa a harkar
ilimi."wayar tasa tayi kara, ya dauka yace, ke ina kikabar
mijin naki kika bugowa mutane waya dasassafe? Kayi
hakuri yaya, wallahi inaso injizainab shine na bugo a
taka.Ta gaisheshi. Ya mikawa zainab wayar, ni'imatana
jinta tace mutuniyar ya akai? Ina taso najiyo ki saina tuna
kefa kurmace yanzu tundabakida waya. Wai ya yayan ne,
komai ya faru ko?Zainab tace oho! Ke kika sani. Yaya ni'ima
inakika barshine?Yana kicin yana soya mana
break.A'uzubillahi, kiji tsoron Allah kina zaune mijinkiyana
kicin."ni'ima tace, ai shiya jawo, bashi ya dora mingajiya ba,
a wahale nake ba abinda zan iyayi. Aiya kuma shiga
kicin."ke yaya ni'ima wace irin gajiya ce da zata
hanakishiga kicin?Ni'ima tace 'a daga jin bayaninki
bakisankomaiba. Wai yaya kallonki ya tsaya ne haryanzu
baiyi miki komai ba?Tace "don Allah yaya ni'ima ki bari ni
bana sonirin wannan maganan.Zainab da wahala fa, nima
nasha wahala bare keda kike yarinya.Zainab tace don Allah
kidaina min irin wannanmagana, Allah zan ryfe
wayar.Ni'ima tace wai yaya na wajen ne koya tashi?Tace
mata, oho ke kika sani, ni dai ki bari banaso."to shikenan
naji matsoraciya, wata rana da kankizaki zomin da zancen
bazan saurareki ba.Tace, eh naji na yarda. Ta rufe wayar
tana dariya.Yaya Aliyu yace, me take gaya miki kike
cewabakya son ji? Gaya min ni."tace kai yaya nidai ba
ruwana. Ta tashi zatagudu daki ya rikota, zeeyta ba zaki
gaya minba,ni inason ji gaya min kinji.Ta boye fuskarta, don
Allah ka bari ni bazan iyaba. Wata wayar ce ta sake
shigowa, da yayi birisda ita saida yaga numbar mai
bugowan sannanya daga.Hello mansura ya akayi?
Hello! Mansura ya akayi? Jin yaambaci mansura tasan
auntynta ce,kawai saita mike zata bar wajen, yazuba mata
ido yana kallon yanayinyanda take tafiyarta kamar bata
sontaka kasa, yarinyar ta shige ransadayawa, yanda yake
jin kaunarta tarinka azalzalar zuciyarsa, dole sai yaganta
koya ji muryanta, inba hakaba baya iya rintsawa. Son
gaskiyakenan, ko yaushe yana ranka. Yaugashi zeey dinshi
a matsayinmatarshi ta aure, ko yaushe mafarkinnasa zai
tabbata ya ganshi manneajikinta suna faranta ran juna?
Tace baka jinane? Yace inajinkimansura ya akayi? Dama
yar lawisakawata ce ta haihu, shine zamujesuna.Yace a'a
bazaki ba.Saboda me? Kana ganin irinamintakar da take
tsakaninmu dalawisa, amma kace bazan je sunanyarta
ba.Eh nace bazaki ba, kada kuma ki sakekiyi min
maganar.Ta kama maganganu, "haka kawai adakeka a
hanaka kuka, ka gama cinamanata ka auri 'yar dana rika
kumani ka rinka takurawa rayuwata kanagallaza min. Haka
kawai kai ba'agidan kake ba kuma ka hanani fita,zanta
zama ne ni kadai kamarmayya?To ya isheki haka, ina gaya
miki kirinka iya bakinki, ki rinka saninkalmar da zaki gaya
min.Ya kashe wayar.Lawisa ta kalleta, tace, to ya ya,
yabarki? Ta tabe baki, ya hananizuwa." lawisa tace mugu,
dayakyaleki muka je wurin malamin nandu taurin kansa sai
yayi laushi, donsaiya lankwasa mik shi, saikin juyashi a
tafin hannunki. Amma yanzuma ba zama za ayiba, ki bani
kudi ninaje miki." tace to. Ta mike ta shigedaki, ta fito da
kudi ta bawa lawisa.Yauwa kin gani ba, ai Aliyu dazainan
sun shiga uku, sai sun sansunci amarki."yauwa aminiyata,
don Allah kikokarta, kada kiji komai kawata.***** ****
*****da daddare ta bar yayan nata a faloyana kallo, tayi
shiri kwanciya bacci,saita rasa ya zatayi saboda yayanyace
kada ta sake rufe kofa takwanta bacci ita kadai a daki. To
yazatayi?Ta dauko bargo da filo takudunduna a kasa kan
kafet, tayiaddu'o'inta ta shafa, ba jimawa bacciya
dauketa.Du da har yau 'yar uwar tashi takisakin jikinta
dashi, saboda tsaninkunyarsa data keji, shidai yana so
yakasance tare da ita, don inya kalletasaiya ji farin
ciki.Intayi magana kalamominta sai sunsanyaya masa
zuciyarsa, yana sonyanayin maganarta cikin shagwabada
sanyi, bata son yawan hayaniyaamma baza a kirata miskila
ba,saboda akwaita da fara'a da kumafaram-faram da
jama'a.Tunda ta mike yaji du zaman kadaiciya isheshi, shi
kadai awajen. Donhaka ya kashe komai ya rufe ko ina.Ya
tofe ko ina da addu'o'i, sannan yashiga dakin ya rufe kofar,
ya ganta akudundune akasa cikin bargo tatakure waje
daya.Yayi murmushi ya tsugunna kasanya janye bargon a
hankali, bacci takesosai. Yasa hannu ya shafikumatunta.
Yasan shidai maikyaune, du inda ya shiga ana yabashi. 'yan
uwa suna zuzuta kamaninsada zainab. Amma ina, shidai
yasanzeey dinshi tafi dhi kyau, yarinyamai hakuri da
nutsuwa, shidai Allahya barshi da zeey dinshi.Ya dauketa
cak ya daurata akangado, ya tofeta da addu'o'i, sannanshi
ya sakko kasa ya kwanta. Shidahakan yafi mashikwanciyar
hankali, da ace zeey dinshitana wani daki shi yana wani
dakidaban.Cikin dare ya manta bai kashewayarsa ba, tai ta
damunshi da karahar zainab ta farka, tayi mamakinganin
yayanta akasa ita kuma akangado, alhalin ba anan ta
kwanta ba.Yayi tsaki cikin yanayin bacci yadaga wayar,
daga can dayanbangaren amininsa, abokin aikinsadaga
kaduna, kanal faruk yayi yomasa wayar, cikin magagin
bacciyace waye ne?Faruk yace, magagin amarci kakeyine
shiyasa baka gane lambarba?Aliyu yace "shegen gari maye
nayomin waya cikin dare haka?Ai tun dazu naso nayo
maka, sainace dai kada na katse maka hanzaribari na bari
ka gama samun untsuwatukunna."Aliyu yace, dan
ganganci, autar tamudanake ji da ita a rayuwata, aiyarinya
ce karama saita wahala.Faruk ya kwashe da dariya,
yacekaidai ko gudunka take yi, yandanasanka da kaunar
zainab anya zakasaurara mata?Ba dole ba tunda ina
tausayinta, waimeyene ka tasheni cikin dare haka?Yanzu da
idon zeey biyu ai da kafirgitamin ita.Faruk yace, ai ya zama
dole nanemeka, aiki aka turamu kasarbayelsa tafiyar
gaggawa jibi-jibnnan.Aliyu yace haba dan Allah, kumadole
saidani basu san inada sabuwaramarya ba? Ina zan tafi na
barta?Faruk yace ai anan zaka tafi ka barta,ai tasan
cigabane yazo ai bazata kicigabanka ba.Aliyu yace, wai
daga ina tafiyar tataso haka?Daga can sama takardar ta iso
manaa dazun nan office, kamata yayigobe ka taho nan
kaduna, jibi dasafe jirginmu zai daga."Aliyu yace innalilahi
wa'inna ilaihiraji'un, banso tafiyar nan ta sameni awannan
lokacin ba, ya zanyi dazeeyta?Faruk yace, kaji ka, saika ce
wanimace, kai ba namiji bane. Kakarfafawa iyalanka gwiwa
har mujemu dawo. Bari na barka sai gobeninka iso."da safe
tun wuri ya tashi, zainab tanakicin tana hada break, tana
fitowataga yayi zugum alamar tunani. Takawo break din ta
jere, tazo tadurkusa agabansa tace, yayamenene?Ya rike
hannunta zainab tafiyace tasamemu ba shiri."
A daure ayi likes da comments
[9:19AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**14, 2**15
YA rike hannunta, zainab tafiya ne ta samemu bashiri.Toh
don Allah yaya meye abun damuwa? Bakasaba tafiye-
tafiyen nan ba, zaka sawa kankadamuwa. Don Allah ka cire
komai daga ranka zomuyi break din.Ya biyota kan tebir, ta
rinka jan ra'ayinsa yanatura abincin aciknsa, har yaci mai
yawa. Yacemata zaije wajen mansura yanzu zai
dawo."yana fita zainab murna ta rinka yi sosai, zatakoma
gidansu kafin yaya ya dawo.Aliyu yana shiga falon
mansura yaji shiru, yashiga cikin dakin tana kudundune
cikin bargo, yazauna gefen gadon ya zanye bargon, ta
budeidonta, tana ganinsa tayi zumbur ta tashi tace,lafiya
yanzu da sassafen nan?Yace lafiya lau ke baki san ma
garin ya waye bako?Karfe goma kina kwance. Kaduna zan
tafi yanzu.Tace au har amaryar ta ginsheka ka fasa yi
matakwana bakwai, yau fa kwananku hudu.Yayi tsaki ya
harareta, ki rinka sanin kalmar dazaki gayamin.Yau zan
koma kaduna zamuyi asubancin tafiyabayelsa aikin
gaggawa.Tayi dariya da shewa, Alhamdulillah, Allah nagode
maka, ai gwanda ka tafi. Ya bude baki yanamamaki, au har
so kike ma na tafi bakya sonzamana kusa daku."tace
wallahi bana so, aini tafiyarka tafi komaikwanciyar hankali
awajena. Ya daga mata hannuto naji, ya kuma isheni haka
kafin ki fara fatannabar duniyar. Kiyi min lis din abunda
kukebukata keda Ahmad. Sito dai cike yake da
kayanabinci.Tace "zaku dade ne?Ya mutsa fuska, eh to
zamu iya yin sati hudu kozuwa sama.Ta hau lissafe-
lissafemai dalili da mara dalili. Yabata damin kudi kamar
yanda tace ya kara matawasu ma akai.Ya mike zai fita yace
mansura kiyi min addu'a,anason addu'ar mace zuwa ga
mijinta, Allah yanaamsawa zan biya makarantar su Ahmad
yanzumuyi sallama, don Allah ki kula da komai, kijagirmanki
da mutuncinki, don Allah kada kuyiabunda zai daga min
hankali.Kinga yaki zamu tafi, ko mudawo da rai koakawo
gawarwakinmu, laifin da kike ganin nayimiki kiyi hakuri ki
yafemin.Jikinta yayi sanyi tace, amma kasani baka
kyautamin bako?Na riki yarinya ka aureta.Yace haba
mansura, ba zaki yarda da kaddara bakinsan bana son
mita. Kiyi hakuri don Allah kibarmaganan nan.Tace to
shikenan naji, Allah ya kiyaye hanya."yace Amin, nagode.Ya
shiga motarsa ya nufi makarantar su Ahmad,har sun fito
break, yana ganinsa ya rungumesayace Abbana har yau
aunty mami bata dawoba.kuma naje gidan Abbanka ban
gantaba, in natambayi mama ina aunty mami saita doke
bakinatace kada na kuma zancenta.Abba zaka kaini wajen
aunty mami? Ya shafakanshi, zan kaikaamma kayi hakuri
kaga yanzu tafiya zanyi wajenaikina, sainayi kwanaki
dayawa zan dawo, karinka kula kana maida kai akan
karatunka kaji.Ya rike hannunsa zuwa wani dan kes na
cikinmakarantar, ya saya masa mitfy da kek da
lemonkwalba, ya zaunar dashi ya cinye indomi da kwaidin,
ya shanye lemon kwalbar yace ya koshi.To sai ya saka
masa mitfy din da kek a jaka,yace ya koma aji.Shikuma ya
tafi gida.Zainab tun bayan fitarsa ta gama share-
sharentada goge-gogenta, ko ina yayi tas yana kyalli,
tayiwanka ta gyara kanta cikin wani material bakimai
gwaldin da gashi-gashi ajiki. Dinkin yayimata das dai-dai
jikinta, farar fatarta ta karamata kyanta da kwarjini acikin
kayan, ta feshejikinta da turararuka.Haka kawai take jin
nishadi, yau zata komagidansu du da dai tasan dole ta rinka
jin kunyarsu umma da ummi, ai saitai ta zama abangarensu
wajen babanta.Yaya Aliyu ne yayi sallama, ya katse
matatunaninta, ta mike tsaye tana yi masa sannu dazuwa,
ya nufo wajenta ya zaunar da ita, ya zaunakusa da ita yana
amsa mata da yauwa. Ya shafikuncinta kinyi kyau
zeeyta."ta mike ta nufi firij ta dauko mishi lemo da ruwa,ta
shiga kicin ta dakko masa gasashen nama takawo masa.
Yace yauwa zeeyta nagode.Yana ci yace, yanzu zeeyta
yanda kika farasangartani da wannan girki naki masu dadi
badole nayi maraicinki ba, wa zai rinka kula daniidan na
koma can?Gashi da yamma zan tafi.Tace yaya inka tafi da
yamma nikuma saida darezan tafi? Yayi saurin cewa ina?
Har yana kokarinkwarewa. Cikin sanyin murya tace, "yaya
gidamana.Kije gida kiyo me?Yaya ba a gida zan zauna
saika dawo ba?Ya girgiza kai, a ina kika taba ganin anyi
haka?Zamanki zakiyi a gidan mijinki har saina dawo.Nan
da nan hawaye ya wanke mata fuska, tadurkusa kasa
agabanshi takama kuka, "don Allahyaya ka mayar dani gida.
Idan ka dawo na dawo.Wallahi yaya tsoro nakeji bazan iya
zama ni kadaiba, kaji yaya.Ya dafa kanta yana rarrashinta,
kiyi hakuri za akawo miki wa'yanda zasu tayaki zama ko
mutumnawa ne a 'yan uwanmu, amma bazan iya
mayardake gida ba, gwanda kina inda na ajiyeki.Nidai nafi
son ka mayar dani gida.Ta kifa kanta a jikin kujera, kuka
take yi masasosai.Ransa du ya baci shi kwata-kwata baya
sonkuka.Bare kukan mace, ballantana kuma zeey
dinshiwanda tun tana yarinya baya kaunar
ganinkukanta.......
Wadda tun tana yarinya baya kaunar ganinkukanta, yanzu
yaji hankalinshi ya tashi, sai yanemo mata komai take so
sannan yake samunnutsuwa, bare yanzu data zama
mallakinsa.Ya sanyaya murya can kasa kamar zaiyi
kuka,yace "zainab so kike ki daga min hankali ko?Bakya
son kwanciyar hankalina zeeyta? Ya kikeso nayi da
rayuwata? Zainab tafiyarki gidaawajena ba karamin tashin
hankali bane. Habazeeyta kiyi hakuri ki zauna agidan ki
rikeminamanar kanki da dukiyata da gidana. Yanzu inkika
tafi bakya nan gidan ai kango zai zama.Ya zauna dirshen a
kasa ya jawota jikinsa yanararrashi, kiyi hakuri zainab ki
kwantar dahankalinki ko na samu nutsuwar zuciyata.Zainab
yaki fa zamu tafi, ko muyi nasara ko akashemu . Tayi
firgigit ya dago kanta daga jikinsacikin razana. Tace yaya
mutuwa? Ya maida kantaya kwantar jikinsa. Yace kada ki
damu, ai hakamuke, nasara tana wajen ubangiji mun
dogaradashi zai karemu, cikin hukuncin ubangiji, Allahzai
bamu nasara akan abunda muka jeyi.kita yimin addu'a kinji
kada ki kuma damuwa.Ta dago kanta tace "yaya kayi hakuri
in na batamaka ka yafe min kaji.Bakomai zainab na hakura
na yafe miki ki dainadamuwa ki taimaka min da addu'a.To
yaya na dau alkawari zan tayi maka nafilfili daaddu'o'in
neman nasara. Yauwa kanwata,nagode. Bari naje gida
nawa su Abba da daddymaganar tafiyan, wa kike so akwo
miki ta tayakizama?Hajiya."yace, hajiya babba?Ta daga
kai. Yace babbar magana, bari na gayamusu, ai 'yar gatan
hajiya ce ke zata zo.Yana fita ta mike ta shiga kicin zata
tanadarmasa abunda zaiyi guziri dashi.Tana gamawa ta
shiga tayi wanka, tayi alwalatayi sallar la'asar, ta tsala
kwalliyarta da orangedin shadda, ta kafa daurinta tayi kyau
tanatasheki kamar ba ita bace tasha kuka dazu ba. Tajeta
bude jakar tafiyar ta zuba mishi kunshin ledamai kyalli guda
hudu, daya hadadden kek ne datayi masa mai kwakwa,
dayar kuma mitfy, dayarkuma kwallon kaza, sai soyayyen
cincin maisugar data ke dashi, ta dibar masa. Daya
kena'uroro sun zo mana masu saukaka mana aiki,shiyasa
nan da nan ta gama.Aliyu kuwa daya jewa iyayensa
maganar tafiya,nasihohi suka yi masa kamar yanda suka
saba,suka yi masa addu'ar samun nasara da
fatanalkhairi.Daya zo wajen hajiya yake fada mata
sakonmuniyarta, hajiya tace "Allah sarki, ai zainab cesaina
zo na tayata zama, yarinya mai hankali danutsuwa, ka gaya
mata ta kwantar da hankalintakana tafiya direba zai
kawoni."Aliyu yace yauwa hajiyarmu, kakarmu ta kanmu,ya
bata kudi mai yawa taita masa godiya, yabawa su umma
suma sukaita masa godiya da saalbarka.Ya amsa da Amin,
ya shige motarsa ya tafigidanshi, yana ganin gimbiyar sai
yaji hankalinshiya tashi daya tua tafiya zaiyi ya barta har
nawani lokaci.Ta tare shi tana murmushi tare dayi masa
sannuda zuwa, ya zuba mata ido da irin kallon nan
maibirkita kwanyar masoyi, ya nufi wajenta, ya
warehannunshi ya rungumeta yana sumbatarta ahankali
kamar zai hadiyeta.Du kunya da nauyinshi ya isheta,
kokarin zamewatake daga jikinsa amma yaki ya bata
damarhakan saima ya kara matseta ajikinshi.Sannan ya
zauna akan kujera yana shafa kanta,du ta noke ajikinsa
kunyarsa take ji sosai.Ya rada mata a kunnenta yaushe zaki
daina minkunyar nan ne Amma zanyi kokari na rabaki
dakunyar nan.ta rufe fuskarta ta zame daga jikinsa tana
maitsananin jin nauyin abunda ya fada mata.Yace baki bani
abinci bafa taso muje ki baniabinci yunwa nake ji.Da kyar
ta mike tayi gaba yana biye da ita harzuwa tebir din, ta
bude abincin kamshinsa yabugeshi. Malmala biyu ta cire
daga ledar sunataturiri ta zuba kan filet din tangaram, ta
zubamiyan cikan tagaran din ta zuba masa kunun aya,ta
rinka tura masa gabansa. A hankali tace kacimana.Ya
jawota ya zaunar da ita acinyarsa, yace waihar yanzu
kunyarce ne? Don Allah ki cire kunyarnan ki bani abaki.
Tace um-um, nidai bazan iyabadon Allah ka kyaleni.Ta mike
da gudu tai cikin daki, yabi ta da kalloyana murmushi, saida
ta shige ciki ya girgiza kaiya kama cin abincin yana mai jin
dadinsa sosai.Ya rinka shan kunun ayar nan da yaji
madararruwa yana santi.Saida ya gama ci, ya shiga
dakinsa ya fadatoilet, yaga ta tara masa ruwan wanka a
baho, yashiga yayi wanka ya fito.Ya shirya cikin kakinsa, ya
fito ya shiga dakinta.Tana zaune abakin gado tayi tagumi,
ya zaunakusa da ita ya cire hannun tagumin yace babukyau
ki daina, ya ciro sabuwar waya akwalinta yamika mata. Ga
waya zainab kullum zamu kasancetare awaya kinji.Ta daga
kai tace nagode.Ya fito da kudi masu yawa ya mika mata,
ungowannan kirike a hannunki ki rinka 'yan bukatunki.Ta
bude baki cike da mamaki, tace ai yaya kudinsunyi yawa,
me zan siya? Komai fa da akwai asito.Ta karba ta raba
kudin biyu, tasa masa rabi aaljihunsa, don Allah yaya ka
barsu wa'yannan masun isa nagode Allah kara budi.Yace
Amin nagode nji dadin addu'arki. Ya mikezainab zan tafi?
Ta dago kanta a sanyaye yayatafiyar zakayi? Sai kuma
hawaye. Ya dawo yazauna, ya jawota jikinsa, sai kuma ta
sakar masakuka......kawaisai tausayinta ya kamani na
tsaya da rubutun ina kallonsu
Bakwa komai
[9:20AM, 05/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 2**16 & 2**17
Ya dawo ya zauna, ya jawota jikinsa, sai kuma tasakar
masa kuka.Ya rinka rarrashinta yana lallaminta
kamaryarinyar goye dake jikin mamanta, kiyi shiruzeeyta
kiyi hakuri bazan dade ba zan dawo, mekike so na siyo
miki? Ta girgiza kai bakomai." yadago kanta yana share
mata hawayen, to kiyishiru bana son kukan nan, yana daga
minhankali.Ta hadiye kukan tana ajiyar zuciya, ya
rinkararrashinta yana lallaminta tare da dan
bubbugabayanta, sanyin iskar data rinka ji ta cikinkunnenta
shiya saukar mata da kasala jikinta yasaki kawai sai bacci
ya dauketa.Ya lallaba a hankali ya shimfideta, sadaf-sadaf
yafita ya shiga dakinsa, ya dauki jakar kayansa yafice ya
fada motarsa, ya sallami mai gadi yayiwaje da gudu ya
dauki hanyar kaduna.A zuciyarshi yana tunani zeey dinshi
saita tashitaga ya tafi.Kai zeey da rigima take, du ta daga
masa hankali,inba dole ba yaushe zai tafi wani waje ya
barta.Ya zari wayarsa ya bugawa hajiya,yace dan Allah
hajiya direba ya kaiki yanzu fanabar zeey ita kadai a
gidan.Hajiya tace ai kayana ma ake sawa a mota
yanzuzamu tafi.Yauwa hajiyata nagode. Ya kashe wayar.
Lokacindaya isa kaduna ya tarar da abokinsa faruk
yanajiransa, suka rungume juna, ya dakkowa Aliyutakardar,
Aliyu ya bude ya karanta yaji bayananda suke ciki.Aliyu ya
ninke yace to Allah ya taimaka mana.Faruk yace, bari na
karasa gida na barka kadanhuta kayi shirye-shiryenka.
Tafiyar asuba zamuyigwanda ka kwanta da wuri. Aliyu yace
badamuwa. Ya rakoshi wajen motarsa ya tafi.Aliyu ya shigo
cikin gida ya wuce dakinsa, yafada toilet yayi wanka yayo
alwala yayi sallah,yayi addu'o'insa ya shafa.Ya shafa
cikinsa daya ji yunwa ta fara matsamasa, yasan yayi
maraicin zainab ko don yandatake kula dashi wajen abinci,
yanzu dole saide yahada shayi yasha, don ya gaji bazai iya
fita gidanwani abinci ba.Gashi yaronsa maiyi masa girki
shima yaje ganingida bai dawo ba. Ya bude wayarsa ya
dannalambar zeey dinshi, ringin daya tayi ana biyu
akadauka, "hello yaya." saita sa masa kukanshagwaba. Ya
kama rarrashi, yi shiru yi hakurizeeyta, daina kukan gaya
min meye? Mene nezeeyta? Gaya min kinji babyna.Yaya
shine kayi min wayo kasani bacci ka guduko? Yaya kuma
kudin dana raba biyu na dau rabinace maka sun isheni na
baka rabin shine kaajiye min ko?Oh! Sorry zeeyta, bazan
kuma ba nadaina kinji,daina kukan kina tsiyayar min da
hawayenki maitsada a kasa, gashi bana kusa bare na
tsotse.Tace, ka gani zaka fara ko?To na daina, hajiya tazo
ko?Hajiya tazo tuntuni, suna falo ita da hamza dasadik
suna hira.Yace, yauwa ai nasan bazasu barmin ke
cikindamuwa ba zasu rinka zuwa suna tayaki hira. Keko dai
kinci abinci? Bana so ki rinka zama dayunwa fa, ki rinka cin
abinci sosai kinji?Tace, to yaya ai kaima baka ci ba.To ni
wa zai bani zeeyta? Yanzu ma zan jonahita na tafasa
ruwan shayi nasha, don yunwanakeji.Ya marairaice masa
tace, haba yaya da kanka?Yace to ya zanyi zeeyta, wa zaiyi
min? Tace yayaka duba cikin kayanka da akwai sako.Sakon
me?Um-um nidai bazan gaya maka ba, ka budeyanzu inka
kashe wayar."yace to.Ya kashe wayar ya jawo jakar kayan
nasa yanabudewa, yaga nadi-nadi na leda har kashi
hudu.Ya rinka warewa ganin abubuwan da suke cikiyasa shi
tsananin mamaki da al'ajabi, a yaushezeey tayi wannan
aikin? Kai wannan yarinyaubangiji Allah yayi mata albarka.
Hakika yaji dadita faranta masa sosai, ya daga hannunsa
yanayiwa Allah godiya. Allah na gode maka da
wannanbaiwa dakayi min nasamun nutsasiyar mace
maihakuri da sanin ya kamata.Ya ware komai ya rinka ci
cikin nutsuwa danishadi, saida yaci ya koshi yasha lemo
yayigyatsa yayi hamda ga ubangiji, yaita shiwazainab
albarka a zuciyarsa.Yayi waya gida ya sanarwa mahaifansa
ya isolafiya, ya bugawa mansura itama ya gaya mataya iso
lafiya, taba shi Ahmad sukayi hirarsu yanagaya masa
abunda zai sissiyo masa.Mansura ma ta karba ta gaya
masa abubuwandatake bukata, sukayi sallama. Yana kashe
wayarzeey dinshi ya sake bugawa.Tana dauka tace, hello!
Yayana ka koshi?Nakoshi zeeyta Allah yayi miki
albarka.Amin yaya nagode.Yace, wai zainab ba zaki rinka
gayamin sunayendana ji kin radamin ba, mazan jiya da
mazaje?Tace "kai yaya nidai ban zan iyaba, da dinma
danbansan kai bane ba.To yanzu me zaki rinka gayamin?
Honey ko myluv?Tace, kai yaya dan Allah ka bari.Yace, au
bazaki gayamin kalmar da zata sanibacci cikin nishadi ba?
Sai ya kashe wayar.Ta dafe kai tace kai yaya da saurin
fushi yake,toni yanzu ya