Showing 1 words to 3000 words out of 40031 words

Chapter 1 - ZINARIYA ROMANTIC HAUSA NOVELS BY AYSHA JB.pdf

[30/11,2025. 3:49 pm] ༺�𝐘𝐒𝐇� 𝐉�༻: *...ZINARIYA*
_Romantic�_

®
AYSHA JB

Farin Jini Writer's Asso..

🔞 1&2.
Alhaji Bilyaminu Saifullahi Pawa, haifaffen garin Lafia Nasarawa stste ne, amma asalinsa fulanin
Yola ne sananne ɗan kasuwa mai kuɗi, inda ya riƙe muƙamai da dama, kuma ga shi sarkin
Pawa, ya yi tashen arziki a lokacin da duniya ke kwance lafiya, marigayi Bilyaminu yana da
mata biyu da tarin 'ya'ya, sai dai du ka yaran na shi mata ne, yayin da É—akin uwargida Binta ke
da yara tara, amariya Fatu tana da bakwai, gidan shi babban gida ne inda yake É—auke da
daƙuna, da dama. Duka matan na shi sun yi aikin Hajji da Umrah shi ya sa yaran suke kiran su
da hajiyoyi, inda suke kiran Binta da Hajiya Babba, Fatu kuma Hajiya ƙarama. Akwai zaman
lafiya da fahimtar juna tsakanin su, sai da ku san É—an'adam da ajizanci, sai da tsufa ya fara
cimma Alhaji Bilyaminu kafin Allah ya azurta shi da samun ƙaruwa ta gefen Hajiya ƙarama a
lokacin har kunya take ji a ga ciki a jikinta, domin yawancin 'ya'yansu duk sun aurar da su. Sai
dai duk nuƙu-nuƙunta sai da aka fahimci tana da ciki inda ya dinga tasbihi ga Allah yana ta
addu'ar Allah Ya sa namiji ne za ta haifa. Yayin da Hajiya Babba take jin baƙinciki sai dai ba ta
nuna a fili ba ta bar shi cikin zuciyarta. Lokacin da Hajiya ƙarama ta haihu kuwa Alhaji Bilyaminu
ya cika da murna wanda ya gaza ɓoye shi. Tsananin murnan ya sa ya raɗa wa yaron sunan
mahaifinshi Saifullahi, karku tona zuciyar Hajiya Babba ku ga irin baƙincikin da take ji idan ta
buɗe ido ta kalli Saifullahi wanda ba ta ƙi a ce mata ya mutu ba, Saifullahi ya ta so cikin gatan
iyaye da 'yan'uwanshi mata musamman ma da ya kasance yaro mai ladabi da biyayya. Ya yi
karatu daga boko har mahamadiya yana da shekara sha tara Allah ya yi wa Alhaji Bilyaminu
rasuwa bayan ya sha fama da jinya. Saifullahi ya ji mutuwar mahaifinshi sosai kasancewar sun
shaƙu da junansu hatta abinci Saifullahi ne yake ba wa mahaifinshi a lokacin da bai da lafiya,
shi ya sa ya yi kuka sosai. A hankali rayuwa ta dinga tafiya inda ya kammala karatunshi ya yi
hidima wa ƙasa (NYSC) bayan ya kammala ne ya haɗu da Salima Nasir mahaifinta shi ma
babban attajiri ne, inda soyayya ta ƙullu tsakaninsu yayin da mahaifin Salima ya kasance
ɗan'uwa ne ga Hajiya Babba, babu ɓata lokaci suka yi aure, auren su ba da jimawa ba Saifullahi
ya samu aiki a Abuja inda suka tattara shi da matar shi suka koma sai dai tsawon lokaci Salima
ko ɓatan wata ba ta taɓa yi ba, tun abin ba ya damun Saifullahi har Salima ta fahimci rashin
haihuwar nata na damun Saifullahi ga 'yan'uwanshi da suka fara janye jikinsu daga nata suna
zancen Saifullahi ya ƙara aure tun da likitoci sun tabbatar da matsalar da ga ita Salimar ce ba
daga gare shi ba, shi kuma ya nuna musu bai da sha'awar ƙarin aure domin matar shi ba ta
rage shi da komai ba. Ita kuwa Salima tana jin zafin duk wanda ya ce wa Saifullahi ya ƙara aure
domin baƙar kishi ne da ita, wannan dalilin ya sa suke samun saɓani da dangin mijin nata. Ko
'yan aikinta ba ta yarda su zo inda take ba muddin Saifullahi na gida, wannan dalilin ya sa ta
kasa zama da ƙwaƙƙwarar mai aiki guda ɗaya.
** ** **

Dum!Dum!!Dum!!! Haka na ji zuciyata na ba da sauti, cikin sauri na miƙe daga kwancen da
nake tare da kunna hasken ɗakin na ƙarasa bakin ƙofar ina faɗin. "Waye?" Tsit na ji, shahadar
kuɗa na yi na buɗe ƙofar a tsorace ina kalle-kalle nan na ga babu kowa, shuru na yi ina jin
yadda zuciyata ke tsananta bugawa. Yau kwanana goma sha takwas da fara aiki a gidan wanda
kusan kullum sai an zo an buga mini ƙofa, da na buɗe sai na ga babu kowa, na rasa me ke
shirin faruwa da ni, kullum cikin zulumi nake da zaran dare ya yi, na jima a tsaye kafin na koma
cikin ɗakin sannan na rufe ƙofar na yi addu'a na kwanta. Washegari kamar yadda na sama tashi
haka na fito bakwai saura na share farfajiyar gidan na yi moping baranta na goge duk inda na
saba gogewa kafin na nufi hanyar cikin domin shi ne hanyar da zai sada ni da falon ƙasa, sai da
na share falon tare da gyara ges room na wanke toilet É—in sannan na haura sama na shiga
gyaran main falon tare da gyara gard room da store É—in da suke ajiye kayan sakawa, tara saura
na kammala komai sannan na sauko na zauna a kujerar da ke jikin window kitchen ina jiran
fitowar Hajiyar gidan wanda sai tara da rabi take saukowa. Don yi wa maigidanta abin kari, ina
nan zaune na ji wani irin ƙamshi na bugi hancina tare da jin motsin kwanuka alamu dai tana
cikin kitchen É—in. "Kee...! Ina jin takaicin wannan suna da madam É—ina take kira na da shi,
haushi ya sa naƙi amsa mata na yi tsaki cikin zuciyata tare da yi mata banza. "Waye a nan?"
Miƙewa na yi na shiga kitchen ɗin ina faɗin. "Barka da safiya."

Kallona ta yi tare da faÉ—in "Koma ki saka hijabinki, na faÉ—a miki ki daina yawo haka bana so
masu aiki suna zama ba tare da sun lulluɓe jikinsu ba." Ta faɗa haka ba tare da ta amsa
gaisuwar da nake mata ba, fita na yi daga kitchen É—in na je na É—auki hijabi ina ta mita cikin raina
dan na lura wannan matar mugun rainin hankali gare ta, ga kitchen É—in da bala'i zafi sannan a
saka mutum saka hijabi saboda kawai mijinta na nan mutumin da ko gaisuwa ma bai taɓa haɗa
ni da shi ba, to yaushe ma na taɓa ganin shi da zan gaishe shi. Ina shigowa ta ce in fito mata da
ƙullun ƙosai da ke cikin firiza, sai da na buga shi ya sake jikinshi kafin na saka maggi na goga
albasa a ciki, ruwan kunu na ta ce na saka a buta, tana suya har ruwan ya tafasa kafin ta ce na
zo na duba ƙosan ita kuma ta dama kunun, ina kallon yadda take sauri jin mijinta na gyaran
murya alamar ya sauko ƙasa, kullum a latti take saukowa ta san mijinta na fita da wuri ba za ta
fito a yi komai cikin nutsuwa ba sai lokaci ya ƙure za ta zo tana ce wa mutum ya yi sauri. Sai da
ta zuba kunun ta ce in zo in haÉ—a tire, haka na É—auko kofuna na É—auraye su sannan na goge
kafin na jera a tire tare da tea spoon, da sugar, "Miƙo min kula." Da sauri na fito da kula na goge
sannan na miƙa mata, tire ɗin kunnu ta ɗauka ta fita da shi, gass ɗin na kashe sannan na ɗauki
na ƙosan na bi bayanta. "Ina za ki je?" Ta faɗa cikin rashin walwala tare da karɓe tiren a
hannuna. "Ki je sama ki gyara min É—aki." To kawai na ce mata sannan na koma kitchen sai da
na gyara inda aka ɓata sannan na ɗauki sauran abin da aka rage min na je na karya, ina
gamawa na É—au tsintsiya da faka, na haÉ—a ruwan moping na haura É—akinta. sai da na yi goge na
gyara gado kafin na yi shara da moping na wanke toilet sannan na fito ina mayar da numfashi.
Zan wuce in ajiye kayan moping É—in na ji ta ce "Kee.." Daga falon mijinta, É—an dakatawa na yi ba
tare da na amsa ba, "Ya sunanki ma?" Kallonta na yi cikin jin haushi domin kullum sai ta
tambaye ni sunana. "Zinariya." Kallona ta yi sosai sannan ta ce. "Ki zo ki kwashe kwanukan nan
ki wanke su." Daga haka ta fito daga falon ta haura É—akinta. Aikin fa kenan kullum babu hutu,
sai da na gyara falon sannan na kwashe kwanukan na wanke su. Shabiyu da rabi na koma
ɗakina na kwanta don hutawa saboda na yi bala’in gajiya, ga ƙwanƙwasona kamar za su ɓalle

saboda ciwo.
'Yar Nokia ta na É—auka tare da kiran Innarmu na gaisheta, ina tambayar ta mutanen gida da
babanmu, nan take sanar min da kowa na nan lafiya mun É—an jima muna gaisawa kafin na
yanke kiran, sallar azahar na yi na kwanta dan ba wani abu zan yi ba gwara na yi barcin kawai.
Haka dai kullum nake aikin wani lokaci da sauƙi wani lokacin kuwa aikin sai ya cakuɗe mini
musamman idan ta yi baƙi ko maigidan ya yi baƙi. Wani lokaci ina kaiwa shaɗayan dare kafin na
kwanta da zaran barci ya fara ɗaukata zuwa biyun dare zan ji ana buga mini ƙofa, ni kam yanzu
tsoron gidan nake ji har ban ƙaunar dare ya yi don katse mini barci ake yi. Yau da wuri na
kammala aiki domin ko goma ba ta yi ba, ina shiga É—aki na nufi toilet ina cikin wanka na ji kamar
an shigo É—akin, amma sai na basar dan ba mai shigowa, babu ma me zuwa side É—in da nake.
Ɗaure da ɗan galen da nake ɗaurawa na fito. "Wayyo Allah!" Na faɗa da ƙarfi ina neman hanyar
guduwa. ÆŠan tsaki ta ja tare da É—auke kanta daga kallona tana faÉ—in. "Ke tun É—azu da nake
kiran ki ba ki ji ba ne?" Tana gama faÉ—ar haka ta fita a É—akin ajiyan zuciya na sauke ina kallon
É—akin, cikin raina na ce Allah ya sa na gyara É—akin bare ta ce min na bar wuri babu gyara.
Doguwar riga na saka tare da himar na fita, na same ta zaune a falo ita da wata, "Kwashe
kayan ki haura sama da su." Gaishe da baƙuwar na yi sannan na ɗauki kayan.
"Wannan ce me aikin?" Na ji baƙuwar tana tambayarta. "Ita ce."
"Da alama ba irin yara masu hayaniya da rawan kan nan ba ne."
"Uhm, to ga ta nan dai." Baƙuwar ta sake cewa, "Yaushe ne tafiyar taku Salima?" daidai zan fita
daga falon na ji an kira sunanta wanda sai yau na ji asalin sunan nata, ni dai Madam nake ce
mata. Salima ta juyo ta kalli baƙuwar tare da faɗin. "A'isha jibi za mu wuce da yamma tare da
Wasila yayar Saifullah, amma gabaÉ—aya ina ji wani iri kamar kar a yi tafiyar nan." "To mene ne abin jin sanyin jiki ke da za ku neman waraka, kin ga fa idan aka dace da wannan
aikin da za a yi miki shi kenan fa ke ma za ki zama uwa, danginsa za su daina goranta miki na
rashin haihuwa, daga ƙarshe shi ma Saifullah idan ya gaji da zama haka ba yara wallahi aure
zai ƙara, ba zai iya jure wannan zaman da kuke yi ba tun da dai ya yi haƙuri ya zauna da ke
tsawon shekara sha biyar ko ɓari ba ki taɓa yi ba... "Saifullah bai ɓata nuna ya gaji da ni don
ban haihu ba, 'yan'uwansa ne dai da shegen damuwa suke uzzura mishi suna so lallai sai ya
rabu da ni ko ya ƙara aure tun da an gano matsalar da ga ni ce ba wai shi ba. Ni kuma kin san
wallahi ina da mugun kishi ba zan iya kallon Saifu da wata mace har su haÉ—a makwanci ba,
gaskiya ba zan iya ba." Salima ta ƙarasa maganar tana mayar da ƙwallan da ke shirin zubo
mata. "Da kin haƙura kin bar shi ya ƙara auren, Saifullah yana ƙaunar ki, ko da ya yi aure ba zai
juya miki baya ba... "Ko da ya haihu da matar da ya aura? Hmmm! Ki bar wannan maganar
kawai don ba zan ma yarda ba." Daga nan suka rufe zancen, ina kwance a É—aki har barci ya
fara ɗaukata na ji an buga min ƙofa, ko da na buɗe ƙofar har ta yanki kwanar hanyar kitchen
haka na bi bayanta, tana zaune a kujera tana danna wayarta na ji ta ce. "Ki dafa tea ya ji kayan
ƙamshi da yaji." To kawai na ce sannan na haɗa kayan tea ɗin na ɗaura a gas. Flacks ɗin
maigidan ta sa na juye sannan na ɗauka na bi bayanta da shi zuwa ɗakinta, a daidai baƙin ƙofar
É—akinta ta amsa sannan na dawo na wanke tukunyar da na dafa tea É—in na koma na kwanta.
2:30AM "Zinariyaa... Na ji murya mai taushi da sanyi ya kira sunana. A hankali na buÉ—e idanuna
tare da miƙa mishi hannuwana kamar yadda shi ma ya miƙo mini na shi, ji na yi lallausan
hannunsa mai kama da auduga ya kama nawa hannun, haka na dinga bin bayanshi ina ta
ƙoƙarin kallon fuskarshi amma ina, na kasa ganin koda haɓarshi ne. Kyakkyawan wurin

shakatawan da ke bayan gidan ya nufa da ni a nan na ga wasu yara suna wasa yayin da suke
ta ƙyaƙyata dariya, ina ji suka rumgume suna faɗin. "Ummi... Kiran sallar assalatu ya farkar da
ni daga wannan mafarkin mai ban mamakin da nake yi. Zaune na yi tsakiyar gado ina ta jin wani
yanayi na sanyi a cikin jikina.
Littafin Zinariya na kuɗi ne, ba zan yi free pages da yawa ba, domin biya za ku tuntuɓi wannan
Number ta WhatsApp. ₦500.
09079740079


Maman Faruk.
[30/11, 3:49 pm] ༺�𝐘𝐒𝐇� 𝐉�༻: *...ZINARIYA*
_Romantic �_

®AYSHA JB

Farin Jini Writer's Asso..

3&4
GabaÉ—aya na ji yanayin wani iri, ina zaune har biyar da rabi sai da na ji ana shirin ta da sallar
subahi kafin na yunƙura na nufi toilet na yi alwala na gabatar da ra'atanil fijir na yi sallar subahi.
Ina zaune har hantsi ta yi kafin na miƙe na fito farfajiyar gidan na fara aikin da na saba. Karfe
takwas na kammala komai na zauna a ƙofar kitchen ina jiran fitowar hajiyar gidan, yau dai an yi
abin kirki an sauko da wuri, "Ke Zinariya... "Wai ita wannan madam É—in ba za ta iya kiran sunan
kurum ba sai ta haÉ—a ni da *ke* ne?" Cikin masifa nake mita ni ma. "Mene?" Na ji ta ce tana
kallona. "Na ce ina kwana?" Ba ta amsa mini ba sai cewa ta yi. "Je ki gyara min É—aki." Cikin
raina na ce za a fita kenan, domin in har ta ce in je in mata gyara war haka na san fita za ta yi
duk da ba ta ce min fitar ne za ta yi ba, don ba na sanin fitarta sai dai na ga ba kowa a gidan.
Haurawa na yi na iske baƙuwarta ta fito da ga wanka, sai da na jira na gama shiryawa sannan
na shiga É—akin na gyara mata. Ina fitowa na tsaya gaban mirror da ke upstair É—in ina kallon
fuskata, zaro ido na yi ina faɗin. "Kam bala’i haka na yi kumamatu? Kai, wallahi kumatu na yi
sosai aikuwa zan kira Innarmu na sheda mata Zinariyarta ta fara zama ɓakutuwa, ga jikinta ma
ya fara murjewa 'yar baƙa ta fara haske." Cike da zallar yarinta take maganar tana taɓa
kumatunta tare da shafo wuyarta, sai da na ga haske ya haskani sanna na tuna ashe da
Camera a gidan. Kallon Cameran na yi ina murguɗa baki na ce. "Kalle ni da kyau ƙiba na yi
jikina ya murje."

"Subahanallahi lafiya? Ke da wa kike magana?" Cewar wannan baƙuwar. Sum-sum na ɗauki
kayan shara na ƙarasa saukowa kamar munafuka, turaren wuta na kunna tare da baɗe gidan
da ƙamshi zuwa lokacin madam Salima ta gama girki ni ina can ina zagaye gida da turare ina
haÉ—a wa da shiririta. "Wannan yarinyar akwai shiririta wallahi." Cewar A'isha a lokacin da suke
yin breakfast "Wa kenan?" Salima ta faÉ—a tana kallonta. "Mai aikin ki mana." Ba ta ce mata
komai ba ta ci gaba da abin da take. "Wannan yarinyar ba na tunanin ta cika sha bakwai...

"Yanzu wai ta shiga sha shida ma." A'isha ta ce. "Haba ai dole za a zuba ruwan shiririta mana,
amma ya kamata a ce tana makaranta ne yanzu." Hmm, kawai Salima ta ce sannan ta dubi
A'isha tana faÉ—in. "Suna da halin kaita makaranta suka kawota aikatau? Ai da suna da wannan
damar ba ma za su turo ta neman kuÉ—i ba." A'isha za ta yi magana Salima ta É—aga mata hannu
tare da faɗin. "Dan Allah ban son surutu." Ta miƙe ta ɗauki na’ura tana kallon shirmen da
Zinariya ta yi ɗazu. Duk wani motsinta tana kallo da yadda ta dinga taɓa kumatunta, tsaki ta yi
tare da rufe wa ta miƙe ta ɗauki key ɗin motar ta suka fita.

Ina kwance na ji fitar motar ta, taɓe baki na yi tare da faɗin. "Zan sha barcina na more." Sai
kusan la'asar na farka, Ina zaune ina jiran dawowarta don na fara jin yunwa wallahi, kuma ta ce
na daina girki sai in tana nan saboda ina cika mata maggi da mai cikin abinci ita kuma ba su cin
su, ni kuma gaskiya ba na son girki salam-lam don a gidanmu ba haka muka saba girki ba.
Kitchen na shiga na buÉ—e firiza na É—auko ragowar taliyar da muka yi jiya na É—uma na ci kayana
na koma É—akina. Sai huÉ—u da rabi ta dawo gidan. Ina ji tana horn alamar ta dawo banza na yi da
ita, sai da na ji kamar za ta tashi gidan kafin na nufi parking space É—in ina mata barka da zuwa.
"Ke tun É—azu ba ki ji ina horn ne da kika yi zamanki?" Ta yi maganar tare da nufar hanyar falo
bayan ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login