Showing 1 words to 3000 words out of 25118 words
Chapter 1 - YADIN MAGE Book Complete writing by oum yasmeen .txt
*⚜️⚜️YADIN MAGE⚜️⚜️*
🐈🐈🐈🐈🐈🐈🐈🐈
_🫧story and writing🫧_
*By*
*{oum yasmeen}*
*littattafai na*
*AFIF*
*YADIN MAGE*
*RASHIN SANI*
*MUBU MU GANI*
*KIN CU CENI*
*DESTINY LOVE*
*BINTA YAR JAGALIYA*
```Bismillahi Rahanir Raheem```
………✍🏼
*Part 1-2*
""A garin kano yau an tashi da wata iriyar rana ga zafin da yake gasa ƙafar ta ga yunwa da ta ke ji
amma halin datake ciki yasa bama ta jin zafin da a keyi babban burin ta be huce ta ganta a gidan baba kabiru
tunda ga dandago take tafiya gashi yanzu ta kusan zuwa nasarawa j .r.a a hamdallah ta yi a ranta domin ta kusan shiga lahin da gidan baba kabiru
gaban wani gida ta tsaya iya tsaruwa ya tsaru daga ganin gidan kasan mai gidan ƙusar gwamnati ne ko hamshakin dan kasuwa bugawa tayi ganin ba ajiba yasa ta ƙara bugawa mai gadin gidan ne ya buɗe ya leƙo kallo daya za kai mai kasan buzune cikin hausar sa mara fita ya ce mata ,
"shine ka dawo alhaji ya ce baya son a din ga barin masu maula shi go mai ina baka haƙuri ka tafi in da ace alhaji yana nan da sai in faɗa mai yana faɗar haka ya rufe ƙofar sa ,
Wasu zafafan hawayai zuka zobo daga idon ta daga hannu sama tayi tace
Ya Allah ka kawo min mafita ka bawa abbana lafiya shikaɗai yara ge mun bani da gata sai kai
wata mota ce ta nufo gidan mai gadi yana jin ƙarar mota ya wangale gate ɗin motarce ta tsaya cikin sauri ta ta shi domin ta gane mai motar tuni farinciki ya ma mayai zuciyar ta
dasauri muhibbat ta fito ta ce
"Samha ke ce yau a gidan na mu ?"
Eh anty muhibba na zo ne man baba ne yau
Okay Allah ya soki baki da rabon ganin ta kaici domin ba kowa a gidan saboda yau jabir zai dawo daga america mun tafi ɗau ko shi ne a na ruga su dawo wa shi go sai ki jira shi
"To, nagoɗe sosai ,
shiga cikin motar tayi to ni AC ta ratsa ta shiru tayi ta shiga tunani anya kuwa baba kabiru yayan innata ne ga irin daular da yake ciki ganin motar ta tsaya alamar sun shi go ya sa tayi saurin fitowa yi ta tsaya
"Hajjiya hajjiya wannan mai barar ka shigo da shi ya fi sati ukku yana zowa alhaji ta ce min ƙar na bar sa ya shigo dan boko haram ne,
What to wannan da kake gani ƴar gidan ƙanin daddy ce ƙar in ƙara ji ka fada mata haka
"To, hajiya na dai na ya bar gun ,
Samha ina ta kalmin ki ƙar de a cikin mota kika baro shi ?"
aa bani da shi
"Okay ya jikin abba ?"
hawayan da take ruƙe wane suka sami na sarar zobo wa cikin muryar kuka ta ce
"kullum rashin lafiyar abba gaba take ga shi tun kafin cutar ta shi tayi tsana ni mai company nin su ya salla mai su yaƙi basu albashin su na wata shiddah kuma saboda ɗau kan shinkafa bayan shi yasami matsala ,
yanzu gobe za a zauna zaman shari'a we baba kabiru yace gidan da muke cike na sane ya kai abba ƙara ya tashi ya bar mai gida
Allah sarki allah ya bashi lafiya
Ameen ta ce shiga wani hadaddan floor sukai a ƙasan carpet ta zauna bata fi minti daya da zama
sai ga ihun su auta da alama sun dawo daddy yana ruƙe da hannun mama suna sanyai da kayan alfarma samin guri sukai suka zauna basu lura da samha ba sai jin gaisuwa sukai asama
"Kee waya baki izinin shigo min gida ?"
kafin ta ce wani abu muhibbat ta ce,
"pls daddy ni na shigo da ita taimako ta zo ne ma dan Allah daddy ka janyai shari'ar nan ƴar kanwar ka ce fa be kamata ba aji ka kai su ƙara kotu duk kuɗin ka akan gida kuma kasan ba naka bane ,,
cikin zafin rai mama ta wanke ta da mari ta ce
"Muhibba yau mahaifin ki shi kike faɗawa haka duk abin da yake yi yana yi dan kune domin kuji daɗi ko bayan ransa ba zaku ta gyayara ba ,,
Ke kuma ta shi ki fitar mana agida shegiya mai kama da aljana kuma ki ce masa dukiyar sa muncin yai ba zamu bayar ba
Dan girman allah kuyi haƙuri ku bar mana gidan mu ba musan ida za muba ku tausaya mana ƙafar baba kabiru ta ruƙe tana kuka mai ban tausayi tace
"Kaji tsoran Allah duniya ba matabba ta bace in da inna ta je zaka je har inna ta mutu ba kaje ba a ina innata ta baka gidan mu ta ce ta bar maka mai yasa kake son cin dukiyar marainiyar Allah
cikin zafin zuciya ya hamɓare ta tuni bakin ta yara zubda jini ya nuna ta da yatsa yace
"ki fitar min daga gida in ba so kike kema in kashe ki ma kamar yarda na kashe........
Sai kuma yayi shiru ya zauna
jikinta a sanyayai ta tamiƙe tsayai ta fara tafiya har taje bakin kofa ta daka ta ta juyo saka maƙon kiran da muhibba tayi mata tsayawa tayi har ta ƙara so inda take
dubu biyu ta miƙo mata tayi mata alama datayi shiru ta gudu aikuwa amsa tayi ta juya aguje ta fita
hello tsagera kubi yarinyar nan da ta shigo ɗazo duk abin da kuka ga dama koyi mata ina so kafin gobe mutuwar ta ta zaga ko ina *........✍🏼*
*⚜️⚜️YADIN MAGE⚜️⚜️*
🐈🐈🐈🐈🐈🐈🐈🐈
_🫧story and writing🫧_
*By*
*Oum yaseem*
_ƴar mutan yakasae_
*Part 3-4*
"TO, an gama oga kitt ya kashe wayar ku mai kike jira yarinyar nan da tashi go tare da ƴar gidan honorable inta zamu bi tuni suka tashi duk a buge suke suna lahi futa sukai a guje yayi da itama tana ta gudu gashi unguwar ma mutane ballan tana su cece ta ganin sun kusa cim matane ya sa ta ƙara gudu
duk inda ta sami lahi shiga take suma haka binta suke ganin ta fara ganin motane tasan ta zo titin state road gudu ta ƙara tuni suka juya
domin ba zasu iya bin ta ba domin sun san titin yana da tsaro sosai yanzu sai a sirin su ya tonu duk da haka ba tayi tafiya cikin kwanciyar hankali ba har ta zo dan/dago
shagon dan asabe tabiya salama tayi
Cikin fara'a ya amsa mata samha yakike ya jikin abba
"TO, dan asabe da sauki za ace amma kullu jikin ƙara rikicewa yake
Allah ta ƙara sauki
"Amin ya Allah ungo bani garin ƙwaki na naira dari ukku sigan dari biyu sai gyaɗa ta naira dari ,
Barshi bazan ƙar ɓaba inkin je gida kice ina yiwa abba sannu
A jiyar zuciya ta saki sanna ta ce ,
ƙarbi kuɗin nan ƙar inna hajarah ta ƙarɓe zan zo gobe da safe in ƙarɓa zan kai abbana asibiti kafin mushiga shari'a
"TO, Allah ya bada nasara ungo ya miƙo mata godiya tayi mai ta ƙarɓa ,
wani rusassan gida ta nufa bashi ma sa ƙofa sai buhu da aka saboda sukare ƙansu ƙar a gano su sallama tayi inna hajarah ce inta da abokanan ta wayanda suke siyan waina da kayan shaye shaye sunfi goma suna zaune suna ƙwasar hira da shiwa
ita kuwa uwar ɗakin su tana gaban kasko hayaƙi ya turnuƙeta r
saboda rashin wada tatciyar iska kuɗine daure a ƙugunta amma ko zasu mutu ita da mahaifin ta ba zasu ciba balle yanzu da bashi da komai kanta aƙasa ta shiga ɗan kukane ya dubi hajara ya ce,
We uwar ɗakinaa yau she zaki bani wannan yarinyar muyi aure sai baki ƙuɗina nake kina cin yewa
ɗagowa tayi tasa wani baƙin tsumma ta goge fuskarta da taci man ƙwailin har wani ja take ta ci jan baki da jagira tajuya gabas ta duba yamma tace,
Kai kabari lokacin da wannan mara amfanin ya mutu ranar zaman makoƙinsa zan ɗaura muku aure dole ta zauna tunda bata da wani gata sai na ubanta
wani ihu suka saki gabaki ɗayan su suka ce sai uwar ɗakin mu shege naki dan banza na ki mai tsinuwar iyayai nake ban da ɗankirki uwar yan iska da ƙangararru ke har karuwai ma nakine
Saboda jin daɗin kirarin da sukai mata saita toro ɗauri gaba ta ce,
Wannan haka yake gani yar malam matar malam naƙi halin malam kayan sata insiya komai da ruwanka ta buga cinya ta juya wainar ta
Da sauri samha ta ƙarasa cikin gida saboda saurin da take har tuntuɓe take
da sauri ta ƙarasa gun mahaifinta saboda ya sakko daga ƙanshin fiɗar da taimai cikin sanyin murya tace ,
Abba sannu nasan kana jin yunwa ko
Cikin tarin daya sarke sa yace
"yauwa yarinyar ƙirki Allah yayi miki albarka ya baki miji na gari ,
Kunya ce ta kamata tace
ABBA bara in kaika makewayi ko naga ka ɓata jikin ka ɗaga shi tayi ta shiga da shi makewayi
Ta ɗebo mai ruwa ta kai mai haɗe da kayan da ta wanke mai da safe ta futo domin ya gyara kansa
bokiti ta ɗauka domin ta ɗebo ruwa ɗan kuka yana ganin ta ya tashi ya ce
Haba my love ya kike min yawa uwar ɗaki na bata wainar riɗa ɗaya yana roƙemata hijabi hannu ta
ɗaga ta wanke fusƙarsa da mari ta ci uban yaka da ɗinki idanunta sunyi ja saboda ɓacin rai tace
" wallahi ko da wasa na ƙara ganin hannuka a jikina saina ɗatsai maka hannu ni ba irin banzayan matan da kuke tare da su bane insha allahu mugun nufinku ba zai faru akai na ba *.........✍🏼*
*OUM YASMEEN*
YADIN MAGE⚜️⚜️*
🐈🐈🐈
🐈🐈🐈🐈
🐈🐈🐈🐈
*🫧story and writing🫧*
*🎀Oum yasmeen🎀*
*part 5-6*
"Cikin cije baki irin na yan daba yace
"keee ni zaki yiwa haka to yasin dan de ina son ki ne amma yasin da nayi fillah fillah da naman ki ,
tsaki ta ja tahuce lahi ta tarar a gun ɗiban ruwan tsayawa tayi a gefe ta shiga tunani ji tayi an faɗi sunanta da sauri ta ɗago kan ta cikin siririyar muryarta tamƙar sarewa ta ce
Ya usman ina hini har ƙasa ta durƙusa
"lafiya qalow ƙanwata ya jikin abba ?"
da sauki gobe ma zamu shiga shari'a gashi ina so in kai shi asibiti amma ƙarfe shabiyu za a shiga
"shiru yayi na wasu sakanni sannan ya ce,
"To, Allah ya kai mu ki jirani zan kaiku na ƙarbo hayar babur mai kafa ukku kingan shi ,
Cike da farinciki ta nufi gun babur ɗin shiga ciki tayi ta dube shi ta ce,
Ya usman ina taya ka murna Allah ya sanya alkhari ya kaɗe fitina
"ameen ya amsa da shi kinga shikkenan in abba ya sami lafiya sai muyi aure kafin lokacin na tara kuɗi da zan miki komai da akeyiwa sa'annin ki ko ?"
cikin jin kunya ta rufe fusƙarta da tafikan hannayan ta tace
bara in jee in ɗibi ruwa sai anjima bokitin ya ƙarɓa
ya huce wajan ɗiban ruwan daya ke lahi yazo kan ta ya fara buga mata tuƙa tuƙa
Nana ce ta fito daga gida taga yaya usman yana buga ruwa aguje ta shiga gida umma umma umma
fitowa tayi daga madafi tana gyara ɗaurin zanin ta tace
Kee nana yau she zaki yi hankali ne kinga yarda faɗarmin da gaba ni nazata wani abune ya same ki
"Umma yana shirin samu wa,,
we ba kin hana yaya usman zowa gun waccan maiyar uwan tale cemin tayi ita ta lashe mata ɗa kuma lashe ƙurwar abba ya ɗena tafiya
ke yanzu zaki yarda ta shigo mana gida ta lallashe mu kuma sannan yan iskan da suke zuwa gidan su naira ashirin shegiya ake bata a tattaɓata ?"
dafe kirji tayi da sauri ta zari takalmi mayafi ta zara akan igiya ta nufi kofar gida aikuwa ya na ko ƙarin shiga gidan su samha aguje ta nufi gunsa ta zab ga mai mari tace,
Usman wannan shine gargadi na ƙarshe da zan maka ka fita a harƙar yarinyar nan mara mutunci mai bin maza in ba haka ba wallahi usman zantsine maka ka ƙara yimata magana
Cikin girgiza kai yadafe kuncin sa ya ɓuɗe baki zaiyi magana samha ta tare shi tace
" dan Allah ƙar kai magana kabi umarnin umma wallahi na san kana sona saiɗw kaddarah ta ruga fata,
juyawa gun umma tayi hawaye na zuba a idon ta bakin ta na rawa tace,
"Dan Allah ki yi haƙuri wallahi ni ba yar iska bace juyawa tayi ta dubi bangaran da nana take ta girgiza kai ta ce,
Umma ƙarki yiwa dan wani fatan lalacewa bacin lalacewar da kike faɗa tana gare ki ta ɗauki ruwa ta shiga gida ta bar umma da baki a buɗi
"Usman kaga abinda nake faɗa maka ko a gaban ka ta za geni ba kai komai ba juyawa yayi yabar guri domin zuciyar sa tana cikin baƙin ciki yayi rashin samha nutsastsiyae yarinya ga tarbiya
ku kuma munafukai sai a koma gida faɗan ya ƙare toni kowa ya shiga gida domin ansan fadan umman nana ta iya tashin hankali yar bala'ice number daya itama gida ta shiga samha kuwa tana shiga dan kuka ya ce
Uwar daki na a she ni ne gatan ta yo kuwa gudunta yake tun da aka hauro akayiwa innarta yankan rago wasuma nacewa ita ma am mata fyaɗe
Ya saki dariya yace
yo ni da nasan haka za ai ranar nima da na zo na kwashi roman damakwaraɗiyyah ya ja ya gutsiri wainar sa ya korada totalin
Yo dan kuka uwan da karaina shi wasu ke so yanzu maga ta yaya usman
bata jira mai zasu ƙara cewa ba ta shiga cikin gida a ƙofar ban daki ta tsaya ta goge hawayanta ta wanke fusƙarta k'ar ya gane anyi wani abun tace,
"Abba ka gama ?"
"Eh samha tun ɗazu ina ta kiranki ashe bakƴa nan ina kika je ?"
Ɗiban ruwa zamaka wanki
"To, Allah yayi miki abarka zoki ɗauke ni shiga tayi ta ɗaga shi ya dafata suna tafiya tabar da ta shin fiɗa mai ta ajiye shi ya zauna kofi ta ɗauko ta zuba gari ta jiƙa mai
Samha ina kika samo kuɗi?
hawayan da take rukewa suka sami nasarar zubuwa muryar ta na rawa ta kwashe komai ta faɗamai
Shiru yayi nawasu zakanin san nan yace ,
Allah yayi miki albarka yasa ki gama da duniya lafiya duk kan wani tsanani yana tare da sauki duk tsananin rayuwa ƙar yasa ki bayar da mutuncinki in kuwa kikai haka samha ban yafe miki ba
Insha allah abba zan kula da kaina ungo ta fara bashi yana sha tana gyara mai gyaɗa tana bashi a haka har suka gama ta fara wanki *………✍🏼*
*⚜️⚜️YADIN MAGE⚜️⚜️*
🐈🐈🐈
🐈🐈🐈🐈
🐈🐈🐈🐈
*🫧story and writing🫧*
*🎀Oum yasmeen🎀*
*part 7-8*
"Shanya kayan datayi wanke tayi ta sami guri ta zauna ta dubi abban ta ta ce,
"ABBA haryan zu baka ga inda ka rubuta number hajiyaba ba tasan fa inna ta mutu ba gashi ni koma ba inda na sani a abuja tunda suka tashi suka koma abuja inna ba zuwa take ba gwara ita in ta bushi iska ta kanzo ta gan mu abba ko inje gidan baba bilyaminu in faɗamai gobe za mu tafi shari'a kaga dole a sami wanne babba na miji wanda zai iya komai ,
"Tunda ta fara magana ya zura mata ido sai da ta ida ya dubeta yace,
*SAMHA* kin san dai halin bilyaminu ina ma binsa kuɗi amma yaƙi bani da aka raba gadon mu aka bamu yace in kawo za mi kasuwanci tashin maganar kake ji
samha ki dogara da Allah sai yayi miki kowa kansa yasani shi kuma kabiru ya jirayi ƙarshan sa ba acin dukiyar maraya domin ita yaɗin mage ce duk wanda yaci sai yayi amanta
wallahi samha ba mutuwa nake tsoro ba ina tsoran in mutu in barki baki da gata sai Allah sai ni ina tausayin ki tunda kika tashi ba kisan wani daɗin rayuwa ba amna komai tayayi tsanani maganin shi Allah
wataran zaki ji daɗi number hajiyar ki nane meta na rasa samha da na san zata iya temaka mana samha yan uwana duk guna suke saboda bani da kuɗin da zan basu wani uban ashar suka ji samha tsaki tayi ta yarfe hannu ta ce abba na tafi
"yar albarka sai kin dawo dan Allah ki kula ƙar ki kula hajara wata kila ita da mutanan ta ne sannan ga wancan ta kalmin na mahaifiyarki ne ki sa ki dena tafiya ba takalmi
"TO, abba dauka tayi ta canza hijabi wannan yana da kyau milk ne amma kana ganin sa kasan ya sha jiki dan ƙwalin da ta daura ya zame saboda ta sa hijib sumar kanta mai kyau ta fito baka siɗik da ita
cire hijin tayi tasa ta shiga ɗakin mamar ta ta ɗauko hula ta sa domin dan ƙwali baya d'au ruwa a kanta lokacin da mamanta ki da rai ita ke ɗaura mata yar kwallar da ta zubo idon ta ta goge tayi mai sallama ta fita ,
"yasin ba mai fita a gidan nan sai na caje shi wato dan iskanci ni zaku ɗaukewa kuɗin waina ta ,
Kee da hallacan ware ni kinsa yan kuɗaɗan ki basa gaba na matsamin in huce kallo daya tai mai ta kauda idanuwanta
domin a wani fige yake da alama ma a buge yake wata gyatsa yayi mata akai ba shiri ta matsa sukwa sauran suna zaune