Showing 3001 words to 6000 words out of 8506 words
Chapter 2 - ALLON SIHIRI Book 4 Littafin Yaki By Abdulaziz Madakin Gini.txt
kamuwa da tsananin son
yaro Ruhaisu fiye da koyaushe a rayuwarsa,don
haka
sai ya tashe shi tsaye ya rungumeshi yana mai
cewa
tabbas ka cika da na gari abin alfahari.Lallai na
yarda da wanan shawara taka kuma zanyi aiki da
ita.Koda jama'a suka ji haka sai suka rude da
shewa,suka kama yiwa sarki Sailur jinjina da
kirari
suna masu nuna soyayyarsu a gareshi.Tun daga
wannan rana Ruhaisu ya tunawa sarki Sailur
cewa
babu abinda yakeso a rayuwarsa sama da ya
koyi
YAKI.Ai kuwa ba tare da wata gardamar komai
ba
sarki Sailur ya shiga koya masa yaki da kansa,ya
zamana cewa a kullum sarki sailur yana shafe
kimanin sa'a guda yana koyawa Ruhaisu yaki.Da
safe suyi sa'a biyu,haka ma da rana da kuma
daddare.A cikin kwanaki goma sha hudu Kacal
Ruhaisu ya iya sarrafa takobi ainun,kuma ya iya
kare
dukkan irin harin da sarki Sailur ke kawo
masa.Koda aka shiga sati na uku kuwa sai gashi
yana iya maidawa sarki sailur martanin kai
hari,har
ma akwai lokacin da saura kiris ya yiwa sarki
Sailur
rauni a lokacin daya kawo masa wani wawan
sara
aka,ya matsa baya cikin zafin nama,amma duk
da
haka sai da kaifin takobin tasa ta zabtare wani
bangare kadan na rawaninsa.Shi kansa sarki
sailur
bai san sa'adda ya kama yiwa yiwa Yaro Ruhaisu
tafi ba.Daga wannan rana ne sarki Sailur yakai
Ruhaisu cikin manyan dakarun yakin kasar ya
cigaba
da daukar HORON YAKI a cikinsu.Abi dai kamar
wasa sai gashi Ruhaisu yana iya jure duk irin
wahalar da manya ke jurewa a matsayinsa na
yaro
karami dan shekara goma.Ashe wannan juriya
tasa
ta samo asalo ne tun daga azabar da sarkin
birnin
Darmis ya rinka yi amsa shi kuma yana
shanyeta.Kai
saida takai cewa barde Ruhaisu yana iya yin yaki
da
karti hudu yana yaro amma duk sai ya kaisu
kasa.Lokacin daya cika shekara goma sha
takwas a
duniya kuwa sai gashi shi kadai yana iya
tarwatsa
mutum arba'in.A wannan shekarar ne aka jarraba
iya
yakin Ruhaisu inda aka shirya wata gagarumar
GASA
ta JARUMAI akan akarfin damtsensu da iya
Yakinsu.Jaruman gasar su dari da goma sha
hudu
ne,amma RUHAISU ne ya karbi KAMBUN
GASAR.Daga wannan lokaci ne sarki sarki ya
sake
jan barde Ruhaisu a jikinsa ainun ya zamana
cewa
duk wani abu da zaiyi na sirri tare dashi
yakeyi.Al'amarin dayasa sarkin yaki ya fara
kyashi
da hassada dashi kenan,kuma ya tsaneshi
ainun,amma sai Ruhaisu ya zame masa
kadangaren
bakin Tulu.Babu irin tuggu da makircin da sarkin
yaki bai shiryawa Barde Ruhaisu ba amma sai
sarki
sailur ya rinka kareshi a boye ba tare da ya sani
ba.Kai sau tari ma akwai
mugayen tarkuna da Ruhaisu yake fadawa ya
kasa
fitar da kansa,amma sai yaga wani yazo tsulum
ya
ceceshi,kuma wanda ya ceceshin ya rufe
fuskarsa da
bakin rawani idanunsa kadai ake gani gaba dayan
kayan jikinsa ma bakake ne.Saida akayi hakan
kusan
sau hudu.Abinda ya faru a karo na hudun shine.
pls Like and comments
15 hrs · PublicALLON SIHIRI
Littafi na Hudu (4)
Part C
A BINDA YA Faru a karo na hudun shine,wata
rana
da magriba Ruhaisu ya dawo daga FARAUTA a
daji
kawai sai yaga wadansu dakarun sumame
kimanin
su arba'in sanye da jajayen tufafi sun dako tsalle
a
sama sun kewayeshi.Su duka sai suka zare
takubbansu suka ja tunga cikin shirin afka
masa.Tunda Barde Ruhaisu yazo duniya bai taba
ganin ZARATAN DAKARU masu kwarjini da kirar
SADAUKAI ba irin wadannan.Nan take jikinsa ya
bashi cewa yau fa ya gamu da gamonsa,amma
da
yake shima jarumi ne mai DAKAKKIYAR ZUCIYA
ko
kadan baiji tsoron yayi kokarin ceton kansa
ba.Abinda ya aiyana aransa shine ko ba komai
sai
yayi iya bakin kokarinsa yaga cewa bai mutu shi
kadai ba.A kalla yana son ya sami nasarar kashe
koda mutum goma ne daga cikin wadannan
zaratan
jarumai da suka kawo masa MAMAYAR
BAZATO.Lokacin da dakarun suka ga Ruhaisu ya
gyara tsayuwarsa yana dafe kufen takobinsa ba
tare
daya nuna alamun tsoro ba ko tunanin
guduwa,sai
su ma suka sha jinin jikinsu,suka fahimci cewa
lallai
shima JAN IDO ne,kuma zai iya yin barna kafin a
gama dashi.Hakan ne yasa dakarun basuyi saurin
afka masa ba suka tsaya daga baya baya suna
nazarinsa tukunna.Shi dai wannan wuri inda
DAKARUN SUMAMEN suka ritsa Ruhaisu wajen
gari
ne sosai a tsakiyar daji inda babu gida gaba ko
baya,kuma babu wani mahaluki dazai tsaya a
wajen
tsawon dakika goma batare daya firgita ba
saboda
waje ne mai yanayi na ban tsoro.Akwai dogayen
bishiyoyi masu duhuwoyi gami da manyan
tsaunika
wanda dole ne baza a rasa mugayen dabbobin
daji
ba akansu.Ko yaushe wajen tsit yake tamkar
babu
wata halitta mai rai a wajen,kai da gani kasan
cewa
ba za'a rasa mugayen MUTANEN BOYE ba a
wajen.Ana cikin wannan hali ne sai tsulum
dakarun
sumamen sukaga wani Badakaren a cikin shigar
bakaken kaya rike da takobi ya duro tsakiyarsu
daga
can sama daga kan wata doguwar bishiya ya
tsaya
daf da Ruhaisu suka hada baya alamar ce
Ruhaisu
ya kawowa dauki.Koda ganin haka sai shugaban
dakarun sumamen yabaiwa sauran yan uwansa
inkiya suka afkawa su Ruhaisu.Nanfa aka
ruguntsume da azababben masifaffen yaki mai
matukar tayar da hankali da muni.Ana fara yin
wannan gumurzu ne kowa ya san cewa KARO DA
KARO sai RAGO!Kamar yadda dakarun sumamen
suke da KARFIN DAMTSE da iya yaki,zafin nama
da
bakin naci,haka Ruhaisu ma da mai bakaken
kayan
nan suke dashi,don haka saida aka shafe sa'a
biyu
da rabi ana dauki ba dadi,in banda karar haduwar
takubba gami da sautin naushin jiki babu abinda
kunne yakeji.Gashi dai an kasa koda lakutar jikin
mutum daya a GUMURZUN bare a fitar masa da
JINI
mai yawa,amma kuma ana naushin juna yadda
yakamata kuma ana shanye naushin sai kace
jikin
kowa bana jini da tsoka bane.Duk wanda ka duba
saidai kaga hancinsa da bakinsa na yoyon
jini.Koda
shugaban sakarun sumamen yaga an bata
wannan
lokaci mai tsawo haka ba tare da sun sami wata
nasara ba saiya fusata ainun ya bayar da wata
inkiya.Take dakarun sumamen suka ja da baya su
duka alokaci guda suka zaro wadansu adduna
guda
dai dai wato ya zamana cewa kowannasu na rike
da
makamai biyu a jikinsa ga TAKOBI ga kuma
ADDA.Koda ganin haka sai wannan badakare mai
bakaken tufafi yai wuf ya zaro wadansu Wukake
guda
biyu a cikin jikinsa ya mikawa Ruhaisu guda ya
karba,suma suka dubi juna sukayi wata inkiya iri
daya.Koda Ruhaisu yaga sunyi inkiya iri daya shi
da
wannan badakare mai bakaken kaya sai
zuciyarsa ta
buga da karfi kuma tsoro ya shigeshi.Ba komai
ne
yasa masa wannan tsoro ba face ya gane cewa
ba
wani bane wannan badakare mai bakaken kaya
face
SARKI SAILUR.Take Ruhaisu ya tambayi kansa a
cikin zuciyarsa yace,saboda ne sarki yake siyar
da
rayuwarsa don ceton tawa rayuwar?Ai wannan ba
karamin ganganci bane a matsayinsa na sarki
yayi
haka kuma idan wani abu ya sameshi nima na
shiga
wani bala'in.Yana cikin wannan tunani ne
dakarun
sumamen suka sake afko musu aka sake
ruguntsumewa da sabon masifaffen yaki a karo
na
biyu wanda yafi na farko tashin hankali da bala'i
domin wannan karon wani irin sabon salon yaki
dakarun sukazo dashi ya zamana cewa sun hada
da
tsalle tsalle da kwance kwance suna yawo a
saman
su Ruhaisu da kasansu suna kai musu hari ta ko
ina.Faruwar hakan keda wuya kuwa sai suka fara
ruda sarki Sailur da Ruhaisu nan take suka sami
nasarar yankar kowannansu sau uku uku,jini yai
tsartuwa daga jikinsu suka kurma ihu sakamakon
tsananin zafi da zogin da suka ji.Nan take jiri ya
kwashi Ruhaisu ya durkushe kasa yana mai cake
takobinsa cikin kasa don kare kansa daga
faduwa.Koda ganin haka sai shugaban dakarun
sumamen ya dako tsalle sama cikin shammace
da
zafin nama ya daga makaman nasa biyu sama da
nufin ya fille masa kai.Koda Sarki Sailur yaga
abinda
ke shirin afkuwa gashi yana yaki da sauran
dakarun
sumamen shi kadai ya hanasu kusantar Ruhaisu
sai
ya daka tsalle sama yayi wata irin katantanwa da
kafafunsa a tsakiya dakarun sumamen ya
tarwatsa
su kuma ya kare saran da shugaban dakarun
sumamen ya kawowa Ruhaisu a gadon
bayansa.Taka takobin da Addar suka datsa
bayan
sarki Sailur jini yai feshi a lokacin da sarki sailur
ya
kurma uban ihu kuma ya fadi kasa tim a
sume.Koda
Ruhaisu yaga abinda ya faru ga Sarki sai ya
kurma
ihun daya ninka na sarki Sailur sau goma kamar
MAHAUKACIN ZAKI ya faso gari.Take gaba
dayan
dakarun sumamen suka firgita suka ja da
baya.Shi
kuwa Ruhaisu zuciyarsa ce ta kekashe ga barin
jin
dukkan tsoro da kasala saboda tafarfasa data
kamayi kamar zata kone saboda fishi bisa ganin
halin da sarki ya shiga,kawai sai gani akayi
Ruhaisu
ya daka tsalle sama tamkar daga cikin BAKA aka
harboshi ya sare kan shugaban na
su kuma ya soka masa wuka a tsakiyar kirjinsa
ta
fullo ta gadon bayansa.Take gangar jikin
shugaban
dakarun sumamen ta sulale kasa matacciya.Shi
kansa Jarumi Ruhaisu yayi matukar mamakin
yadda
akayiyayi wannan gagarumar BAJINTA da
JARUMTAKA.Koda sauran dakarun sumamen
suka
ga yadda Ruhaisu yayi da abin dogaronsu,wato
shugaban nasu sai suka firgice suka zubar da
makamansu suka cika wandunansu da iska.Kafin
kace wani abu babu dayansu a kusa.A sannan ne
Ruhaisu ya fashe da kuka ya fara dinke raunikan
dake gadon bayansarki sailur cikin razana da
dimauta yana ta fama rusa kuka domin a lokacin
ma
gani yake kamar tuni sarki ya dade da
mutuwa.Bayan ya gama dinke masa raunikan ne
yaga har a sannan jini bai daina zuba daga cikin
raunikan,al'amarin daya dugunzuma hankalinsa
kenan ya ruga da gudu izuwa cikin daji ya samo
wadansu saiwoyin bishiyoyi yazo ya dakesu ya
shafe
raunin dasu.A sannan ne jinin ya daina zuba,har
izuwa wannan lokaci Ruhaisu bai daina kuka ba
saboda ko kadan babu alamar numfashi akan
kirjin
sarki Sailur,kuma babu inda yake motsi a
jikinsa.A
daidai wannan lokaci ne Ruhaisu ya fara sakar
zuci
wata zuciyar tace dashi menene amfanin
rayuwarka
a duniya tunda ka rasa wannan BABBAN MASOYI
wanda baka da kamarsa a duniya.Ai gwara kaima
ka
kashe kanka tunda idan ma ka dauki gawarsa ka
kaita cikin gari babu yadda za'ayi ka tsira daga
zargin cewa kaine ka kasheshi.Koda gama aiyana
hakan sai Ruhaisu ya sake fashewa da
matsanancin
kuka na bakin ciki har izuwa lokaci mai dan
tsawo.Daga can kuma saiya daga takobinsa
sama
da nufin ya cakata a cikinsa ya kashe
kansa.Kwatsam ba zato ba tsammani sai yaga
sarki
sailur yayi wuf ya taso zaune ya rike hannunsa
kuma
ya budi baki da kyar cikin matukar karfin hali
yace,dakai ka mutu gwara ni na mutu kai ka rayu
saboda indai ban samu haihuwa ba kai nakeso ka
gajeni.Har yau har gobe wannan shine babban
BURIN ZUCIYATA.Koda sarki Sailur yazo nan a
zancensa sai Ruhaisu ya rungumeshi cikin
tsananin
farin ciki bisa ganin cewa bai mutu ba.Kafin sarki
Sailur ya sake budar baki yace da Ruhaisu wani
abu
sai Ruhaisu yayi wuf ya goyashi a bayansa ya
falfala
da azababben gudu izuwa hanyar dazata kaisu
cikin
gari.Nanfa ya rinka yin wani irin gudu na ban
al'ajabi
yana gifta bishiyoyi tamkar giftawar tauraruwa
mai
wutsiya.Cikin kankanin lokaci suka iso cikin gari
suka karasa fada,tun a kofar gidan sarautar
Ruhaisu
ya kwallawa likitan sarki Sailur kira don haka
kafin
su karasa turakar sarki sailur tuni anje an kirawo
likitan ya karaso da gudu izuwa cikin
turakar.Nandai
Likitan ya shiga aikinsa ya baiwa sarki sailur
wadansu magunguna wajen kala uku yasha kuma
ya
shafa wani maganin akan rauninsa.Faruwar
hakan
keda wuya sai barci ya sace sarki.Saida sarki
Sailur
ya shafe sati uku a kwance yana jinyar wannan
rauni
na gadon bayansa sannan ya warke
sumul,tamkar
bai taba samun wani rauni ba ma.Sa'ar dayayi
itace
saran da akayi masa bai taba kashi ba,tsokar
nama
ce kawai ta dare.Wannan shine takaitaccen
tarihin
Barde Ruhaisu.
¤¤¤ ¤¤¤ ¤¤¤
BAYAN SARKI SAILUR da Barde Ruhaisu sun dan
jima a tsaye rungume da junansu suna kuka sai
sarki sailur ya janye jikinsa daga cikin na Ruhaisu
ya
dubeshi a nutse yace,yakai dana kayi sani cewa
ba
komai nake so kayi mini ba face ka yiwa
surukata
Yazarina rakiya izuwa tafiya neman mijinta
dan'uwanka Yarima Lubainu.Ka sani cewa tuni
mun
gama shirya komai ni da mahaifinta Abu Yazarina
saboda haka a cikin wannan dare nake so kayi
wannan tafiya kuma zan hada ka da wadansu
amintattun zakwakuran dakaru nawa kamar
mutum
dari kacal wadanda zasu taimaka maka.Ina son
kuyi
bad-da-kama a cikin daren yau zaku bar garin
nan
domin a samu cikakken sirri.Koda Sarki Sailur
yazo
nan a zancensa sai farinciki ya lullube barde
Ruhaisu ya dubi sarki sailur fuskarsa cike da
annuri
yace,yakai Abbana kayi sani cewa a iya tsawon
rayuwata ban taba jin farin ciki ba a raina irin na
yau
saboda yaune ranar farko daka taba neman wata
alfarma a wajena.Tun daga kuruciyata kawo
izuwa
girmana bantaba saka maka ba da abin alherin
daka
ke yi mini tsawon shekaru,amma yau gashi ka
bani
damar dazan iya kwatantawa.Na rantse da
darajar
kauna da soyayyar dake tsakaninmu dakai zan
sallama rayuwata don kare ta surukarka,kuma
duk
inda dan'uwa na Yarima Lubainu yake a cikin
duniya
sai na damka Yazarina a hannunsa cikin koshin
lafiya kuma a raye.Koda jin wannan batu sai farin
ciki ya sake baibaye sarki sailur ya rungume
barde
Ruhaisu a karo na biyu yace,ina alfahari dakai
yakai
yayan Lubainu,kuma nasan cewa saika cika
wannan
aiki dana baka bisa amana.Ni yanzu babbar
masifar
dazan fuskanta itace ta kewarka a yayin daka yi
wannan tafiya.Ka tuna cewa tun daga ranar dana
daukoka a gidan sarautar Birnin Darnis kawo
izuwa
yau bamu taba rabuwa daidai da rana daya
ba,yanzu
gashi zakayi wannan tafiya mai mugun hadari
wacce
bansan ranar dawowarka ba.Koda sarki sailur
yazo
nan a zancensa sai ya sake kankame barde
Ruhaisu
a kirjinsa ya fashe da matsanancin
kuka.Al'amarin
daya karya zuciyar barde Ruhaisu kenan,shima ya
fara yin sabon kukan.Tabbas irin son da sarki
Sailur
yake yiwa Barde Ruhaisu har yafi wanda yake
yiwa
Yarima Lubainu duk da ya san cewa barde
Ruhaisu
ba dansa bane na cikinsa,'da ne na TSUNTUWA
wanda ma baisan asalinsa ba.Tsananun tausayin
barde Ruhaisu da yakeyi be yasa yake kaunarsa
fiye
da Yarima Lubainu.Sarki Sailur bai taba fifitashi
ba
kan Ruhaisu,kuma kowanne taro sarki zai tura
wakilci bai taba tura Yarima Lubainu ba saidai ya
tura barde Ruhaisu.Kai saida takai cewa Yarima
Lubainu ya fara
nuna kishinsa a fili akan Barde Ruhaisu saboda
ganin yadda sarki ke fifitashi akansa.Daga ranar
da
sarki sailur ya baiwa Yarima Lubainu labarin
haduwarsu tun yana dan shekara goma kawo
izuwa
girmansa shike nan sai Yarima Lubainu ya
kaunaci
barde Ruhaisu fiye da yadda ma sarki ke
sonsa,kuma suka zamo manyan abokai yan'uwa
kuma aminan da basa son rabuwa.A ranar da
Yarima Lubainu zaiyi wannan tafiya saida suka
shafe
rabin sa'a cif a tsaye rungume da junansu suna
kuka na bakin cikin rabuwa,da kyar suka saki
juna
Yarima Lubainu ya tafi,domin a cikin zukatansu ji
suke kamar dama can sun kasance yan'uwan
juna
na jini.Bayan bardw Ruhaisu da sarki Sailur sun
dan
sake jimawa a kankame da juna sai Ruhaisu ya
janye jikinsa daga cikin nasa suka fuskanci juna
yana mai share hawayensa yace,yakai Abbana
kayi
sani cewa akwai bukatar naje na kammala
dukkan
shirye shiryena yanzu tunda bani da isasshen
lokaci
kuma nayi bankwana da matata.Sarki sailur ya
gyada kai a lokacin da hawaye ya subuto masa
yace
wannan gaskiya ne,kuma ka nema mini gafara a
wajen surukata matar taka tunda na rabata dakai
a
lokacin datafi koyaushe kewarka.Na sani cewa
bata
da burin dayafi ta haihu kana nan ku raini abinda
kuka haifa tare domin babu takaicin dayafi na
rabuwa da IYAYE tun mutum yana karami.Gashi
kai
ka rabu da iyayenka a lokacin ma baka sansu
ba,amma na sani kuma naji a jikina cewa tarihi
bazai maimaita kansa akanka ba,lallai kai zaka
dawo
gida a raye cikin koshin lafiya tun kafin 'danka ko
'yarka tayi wayo.Koda jin haka sai fuskar Barde
Ruhaisu ta fadada da murmushi ya yiwa sarki
Sailur
godiya sannan ya juya da sauri ya fice daga cikin
turakar ba tare daya yarda ya sake waigowa
ba.Take
Barde Ruhaisu ya nufi izuwa gidansa.
2 mins · PublicALLON SIHIRI
Littafi na Hudu (4)
Part D
DA ISAR BARDE RUHAISU gidansa sai ya iske
matarsa ZASMIN tsaye a falo dauke da tsohon
juna
biyu tana kai kawo cikin alamun damuwa.koda ta
hango shigowar Barde Ruhaisu sai ta taho
gareshi
fuskarsa cike da annuri suka rungume,amma
yayin
data janye jikinta daga nasa taga idanunsa sunyi
jajir alamar cewa yasha kuka sai zuciyarta ta
buga
da karfi ta dubeshi cikin alamun tsananin tashi
hankali tace,gaya min gaskiya yakai mijina yau
kuma menene ya faru a fada?Lallai ba ka taba
dawowa gida a cikin irin wannan yanayin ba.Shin
wani makusancinka ne ya mutu ko kuwa wani
abu
ne ya sami sarki?Tabbas yadda na sanka da
DAKAKKIYAR ZUCIYA in ba wadannan abubuwa
ba
babu abinda zai saka kuka.Koda jin wannan
tambaya
sai Barde Ruhaisu ya suri Zasmin ya dagata
sama
yana mai rungumeta a kirjinsa yayi juyi da ita don
haka bata san sa'adda ta kama kyalkyala dariya
ba.A hankali Ruhaisu yaje ya shimfide Zasmin
akan
gado ya kama wasa da gashin kanta suna kallon
juna cikin murmushi.A sannan ne ya kwashe
labarin
dukkan abinda ya faru tsakaninsa da sarki Sailur
ya
zayyane mata.Koda gama bata wannan labari sai
yaga ta kyalkyale da dariya,amma kuma hawaye
na
zuba a cikin idanunta.Al'amarin dayai matukar
bashi
mamaki kenan kuma ya kadu,cikin mamaki
yace,yake matata ina dalilin wannan dariya taki
gami
da kuka a lokaci guda.?Sa'adda Zasmin taji
wannan
tambaya sai ta nutsu ta dubeshi da kyau tace,ya
kai
mijina abin begena dare da rana,kayi sani cewa
ba
komai ne ya sakani wannan kuka ba face yau ne
ranar farko da zan fara rabuwa dakai tun daga
lokacin aurenmu.Alhinin rabuwar tamu ne kawai
ya
sakani kuka,amma ina ji a jikina cewa tabbas
zaka
dawo gareni.Abinda ya sani nake yin wannan
dariya
kuwa ba komai bane face tsananin tayaka
farincikin
samun damar dazaka iya sakawa sarki kadan
daga
cikin irin abubuwan alherin dayayi maka.Kash!In
badon ina dauke da wannan TSOHON CIKI ba da
lallai tare dani za'ayi wannan tafiya,sabida inason
na
haife maka danka a lokacin da kake cikin
GWAGWARMAYA ko shima dan naka ya sami
tabarraki irin naka.Koda Zasmin tazo nan a
jawabinta sai farin ciki ya lullube Ruhaisu ya
rungumeta ya kama sumbatarta yana sa mata
albarka.Nan take Zasmin ta mike tsaye da kanta
ta
fara debo kayan Ruhaisu tana zuba su cikin jakar
guzuri don kammala shirye shiryen
tafiya.Al'amarin
daya kara bashi mamaki kenan,kuma yaji ya
kamu
da tsananin sonta fiye da koyaushe.Cikin
kankanin
lokaci ta gama shirya masa dukkan kayansa
sannan
suka yi bankwana ya saba jakarsa a kafadarsa
bayan
yayi shigar bad-da-kama irin ta fatake sannan ya
koma can kofar gidan sarautar.A wannan lokaco
tuni
Sarki Sailur ya gama shirya komai,domin a samu
cikakken shiri dangane da wannan tafiya Tasu
Ruhaisu saida aka sauya masu gadin kafor gidan
sarautar gaba daya a cikin daren aka zuba
wadanda
ya tabbatar da cewa masoyansa ne na gani
kasheni,kuma ya gargadesu akan cewa duk
abinda
suka gani ko sukaji a wannan dare su barshi a
cikin
zukatansu kada su kuskura su sanar da wani.D
isowar Barde Ruhaisu bakin kofar gidan sarautar
sai
ya iske sarki Sailur tsaye a gaban wadansu
dakaru
guda dari suna bisa kan dawakai dauke da hajoji
da
makaman yaki alamar cewa su fatake ne.Tun
daga
nesa Barde Ruhaisu ya fara nazarin fuskokin
wadannan dakaru,koda ya shaidasu sai ya kamu
da
tsananin farinciki da mamaki.Ba komai ne ya
haddasa hakan ba face ganin cewa gaba daya
sa'anninsa ne kuma manyan abokansa wadanda
ya
aminta dasu a cikin dakarun yakin kasar.Koda
sarki
Sailur ya hango tahowar Barde Ruhaisu sai ya
tafi
gareshi cikin murna yace,yakai dana an gama
shirin
komai dama kai kadai ake jira saboda haka sai
kayi
haramar tafiya.Koda jin haka sai Ruhaisu ya
kama
hannayen sarki guda biyu ya sumbacesu kawai
sai
ya sake rungume junansu suka dan jima a
kankame
da juna.Al'amarin daya karya zukatan sauran
dakarin
kenan suka kamu da tausayinsu saboda sunsan
irin
shakuwar dake tsakaninsu.Nandai Barde Ruhaisu
da
Sarki Sailur suka rabu bisa dole sunayin kwallah
badon suna so ba,aka kawowa Barde Ruhaisu
wani
farin INGARMAN DOKI wanda ya fita dabam da
dukkan dawakan abokan nasa ya kama ya
hau.Take
ya kada linzamin dokinsa ya fice daga cikin
gidan
sarautar ba tare daya yarda ya sake waigowa
ba.Ai
kuwa sai sauran dakarun guda dari suka rufa
masa
baya da sauri shi kuwa sarki Sailur sai ya bisu da
kallo kawai,bai bar wajen ba har saida suka kule
ya
zamana cewa ko kurarsu baya iya
hangowa,sannan
ya juya ya koma izuwa cikin gidan sarautar yana
mai
zubar da hawaye.
¤¤¤ ¤¤¤ ¤¤¤
A CAN BIRNIN Sarki Alkasu kuwa tun da aka
gama
wannan gasa ta neman Auren YAZARINA
tsakanin
YARIMA LUBAINU da YARIMA MANGUL suka
dawo
gida sai sarki Alkas ya sanya hijabi tsakaninsa da
Yarima Mangul.Suna dawowa gida yayi masa
korar
kare daga fada kuma ya gaya masa cewa idan ya
sake sa kafarsa a cikin harabar gidan sarautarsa
zai
yanke masa hukuncin daurin rai da rai a gidan
kurkuku.Koda jin wannan batu sai mamaki da
bakin
ciki ya turnuke Yarima Mangul ya dubi dungulmin
hannunsa a lokacin da hawaye yake zubo masa
sannan ya dubi Sarki Alkas yace saboda mezaka
kyamaceni alokacin dana fi bukatarka?Ka dubi
yadda
na zamo musaki ka tuna cewa nine fa kadai
danka
guda wanda zai gaji karagarka?Ka tuno da irin
tsananin son daka keyi min saboda me yau zaka
bari zuciyarka ta rinjayi soyayyar danka?Kafin
Yarima Mangul ya gama rufe bakinsa tuni sarki
Alkas ya daka masa tsawa a lokacin da shima
hawaye ya zubo masa ya dubeshi yace,karka
sake
kirana da matsayin ubanka domin tuni nasaka
TAKOBI na datse wannan
alaka dake tsakaninmu kamar yadda ka datse
wacce
ke tsakanina da Abokaina kuma manyan
masoyana
sarki Sailur da Attajiri Abu Yazarina.Ka sani cewa
ka
jefa wadannan masoya nawa a cikin bakin cikin
da
har abada babu abinda zai gusar dashi tunda ka
rana Yarima Lubainu da lafiyarsa ka sanya masa
cutar da bata da magani kuma a sanadiyyar
hakan
yayi rabuwar doke da masoyiyar tasa rabuwar da
ba
lallai bane su sake saduwa ba.Kaga keknan ka
raba
iyaye