Showing 99001 words to 102000 words out of 188939 words

Chapter 34 - SAKAYYA Book 1 complete BY GARKUWA.txt

kamar ƙasa na amsawa.
Atake zuciyarsu ya buga da mugun ƙarfi tare da bada sautin dib-dab-dib-dab-difffh yayin da yake jin wani irin masifaffen abu na tsirgar masa lokaci ɗaya lafiyarsa sa ta shaida mushi kasantuwarsa cikekken Namiji.
Ita kuwa khausar tana jin yatsarta cikin ɗan hudan cibiyarsa amma tsananin tsoron da take ciki yasa ta kasa fahimtar menene sai cusa kanta da ta kumayi a kirjinsa.
Shi kam Moddibo wani irin rungumeta yayi da masifar ƙarfi yana mai sakin wani irin amintaccen nish....!


*Free page sun ƙare daga wannan, ko kin ga littafin a wani wuri na satane, littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin da nan kadai zanke posting*






SAKAYAH


18


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇




Spjt. Rungume juna sukayu tamkar zasu shige cikin jikin junansu, yayin da ruwan sama kuwa ke cigaba da sauƙa tamkar da bakin ƙwarya, kana ga walƙiya da tsawa dake cigaba da sauƙa.
Moddibo shi kam baki ɗaya ya burkice ya rasa tunaninsa, na wushin gadi, gaba ɗaya jinshi yake a wata duniya ta da ban,
ga wani matsanancin tsoro daya lulluɓe sa kana ga wani baƙon yanayi da yake ji yana yawo agaba ɗaya ilahirin ajikinsa, wani irin rawa lips ɗin sa keyi tamkar mai jin tsananin sanyi, ga kuma wani irin azabebben buguwan da zuciyarsa keyi da masifaffen ƙarfi yana bada sautin dib-dab-dib-dab.


Haka zalika Khausar dake rungume dashi, itama haka zuciyarta ke bugawa,
sake ƙanƙamesa tayi da ƙarfi tana mai tura kanta afaffaɗan ƙirjinsa da bottle din gaban rigar suka buɗe, hakan ya bawa fuskarta damar mannewa farar afaffaɗan ƙirjinsa dake ƙawace da tattausan gashi baƙi mai sulɓi.
Wani irin fusga numfashinta keyi saboda tsananin tsoro da firgici da tashin hankali, haka yasa idan taja numfashin sai ta ɗauki sekon talatin Kafin ya dawo.
Ko kaɗan Moddibo bai da wani kataɓus sabida yanayin da suka kasance a ciki, sake rungumeta yayi tare da cusa kansa atsakanin wuyanta da kafaɗarta.
Daga can bayansa yake jiyo sautin ƙaran mota tana danna masa ɗiyyyyttt-ɗiyyyytttt, yasan shi akeyiwa hon ɗin, amman sam baya jin zai iya koda kwakwaran motsine.
Shi kuwa mai motar dake bayansa, ganin shiru bai motsa bane, yasa ya ɗan ratsa ta gefensu ya fuce yana dan leƙawa ganin ko lafiya kasancewar. Atsakiyar titin suke ganin babu wani alamun hatsari ko damuwa yasa ya wuce.


Moddibo kuwa da ƙyar ya iya buɗe Idanunsa tare da ɗago kansa still ruwan ake sheƙawa zuwa yanzu harda ƙanƙara yana jin yanda sautin ƙanƙarar ke sauka asaman motarsa fat-fat-fat ko kaɗan baya kallon komai duk da kuwa gashi idanunnasa abuɗe suke, amman ina ganinsa ya ɗauke makanta ta meye gurbin ganinsa, ya zama sam baya gani, kana ji yake jikinsa kamar shanyeyye.
Daƙyar ya iya ɗaga hannunsa tare da dafe kansa da yake jin wani irin jiri na fizgarsa tare da sarawa, da sauri ya sake sunkuyar da kansa akan wuyanta kana ya sake rungumeta da ƙarfi baki ɗaya ya rasa wani irin yanayi yake ciki.


Khausar kam sam batama san wani irin yanayi take ciki ba sam bata cikin hayyacinsa, hakan yasa ta sake rungume Moddibo da ƙarfi,
Jin yadda take liƙewa a jikinsa ne, yasa shima ya saƙe yi mata wani irin amintaccen rugguma tare da fesar da wani irin raunataccen numfashin yana mai shaƙan ƙamshin jikinta.
Itama sake rungumesa tayi cikin mawuyacin hali tana neman numfashi domin numfashinta na ƙoƙarin ɗauke wa gaba daya tsananin tsoro da tashin hankali ya bayyana asaman fuskarta, duk da sanyi garin da kuma yanda ake tsuga ruwa amma goshinta na na tsastsafo da zufa kana jikinta ya ɗauki ɗumi.


Cikin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa da ficewar hayyaci Moddibo ya sake rungumeta yana jin ɗumin jikinta kana yana mai furta.
“Hasbullahu wani'imal wakin, Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n La'ilaha Illah anta subhanaka Inni ukuntu Minal Zhalimin, Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha”,Kana ya cigaba da karo to duk wata addu'a da tazo bakinsa cikin fitar hayyaci, Allah ya sani kuma shine shaidarsa ya rasa yanayin da yake ciki shin mutuwa zaiyi ne, koko kuma sumewa yake shirin yi,
domin jinsa yakeyi tamkar yana tafiya cikin sararin samaniya ne bisa gajumare,
ji yake tamkar fuka-fuki garesa ya kasa tantance shin mafarki yake ko kuma azahirance ne kana yakasa tantance shin a sumen yake ko kuma amace yake, cikin rashin sanin madafa ya cigaba da karanto duk wata addu'a da tazo bakinsa.
Yayin da numfashi Khausar ke cigaba da fusga,
adduo'i ya cigaba dayi cikin ikon Allah Albarkanci Adduo'i da yake da kuma zuciyar namiji dake da dakiya yasa yafara dawowa hayyacinsa amma still Idanunsa basa gani mai kyau.


Ganinta kwance ajikinsa tana fuzgar numfashi yasanya shi sa. Lallausan tafin hannunsa ya tallabo fuskarta tare buɗe manyan idanunsa da ƙyar dan har yanzu dishi-dushi yake gani, idanu ya tsirawa kan goshinta daya tsats-tsafo da zufa, sai kuma ya rumtse idanun da karfi kana ya buɗesu tare da zura ido na daƙiƙu bakwai sai kuma ya juya idanun zuwa kan wuyan hijabinta daya zame daga kanta zuwa kafaɗarta yalwataccen sumar kanta mai tsayi da ƙamshi ya zuba agadon bayanta, yayinda saura kuma ya zuba asaman fuskarta, kallonsa ya mayar kan fuskarta jin, yanda numfashinta ke fusga. Idanunsa ya mayar kan ƙirjinta da sauri ya lumshe idanun sai kuma ya buɗesu, ganin yanda numfashinta ke hawa da sauka alamun zata sume a ko wanne lokacin.


Ganin tana gab da sumewane ya sanyashi sun kuyar da kansa kaɗan, zuwa kan fuskarta kana ya ɗaura lips ɗin da suke masifar rawan sanyi akan karan hancinta, lumshe manyan idanunsa da suka sauya launi zuwa ja yayi, tare da fesa mata sanyayyan numfashinsa domin dai-dai ta mata nata numfashin, domin duk da tsoron da kuma firgicin da yake ciki hakan, bai sanya numfashinsa ɗauke wa ba, kana yana kallon fuskarta wanda akowani lokaci zata iya suma, sai kuma ya sanya hannu ya toshe hancinta tare da ɗaura sanyayyan lips ɗin sa akan nata ya riƙa hura mata iskar bakinsa mai ɗumi da kamshi ceto rayuwa zuwa gareta,
Wani irin dogon numfashi taja mai nauyi tare da fesar dashi da ƙarfi, cikin daƙiƙu kaɗan numfashinta ya soma dawowa dai-dai kana duk abinda ke faruwa idanunta na lumshe.
Sannan har zuwa lokacin hannunta na kan mararsa, saman yatsarta na kan hudan cibiyarsa, sannu ahankali numfashinta ya dai-dai ta sai dai har zuwa lokacin bata dawo hayyacinta ba, still kuma ruwan ake cigaba dayi tamkar da bakin ƙwarya ita ko sai wani irin sakewa tayi tare da lafewa a jikinsa tana shaƙar ƙamshinsa.
Shi kuwa Moddibo sannu ahankali ya fara dawowa hayyacinsa da nitsuwarsa.
Sake lafewa Khausar tayi ajikinsa tare da lumshe Idanunta domin ganin abun take kamar mafarki, ko kuma mutuwa tayi tsaban masifar tsoron rugugin da take.


Shi kuwa Moddibo sannu ahankali cikin ikon Allah ya dawo hayyacinsa, kana har zuwa yanzu tsikar jikinsa na tashi yayin da kansa ke juyawa jiri na ɗibarsa.
Ahankali ya sauƙe idanunsa akanta data manna a ƙirjinsa, yayinda tattausan suman kanta ya baje aƙirjinsa, kallonta yakeyi kamar ya samu sabuwar halitta, kana aƙasan ransa ke mgnar zuci,
Wai yaya haka ne? Mekw faruwa? Wai ma waye ni?
Ya tambayi kansa da kansa,
Kaine Moddibo, sannan wannan Khausar ce kwance ajikika tana rungume dakai cikin yanayin da ma'aurata ne kaɗai ya halatta su kasance ciki.
Wani sashi na zuciyarsa ya bashi amsa.
Lokaci ɗaya kuma jikinsa ya sake ɗaukar rawa far-far tamkar wanda ake sheƙa masa ruwan ƙanƙara lips inshi kuwa, wani irin masifeffen tsuma sukeyi,
lumshe idanunsa yayi jin jikinsa babu kuzari kona misƙala zarratin, ji yake tamkar an zare masa lakar jikinsa cikin sanyi da rashin kuzari dake tare dashi.
A hankali ya sake birkitota tare da ɗago kanta ya ɓanɓareta daga jikinsa gani yayi Idanunta alumshe.


Ita kuwa Khausar ji take tamkar cikin bacci take, ko kuma suma ta kasa fahimtar kalar yanayin
da dai take ciki,
Shi kuwa Modibbo kanta ya tallabe da hannunsa ɗaya yayin da ɗaya hannu yake ɗan marin fuskar yana faɗin.
“Ke! Keh!!”.
Shiru bata motsaba, hakan yasa ya sake ɗan fizgo muryasa tare da faɗin.
“Khausar! Khausar!!”.
har zuwa lokacin tana rungume jikinsa
For the first time arayuwarsa da bakinsa yafara kiran sunanta.


Fuskarta yake ɗan yiwa ƙananan maruka ahankali kana cikin wata Sanyayyar murya mai cike da tattausan lafazin yake fadin.
“Khausar!, Khausar!! Khausaaaar!!!”.
Lumshe idanunsa yayi shi kansa bai san yana da irin wannan raunataccen muryar ba, ya rasa taƙamemmen yana yin da yake ciki, yayin da aƙasan ransa so yake ya mata faɗa da tsawa da masifar ta sauƙa jikinsa, amma ya kasa kasancewar har zuwa lokacin bai gama dawowa cikin ainihin nutsuwarsa ba.
Kumatunta ya cigaba da ɗan mara yana faɗin.
“Khausar!, Khausar!!”.
A hankali kanta ya zame daga hannunsa ya tafi gefe luuuh kamar sumammiya.
Lokaci ɗaya zuciyarsa ta buga da ƙarfin gaske tare da jin tsinkewar zuciya ganin yanda Kanta yayi kamar ta mutu!.


Cikin ɗaga sautin murya ya sake ɗan marin kuncinta tare da cewa.
“Khausar, *Lelewal*”.
Khausar kuwa still Idanunta na lumshe take Jin sautin muryar Moddibo na kiran sunanta kamar amafarki ko kuma daga can sama.
Sai kuma ta sake jiyo sautin muryarsa da alamun kiɗima yake cewa.
“Ya salam Lelewal meya faru? me ya sameki?”.


Ahankali ya sanya hannunsa tare da ture hijabinta kana ya sanya hannunsa aƙirjinta wanda har yana iya jin tudun caɓɓullen ta ahannunsa ji yayi ƙirjinta na bugawa da ƙarfi-ƙarfi.
Hannunsa ya cire tare da sunkuyar da kansa har suna shaƙar numfashi bakin juna, bakishin yakai kan kunnenta kamar meyu mata raɗa yake faɗin.
“Lelewal tashi! Lelewal buɗe idonki!! Lelewal kalleni”.
Lumshe Idanunsa yayi akaro na barkatai tare da kai bakinsa cikin kunnenta kana cikin Sanyayyar murya mai taushi yace.
*“Fattanah!”.*
Dogon numfashi taja tare da sauƙe nan-nauyan ajiyar zuciya tare da buɗe Idanunta sai kuma ta sake runtsesu da sauri gani take tamkar har yanzu rugugin akeyi kana walƙiyar zai iya kashe mata Idanu.
Bayan kamar daƙiƙa ɗaya ta sake buɗe Idanunta still yana ronƙofe akanta yana shaƙar ƙamshin numfashin dana gashinta dake baje.
Yayin da har zuwa yanzu hannunta ke cikin sa yatsunta guda uku nakan cibiyarsa tafin hannunta da sauran yatsu biyun nakan ainihin mararsa ta danne.
Cikin wata sanyayyar murya ya tsira mata idanu tare da faɗin.
“Lelewal”,Ya faɗa still yana tallafe da kanta.
Buɗe Idanunta tayi sai kuma ta sake rufewa,
Akuma dai-dai lokacin Moddibo da itan duk suka gama dawowa cikin hayyacinsu tare da nutsuwar.
Cikin sauri tare da fushi
Moddibo ya kalleta a tsawace yace.
“Keee!!! Tafi can Mage uwar fitina tashi akaina ko in kakkaryaki”.
Ya dire mgnar cike da tsawa tare da yarfa mata mari da bayan hannunsa.
Shi kansa jin maganar yayi ta fito daga zuciyarsa kai tsaye kamar an fisgo a bakinsa.


Azabure Khausar ta buɗe Idanunta dake lumshe tare da janye jikinta daga nasa amma still hannunta na kan cikinsa tana murza cibiyarsa.
Wani mugun kallo mai cike tarin kufula, takaici, tsuyan zuciya, da tarin ƙunci ya watsa mata firgitaccen kallo. Ta da ɗaga hannunsa cikin wani irin masifeffen rawan jiki da gigitan yanayi yasanya tafin hannunsa ya finciko hannunta dake kan cikin sa da masifar ƙarfi ya yarfa hannun nata har saida ta saki ƙara, dan ji tayi kamar zai ɓalla mata hannun.
Shi kuwa a take kuma tsikar jikinsa ta mimmiki ta tashi.


Cikin tsananin tsoro da firgici Khausar ta janye jikinta kana ta koma ta mannu da jikin kujera tare da rungume kanta a can gefen jikin kujeran motar tana mai jin raɗaɗin marin.
Moddibo kuwa da ƙarfi ya rumtse idanunsa sabida wani irin masifaffen har bawa da yaji zuciysrsa nayi da masifar ƙarfi, lokaci ɗaya wani azabebben zufa ya wanke sa kana rawan da lips ɗinsa keyi ya tsananta karkarwa yayin da har hakoransa ke rawa har suna bugun juna saboda wani masifaffen abu da yaji yana yawo cikin kwanyar kansa, wani irin baƙon yanayi yaji ya taso masa da azaban ƙarfi, abinda bai taɓa jiba atsawon shekaru.
Cike da dauriya da kuma fushi ya figi motar da gudu yayin da zuciyarsa ke wani irin azalzala idanunsa kuwa har yanzu dishi-dishi suke gani sanna, sai wani irin rawa jikinsa da lips inda keyi, cikin mintunan da basu gaza goma ba taji yayi Parking aƙofar gidansu.


Cikin tsananin tsoro da ruɗu ta buɗe murfin motar, cikin sauri ta fice batare data lura da ɗan kwalinta da kuma hankief ɗin ta dake kan cinyar Moddibo ba.
Da ƙarfi yafi gi motar cikin mintuna kaɗan ya isa gidan yana parking ya fito.
Lokacin ɗaya ya jiƙe jikib saboda ruwan da ake cigaba dayi kamar da bakin ƙwarya.
Cak ya tsaya Atsakiyar gidan nasu, ruwan na sauƙa atsakiyar kansa saboda masifeffiyar baƙon yanayi da yake ji ga kuma suya da raɗaɗin da zuciyarsa keyi, na firgicin saɓawa Ubangiji da yayi, tsoron Allah da tarin damuwa ne ya sanya idanunsa fara zubda wasu irin zafafan hawaye masu ƙuna.
Rumtse idanun da yayi tare da furta.
“Astagfirullah wa,atubu ilaik, Ya Allah kaine mafi sanin zuciyata, Yah Allah ka gafarta min ya Allah ka shafe min wannan zunubi, ya rabbi kada ka sake bani damar sake saɓa maka Yah Allah ka sani ban taɓa aikata makamancin hakaba,”. Gaba ɗaya muryarshi rawa takeyi, yayinda idanunsa ke kwaranyar da hawaye.
Duk da ruwan na dukansa amma ko kaɗan baiga alamar zaiji sauƙin abinda ke damunsa ba. ji yayi tamkar ya ɗora hannunsa a ka ya rinƙa ihu da kururuwa. Duk da dauriyarsa kuwa, bai san sanda kuka ya kubce masa, domin duk sauƙan ruwan akansa ji yake kamar ana ƙara rurumashi wutar fitina a jikinsa, ga kuma ƙuncin zaciya da yake ji,
Har lau haƙoran sake dukan juna suke nusa bada sautin Ƙat-ƙat-ƙat baki ɗaya jikinsa rawa yake tamkar mazari ahankali ya sunkuyar da kansa gani yayi yadda muhallin sa ya sake masifar nuna zalamarsa.


Cikin mawuyacin hali ya dafe kansa da hannunsa na hagu murya narawa yace.
“Wannan wace irin masiface? shin wannan wani irin abune mai wuyar jurewa me yake yafaru dani ne wai? Shegiyar yarinya mai fitintinun al'amura, ya Allah ka isarmin da cutar dani da tayi, Yah Allah kaga ita ta riskeni kaine shaida ni ban nufetaba, Allah ka isarmin kan wannan muguwar yarinya mai jikin zalumci Astagfurullah”.
Ya ida maganar tare da fashewa da kuka, still dai yana tsaye acikin ruwan yana cigaba da dukansa, ganin sam kuma abin nasa yaƙi nitsuwa ne yasa ya nufi hanyar sashensa domin sakarwa da kansa ruwan ɗumi koda zaiji sauƙin abinda ke damunsa, abakin faradan Falon sa ya tsaya tare da zare rigar dake jikinsa kana ya zame wandon ya shanya ya rage daga shi sai boxer Kai tsaye toilet ɗin sa dake cikin Bedroom ɗinsa ya nufa yana shiga ya sakarwa da kansa ruwan ɗumi batare daya cire boxer ba yana tsaye ruwan ɗumin ya cigaba da zuba akansa amma babu abinda ke yawo a idanunsa kamar lokacin daya rungumi yarinyar ga wani masifaffen ƙamshinta da yake ji ajikinsa da ƙarfi ya matse jikinsa waje ɗaya kana cikin tsanananin tsoron Allah ya ci gaba istigfari.
“Astagfurullah wa'atubu Ilaik ³ ya Allah na tuba kayafe min wannan abin da nayi. Ya Ubangijina na tuba”.
Kai kawai yake girgiza wa cike da tashin hankali mara misaltuwa daya rufe idanunsa babu abinda yake hange face yanayin da suka kasance amota.


Acan ɓangaren Khausar kuwa da gudu ta shiga gida tare da wucewa Falon su.
Tsaye ta samu Mommyn ta cikin yanayin damuwa da tashin hankalin.
Mommy na ganinta ta saki ajiyar zuciya mai nauyi tare da cewa.
“Alhamdulillah Khausar kin dawo, gaba ɗaya hankalina ya tashi na kasa zaune na kasa tsaye, tunda Haiydar ya dawo ya faɗa min yanda ku kayi da Amina!”.
Ida mgnar taba kallon yadda jikin Khausar ke ɗigar da ruwa ga wani rawa da jikinta keyi cikin jin ƙai da tausayawa tace.
“Amina bata kyauta min ba. Wallahi Allah Amina bata taɓa yimin abinda ya ɓata min rai irin na yau ba, ya za'a yi cikin wannan hadarin cikin wannan yanayin ta baro min ke a makaranta.
Yanzu waya dawo dake?”.
Cikin karkarwa na tsoro da sanyi ga kuma zogin mari tace.
“Uhhhmmm”.
Ita kuwa Mommyn cikin sanyi tace.
“Yanzun nan dama Abbanku nake jira? ya dawo dan baya nan na faɗa masa kina cikin makaranta. Yanzu yana dawowa ne akan zai ɗaukeni muje can ɗin”.


Cikin sanyi da yanayin tsoro da kuma ruɗu Khausar ta dubi Mommy yayinda, jikinta ke rawa kamar zata faɗi.
Kallonta Mommy tayi cike da tausayinta ta girgiza kai kana tace.
“Gashi na sani Khausar yanda kike rikicewa idan kikaji rugugi kike fita hayyacinki idan kika ga walƙiya bare kuma kiji tsawa!.
Gashi yau kuma ruwan yazo da wasu irin tswawwaki masu ban tsoro.


Cikin rawan jiki ta sanya hannunta dake ta karkarwa ta janye Hijabinta kana ta kalli Mommyn Muryanta na rawa tace.
“Yah Jameel ne ya kawo ni”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace.
“Kai Ubangiji Allah yayi masa albarka. Allah ya saka masa da mafi kyawun sakamakon”.
Kai Khausar ta gyaɗa still jikinta na tsuma tace.
“Ameen Mommy bari in cire kayana”.
Ta ida mgnar tare da wucewa Bedroom ɗin ta tana shiga ta kalli hannunta lokaci ɗaya ta sake shiga sabon tashin hankali, cike da damuwa ta yarfe hannunta kana tace.
“Nashiga uku Ni Faɗimatuzzahara ina nasanya hannu na! Ni Batula?”.
Duk da cewa tana cikin tsoro amma tana sane da inda ya zaro hannunta kai tsaye toilet ta Wuce tare da cire kayan jikinta ta sakarwa kanta ruwan ɗumi sabulu ta ɗauka ta mulke hannunta dashi kana ta shiga gogawa ajikin tiles dake jikin bangon tana Girgiza Kai kana tana mai Furta.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Astagfirullah wa'atubu ilaik Subhanallah ya Salam Allah na tuba”.
Da ƙyar ta iya yin wankan ta fito bayan ta ɗaura alawalan tare da buɗe Siff ta ɗauki dogon riga na roba baƙi ta sanya har zuwa lokacin jikinta na ƙamshin tularensa Sallaya ta shimfiɗa ta gabatar da Sallah kana ta riƙe carbi tana hawaye da Istigfari.


Acan ɓangaren Moddibo kuwa bayan ya gama wanka al'wala ya ɗaura tare da fitowa har zuwa lokacin zuciyar sa na tsaye alamar zai samu nitsuwa Siff ya buɗe tare da ɗaukar Boxes ya sa sai kuma ya tsaya yana kallon kansa, ya tabbata idan yasa Jallabiya mutane zasu iya fahimtar halin da yake ciki wani dogon tsaki yaja.
“Mitsssssssss!!! Yar iskar yarinya”.
tare da sanya hannunsa ya matse muhallinsa da ƙarfi wai ko zai masa biyayya cikin yanayin tashin hankali ya kalli kuma sunkuyar da kansa tare da faɗin.
“Wai wannan wacce iriyar Masifa ce!?”.
Sake buɗe sabbin boxers ɗin sa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login