Showing 18001 words to 21000 words out of 27791 words

Chapter 7 - ZARINAT (زرينة) book 1 free page's by zainab dodo.pdf

04 Jun 2025

1871

tashi lungu da sak'o na ko ina,
wanka ta shiga, ta fito d'aure da towel ta tsaya gaban mirror, ta bushe gashin ta daya jik'e wajen
wanka ta fara mulke jikinta da mayuka masu k'amshi da gyaran fata, bayan ta gama ta kawo
humrar ta itama ta mulke jikinta da ita, ta gyara fuskarta ta shafa lipgloss

Already daman ta fitar da kayan da zata saka, riga da siket sun zauna tsaff a jikinta tayi d'aurin
d'ankwalli mai kyau ta saka yan kunne da agogo ta d'auko fashion hijab d'in ta da fashion bag
ta rik'e a hannu taje gaban mirror ta k'ara feshe jikin ta da turare sannan ta fito falo

Tea ta had'a mai kauri sai k'amshi yakeyi, ta dawo falo saboda bata san cin abinci a dining, tuna
tayi bata d'auko filet ba ta tashi taje kitchen ta d'auko, shigarta kitchen yayi dai_dai da shigowar
yah ansar, yana sanye cikin dakakkiyar shadda fara yayi kyau sosai sajensa ya kwanta
gemunsa har k'yalli yakeso akan tsananin gyaran da yake sha, hannun sa rik'e da jakar aikin sa
shima ya shirya zai fita

Ganin kula a tsakiyar falon yasa yayi hamdallah ga allah dan yana da yak'inin cewa breakfast
ne a ciki

Fitowa tayi ta gansa tsaye, shi kuma tunda ta fito yake ya kafeta da ido har ta iso, ta aje filet d'in
hannunta tare da durk'usawa ta masa ina kwana amsawa yayi tare da k'ara sowa cikin falon ya
nemi guri ya zauna ita ma ta zauna, dukan su sukayi shuru shikam idanunsa akanta

Maganar zuci ta shigayi ita dai gaskiya bazata iya cin abinci a gabansa ba idan ma taci to a ta
kure zata ci gashi shima ya shirya da alama aiki zai je amman taga baya ma da alamun tashi to
ko baiyi breakfast bane? kai ina bama zai yuwuba nasan matarsa zata masa amman dai bara
na taya masa ko zai ci, tana gama fad'in haka a zuci ta tashi ta nufi kulolin ta bud'e ta zuba
soyayyar doya da kwai, wacce ta zuba a filet ta fi yawa akan wacce ke cikin kula, ta bud'e d'aya
kular egg sauce ta zuba a gefe ta d'aura filet d'in saman table d'in wajen taja takai gabansa ta
d'auki tea da ta had'oma kanta shima ta aza masa, ga mamakinta sai taga kamar yayi
murmushi ta koma ta zauna, ganin tayi ya k'ara jan table d'in gabansa ya cire hular kansa ya aje
gefe ya kai hannu ya d'auki cup d'in tea yakai baki, yaji dad'in sa sosai dan sai da yasha kamar
kusan rabi sannan ya aje ya fara cin doyar, spoon d'in da ta saka masa ma aje shi yayi yasa
hannu yana ci


Zarinat tashi tayi taje ta sake had'o wani tea tana sha, kallan ta yayi yaga bata sakama kanta ba
yace "Ke baza ki ci bane? zonan ki zauna muci tare" ya fad'a tare da nuna mata gefen sa "
Yaya wannan ya isheni" wani kallo yayi mata tare da fad'in "Tea ne zai k'osar dake" Yaya
damanfa banajin yunwa kuma idan nace zan ci yanzu to zan makara school "Ga gaskiyar
magana nan ta fito saboda kada ki makara yasa baza ki ci ba ko to ba inda zakije sai kinci ko
zaki makara" Marairaice fuska tayi tare da fad'in " Allah banajin yunwa" Breakfast ne ko bakyajin
yunwa sai kin ci, hak'uri tayi ta basa tare da magiya sannan yace "alright jira ni nagama sai na
sauke ki"

Aje shan tea ma tayi tasaka hijab d'in ta ta rataya jakarta ta samo masa wajen da zai wanke
hannun sa idan ya gama tayi zaune tana jiran sa, ajima ajima ta kalli agogon hannun ta ganin
lokaci na tafiya, yana lura da duk abunda takeyi

Sai da ya cinye gaba d'aya sannan ta taso ta zuba masa ruwa ya wanke hannun sa ta Mik'a
masa tissue ya k'ara goge hannun sa ta kaushe kayan takai kitchen ta fito tana sauri dan ta
k'osa suje ta kusa makara, suka fito yana gaba tana bayansa
har suka isa wajen mota suka shiga ya tada

Har kusa da inda zasuyi lecture ya kaita dan yaga 8 har ta wuce, yana tsayawa ta fito da d'an
sauri ta nufi hol d'in da zasuyi lecture

Tana zuwa kawai ta tura kai ta shige tare da yin sallama cikin zazzak'ar muryar ta

hol d'in anyi shu tsiff_tsiff_tsiff kamar ba mutane a ciki, saboda malamin yanada tsauri sabon
zuwa ne baya wasa sannan idan har ya riga ya shigo ba wanda zai sake shigowa kuma ba mai
fita, koda 8;1 ka shigo tofa sai ka fita, surutu haramun ne indai yana ciki idan kuma kayi ya
kamaka zai baka kyautar C/O shiyasa bamai wasa
Dr abbas da ido ya bita har ta samu waje ta zauna kusa da wata sabuwar zuwa, Dr abbas
tsintar kansa yayi da kasa korarta yadai bita da ido, ci gaba yayi da lecture, yan class sunyi
mamaki sosai ganin bai koreta ba bayan kuma kafin tazo akwai wad'an da suka zo ya kore su
amman ita ya kyaleta, har hakan yaja aka fara yan surutai sai da ya daka musu tsawa sannan
Yana lecture yana kallan ta har ya gama ya fita, bayan ya fita wacce ta zauna kusa da ita tace "
Sister sannu"Yawwa "Sunana faridah Kefe ? " Zarinat "Nice name" Thank you " welcome kusan
sati na d'aya da zuwa but ban ta'ba ganin ki ba" Nayi tafiya ne " zarinat ta fad'a
" Okay sannu da hanya "Yawwa" Kar kiga na dameki fa idan kina so sai na yi miki bayanin
lectures d'in da akayi bakya nan " Kai dako na gode wallahi" Kai ba komai zamu iya farawa
yanzu kenan " Eh" To amman gaskiya ba lallai ne namiki bayanin su duka yau ba " To shikenan
ko rabi mukayi yau gobe sai mu ida" Okay " faridah ta bud'e jakarta ta ciro littafin ta da take
jotting a ciki, nan ta fara yi mata bayani kuma ba laifi zarinat ta gane sosai


Faridah irin black beauti nan ne sannan allah ya bata ilimi ga son jama'a



Exchanging numbers sukayi, zarinat taje suka gaisa dasu saudat ta dawo suka fita ita da
faridah dan suje su siyo ruwa, suna tafiya faridah na fad'a ma zarinat k'a'idojin Dr abbas zarinat
tace "Ahh lallai kice d'azu sa'a naci" Wallahi kuwa " suna tafiya suna fira suka siyo ruwa suka
dawo a hanyar su suka had'u da Dr abbas tun daga nesa ya kafe zarinat da ido har suka iso
kusa dashi saboda nan ne hanyar da zasu bi take, gaidasa sukayi ya amsa hankalinsa nakan
zarinat har suka wuce bai dena kallon ta ba sai da suka shige class sannan ya nisa tare da
sakin murmushi yabi hanyar sa, suna shiga malamin da zai shugo musu ya zo
Suka fara karatu

Shabiyu daidai ya fita, wanda zai shigo 12 ya fita 2 yace bazai samu daman zuwa ba su had'u
wani sati, suna fitowa taga driver, tun d'azu yazo saboda baisan time d'in da zasu tashi ba,
sallama sukayi ita da faridah ta wuce............................................















Comment and share fisabilillah ♥️


ZARINAT ( ةنيرز )







Mallakar
Zainab dodo✍️









Wannan shafin sadaukarwa ne a gareku masoyan wannan littafin masu bibiyarsa much love
for you fisabillilah ♥️♥️♥️♥️♥️♥️♥️♥️♥️♥️ alkhairin allah da rahamarsa ya kai muku aduk

inda kuke allah ya lullu'be ku da bargon rahamarsa ✨ love's you
all masoya masu k'amshin tufa




Maison magana dani zata iya tuntub'ana ta Wannan number
09046495943
Chart only




_____________________________
_______________
________
TASKIRA WRITER'S FORUM
T. W. F

Rubutu Baiwace Ga Wanda Allah Ya Baiwa Da Hikimar Mu Muke Alfahari

TASKIRA ASIRIN MARUBUTA
_____________________________
_________________
________
________
BISMILLAHI Rahmanirahim
________
Page 1️⃣5️⃣

Inna ce ta fito daga d'aki fatima na zaune tana aiki, kamar ance ta d'ago kanta sai ga fuskar
inna, ta shafa barbad'a kumatu (k'yalk'alin balaga) ta shafa shi kamar powder ya mannu a
fuskar sai k'yalli takeyi

wata irin dariya ce tazo ma fatima sai dai ba damar yi dole ta k'umshe abarta amman duk da
haka sai da ta rik'a yi k'asa_k'asa

Nasir na shigowa yaganta baisan lokacin da dariya ta kubce masa ba yayi ta yin dariyar sa har
inna ta k'ulu dan bata san abinda yakema dariya ba ta zabga masa ashar tayi sannan ya daina
yace " Inna hala dai baki kalli madubi bane ? kinga yarda fuskarki ta koma kuwa? hhhhhh
"Ahhahhhh ga ja'irin yaro me fuskar tawa tayi ne da kazo ka sakani gaba kana dariya " Fatima"
Naam " Je ki samomin madubi"To" ta fad'a tare da Mik'e wa tayi d'akinta ta d'auko wani k'ara
min mirror ta kawo masa, Mik'a ma inna yayi tare da fad'in ta duba ta gani

"Innalillahi wannan wace irin y'ar banzar hoda ce haka wallahi sun suceka sun siyarma da
wacce ta lalace " Hhhhhhh inna sai da na fad'a miki wannan ba irin naku bane ba haka ake
shafa shi ba"To kunsan yarda ake shafawa amman kuka kyaleni bakuyimin bayani ba bama ba
laifin ka bane duk laifin waccen bak'ar munafuka ce, ta fad'a tare da nuna fatima" tunda taga
bata samu masu kyau irin nawa ba shine tak'i sanar min yarda ake shafa wa dan kar nayi
kyawo to ta allah ba taki ba "Haba inna miye kuma laifin ta a ciki" Eh ai dole ka goyi bayan ta
tunda kana tsoron ta "Allah ya huci zuciyar ki kiyi hak'uri yanzu idan na fita zan siyo miki mai
kyau"Kuma wallahi mai tsada zaka siyo dan nama lura kamar nata sunfi kud'i " Girgiza kai
kawai yayi, fatima na duk'e tana aikin ta bata ce komai ba


Nasir ya wuce ya shige d'aki ita ma ta aje aikin da take tabi bayansa inna ta bisu da harara tare
da fad'in" Jarababbu kawai " ta d'auki buta tana wanke fuskarta














Zarinat yanzu idan zata dafa abinci to na mutum biyu take dafawa ita da yah ansar saboda a
wajen ta yake cin abinci safe da rana da dare duk anan yake ci sai dai har yanzu bai ta'ba
kwana 'bangaren nata ba idan ya shiga dai zai jima a can suyi hira sometimes har 12 yake kai
sai idan yaga tana son yin bacci zai tafi,

Zarinat da faridah sun shak'u sosai k'awance su suke cikin aminci da yarda

'Bangaren husna kuwa tuni suka shirya ita da odu suka ci gaba da gudanar da haramtacciyar
soyayyar su


Dr abbas ya fad'a cikin matsanancin son zarinat, ko wacce safiya gani yake son ta na k'ara
ninkuwa a zuciyarsa, idan aka tashi school ya koma gida har allah allah yake safiya ta waye
yazo makaranta ya ganta hankalin sa ya kwanta, idan har ya shigo musu lecture har ya fita

idanunsa a kanta wanda har hakan yasa bata ma san ya shigo musu, duk da bata san abunda
ke zuciyar sa ba, saboda kawai yaji zazzak'ar muryar ta yakesa wani lokacin ya jefa mata
tambaya cikin ikon allah kuwa duk tambayarda yayi mata sai ta bayar da amsa


Yau ma fitowar su daga lecture kenan sun gama zasuje gida sai ga Dr abbas ya tsayar dasu
tare da fad'in " Har kun gama lectures d'in ne? "Eh, faridah ta fad'a " Okay zarinat ko?" Ya fad'a
tare da nuna ta, kai ta gyad'a masa yace " Good akwai group assignment da nakeson bayar wa
ina san ki zamo leader sai ki bani number ki idan na fitar na sanar miki " Okay sir amman ni
banada waya sai dai ko ka kar'bi number faridah" Haba big girl kamar ki ace bata da waya "
Murmushi tayi tare da fad'in" Sir banada " is okay bama saina kar'bi tataba idan na fitar zan
sanar miki"okay sir, ta fad'a tare da kama hannun faridah suka wuce

Faridah tace"Masoyiya wallahi gwauda da baki basa number ba dan ni Dr abbas d'in nan take
takensa ya fara yawa " Abar K'auna bari kawai ai shiyasa nace banada waya" To daki ka ce
masa ga tawa daya ce abasa fa "Hhhhhhh ai nasan bazai kar'ba ba ne" gwaunda hakan" suna
tafiya suna maganar
Dr abbas kuwa yana nan tsaye inda suka barshi kamar an dasa icce, ba wani group assignment
da zai bayar kawai dai yayi haka ne ko zai samu number ta ne, ya dad'e a wajen tsaye har su
zarinat suka bar makaranta yana wajen






Tana dawowa school ta d'ora girki yau tuwo take da sha'awan ci, cikin k'ank'anin lokaci ta
kammala girkin tuwon shinkafa da miyar alayyahu taji egusi sosai dan idan ba am fad'a maka
miyar alayyahu bace bazaka gane ba, gashi tayi kauri sosai tayi kyau sosai a ido sai k'amshi ke
tashi, tana gamawa ta fad'a toilet tayi wanka tare da d'auro alwala
Sai da ta fara yin sallah sannan ta shirya cikin wasu k'ananun kaya riga da wando na roba black
colour, kayan sun mata kyau sosai kuma sun kama jikinta ta saka hula white colour, sai ni'iman
taccen k'amshin ke tashi a jikinta ta fito falo


Yah ansar na dannar waya k'amshin turaren ta da yaji yasa ya d'ago kansa tare da zube
idanunsa a kanta " Tsarki ya k'ara tabbatar ga ubangijin sammai da k'asassai ma halaccin
wannan kyakkyawar halittar kai subhanallah " ya ansar ya fad'a a zuci lokacin da take isowa
wajen sai da ta gaidasa sannan ta zauna
Kallan da yake mata taga yayi yawa ta turo baki gaba cikin shagwa'ba tare da fad'in " Uhmm

uhmm yaya ni sai kayita kallo na kamar yabaka sanni ba" ta fad'a tana wasa da k'umbar hannun
ta, murmushi yayi mai sauti tare da fad'in " In banda abunki reena idan ban kalleki ba wazan
kallah? Kefa matata ce ko haramunne miji ya kalli matarsa? " Uhmmm nidai ban ce ba" ta fad'a
tare da Mik'ewa ta nufi dinning, bayanta yabi da kallo ganin duk yarda ta taka sai jikinta ya raya
mussaman mazaunanta da k'irjin ta da suke cike taf

Kawar da kansa yayi daga kallanta dan bazai iya jurar kallan ta ba har wani abu yake ji a
jikinsa..................................................

















Comment and share fisabilillah ♥️
ZARINAT ( ةنيرز )







Mallakar
Zainab dodo✍️

Maison magana dani zata iya tuntub'ana ta Wannan number
09046495943
Chart only




_____________________________
_______________
________
TASKIRA WRITER'S FORUM
T. W. F

Rubutu Baiwace Ga Wanda Allah Ya Baiwa Da Hikimar Mu Muke Alfahari

TASKIRA ASIRIN MARUBUTA
_____________________________
_________________
________
________
BISMILLAHI Rahmanirahim
________
Page 1️⃣6️⃣

Abinci ta kawo masa yaci yaji dad'in tuwon sosai yarda bakuyi tsammani ba har santi ya rik'a
zuwa ba, zarinat kuwa sai aikin dariya take, bayan ya gama ta kawo masa waje ya wanke
hannun sa, dan shi yafi san cin abinci da hannu bai cika cin abinci da spoon ba


Ta kaushe kayan takai kitchen ta dawo wayarta da ta aje tun d'azu a falo ta d'auka missed call
tagani dayawa, tana k'ok'arin duba wanda ya kirata sai ga kiran mom ya shigo ta d'aga tare da
kai wayar kunnenta

" Assalamu alaikum" princess lafiya ina kika shiga ne nayita nemanki a waya baki d'aga ba"
daga 'bangaren mom ta fad'a
" Ohh I'm very sorry mom nabar wayar ne a falo " Okay fatan dai kina lafiya" Lafiya k'alau mom "
Ma sha allah auntyn ki tace itama tayi kiran ki bagi d'aga ba " Mom ban gani bane" Okay to
albishirin ki " Goro kuma fari k'alk'alk'al, ta fad'a tare da yin fari da idanunta, yah ansar ya tasa

ta gaba yana kallo kamar ya samu tv


Mom sai da tayi dariya sannan tace" To auntyn ki ta sauka lafiya an samu d'ah namiji "
Yeeeeeeeeeee, ta fad'a da k'arfi tare dayin tsalle, mom sai da ta janye wayar a kunnenta
saboda k'arar da tayi

Suna had'a ido da yah ansar ya girgiza kai, gefen fuskarta ta shafa, wai ita taji kunya ta koma ta
zauna

Fira suka d'an ta'ba da mom, zarinat sai shagwa'ba take zuba mata, zasuyi sallama yah ansar
ya amshi wayar suka gaisa da mom tare da mata barka ya Mik'a ma zarinat waya, mom tace "
Princess wai daman yana kusa kike wannan abun" Uhmmmm, ta fad'a tare da turo baki " Allah
ya shiryamin ke" Amin mom let me call aunty " Okay, sukayi sallama

Ta kira aunty maryam tayi mata barka, yah ansar shima yayi mata barka, ta bama yaya bilal
suka gaisa





Kwana biyu da haihuwar zarinat ta fara yi masa maganar tafiya, to kawai ya cewa,


sunah sauran kwana uku ta masa magana har yafi a k'irga ce mata kawai yake yaji, har tayi
fushi ta daina yi masa maganar harda zaman da suke suyi fira ta daina da ta kawo masa abinci
zata shige bedroom sai ya fita take fitowa, wanda hakan na damunsa dan ya saba da su zauna
suna fira ko suyi kallo tare, shi bawai hana mata zuwa yayi ba aah yafi son sai ranar sunah sai
suje tare marece

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login