Showing 75001 words to 76736 words out of 76736 words

Chapter 26 - MIJIN ALJANAH 1 to end Complete Hausa Novels by King Boy.txt

18 Nov 2025

1209

M. nasir din.


Da suka shiga bayan ya gaida matar gidan ya tambaya ina malam?. matar tace wllh yaje can gidan su basmah wai iskokanta ne suka dawo.


Zainab tace iskokan basmah sun dawo! yayi yi sauri muje can din. ba'a dau lokaci ba suka karaso gidan su basmah din. malam zaune yake sai fama yake da Marsiyya taki ta fita shi har yama Rasa ya zaiyi da ita.


A lokacin suka shigo da Al ameen. Abun mamaki ana shigowa gidan al ameen ya dawo garas wato kursiyya ta tsere. Tambayar husaini yake wai me suka zo yi nan? husaini ma yayi mamaki ganin al ameen din da yake yunkurin kashe kansa amma gashi yanzu garas.



A zuciyarsa ya kawo cewa aljanar ce ta gudu da aka zo shigowa. Malam Al amarin marsiya ya bashi haushi ainun hakan yasa shi cewa a kawo mishi Ruwa a kwano. kafin a kawo da husaini yaga da dan space sai yace amma shima wannan aljana ce,



A jikinsa amma muna shigowa nan kaga ya ware" hannu kawai malam ya daga mishi.da aka kawo Ruwan yayi Ruk-yah a ciki tukun ya dinga karanta suratul baqara kuma yana dibar Ruwan yana watsawa a fuskan basmah din.


Marsiyya ihuu! take kamar wacce za'a cire wa Rai amma dan taurin kai cewa taki bazata Fita ba Sai dai in a kashe ta. lokacin Naga sauran dangi sun karaso su abba da dady har da Yasmeen.



A rude Yasmeen saida taga Al ameen din a zaune ya Natsu tukun itama ta sama nuTsuwa, kawu kasumu ta gani a gefe a zaune a zuciyar ta tace shi kuma wannan me yazo yi nan, lokacin ya waigo ta kuwa galla mishi harara, sunkuyar da kai kawai yayi, hajara ma tayi mamakin ganinsa amma ko kallonsa batayi ba. malam kam baya da Alamu tsayawa,



A karatunsa marsiyya kuwa sai kuka take tana ihuu! kursiyya ta fara kira "aunty ki taimake ni ki cece ni" kursiyya dake gefe Rasa yanda zatayi tayi domin tasa in har ta shiga hannun malam ta banu. Ganin ana neman hallaka kanwarta marsiyya kuma tasan halinta da Taurin kai ko tace ta fita bazata fita ba. haka yasa ta Yankr shawarar bawa malam hakuri. Jikin basmah din itama ta shiga.


A lokacin suka ji murya ta Rabu biyu daya nabawa malam hakuri daya kuma na kara. malam yace,"ke kuma wacece?." "sunana kursiyya kuma ni yayartq ce dan allah kayi hakuri kabar toya ta"



Al ameen Tsuru yayi yana kallan basmah da bakinta ne ke mutsi amma duk wanda yaji yasan ba ita ke magana ba. malam, "au dama kece kursiyyar ke me yasa kika addabi Rayuwar wannan bawan allahn kuma har ta kai ga kina neman halaka shi kina so ki rabashi da Rayuwarsa"



"Malam shi yasan abunda yayi min Aure na yayi ta waya bayan baisan ko ni din wacece ba kuma baiji ko muryata ba balle yaga pic dina a haka ya aure ni ya Rabani da masoyina kuma yamin alkawarin bazan kara aure ba sai gashi nazo gidansa naga yana da mata amma sbd san da nake mishi banyi mishi komai ba a lokacin kuma sai na boye kaina ma idan ma ina san wani abu a gurin shi sai dai inyi suffar matarshi."


Al ameen da Yasmeen suka kalli juna, Yasmeen cike da tabbatar da zargin da ta dinga yi a baya. malam ya juyo. 'ya tambayi Al ameen shin haka ne duk abunda ta fada" Al ameen yace kwarai haka ne malam Amma ni bansan Al jana bace kuma ni a wasa na dauki abun ba da gaske ba..."


A lolacin Tsawa basmah ta daka mishi cikin wata kakausar murya tace, Rufe min baki Al ameen ksr in hallaka ka yanzu" malam najin haka Sai yaci gaba da karatu hade da watsa musu wannan Ruwa,



A tare su biyun sukayi wani uban kara Kursiyya ta fara cewa malam kayi hskuri kabar toya mu" Marsiyya kuwa dan tsabar taurin kai ko magana bata yi sai dai kara, malam yace. "To anji yayi miki laifi amma cikin Rashin Sani ne to dan haka kiyi mishi hakuri ki fita daga Rayuwarsa ki koma can wajen danginki.."



kafin ya karashe maganar tace, "bazai yuyu ba malam sai dai kayi duk abunda Zakayi Domin kuwa bazan taba hakura ba Sai na dau fansa. sai dai ka kashe ni amma bazan fasa kudirina ba domin yanzu yana fita daga gidan nan ni zan kashe shi da kaina bawai in shiga jikinsa insa ya kashe kansa ba"



Malam yayi murmushi, "ina dai ce sai kin fita daga hannuna ne sannan zaki cutar da shi, ina so ki sani bazan taba barin ki ki fata daga hannuna ba tunda abun naki haka ne" yana gama fadin haka ya juya ya dauko wata kwalba addu'a yayi kafin ya bude a ciki ma ya yi addu'a ya tofa. karata yayi a saitin bakin basmah yaci gaba da addu'a, su kuwa su marsiyya ba abunda suke yi in ba ihuu! ba, daga karshe marsiyya ta daka wani uban ihu wanda kowa na wajen sai da ya rufe kunnan sa, ihuun ya fito da ambaton "baaabaaah" can wani bakin hayaki ya dinga fitowa daga bakin basmah yana shiga kwalbar, baysn ya shige tas! malam yasa murfi ya Rufe bakin kwalbar.


A daidai lokacin wasu Aljanu suka fara bayyana ta ko'ina na gidan...........................................................................

Good morning my friends, KOMAI YAYAI FARKO?? sauran 1 page isha'allah

Shiga nan ka/ki yi like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn
https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarksbookmarks





✍🏼Autan marubuta ✍🏼



👑King boy👑












🎃🤖💩 aljanu ne suka ta bayana suka cika gidan🤢👹👺 kowa a wajen ya firgita bama kamar mata. wani farin Aljani ne mai fararen kaya👳🏼 ya bullo Akan wata kujerar sarauta gefe-da-gefan sa kuwa wasu kyawawan yan mata ne farare ke mishi fir-fita da wani kalan mafici.

gashin sa na kai har jan kasa yake haka ma gemonsa ya zo har wajen cibiya gashin girarsa ma haka dogo ne. mutumin duk da yana suffa irin ta mutun amma idan ka mishi kallo daya Sai ka tsorata. Cikin wata murya mai dan dadi wacce baza'a kushe ba, "yan adam ku kwantar da hankalin ku muma musulmi ne baki dayan mu baza mu cutar da ku ba," malam juyawa yayi yana kallansa kafin yace. " To kai din waye?" Aljanin yace sunana Mukurik dan jamka-jamka amma a halin yanzu na musulinta sunana Muh'd, Ni a yanzu Sarki ne na aljanun duk African wannan kuma da kake gani su biyun wato, marsiyya da kursiyya, yara nane su biyu na mallaka. A lokacin da na gane gaskiya na muslinta su kuwa sai sukayi taurin kai suka ki muslinta gaba daya ma suka baro gida, ita kursiyya sai tabi saurayinta wanda shima yaki muslinta a lokacin wato dursum amma a yanzu ya muslinta sunansa Zaid, Gashi a gabana."



malam ya gyara zama ya gyada kai yace " naji kuma na yarda domin ga alamu nan duk jikin ku fararen kayane, ya daga kwalba da su kursiyya ke ciki, wannan yaran naka Taurin kansu ne yayi yawa Domin ita babbar ta samu wannan bawan allahn, malam ya nuna Al ameen, wai ta aure shi bayan kuma ya gano aljana ce a yanzu kuma nema take ta halaka shi, ita kuwa karamar ta like wa wannan yarinyar ba tare da ta mata laifin komai ba na bata hakuri amma taki wannan Ruk-yah ta biyu ce kuna a wannan karon tace bazata fita ba shi yasa nasaka su cikin kwalba amna a yanzu ya kake so ayi yakai wannan sarkin aljanun?"


Sarkin aljanu yayi ajiyar zuciya tukun yace "Nima hukunci biyu ne dani a tare da su bude su a yanzu A tambaye su idan sun yarda zasu muslinta kuma zasu Rabu da wannan yaran mu koma gida su auri jinsin su to In sun yarda sai in nema afuwa a gurin ka ka sake su yakai wannan malamin bil adaman idan kuwa basu yarda ba to a nan zan bar maka su kayi duk yanda kaga dama da su,"


malam baiyi gardama ba ys bude su kursiyya sai hayakin ya fito yaje ya taru waje daya ana jimawa sai ya rikide ya dawo su kursiyya a galabaice suke duk sunci wuya jikinsu duk kuna ce domin cikin kwalbarma toya su ake addu'a da malam yayi a ciki, Baban su ne ya maida musu jawabi a kan sharudan da ya gindaya a kansu ya zabi na gare su.


Da sauri marsiyya tace "Abba ka yafe min wllh ni dai na yarda zan muslinta kuma in rabu da basmah na gwammace inyi haka da a mayar dani cikin wannan azababiyar kwalbar". Haka jawabin ya fito daga bakin itama kursiyya. Sarki yace to Alhamdulilah kaji yanda suka ce malam, malam shima hamdala sukayi tare da duk jama'ar wajen sannan yace, "Yanzu abunda ya kamata shine ku fara karbar muslinci tukun. malam ya dinga biya musu kalmar shahad suna fada bayan sun gama yace to Alhamdulilah yanzu kun zama musilmai kuma ku sani muslinci addini ne mai a dalci ba cuta ko zalunci a ciki sauran bayani abbanku zai muku bayan kun koma gida, yanzu abunda ya kamata sai ku nema yafiya gurin wanda kuka cutar bama kamar ke kursiyya.


Nan aka shiga yafiya tsakanin mutane da Aljanu, marsiyya tace wa su hajara, "Ina so ku sani duk abunda kawu kasumu yayi ni na umarce shi kuma kursiyya ce ta Rikide zuwa Al ameen ta saki Yasmeen a lokacin ba al ameen din gaskiya bane" yar ido suka shiga yi suna ta mamakin wannan abun hatta su abba sunyi mamaki. kursiyya da su aunty hajara suka nemi yafiya gurin kawu kasumu yace ba komai ai kuma naji dadi da gaskiya ta bayyana ba wanda zamu godewa sai Allah. malam ya juya yawa su Al ameen Nasiha domin sakaci da addu'a duk shi ya jawo musu wannan a matsayin su na musilmi da sun Rike addu'a da abun ya dinga zuwa da sauki sannan yayi gargadi ga Al ameen cewa ya kiyaye ta kafar sadarwa yasan irin wanda zai dinga mu'amula da su, Al ameen yace na gode malam isha'allah zamu shiga makaranta koda kuwa ta dare ce domin duk Rashin ilimin addini ne yajawo muna.



Rabuwar arziki akayi da sarkin aljanu batt suka bace gaba daya aljanun gidan hadda su kursiyya ba'a bari ba.


Husaini

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login