Showing 42001 words to 45000 words out of 163126 words

Chapter 15 - TURKEN GIDA BOOK 3 COMPLETE BY JANAFTY.txt

Janafty   

18 Dec 2025

1078

mata na san tana yi ba. Kwanaki har sa'in mun yi da ita amma ban faɗa ma kowa ba. Saboda Yallaɓai ya yi mini kara ya kuma darajani ya nuna mata in ta ce za ta mini rashin ɗa'a to kamar shi ta yi mawa! Me ya jawo mini wannan darajan? Haƙurina da nuna komai ba komai ba. Na san kishi da zafi na san kishi na da raɗaɗi amma don Allah ki daure ki yi addu'a  in sha Allahu za ki samu sauƙi samun sauƙin ki kuma shi zai ba ki damar da za ki zauna ki yi ma kan ki tunanin mafita. Mafitan kuma shi ne haƙuri da kauda kai. Wata rana sai labari Ma'u. Haka  duk wata macen da aka yi ma abokiyar zama ta ke ji da farko amma in ta yi haƙuri wata rana sai dai ta tuna."

"Wannan gaskiya ne."

In Ya Aina. Ya Balki ma ta ce shawara mai kyau. Har Ya Murja sai da ta ce na gama ba ta dukkan shawaran da za su ba ta. Ma'u sai sharan ƙwalla tana mini godiya na ce yiwa kai ne amma na jadadda mata faɗa da miji ba na ta ba ne. Itama uwargidan nata na yi ne saboda ta ga ta ɗaga hankalin ta in ta ga ta kwantar da hankalinta da kanta za ta daina. Daman ai kulawa yabawa ta ga ana yabawan ne shi ya sa.

Har na koma gida auren mijin Ma'u ya tsaya mini a rai. Na tausaya mata matuka. Ba ita kaɗai duk macen da za a yi ma abokiyar zama tausayi take ba ni. Mace ba ta sanin gwagwarmayan zamantakewa har sai an yi mata abokiyar zama. In shekaru dubu za ki kwashe da mijin ki in dai bai ƙara aure ba, to ba ki san zamantakewa mai cike da fafutuka ba. Mu da a ka yi mawa muke zaune da su mu kadai ne za mu iya faɗin irin fafutukan da muke yi a zamantakewar mu na yau da kullum.

Na daɗe ban cire abin a raina ba. Kuma kusan ɗan'uwa rabin jiki duk yadda na ke jin haushin Ma'u tausayinta ya danne haushin nata bayan kwana biyu na kira ta a waya na ƙara tausarta ta, da ba ta shawarwarin da za ta riƙe su amfane ta. Tana kuka tana faɗa  mini.

"Na gode Sadiya. Na gode Allah ya saka da alheri."

"Bakomai yiwa kai ne Ma'u"

"Duk da haka dai zan yi miki godiya. Duk da tarin abubuwan ƙin da na yi miki ba ki riƙe ni ba. Matsala ta tunkaro ni kin nuna mini ke ɗin ɗin yar'uwata ce. Ba ki yi mini dariya kamar yadda na ke yi miki ba in kin shiga matsala. Sai ki ka zabi ki jawo ni a jiki ki saboda mu gudu tare mu yi tsiran tare. Na gode Sadiya kin ƙara haska mini rayuwa. Na gode ina fatan ki yafe mini duka laifukan da na yi miki."

Sai ta ba ni tausayi har sai da ruwa ya cika kwarmin idanuwana

"Na yafe miki Ma'u. Allah ya yafe mana gabaɗaya."

Muka yi sallama kamar ta yi min sujjada. Rayuwa kenan ban taɓa tunanin Ma'u za ta yi laushi haka ba sai ga shi a cikin lokaci ƙalilan Namiji ya birkita mata tunani. Hmm namiji. Namiji buhun ƙaya ne. Mai sauya launi gabansa fari bayan sa baƙi.





*Janafty**TKGB30G07*

Lokaci bayan lokaci ina kiran Ma'u na ji yadda a ke ciki. Zamantakewarta da Alhajin nata dai sai a hankali, tun da ya yi niyyar auren nan sai ya yi ita kuma Ma'u rashin haƙurin ta ya sa duk ta zube a wajen shi. Shi fa daman Namiji haka yake. In suka tashi ƙara aure to ba sa ji ba sa gani ne in ba ka yi haƙuri ba to za ka yi nadama ko kuma ka ga a na yi. Kuma a yadda na lura ita Uwargidan Ma'u ta na yin komai da gayya ne saboda tura ma Ma'u haushi. Ko ramuwa ta ke yi wa ya sanin mata. Domin Ma'u ta yi lokacin ta yanzu ne alƙadarinta ya ƙarye take girban a bin da ta shuƙa.

Ni dai haƙuri nake ba ta domin babu kamar haƙuri. Ba a yanzu za ta ga riban hakurin ba sai nan gaba. In dai za mu yi waya da Ma'u sai na ji ta cikin kuka Allah sarki wallahi tausayinta nake ji. Saboda ni na san zafin ƙishi, ga kuma ita abu ya haɗe mata biyu ga kishi ga ba zaman lafiya da miji. dole ta yi kuka, abin da ya ba ni mamaki cikin lokaci ƙankani wannan rashin jituwar dake tsakanina da Ma'u ya gushe. Har mantawa na ke yi da ba ma jituwa, ko ban kira ta abu kaɗan za ta kirani ta na faɗa mini ni kuma na yi ta ba ta hakuri domin shi ne kaɗai abin da zan iya faɗa mata. Sannan shawaran haƙuri na da zafi sai dai tana da riba a nan gaba.

Tana kawo mini ƙorafin cewa ranar da ya ke gidanta kusan raba dare ya ke yi waya ko chart in ta yi magana sai ya ce ba ta isa ta hana shi yin waya ba. Na yi ta ce mata ta yi haƙuri ta ƙyale shi ta riƙa shigewa cikin ɗakin ta, ba ta ji ba ballanta hankalinta ya tashi tun da ta faɗa mini ba a ɗakinta ya ke wayar ba ko falo ko cikin Bedroom ɗin shi. Sannan ta ce ba ya mgana da ita ko gaishe shi ta yi da ƙyar ya ke amsawa. Ya kuma je can Kura ya karɓo yaran ya kai su gidan Uwargidan, da ita kawai ya ke shawara yanzu ita ce ke kitsa masa komai a kanta duk na ce ta kauda kanta daman yana yi ne saboda ta yi mgana to ta yi kamar ba ta ji ba kuma ba ta gani ba. Ni ko Yallaɓai ban taɓa masa mganar ba sai ranar ya na gida na ya ji muna waya duk da tashi na yi daga falon saboda sirrina bai kamata na yi wayar yana wajen ba.

Sai da na dawo falon ne jin bai tambaye ni ba, na san halin shi Yallaɓai bai cika bin diddigi ba. Ni ce ma na faɗa masa Alhaji Mustapha zai ƙara aure. Kawai sai ya fashe da dariya ya na faɗin."Ma sha Allah. Ta uku fa zai yi ko?
Ya faɗa ya na kallona sai kawai na gyaɗa masa kai ban samu zarafin mgana ba.

"Kai ya yi ƙoƙari da kyau. Gwara in kana da shi ka cike sunnar gabaɗaya."

Kawai sai na yi jagale ina kallon Yallaɓai har wani dariyan nishaɗi yake yi.

"Yaushe ne bikin?

"Ban sani ba."

Na faɗa ina tsumewa, sai ya sake kallona yana mini dariya. Haɗe rai na yi ina kauda kai kafin na ce" Yallaɓai ko kai ma kana shirin yo ta ukun ne?
Sai ya kalleni kafin ya ce" To in Allah ya kaddara min zan ce ba na so ne?
Har sai da na buɗe baki saboda mamakin sa. Ni fa daman tuni na sha jinin jikina Yallaɓai zai iya ƙara aure in ma bai cike ƙofa ba.

"Kishi kike yi? Ba ki so na ƙara aure?

Tsaki na so na ja amma sai na yi shi a ƙasan raina.

"Ai ni ka gama mini kishiya Yallaɓai. Duk wacce za ta zo daga baya ba za ta ɗaga mini hankali ba."

"Ki ce wallahi."

Ya faɗa ya na mini dariya sai na ga ya mai da ni kamar wata shashasha. Hararan sa na yi, ban sake mgana ba.

"Ki rantse in yanzu na ce zan ƙara aure ba za ki ji komai a ranki ba?

"Ba zan ji ba. Ba kuma sai na rantse ba."

Kawai sai Yallaɓai ya ta so ya zo gabana ya durƙusa.

"Ki ce wallahi ba za ki yi kishi ba."

Sai kawai na kalle shi, lura na yi maganar ma nishaɗi take saka shi.

"Ba sai na rantse ba."

"To ƙarya ne. Ke ɗin ce ba za ki ki kishi ba?

Ya faɗa har ya na jan mini kumatu, na ture hannunshi kafin na ce" Me ya sa zan yi kishi! Na faɗa maka ni ka ga mini kishiya. Yanzu ai tsakanin ka da Gimbiyar ka ne."

"Saboda kina sona Sadiya. Shi ya sa za ki ji kishi na."

Kamar zan yi mgana sai na fasa ganin ko na tanka ba zai bar maganar ba zai ta tsokana ne yana mini dariya sai kawai na kauda kaina ban yi magana ba. Cikina ya shafa kafin ya ce.

"Bomboy fito ka ga mamanka sarkin kishi."

Da dai ya ga ban kula shi ba sai ya koma wajen zaman shi daman aiki ya ke yi a cikin system ɗin shi ya baro ya zo jin ta baki ganin kuma na ɗaure fuska ya sa dole ya ƙyaleni a cewar s na zama jagwam magana ma masifa ce da faɗa a wajena. Saboda ma yadda ya yi ban samu faɗa masa matsalan Ma'u ba na kama kaina sanin ina ma faɗa masa sai ya ce laifinta ne tun da Namiji ne, ba zai ga laifin ɗan'uwansa ba.

Mun yi waya da Ma'u kwana biyu ranar wata laraba Yallaɓai ma ba gidana yake ba, misalin tara na dare sai ga Ma'u a gidana afujajan cikin kuka sai da na ji gabaɗaya hankalina ya ɗaga, Yallaɓai ya fita kenan ya zo yi mana sallama ina tunanin ko gida bai kai ba lokacin da ta zo. Ɗaki na ja ta cikin tashin hankalin ina tambayan ta ko lafiya na girgiza da take faɗa mini Alhaji Mustapha ne ya ce ta bar masa gidansa ya sake ta saki ɗaya. Sannan lamarin bai tsaya a nan ba sai da ya haɗa mata da mari gabaɗaya farar fuskarta gefen hagu ya ta sa da shatin hannunsa.

"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un har da mari?

Na faɗa ina cikin matsanancin tashin hankali.
Ma'u ko kuka kawai take yi ta ma kasa mgana gabaɗaya sai na ji ƙafafuwana sun yi sanyi. Cikin jikina sai da na ji ya cire waje ɗaya ya motsa saboda tashin hankali.

"Me kika yi masa da zafi haka Ma'u?

Na faɗa ina mai dafa kafaɗanta cikin yanayina na damuwa. Da ƙyar na samu ta tsaigata da kukan nata ta yi mini bayani da cewa yau a gidanta ya ke yi jiya ma haka to a cewarta jiya sai wajen sha ɗaya ya shigo gidan kuma ya yi shigewarsa ɗakin sa ko da ta shiga yana ta waya haushi ya sa ta fita ta bar masa ɗakin shi ne yau da ya dawo ya shiga ɗakinta a kan gadon ta yana waya da budurwansa ita kuma ranta ya ɓaci ta fizge wayar ta haɗa da bango ta fashe shi ne ya kifa mata mari, ita kuma ranta ya ɓaci ta yi ta faɗin mganganu shima yana faɗa daga ƙarshe ya ce ta bar masa gida ya saketa saki ɗaya.

"Innalillahi Ma'u me ya aike ki? Me ya sa kika biye masa?

"Haba Sadiya a kan gadona na sunna zai kwanta yama yi mini waya da budurwa na yi magana yana ce mini ai ba budurwa ba ce matarsa ce tun da saura wata ɗaya auren su. Ni kuma raina ya ɓaci na fasa wayar shi ne ya mare ni. Sadiya bai ishe shi ba har sai da ya ce ya sake ni, ni fa wai Alhaji ya saka ni fa Ma'u"

Ta faɗa cikin gunjin kuka gabaɗaya sai na ji kaina ya sara. Ba ni a ka saka ba amma na ji sakin nan a raina. A raina ina tunanin yadda Alhaji Mustapa ke son Ma'u ya na ririta yau ita ce ya sake ta saboda wata mace. Macen ma da bai aure ta ba. Lalle duniya juyi juyi na gaba ya koma baya. Lallashinta nake yi amma ni kaina na rasa kalaman bakina, lamarin ya dake ni, na ji abun a cikin raina na rasa yadda zan yi da Ma'u kuka kawai take lamarin akwai cin rai da baƙin ciki namiji ya sake ka saboda wata mace macen ma ba ta ma shigo gidan ba, to in ta shigo kenan sai abin da ya yi gaba.

Ni kaina kamar in yi kuka idanuwana har sun kaɗa hawaye sun tarun mini a ƙwarmin idanuwana, abin da Alhaji Mustapha ya yi zalinci ne kuma rashin adalci ne a kan gadon aurenta? Tsakani ga Allah ya kyauta kenan, sai na fahimci so kawai yake yi daman ya ga yadda Ma'un za ta yi ne. Duk yadda na ke cewa ta yi hakuri sai na ji hakan da ta yi ta ni a wajena dai-dai ta yi ta kuma san mutumcinta amma marin ne da ta bari a ka yi shi ne kuskurenta sannan me ya sa ta fasa ma sa waya? Da da ta yi masa magana bai ji ba sai ta bar masa ɗakin duk tsiya dai ba kwana zai yi ai ya na wayar ba. Kai gabaɗaya na girgiza da lamarin nan jikina ya yi sanyi matuƙa har na gaza wajen lallashin Ma'u.

Na bar Ma'u a ciki na fito falo Baby ta yi barci Jidda ce kaɗai ba ta yi barci ba. Amma na kora ta ɗaki daman tana falon su tana karatu ne. Jidda fa ba ta yarda ta yi zaman gida a banza ba ko da yaushe cikin duba littafanta na makaranta take yi. Na zauna na rasa mafita wa zan kira a daran nan? Har na yi tunanin kiran Ya Aina sai na fasa in na yi tunanin Ɗorayi sai na ji gwiwata ta yi sanyi. Duk wanda zan kira yanzu wataƙila ma sun kai ga kwanciya kar na ɗaga musu hankali, Yallaɓai na ji shawaran na kira shi ya kwanta mini a zuciyata har na ciro wayar a chaji zan kira shi sai na fasa tuna yana gidan Gimbiya bai da ce na kira shi ba, ko ba domin komai ba akwai sirrin da ba na so ta ji, shawaran na tsayar ni da zuciyata a kan da safe sai na kira shi, da haka na koma ciki na samu Ma'u har lokacin na dirjan kuka nan fa na zauna ina ta ba ta haƙuri na san lamarin akwai ciwo amma ta yi hakuri zuwa da safe sai mu ga yadda za mu yi ta koma gidan mijinta.

"Ba zan koma ba Sadiya. Allah na gama zama da shi tun da har ni zai wulaƙanta a kan wata macen da bai aura ba."

"A'a Ma'u ba za a yi haka ba. Za ki koma gidan ki. In ba ki koma ba ta vi riba kenan kin bari wata macen da ba ta ma shigo ba ta kore ki daga gidan mijin ki da ƴaƴanki."
Na gama faɗa ina bubbuga bayanta alamun lallashi.

"Duk ma abin da ya faru ai shi ya so haka Sadiya. Tun da ya ɗauko maganar auren nan ba irin cin kashin da Alhaji bai yi mini ina ta kauda kai ba saboda kin ce na yi haƙuri amma yau ya kureni har da mari fa? Sannan ya ce mini ya sake ni na bar masa gida. Ni Ma'u ni ce wai namiji ya sake ni kuma ya yi mini koran wulaƙanci?

Sai ta sake fashewa da kuka tabbas an yi mata tozarci duk da dai shima ina tunanin cikin ɓacin rai ya yi saki amma dai abin da ya yi bai kyautu ba, a yadda na ke jin zuciyata in ni ce ka yi ma wannan tozarci wallahi ba ma zan tsaya a kusa ba tafiya zan yi in da sai ka fara kuka kafin na dawo. Ni a tunanina ko na ce a hange na saki shi ne ƙarshen tozarcin da namiji zai yi ma mace saboda zai ƙara aure.

Amma ba zan ce Ma'u kar ta koma gidan ta ba, sulhu a ke nema, gidan ta daban nawa gidan dabam haka zalika, zuciyarmu ba iri ɗaya ba ne amma ni kam ba zan zauna ka mare ni ka mari banza ba, duk da haka tun da ta zo wajena da kukanta sai na tabbatar da an ƙwatar mata yancin ta. Tuni Alhajin ya zube min a idona ina ganinsa da ɗan kima a baya amma a daran na ji gabaɗaya na daina mutumtata shi.

Mun kai har wajen misalin biyun dare ina ba ma Ma'u baki a ɗakina mu ka kwana ni da ita saboda na ga ba ta ma cikin natsuwarta. Tana fashin salla ai da na saka ta mun yi tsayuwar dare a kan Alhaji Mustapha amma ni sai da na yi raka'a biyu sannan na kwanta. Duk da nauyin cikina amma ina ƙoƙarin yin salololin dare tun da na riga na saba. Ina da tabbacin Ma'u ba ta samu barci a daren ba duk lokacin da zan farka idanuwanta biyu. Baiwar Allah ta ba ni tausayi ni ma ai na shiga haka a baya kuma na san yadda mutun ke ji a zuciyarsa. Na so na zauna nima ban yi barci ba na ta ya ta jimami da ban baki amma ina barci ɓarawo sai da ya sace ni sai asuba na farka har ma mun kusa makara. Ina idar da salla na fita zuwa ɗakin su Jidda ganin Ma'u ta samu barci can na je muka yi azkar da karatun Qur'ani sai bakwai saura na baro ɗakin na bar su su ɗan ƙara runtsawa tun da ba zuwa makaranta yanzu mun kan kai sha ɗaya ma ba mu tashi ba in ba Yallabai na gidan ba ne in zai fita da wuri.

Falo na dawo na cire waya ta a chaji ta daɗe da cika tun jiya amma na manta ban cire ba. Yallabai na kira sai da ta shiga ma na ga kamar ya yi safe da yawa ina ma wannan tunanin na ji ya ɗaga wayar a muryansa na fahimci kamar ya na barci ne na tashe shi.

"Sadiya me ya faru?

Ya faɗa da sauri Allah sarki bawan Allah shi ma hankalin shi ya tashi ganin kirana a wannan lokacin. Ina da ciki fargabansa kar ya zo wani abu ne ya faru mara daɗi.

"Ka kwantar da hankalin ka bakomai."

Na faɗa cikin kwantar da murya ina jin ajiyar zuciyarsa.

"To ina kwana? Wallahi na tsorata da na ga kiran ki, "

Saboda ya san ni ba mai damun sa da waya ba ne in har ya na can gidan, in kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login