Showing 21001 words to 24000 words out of 38761 words
saboda bata ganima sosai tahaye sama kai tsaye babu wanda ta saurara dukda kowa ya lura da halin da take ciki babu lpy haka taje tasakama kofanta key tabarshi ajiki,
Su safiyya kuwa kamar za ah cinye su gida yakara kaca mewa ana maida yanda akayi duka ' yan uwan auntie babu wanda yake wal wala fuskar kowa a daure take kallon tara saura kwata kawai suke antayawa 'yan adamawa,
Matar yayan auntie harta gaji da buga mata kofa ta dawo tazauna.
SU hassan koda sukayi arba da twins kannen hasana sukayi ram dasu suna cikin fira yaji an kirata da hasana da mamaki ya kalleta, yace " sister ina taki 'yar uwar take?"
Murmushi hasana tayi masa tace" sister na ta rasu tun muna 3 years ma"
Tausayine ya bayyana a fuskarsu hassan din yace " Allah yajikanta itama kanwar mu nabiha tata sister din nawal Allah yay mata rasuwa tunkan a yaye su ma"
Hasana ta jinjina kai tace" Allah sarki"
Matsowa kusa da ita hassan yayi yace. " my sister zaki koya mana fulatanci?"
" Meze hana sena koya muku, amma auntie safiyya bata taba koya muku bah duk wannan lokacin"
Tabe baki hassan yay yace " inafa ay daddy hausa kawai yadage muka koya,kuma ay bamisan ta iya fulatan ciba harshi daddy din, seda sukazo adamawa tukunna yaga abin mamaki"
Suna cikin hira hassan yaji an rike masa hannu, koda yajuyo yaga meenal ce zaune gefenshi tana zubar hawaye, saurin karkatowa yayi gareta yarike mata hannu dakyau cikin damuwa yace.
" Yaya meyake faruwa ne?"
Cikin muryar kuka tace." nakasa yaddar ma kaina da wannan abubuwan dasuke faruwa, shin meyasa mahaifiyata da daddy zasuyi min haka? narayu batare da soyayyar mahaifiya bah"
Zama usain yayi gefenta yana share mata hawayen yace. " An sorry sister ni nasan irin zafinda kikeji a yanzu,ki kwanzar da hankalinki daddy zai miki bayni komai kada kiga laifin mahaifiyar mu, auntien ki itace ta haddasa duk wani abu dayake faruwa, haryanzun mommyn mu batada cikakkiyar lpy, kullum tanayin kuka akan rayuwarki tana begenki burinta itama be wuce wan nan ranar bah dazata halacci taron bikin ku keda ya muhammad, tunda ga ranar da akai muku aure ta dukufa tana addu ah Allah yakare ku daga sharrin makiya yasanya albarka a rayuwar auren ku keda ya muhammad"
Tunda usain yasoma ambaton muhammad tasoma dena fahimta, tsaida shi tayi tace.
" Wai shima ya muhammad kana nufin yayi aure ne?"
Kowa poster yay yana kallon meenal da mamaki,
" To wai yayarmu idan kina nufin bakisan ya muhammad shine mijin kiba?" hasan yay mata tambayar cike da mamaki.
Wata irin zabura meenal tayi tamike tana galla masa harara alamun karya yake,
Dariya hasana tayi tana rike baki tace " babbar magana "
" To wai inbashi bane mijinki! ina mijin naki yake? kuma ma meyesa muka ganku a tare gurin dinner?" hassan yay mata wan nan tambayar yana shirin yin dariya!
Kasa motsawa meenal tayi sabida komai seyanzu yake dawo mata cikin kwa kwalwar kanta....
TAKU A KULLUM NANA BMB
08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: ❣ RABON KWADO....!!
BOOK 3
NA NANA BMB
GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION
{ Marubuta masu garkuwa da alkalami domin fadakar da al'ummah }
page 37 - 38
Ganin halinda tashiga ne yasa daddy kallon mujaheed yace." Jeka kiramin shi tunda yaki daga wayan" yayi maganar yana murmusawa,
Shima murmushin yayi yamike yafita, " Karaso ki zauna mana meenal" cewar daddy kenan don yaga neman guduwa ma meenal keshirin yi,
Yana daga kwancen yaji saukan duka kan laps dinsa, be bude idanun sa dasuke rufe bah sema dafe kansa dayayi don yasan bawani bane se mujaheed.
" Taso natemaka maka mushiga ciki tunda naga ko wayar daddy ka kasa dagawa,kasan baka da juriya meyasa ka tsokalowa kanka" mujaheed yana kokarin jan hannun sa yake maganar,saurin mikewa yayi dayaji furucin na mujaheed yadauki wayan nasa yaga har 3 missed calls na daddy
" Ya salam! wlh nazaci kaine kake kirana fiti nan ne kawai yana ina daddyn?"
muhammad yay maganar yana me mikewa tsaye, murmushin mugunta mujaheed yasaki yaki gaya masa komai illah gaba ma dayayi ya kyaleshi shikuma yabi bayansa har zuwa parlour din na daddy,
Ya Allah muhammad sam beyi tsammanin ganinsu haka dayawa bah ga kallon da kowa ke masa shima hakanne yasa shi tsarguwa kunya takama shi, guri daya suka zauna da mujaheed yana fuskantar sa yasoma antaya masa harara kuwa, shikuma yana guntse dariyar muguntar dake cinsa, mussam man yadda ya hangi meenal tayi tsumu gefen mimi,
Seda daddy yay gyaran murya sannan yafara magana kamar haka.
" Shekara 14 kenan dana furta rasuwar safiyya, kaf jama ah sunyi tunanin safiyya mutuwar gaske tayi, to amma a zahirin gaskiya tana raye bata rasu bah, safiyya taga jarabawar rayuwa kala kala tundaga ranar da tabar gidansu ta rasa farin ciki, tayi rayuwa mara dadi ita da mijinta har zuwa lokacin da ya saketa yatafi yabar ta alokacin tana da yaron ciki, wan nan dalilinne yasa nake kulawa da ita har Allah yasauketa lpy, daga nan kuma na dawo da ita gidana tana karkashin kulawa ta saboda tashida min ita marai niyace bata da kowa se mijin ta daya saketa, tunda safiyya tasoma rayuwa a gidana tacigaba da fuskantar kalu bale kala kala daga gurin matata babu irin gallaza war rayuwar dabatayi musuba itada diyarta da hantara zagi cin mutumci, hatta nikai na seda narasa jin dadi a cikin gidana, to daga karshe ma maryam ita da aminiyar ta suka yanke hukun cin kashe safiyya gaba daya,
Duk dan saboda wani banzan tunani nata da asa rarren kishi irin nata, tana zargin mu ne nida safiyya kan cewar karuwa tace ita nakawo gidana na ajiye harta ma haifamin meenal,ahankali da salon yaudarar ta tasoma zubawa safiyya wasu kwayu a lemo tana sha batare da tasaniba safiyyan, sannu sannu jikin ta yasoma saki jiji yoyin jikinta suna saki harta kaiga bata iya tabuka komai, to daga karshe ma gaba daya allaurar kashe jijiyan jikin dan adam maryam tamata to a ranar ne bata kwana da numfashi bah tayi doguwar suma, likitoci dayawa sun kasa shawo kan matsalar ta safiyya saboda rayuwar ta tana tsaka me wuya,
Dr bello shine yabani shawarar na hanzarta fita da safiyya kasar waje domin ceton lpyn ta inba hakaba kam basuda yadda zasuyi wa jikin nata, koda na amince da shawarar shi ne yahadani da wani babban Dr a kasar dubai da address dinsa,
Tabbas abinda maryam tayi ya girgiza rayuwata matuka kuma yatabamin zuciya ganin idona nakamata tana gayawa aminiyar ta duk abinda tayiwa safiyya, hakanne yasa nagayawa Dr bello asanar wa kowa safiyya ta rasu don cikin sirri zan bar kasar da ita batare da kowa yasani bah wan nan hanyar ce kadai zatasa safiyya ta tsira, aranar seda nagamawa safiyya komai na tafiya tukunna nadawo gida nasami maryam wanda se alokacin takeyin nadama mara amfani, nikuma nariga da na yanke shawarar maka safiyya a kotu dole se itama tabar duniyar nan to, koda nakira mahaifina nashaida masa duka abinda yake faruwa yashida min cewar kada nayi haka tunda Allah yayi da kwanan safiyyan a gaba, kawai na dauketa mutafin can din ayi mata magani, kada kuma kowa yasan da hakan, kawai dai nabida maryam amatsayin takashe tan kuma kada nasaketa kodan yaran da ke gabanmu nana da kuma meenal, muddin na dauke meenal a gidan zata iya zargin wani abu, wan nan dalilin yasa hatta a gurin meenal mahaifiyar ta tazamo matat tah saboda ina kiyaye lafiyan safiyya duk wani abu daze bayyana gaskiya na tosheshi, bisa hukun cin da mahaifina ya yanke, kafin mutafi yakirani ya daura mata aure nida safiyya, a washe gari kuma na dauketa muka tafi bayan maryam tayi al kawarin zamewa meenal mahaifiya,
Seda safiyya tashafe watanni tukunna tasoma iya gane wanda yake kanta sedai bata iya komai sedai ayi mata, tayi kuka tashiga kunci tashin hankali saboda hankalin ta yana kan 'yar ta meenal kullum cikin magiya takemin na kawo mata diyarta sedai na bata hakuri wan nan damuwan data sawa kantane yahai far mata da ciwon zuciya abin yahade mata biyu lafiyanta tazama se a hankali,
Seda ta kwase watanni tukunna aka sallame mu a hospital bayan sun dorata akan magani kuma duk sati muna zuwa ganin Dr din nata wan nan dalilin ne yasa nace zaman dubai yakama ni nida ita, don akai akai ciwonta yana tashi dole bayanda za ayi lafiyan ta tazama kamar da amma likita yana iya bakin kokarin sa akanta, bata aikin komai duka nazuba mata 'yan aiki a gidan nata dana siya mana muke rayuwa a ciki yadda banida wani fargaba koda nataho Nigeria,
Sam safiyya batada walwala kullum cikin damuwa take akan yarin yarta kada maryam tayi mata wani mugun abun, dukda haka kuma nake rarrashin ta da bata hakuri takuma dage dawa 'yar tata addu ah, munshe kara da wani abune dayin aure safiyya ta haifa min twins bakaramin farin ciki mukaya da hakanba, se alokacinne safiyya tasoma walwala ganinta da babies dinta, a lokacin kuma ta shida min cewar tabawa muhammad meenal sosai nayi farin ciki da hakan don dama abin yana raina inason nafurta domin inason wanke zargin da maryam kemin dama wasu magul mata kan cewar meenal 'ya tace,
A ranar da safiyya ta haifi 'ya'yan ta nabiyu Aranar aka daura auren muhammad da meenal, hakan ya faranta mata ranta sosai, sedai tana cikin shayar da 'yan biyunta nabiha da nawal Allah yay wa nawal din rasuwa, tundada lokacin safiyya tasoma nuna wasu ala momi dasuke sakani shakku akanta don tabbas zuciyata taki yarda dacewa safiyya marai niyace akwai abinda take boyemin, kamar yadda nake tsammani kuwa a wata rana na tambayeta shin wacece ita wai ina ne asalinta? sam bata iya bani amsa bah karshe mah aman jini tafara muka tafi asibiti seda takusa wata acan, wan nan dalilin ne yasa bankuma yimata wan nan tambayar bah nadu kufa da addu ah Allah ya warware matsalar don naga akwai abunda yake matukar cimata rai, haka zalika in ta tuna da butulcin da imam yamata zatayita kuka sosai safiyya takoma se a hankali,
Gabda meenal zata tafi bauchi hutu, ina dubai a lokacin muna kwance da safiyya cikin baccin ta naji tana ambaton sunan 'yar uwarta, tundaga wan nan rana nafara tunanin to itama safiyya 'yan biyune kenan? inata wasi wasi har Allah yazo ya baiyana gaskiya gameda family dinta"
Seda yasauke doguwan ajiyan zuciya ya kalli meenal yace.
" Kiyi hakuri meenal mahaifiyar ki tana kaunar ki kawai dai kaddara ce tasa tanisan ceki kullum dake take kwana take tashi cikin zuciyan ta babu ranar dazata zo tawuce bata ambace kiba,kiyi hakuri kinjee tabbas kema kinga rayuwa meenal sedai mugodewa ubangiji daya kawo mana karshen komai, gaki ga mahaifi yar ki gakuma dangin mahaifiyar ki kisa aranki kuma har abada ni baban kine"
Rarrafawa meenal tayi taje ta kankame safiyya tana kuka me tsuma zuciya, to itama cikin zubar hawaye takara rungume diyar tata taname jin sanyi azuciyan ta koba komai burinta yacika tadawo tasami diyarta cikin koshin lpy
Ummi kuka take itama tana juya kai tana me jin takaicin yadda aka nakasta mata rayuwar 'yar uwarta,shikuwa muhammad kamewa yayi azaune hawaye taf acikin idanun sa haka mujaheed, sam muhammad betaba tsamma nin auntie zata iya aikata wan nan ta asarba,
Hannu biyu nana tadora akanta cikin kuka tace. " Nashiga uku! Auntie bantaba tunanin cewar halinki harya kai hakaba,sam banyi dacen mahaifiya bah bakiyi wa kanki adalci bah"
To su mummy madai suna gefe inbanda matsar kwalla babu abinda sukeyi sunyi sallallamin harsun gajee, mimi ma gurin ummin tasu taje tarungume ta tana wani marayan kuka sosai dakin ya kaure da koke koke, seda daddy yamusu magana tukunna sukayi shiru, wasu keys ne daddy ya ciro a aljihunsa dayawa kowa yasoma binsa da idanu,guda daya ya wara yakalli muhammad yakirashi yataso jiki a sanyaye ya zauna a gaban mahaifin nashi.
" muhammad wadan nan mukullan gidan kane halak malak nasiya maka shi domin kazauna da matarka cikin kwanciyar hankali babu abinda zaku bukata a gidan komai ansaka muku nabukatar rayuwa sannan lefen meenal ma yana cikin gidan naku wan nan aikin auntie safiyyan kane itace tahadawa matarka lefe sekayi godiya ga ubangiji ba ah garemu bah"
Bayan ya dankawa muhammad keys dinsa mujaheed ya kira shima yazo yazauna gefen muhammad,daddy wasu keys din yabashi yace.
" Kasan cewar aurenka yazo kaitsaye yasa nagyara maka part dina nagidan ku zaka zauna a ciki kaida amaryar ka kafin a kammala naka ginin gidan babu abinda zaku bukata agidan nida iyayenka mun gama muku komai itama lefenta yana can amarya kawai yake jira"
Sosai mujaheed yake zubawa daddy godiya, ragowan keys din daddy yadaga yace "wan nan kuma makullan gidan safiyya ne dazata tare gobe insha Allah kuma acanne za ayi walima ta karshe amika amare dakinsu wan nan gida daga yau yazama mallakin safiyya ita kadai Ga wasu karin shedun ma a rubuce" dakanshi yaje ya danka mata takaddun gidan ta da mukallan sannan yabawa muhammad nashi takaddun gidan daki fah ya kacame kowa jinjinawa daddy yake da godiya a garesa kowa zuciyar sa ta mamaye da farin ciki Da wannan abun al khairi din da yayi....
TAKU A KULLUM NANA BMB
08147110349
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: ❣ RABON KWADO....!!
BOOK 3
NA NANA BMB
GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION
{ Marubuta masu garkuwa da alkalami domin fadakar da al'ummah }
page 43 - 44
WASHE GARI
Alhmdlh jikin safiyya yayi normal ta tashi garau, hankalin daddy yakara kwantawa shiko takan Dr bayabi kogidan yaki komawa sabgarsa kawai yake,
Harseda rana tafito tukunna amarya tasoma motsawa alamun zata tashi, to motsin da takeyi ne yasa muhammad farkawa shima, ahankali ta bude idanunta tasaukesu kan faffadan kirjinsa, hakanne yasata fiddo idanuwa waje tana kokarin mikewa sedai tsam hannuwan sa suna ta bayanta bahalin mikewa, koda yabude idonsa ya kalleta ganin abinda take shirin yi, idonsa ne yakai kan time yaga 8 ma ta gota zaro idanu yay yamikar da ita, ganin babu sutura ajikin tane yasata sakin kara tai kasa tana kare kirjinta, haushi hakan yabawa muhammad kawai ya harare ta yashige bathroom yana cije baki sauri sauri yayo alwala yazo ya tada sallah ita kuwa tana zaune gefen bed din ta nade jikinta da blanket koda ya idar yajuyo yana kallonta diriri cewa tayi saboda tayi tunanin zece ta tashi tayi sallah ne, murmushi yayi yace." Ay nasan bakyayi kwantar da hankalinki bacewa zanyi jeki sallah bah " meenal koda tajee haka wata irin kunyace takara lullubeta hakan ya sa ta shigar da kanta cikin bargon, sam batayi tsammani ba taji ya jaye bargon gaba daya daga jikin ta bayan ya zare jallabiyyan dayasa, takuwa rintse idanun ta ta cukurkude guri daya sunkuyowa yayi yana kare mata kallo yace." Sweety banace kidena jin kunyata bah, banason hakan" sam kasa tanka masa tayi ko idon nata takasa budewa.
" ' Hmmmm! bazaki dena bah kenan, to bari kigani"
Ay kafin ta bude baki tayi magana ta sureta ya azata a gado, cikin kwalalo idanu tabudi baki zata kumayin magana ya cafke lips din nata da nashi, sotake kawai takwaci bakinta takasa hakanne ma yasashi zura hannu ya balle bra din tata sakin bakin dayayi ne tasoma maida numfashi cikin sauri murya na rawa tasoma cewa." pls ya muhammad" magiyan ne bayason jima yasa hannunsa kan bakin nata ko ina najikinta yake kai bakinsa mussam man breast dinta daya kusa zautashi,
Sam besan iya adadin lokacin daya daukaba yana sarrafata son ranshi, tukunna ya barta yamike yashiga bathroom abinsa donyin wanka, ita kuwa luff tayi taname zubar hawaye don haryanzu takasa yadda ya muhammad din tane yake mata haka, yajuma a bathroom din tukunna yafito daure da dan guntun towel yazo har inda take cak ya dauketa izuwa bathroom din ya ajeta yana murmushi ganin takama idanu ta makale yace." To sarkin kunya ayi wanka a fito koh"
Juyawa yayi yarufe mata kofar yasoma shiryawa harya gama shirinsa yafita takasa fitowa yana sane da ita yafice kawai abinsa, tanadena jin mitsinsa kuwa tafito cikin sanda tana leke don batajin zata iya hada ido da ya muhammad din nata yanzu,shikuwa koda yashiga gidan nasu yata rar 'yan tafiya anata shiri, bakaramin farin ciki yayiba ganin auntie safiyya anata hada hada da ita, hasana ya tambaya ina hasan da usain ne? take shaida masa ai nasuma tashiba, Da mamaki ya jinjina kai yace." Lallai ne yaranne dole"
Yajima yana knocking kafin su bude masa kofan, yana zura kai yaga usain a tsaye daganin shi yanzu yatashi, haba ya rike yace." dakyau 'yan hutu ayse a tashi haka koh, anata shiri ku kuma kuna nan kun jibge"