Showing 3001 words to 6000 words out of 20000 words

Chapter 2 - MACE GUDA DAYA TILO HAUSA NOVELS BY SAKINAT.txt

nufi makarantar zuciyarta cike da fatan dama
taga wannan matashin saurayin.
[3/22, 4:24 PM] Ummi A'isha: MACE GUDA
DAYA TILO...
1⃣8⃣
Na
UMMI A'ISHA
Da wannan tunanin ta isa cikin makaranta kowa
mamakin canjawarta yake tun ranar da abin
yafaru bata kara yiwa kowa maganar bacin rai
ba sannan yanzu ta daina makara da wuri take
zuwa school sabanin da dasai lokacin data
gadama kuma babu wanda ya isa ya hanata
shiga lecture, ahankali tashiga hall din ta zauna
ziciyarta cike da dana sanin fadawa director
datayi har aka kori wannan dan bautar kasar da
haka tagama sauraron lectures din ta tashi ta
tafi gida. Shi kuwa lamin tuni yafara zuwa
lecturing a kano B. U. K wani dan madaidaicin
gida ya kama a unguwar jan bulo kabuga tuni
budurwarsa Vicky ta yi masauki agidan tana
tafiya Mary tazo, haka ya rinka sheke ayarsa
batare da iyayensa sun sani ba dama ko lokacin
da yake Malaysia haka haka yake ajiyesu
agidansa daga wannan ta tafi wannan zatazo.
Yan matan jami'a kuwa ba acewa komai domin
ganinshi kyakkyawa mai class kuma ga kudi nan
da nan suka Fara cusa kansu wurinsa sai dai
har yanzu babu wadda ta samu shiga domin shi
baya harka da hausawa duk yan matansa
Christian ne babu musulma ko daya kuma
bashida standard budurwa domin bai shirya aure
yanzu ba sai auren ramuwar gayya.
[3/22, 4:25 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA
DAYA TILO...
1⃣9⃣
Na
UMMI A'ISHA
Yau tunda yagama lecture yakoma gida yafara
hada kayansa ya gama Mary dake kwance tana
bacci yafara tashi dakyar ta tashi tana faman
murtsuke ido tana tambayarsa har yadawo eh
ya amsa mata sannan yace kitashi ki shirya
kitafi sai next week zan dawo kinga yanzu ni
nagama shiryawa kamar mai shirin yin kuka tace
to sai munyi waya tashi yayi yadau jakarsa
yatafi tareda bar mata sallahun idan tagama ta
rufe gidan. Karfe 2 na rana ya isa gida mummy
yatarar zaune afalo yan biyunta sun zagayeta
sai surutu suke mata ganinsa da sukayi yasa
suka dan nutsu suna fadin oyoyo yaya harara
yabisu da ita yace kunzo kun wani zagayeta
kamar wasu kananan yara, ke hasna kin share
min dakin dana saki? Dasauri tace yaya bani
bace sai dai ko husna cikin sauri itama tace wlh
bani bace banza yayi dasu domin dama haka
suke masa irin wannan rainin hankalin idan yasa
daya aiki to idan batayi ba sun rika cewa wance
ce itama dayar tace ba ita bace ,mummy ya
kalla yace mummy ina wuni cikin fara'a tace lfy
babana kallonta ya sakeyi yace yakukayi da
dady akan maganar nan? Dariya tayi tace kaifa
kafiya zumudi ai mun gama maganar dashi
ashema yar gidan Alh mukhtar magashi ce? Ai
tuni dadynku yayi masa magana kuma yace bai
mata miji ba dan haka yabaka ita yanzu saura
aje ayanke rana, farin ciki ne ya cikashi ya mike
ya nufi side dinshi.
[3/22, 4:27 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA
DAYA TILO..
2⃣0⃣
Na
UMMI A'ISHA
Zuciyarsa fes ya shiga dakinsa yasamu wuri
ya zauna yana tunanin ta inda zai bullowa
wannan yarinyar junada. Mukhtar wani
malalacin murmushi yayi dalilin samo abinda
zaiyi mata cikin haka yaji phone dinshi tana kara
ahankali ya cirota daga cikin wandon jeans din
dake jikinsa Angelina yagani a rubuce tsaki yayi
ya ajiye wayar batare da ya daga ba daga
karshema da yaga tana neman damunshi sai ya
kashe wayar gaba daya. Ita kuwa junada kullum
da tunanin lamin take kwana take tashi kafin ta
ankara sonsa yagama cika zuciyarta, yau kamar
kullum ta dawo daga school ta kwanta tayi
bacci ta huta sannan tayi wanka ta fita zuwa
falo amma bataga mahaifiyarta ba dan haka ta
wuce dakinta adakin ta sameta tana zaune
bakin gado tana waya kusada ita taje ta zauna
tana sauraronta har tagama, gamawarta keda
wuya ta juyo gareta tana cewa junada har kin
tashi daga barcin? Dazu nashiga dakin naki
naga kina bacci dama mahaifinki ne yabani sako
nasanar dake yabada ke ga dan abokinsa ras
junada taji gabanta yafadi kallon mahaifiyar tata
tayi sannan tace a ina yake? Murmushi uwar
tayi sannan tace dan gidan Alh kabir sulaiman
yola ne mahaifinshi shine SSG na Adamawa
state kuma yanada sarauta makaman Adamawa
Turakin yola gashi kuma classmate din
mahaifinki ne domin tare sukayi makaranta
kedai kawai abinda nake so dake shine kiyi
kokari kiyi biyayya insha Allahu zakiji dadi agaba
don kin san mahaifinki bazai taba zaba miki
mijin da ba nagari ba ita dai junada shiru tayi
batace komai ba domin hankalinta yagama tashi
amma duk da haka ta kuduri niyyar yiwa
mahaifinta biyayya ahankali tace to umma naji
abinda kikace Allah ya zaba min mafi alkhairi
cikin jin dadi mahaiyarta tace amin Allah yayi
miki albarka.
[3/22, 7:56 PM] Ummi A'isha: [3/22, 4:37 PM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...
2⃣1⃣
Na
UMMI A'ISHA
Tuni mahaifin lamin ya shirya shida yan
tawagarsa yaje gidan su junada domin nemawa
dansa aurenta batareda wani bata lokaciba
mahaifinta ya amince tareda sanya ranar auren
dai dai da ranar da za ayi na yayansa
Abdulrahman sun rabu cike da farin ciki da
girmama juna, ita dai junada bata cewa domin
dama bata damu da tasan ko waye angon ba
saboda tasan ba zabinta bane zabin iyaye ne
(sunan wani littafi na hafsata bounzer) dan haka
kawai hidimar gabanta takeyi. Abangaren lamin
kuwa yafi kowa murna da sanya wannan rana,
tuni ya koma kano yaje ya dora daga inda ya
tsaya wannan karon Angelina da blessing ne
suka je gidan nasa amma kullum cikin fada suke
da zarar ya fita zasu fara dambe ganin haka
yasa ya tattarasu yakora yayiwa Mary waya
yace tazo.
[3/22, 4:39 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA
DAYA TILO...
2⃣2⃣
Na
UMMI A'ISHA
Biki ya rage saura sati 2 lamin ya shirya
shida yayansa sukaje bauchi domin gaisheda
iyayen junada ita kuwa lokacin bama ta kasar
sun tafi sudan itada kanwar mahaifiyarta mami
inda za ayi mata gyaran jiki da sauran abubuwa
na amare kuma bazasu dawo ba sai ana saura 3
days biki,cike da girmamawa da mutuntawa su
lamin suka gaisa da kowa lfy sannan suka koma
yola inda acanma shirye shiryen bikin ake tayi
dan har an harhada lefe aranar aka kai na matar
abdulrahman mai suna kausar yar gidan sarkin
yola ce yayinda na junada akace sai washe gari.
Hakan kuwa akayi washe gari yan kaiwa kaya
suka nufi bauchi kayane na kece raini akwati 24
set daya brown daya set din kuma pink colour
yan uwan junada sunyi mutukar murna hakan
nema yasa suka bada tukwici na naira dubu dari
biyu. Tunda biki ya rage saura kwana 8 gidansu
lamin suka fara shirye shiryen komawa sabon
gida domin acanne za a gudanar da bikin, wani
tangamemen gida state government ta ginawa
mahaifinsu akusada government house gidan
unguwa gudane domin part guda 5 ne acikin
gidan dan haka ananma su lamin din zasu
zauna.
[3/22, 4:40 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA
DAYA TILO..
2⃣3⃣
Na
UMMI A'ISHA
Ana saura kwana 3 biki su junada suka dawo
daga Sudan tasha gyara tayi tsananin kyau sai
sheki da kyalli take tamkar wata tauraruwa,
gaba daya ta yi wata kala ga uwar rama datayi
saboda bata iya cin abinci. Shi kuwa lamin
baima yi gayya ba domin acewarsa wannan ba
biki zaiyi ba zaiyi bikinsa sai nan gaba yanzu
bai isa aureba, ana igobe za afara shagalin biki
suka koma sabon gidansu anan aka fara
gudanar da biki washe gari akaje aka daura
auren Abdulrahman da Kausar sannan aka wuce
garin bauchi inda jama'a sukayi dafifi domin
jiran daurin auren, ango yayi kyau cikin wata
shudiyar shadda wadda tasha dinki mai tsadar
gaske 12 dai dai aka daura auren junada
mukhtar da angonta Lamin Kabir sulaiman akan
sadaki dubu dari, ana daura auren lamin yayi
tafiyarsa batare da ya nemi ganin amaryar ba.
Ita kuwa dama ko sha'awar ganin fuskarsa
batayi domin batasan waye ba kuma bata son
tasanshi haka aka wuni ana kade kade da raye
raye gamida bushe bushe yamma tanayi aka
dauki amarya sai garin yola inda aka kaita
dakinta.
[3/22, 4:42 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA
DAYA TILO..
2⃣4⃣
Na
UMMI A'ISHA
Wurin iyayen mijinta aka fara kaita sannan
aka nufi sashenta da ita. Bayan kowa ya tafi ne
husna da hasna suka shigo dakin nata idonta
jajur kamar barkono tafara kallonsu dam taji
gabanta yafadi domin sunyi mutukar yi mata
kama da wannan copper din zama sukayi akusa
da ita suka fara zuba mata surutu kallo ita dai
take binsu dashi acikin ranta tana fadin waw
identical twins dan hatta muryarsu iri dayace
komai nasu iri daya babu ta inda suka banbanta,
basu suka bar side dinta ba sai 10 nadare ita
kuwa zaune tayi tana ta faman kuka shiru shiru
babu ango babu dalilinsa har bacci ya dauketa.
Karfe 6 ta tashi tashiga tayi wanka ta shirya
cikin wata atamfa super purple colour dinkin
bubu yayi mutukar amsarta, window din dakinta
ta leka girman fadin tsakar gidan ne yaso
tsoratata don babbane sosai part biyar tagani
duk iri daya daga can gaba katon filin wasa ne
an sassaka kayan motsa jiki ga wurin basketball
da volleyball nan daga gaba kuma wurin table
tannins ne komai dai na wasa an tanada awurin
window din tasaki takoma na daya bangaren ta
daga wani katon swimming poll ta hango gaba
dashi kuma garden ne kawatacce.
[3/22, 4:44 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA
DAYA TILO
2⃣5⃣
Na
UMMI A'ISHA
Dakin nata tabi da kallo yasha furnitures
masu tsada komai red da ratsin baki fitowa
daga cikin dakin tayi wani dakin tagani yana
kallon nata tsakiyarsu kuma dan karamin falo ne
shima tunda ga kujerun zuwa labulayen duk red
and black ne ga madaidaiciyar plasma tv manne
ajikin bango, dakin dayake kallon nata ta bude
tashiga shima babu laifi ya kawatu mutuka da
kaya irin na zamani komai naciki red colour ne
da toilet aciki fitowa daga ciki tayi ta murda
kofar falon wani tangamemen falo tagani wanda
ya sha luntsuma luntsuman kujeru har kala biyu
daya ash colour dayan kuma pink colour ne dan
haka labulayen ma sai suka kasance pink da
ash colour ga wata jibgegiyar plasma manne
abangon falon daga gaba kadan dining area ne
taciki ga kitchen nan da store agefe, gefenta ta
kalla shima dai wata kofar ce da alama shima
irin dakunanta ne da dan falo aciki ma'ana dai
sun saka tangamemen falon a tsakiya sukuma
suna facing din juna dan haka shima ji tayi tana
sha'awar ganin yanda aka tsarashi da karfin
gwiwarta ta murda kofar tashiga dan karamin
falo ne kamar nata da kujeru light green kanta
ta daga tafara bin hotunan dake manne ajikin
bangon falon da kallo cak! Taji numfashinta ya
tsaya sakamakon ganinsa da tayi ajikin
tangamemen hoton yana sanye da bakar riga ya
gyara sumarsa yana murmushi.
[3/23, 9:51 AM] Ummi A'isha🏻: [3/23, 9:21 AM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO
2⃣6⃣
Na
UMMI A'ISHA
Idanuwansa manya farare tatas kamar an
diga zaiba aciki babu abinda yafi burgeta irin
jajayen lips dinsa yayi bala'in yimata kyau sosai
dadine ya kamata azuciyarta tafara fadin ya
Allah kasa ba gizo wannan bawan naka yake
min ba Allah kasa dagaske shine abokin
rayuwata na har abada,sallamar da ta jiyo a
babban falone yasata saurin fita daga cikin falon
nasa hasna da husna tagani dauke da kayan
breakfast sunsha ado sosai dasauri ta taresu
tana fara'a a'a yan biyune sukazo sannunku da
zuwa hasna ce tace sannu matar yaya ranta fari
tas tazauna dasu suka fara hira har azahar tayi
sannan suka bar side din nata suka koma nasu
shiru shiru bata ga ango ba da haka har akayi
kwana 5 da bikinsu sai dai kullum su hasna
nazuwa su tayata hira wuni sukeyi awurinta
wani lokacinma har dare suke kaiwa, yau tunda
safe tafito babban falon ta zauna sallamar wata
yar kyakkyawar mace taji ta amsa mata tashigo
ciki bayan sun gaisa tace mata Kausar ce matar
Abdul brother din lamin murmushi tayi tace
sannu da zuwa yau kin fito kenan itama
murmushin tayi tace eh yanzuma sallama nazo
miki zamu tafi Uganda ne nida shi shiyasa nace
baxan tafiba sai nashigo munga juna mikewa
tayi tace yana waje yana jirana dan har mun fito
itama mikewar tayi tabi bayanta tana cewa Allah
ya saukeku lfy.
MACE GUDA DAYA👆TILO
2⃣7⃣
Na
UMMI A'ISHA
Suna fita tsakar gida ta hangoshi gabanta
yayi mummunar faduwa ahaka suka karasa inda
suke tsaye suna jiransu sai da sukaje daf dasu
sannan taga ashe ba mijinta bane sai dai suna
mutukar kama sosai amma mijinta yafishi kyau
nesa ba kusa ba kuma yafishi fari russunawa
tayi ta gaida shi cikin sakin fuska ya amsa su
husna ne suka runtumo suka zo suka rungumeta
suna dariya itama dariyar tafara yi musu
sallama sukayi dasu Kausar suka tafi ita kuma
su hasna tabi side din mummy yaune karo na
farko da ta fito tun zuwanta gidan side din
mummy irin nata ne sak,adaki ta taradda ita ta
sunkuya har kasa ta gaida ta amsa cikin kulawa
sannan tace ai mijin naki yace gobe zai dawo
daga kanon ko? Dam tayi sannan tace ehh dan
bata son mummy ta fahinci har yau bata ganshi
ba mummyn ce taci gaba da cewa jiya nake
cewa aturo miki masu aiki guda uku da mai
shara da wanke wanke da mai girki sai mai
wanki shine lamin yace ai kince baki bukata zaki
nayi duk da kanki kuma bakida ra'ayinsu
shiyasa ma bakiyi magana ba kanta ta daga
tace eh ninace kar akawo itadai mummy
mamakine ya cikata saboda daga ganin wannan
yarinyar kasan yar hutuce babu wahala atare da
ita amma tunda ita tace bata ra'ayi shikenan
mikewa tayi ta shiga dakin su husna nanfa suka
fara hira babu laifi ta saba dasu dan haka ta
sake dasu sosai fiyeda mummy domin tana dan
jin nauyinta anan ta wuni har yamma sai da
la'asar lis sannan suka dunguma suka koma
bangarenta sai wurin goma sukayi mata sallama
suka tafi.
MACE GUDA DAYA TILO
2⃣8⃣
Na
UMMI A'ISHA
Yau a lissafinta kwanasu 10 da aure amma
bata taba dora idonta akan mijinta ba kullum ita
take yin aikinta shara wanke wanke girkine ake
kawo mata daga wurin mummy kullum acan
take wuni sai dare take dawowa side dinta.
Wanka tayi taci kwalliya cikin wani material ja
tafito da niyyar taje wurin mummy tana fitowa
ta hango wata sabuwar mota blue kirar
Mercedes 2015 new model tana shigowa tana
karasowa ciki akaje akayi packing dinta a
garage ya bude ya fito yana sanye cikin bakar
riga an zana stars guda uku ajiki an rubuta just
bring it ajiki yasa bakin wando yayi mutukar
kyau fuska adaure ya karaso inda take yace ina
zaki? Wata irin faduwa taji gabanta yayi yayin
da zuciyarta ke dukan uku uku ba kakkautawa
wurin mummy zani to muje ciki ina son magana
dake yafada yana ta faman huci sim sim ta
wuce yana biye da ita har cikin babban falon
kujera ya samu ya zauna yayinda ita kuma ta
zauna can nesa dashi kallo yabita dashi sannan
yace ke! Karkiyi tunanin ko na aureki ne dan kin
burgeni ko dan ina sonki no na aureki ne domin
na wulakanta ki na nuna miki ke ba kowa bace
face baiwa dan awurina baki da maraba da
kuyanga zan maida ke tamkar baiwa wadda
zata zama abin kwatance agari nine nan na
hana mummy ta kawo miki yan aiki saboda
wannan yana daya daga cikin horon da zanyi
miki acikin gidan nan saina gama azabtar dake
sannan zanyi miki saki uku kwarara yanda zaki
dade kina jin bakin ciki arayuwarki, daga yau
kece zaki nayin duk wani aiki nawa kama daga
abinci wankin kayana gyaran dakina da sauran
ayyuka kuma wlh koda wasa kika fadawa
mummy saina raunata ki banza kawai ki kalleni
da kyau ni ba class dinki bane wlh level dina ya
wuce naki.
[3/23, 9:25 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA
DAYA TILO
2⃣9⃣
Na
UMMI A'ISHA
Tunda yafara bayaninsa binsa kawai take da
ido batare da tayi koda motsi ba har ya diga aya
wani mugun kallo ya watsa mata yace kalleta
kamar mutuniyar kirki mai kamada aljana kawai
sannan magana ta karshe duk abinda kika gani
adakina kar ki kuskura ki taba mun ki bar min a
mazauninsa idan kuma ba hakaba zaki yabawa
aya zakinta dan sai jikinki ya gaya miki wlh
yana kaiwa nan ya mike ya shige dakinsa ita
kuwa ta kasa koda motsi dan fargabar irin
zaman da zatayi dashi sai dai ita kuma har
acikin ranta taji tana tsananin sonsa sannan
kuma yana burgeta tun ranar farko data fara
ganinsa ta dade azaune sannan ta tashi ta shiga
kitchen ta dora abinci akaro na farko tun
zuwanta gidan domin kullum mummy ce take
bayarwa ake kawo mata shinkafa da miya ta
dafa sa'arta daya ta iya girki domin ko agida
wani lokacin itace take yiwa abbansu girki
musamman ma idan zaiyi baki na kunya haka ta
shirya abincinta mai rai da lafiya taje ta jera
akan dining sannan ta wuce dakinta har yanzu
bata jin zafin sa sai dai abu dayane ya tsaya
mata arai auren ramuwar gayyar da yayi da ita
shine har yanzu yake damunta tana daga cikin
dakinta ta jiyoshi yana waya amma ba zata
tantance da mace yakeyi ko da namiji ba abincin
ya danci kadan sannan ya wuce side din
mummy tundaga babban falo ya fara jiyo
muryarsu husna suna cewa wlh mummy yaya
lamin yafi yaya Abdul iya zabe matarsa tafi Anty
Kausar kyau daya daga cikinsu yaji tana cewa to
danma ba kiga gashinta ba ni jiya dana shiga
dakinta lokacin ta fito daga wanka tsorata nayi
gashinta fa har kugunta yanda kika san yar
India murmushi momyn tayi tace ai dama daga
ganinta zatayi gashi dai dai lokacin ya shiga
cikin falon mummy suna ganinsa sukayi tsit sim
sim suka fara kokarin fita suna cewa sannu da
zuwa yaya lamin side din junada suka nufa suna
fadin umm su anty junada yau honey ya dawo.
MACE GUDA DAYA TILO
3⃣0⃣
Na
UMMI A'ISHA
Suna shiga suka sameta zaune acikin falonta
tana kallon wani Nigerian film a tashar
Nollywood zama sukayi suka fara tsokanarta
yau anty junada ko nemanmu ba kyayi saboda
yaya yadawo ko? Murmushi tayi tace ku kuka
sani dai hasna ce tace wai anty junada ke yaya
yana yimiki dariya husna ce tayi tsagal tace ba
dolensa ba ita dai bata tanka musu ba haka
suka karaci surutunsu nan suka zauna har
magriba sai da sukaji shigowarsa sannan suka
bar bangaren nata suka nufi nasu. Haka
zamansu ya kasance Ita dashi kullum tana shiga
tana gyara masa daki yauma kamar kullum tana
jin fitarsa ta nufi dakinsa tashiga da toilet tafara
sai da wankeshi tas sannan ta dawo cikin dakin
tafara gyarawa ta shareshi tas ta goge tile din
ta fito da kananan kayansa ta wankesu sannan
ta fesa air freshener adakin drawer mudubinsa
ta jawo tana shirya masa wasu takardu da
tagani ya barbaza akan gado da alama test
yayiwa dalibansa shine da yagama marking ya
bazasu anan yatashi ya barsu awurin tana gama
shiryasu kamar ance buda ta kasan ta jawo ta
bude me zata gani wani kwali tagani yanata
kyalli ta dauko tana budawa taga sun zubo tana
duba jikin kwalin taga an rubuta condom
gabanta ne yafara faduwa dasauri ta mayar
masa inda yake ta ajiye ta rufe drawer ta koma
dakinta innalillahi kawai take fada ba dai lamin
neman mata yake yi ba? Tambayar da take ta
yiwa kanta kenan innalillahi wa inna ilaihi raji'un
zina? Kukane ya subuce mata nan ta zauna ta
sha kukanta ta more wani kishine ya turnuke ta
ganin kukan bashine mafita ba yasa ta tashi
tashiga bathroom ta wanke fuskarta ta fito ta
tsaya agaban mudubi ta gyara fuskarta fes ta
fito ta nufi side din mummy tana shiga ta hango
shi a babban falon yana kishingide yana karanta
jarida ta gabanshi tabi ta wuce tashiga falon
mummy ta samesu zaune ita dasu hasna suna
ganinta suka fara murna oyoyo antynmu yanzu
muke cewa bari mu tashi muzo tunda ke baki
shigo ba har yanzu.
[3/23, 9:51 AM] Ummi A'isha🏻: [3/23, 9:29 AM]
Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO
3⃣1⃣
Na
UMMI A'ISHA
Murmushi tayi sannan tace ku dai kuyi shiru
kawai tunda gashi na zo shikenan ta durkusa
tana gaida mummy sannan suka dunguma zuwa
dakinsu su husna anan suka zauna suka fara
hira sai da rana tayi sannan tafito mummy ta
hango tana kokarin shiga kitchen ta dora girki da
sauri ta bita tace mummy me za adora? Cike da
jin dadi tace jalop rice zan dafa to mummy
barshi zan dafa cikin jin dadi mummyn tace to
Allah yayi miki albarka ta juya ta fita daga cikin
kitchen din cike da jin dadin yadda junada take
darajata kuma take mutunta ta a falo ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login