Showing 15001 words to 18000 words out of 46188 words

Chapter 6 - ZURFIN CIKI book 2 Complete by halima Abdullahi K Mashi .pdf

abnci tayi. Da suka
zauna da Umma a daran ta ce Umma baki fada
ma Alhj bani da tsayayyen saurayi ba?Umma ta
kalleta,ba shi yasa na ce Kitsada ba,amma ba kya
son fita. Duk kin bi kin kori masu sonki Abba na
daure miki gindi,kin san dai Alhj ba yarda zai yi ki
wani ci gaba ba,gara ma kin yi kokarin fidda miji
kafin lkcn da ya dibar miki,in ki ba haka ba ya
daki da mai rabo. Ummi tasa kuka ranar,kwana
tayi tunani hr ta yanke shawarar zata fada ma
Alhj Ya Abba take so. Da safen taje hr dakin Alhjn
ta gaishe shi,ya ce uwata naga kamar bakinki da
magana ko?Ta dube shi "Eh,a'a ba komai.Ta
mike,dakin Tsohuwa ta shiga ta haye gado ta
soma kuka. Tsohuwa ta dubeta a rude,Takwara
ke da waye,? Nasan ba zai wuce me sunan
Malam ba,dn shi ne kadai ke hana ki sukuni. A
ran Ummi ta ce,shi ne kam,amma ba irin wanda
ki ka sani ba. Amma a fili sai ta ce,Tsohuwa Alhj
ne wai in fito da miji,kuma abn da ke damuna ni
ba wanda na ke so. Tsohuwa ta ce, "Au, shi ne
abn kuka?To bari kiji bana ba zan goyi bayabki
ba,dn da ubanki ya ji ta tawa da yanzyn kina da
diya 2 in da rabo. Amma mai sunan Malam ya ce
za ki ci gaba da krt,yamzun ko tun da Allah ya
kawu mu angama wannan kaddararriyar mkrnt ba
sai aure ba? Ga Bunta nan hr an yi baiko, to rana
guda za a yi shi in muna cikin masu rai. FUU
Ummi ta fice,ta shiga dakin Umma tana tunanin
wa zata fada ma matsalarta?kamar an tsikareta
ta dauki mayafi zata fice. Umma ta ce, "Zo nan,
ina za ki? ta ce "Wurin Fati. Tana shiga Bashir
zai fito . Ya ce Yauwa Ummi ina son magana da
ke. Ta dawo baya ya fita kofar gida ita ma ta
fito,suka tsaya ya ce "Ummi gaskiya dama ba
wani abu ba ne, ni dai na tsinci kaina da sonki.
Ummi ta dafe kirji da sauri."Sona?" ya ce kwarai
kuwa, dn haka za ya ki ka gani?ta dube shi,sam
babu wata alama da ke nuna cewa dan uwan Ya
Abba ne. Ta girgiza kai "kayi hakuri kawai Ya
Bashir,wlhy zuciyata ta jima da kamuwa da son
waninka." ya ce, Me ki ke nufi?Kin fi son bare da

ni jininku? Ummi ta ce,"Ni dai na fada maka." Ya
ce, "To kin fada min,ni kuma zan fada wa su
Alhj." Gabanta ya fadi. Shi kuma ya yi tafiyarsa, .
Sabon tashin hankali kenan. Sai damuwa ta
lunku,bata ta6a marmarin zamn mkrntr kwana ba
sai ranar. Ta rasa me zata yi taji dadi,gida ta
koma cike da nadamar fitowa,ta zauna a falon
Umma ta soma kuka. Umman tana dakin mijinta
ya yi karin kummali. Sai da ya fita sannan Umma
ta maido hankalnta ga lamuran gidan, kan kujera
ta samu Ummi ta nata rera kuka. Umma ta ce
"Ke Ummi lafiyanki? Abun ya soma zama iya
shege,daga cewa ki fito da miji sai ki tsira kuka?
To ina ganin kwadantaki zamu yi muci. Ummi ta
ce, "Ni fa ba kukan da nike yi ba kenan,ni fa Ya
Bashir ne fa. Umma ta ce Bashir me,? kiranki aka
yi? Gara daya da ke ki. ta ce ba fa dukana ya yi
ba wai cewa yai wai fa yana sona. Tab,Allah ya
tsare ni. Umma dn Allah bana sonshi,gaban
Umma jikinta a mace ta ce "Tabdi,ai ko in Alhj ya
ji wannan zancan ta zauna. Ummi ta sake
firgicewa, cikin kuka ta ce Da na shiga 3 Umma,
ya ya zan yi ne don Allah?Umma ta ce,"Mafita
daya ce ki fidda wani kafin zancan yaje wurin
Alhj. Yinin ranar Ummi ta rasa mafita Addu'arta
daya,Allah ya turo mata ko ma waye a daran yau
ta ce ya turo iyayenshi. Wayar Umma tana
hannunta,ta rubuta text ta goge yafi sau 20 da
niyyar ta tura ma Ya Abba cewa tana
sonshi,amma da ta tuno da irin dukan da zai zo
gidan ya yi mata in ya karanta sai ta share. Ita
dai ta san shi kadai take so. Tayi Sallar Istihara
kusan sau 3,amma hr yau zcyrta na nan makale
da son Ya Abba. Don bayan Isha'i kuwa a ka aiki
kiranta, ai tare da dan aike suka fita. Wani
saurayi ne wai shi Sahabi,dan unguwar ne Kuma
sana'ar aca6a yake yi. Na dai manta. Suka gaisa
ya gabatar da kanshi sannan ya fada mata dalilin
zuwanshi ba tare da wani nazari ba,ta ce ta
amnice. suka yi sallama ta dawo gida,umma ta
tambaye ta wanene?Ta fada mata,sai dai Umma
bata gane shi ba. Can jimawa Bashir ya aiko
Kamal kaninsa wai Ummi tazo,ta ce kaje ka ce

masa ba zan zo ba,ya sake aiko shi cewa in bata
zo ba shi zai shigo. Umma ta ce mata tashi kije.
Ummi hr d kuka ta fita,dn a rayuwarta ta tsani
Bashir,sbd yanda ya raina Umma. Kuma ba ya
ganin kowa da gashi sannan tana ganin in hr ta
auri Bashir zai mata tsakani da auren Abba. Tana
zuwa ta same shi zaune a dakalin kaofar gida,ta
isa gurishin. Ya Bashir kiran me ka ke min? Ya
ce,kin sani kema. Ta ce Ya Bashir dn girmn Allah
ka bar ni ba,Usaina gidan kurma ce buduwarka
ba? Ya ce Da ba, ya ci gaba da cewa,Ummi ina
sonki so na hakika nayi mamakin yadda lkc daya
zcyta ta kamu da sonki,to wai dn Allah ni me
yasa ba ki sona? ta ce Ya Bashir ina da wanda
nake so tun farko..........kamar daga sama suka ji
muryar Abba yana cewa,Kai Bashir me ka ke
fada? ya ce sonta nake. Abba sai da wayarshi da
ke hannunshi ta kwace ta fadi don figici,bai bi
takan wayar ba ya isa gabn Bashir ya ce, In ka
kuma furta kalmar so ga Ummi sai na maka
matsiyacin duka,ke kuma hr da fitowa kin zo tadi
ko? kafin tayi magana ya ce,Bace min daga nan.
Bashir ya ce,Amma ai ba laifi ba ne don nace ina
sonta? Abba ya bige mishi baki tare da cewa In ji
wa ya ce maka ba laifi ba ne?Bashir ya ce,An
haramta aure tsakaninmu ne? Abba ya cakumo
wuyan rigarsa Ni ne nan na haramta haka,kuma
kar in kara jin wannan mgnr. Bashir ya fige ya
nufi gida yana fadin cewa Yau zan samu Alhj da
mgnr. Ina ruwanaka da zaka ce ka haramta min
sonta? . Abba jikinshi hr 6ari yake dn tashin
hankali, yasan in mgnr taje teburin Alhj to ta kullu
yanda yake mishi mgnr hada auran Ummi da Fat.
Har ya saka kafa a zauran gidan su Umma,sai
kuma ya fasa ya dawo ya nufi gidan su Bashir
din,yana saka kafa a zauren gidn Alhj Krm na
fitowa. Don haka sai yaja baya,Alhj ya fito ya
ce,A'a Abba ne? Abba ya ce "Eh ni ne. Ya gaida
Mahaifin nasa,sannan Alhj ya tambaye shi cewa
Babn naka yana gida? Gaban Abba ya yi
mummunan faduwa,ko dai Bashir ya fada wa
mahaifinsu ne? Alhjn ya ce ko ba ka ji ba?Abba
ya ce "Eh a'a ban riga na shiga gidan ba. Alhjn

ya ce To bari in ganshi. Nan jikin Abba ya jike da
zufa. Da azama ya shiga gidan. Mahaifiyarsu tana
alwala ya ce Umma ina Bashir? ta dube shi
Lafiya ba ko sallama? ya ce Nayi ba ki ji ba ne?
ta amsa sannan ta ce lfy ka ke nemanshi? ya ce
lfy lau. ta ce Yana daki,shima na ganshi ya shigo
a fusace. Abba ya nufi dakin. Bashir na zaune kan
katifar idonshi na kasa yana girgiza kafarshi ta
dama,Abba ya shiga ya ce,Bashir nazo ne in sake
gargadinka a kan Ummi,sai dai naga hr kayi
kuskuren fada ma Alhj krm ko,? Bashir ya mike
ya daga sauti Ban fada mishi ba,amma ina da
niyya. Ina sonta babu wanda kuma ya isa ya
hana ni sonta. Abba ya kashe masa fuska da
mari. Sai suka ji muryar Mahaifiyar tana cewa,
Kara mishi Abba,ka cika dana. Ta shigo dakin hr
gabn Bashir ta ce, Ni za ka tozarta? kayi kuskure.
Ai da in ga ranar aurenka da Ummi gara naga
gawarka kwance yafi min sauki. Abba da Bashir
suka dubeta a rude. Ta ci gaba da cewa Bashir
kai ma kasan ba zai ta6a sa6uwa ba ne in hada
jini da Suwaiba,kafi kowa sanin kin da nike
mata,zan iya daukar ranta ba don tsoron hukuma
ba. Kuma hr dny ta nade ba zan ta6a kaunarta
ba,kai ko fatan alheri ba zan ta6a mata ba. Ta
kalli Abba, Baka ta6a faranta min rai ba irin
yau,dama nasan cewa dole wata rana ka bayyana
dana in dai kai jinina ne,na gode Allah da yasa ka
zama mai kishina Kuma ka wanke dukkan
laifukan da ka min a baya da ka nusar da ni
Bashir na shirin jefa rayuwata a cikin garari,da ba
ka mishi mgn ba yaushe zan san yana shirin jefa
ni cikin bala'i. . Abn da Umma bata sani ba shi
ne,tuni Abba ya yi mutuwar tsaye,hnklshi ya
ninka na Bashir tashi,dn haka Bashir ya riga shi
fita daga dakin. Da kyar Abba ya dago ido ya kalli
Umma,ta ce Daina damun kanka shi ma din ko
ba don Allah ba zai dawo hanya,duku-dukayau
sati guda fa kenan da naje kauye na saida 'yar
Akuyata guda daya sannan na bada kaji 2 ga
Bokan kuka sbd a min akin da Ummi ba zata
samu miji ba. Sai kuma a ce ko satin bai rufe ba
dana na cikina ya zo ya ce yana sonta? Da sauri

Abba ya dafa kirji Umma Boka! Boka ki ka ce
Umma? Inna lillahi wa'inna ilaihin raji'un,Umma
kin san cewa zuwa gurin Boka shirka ne ga
Allah? kin san duk wanda ya mutu a shirka Allah
ya yi alkawarin kona shi a wuta?Umma kina cikin
hadari............ta kaste shi. Kai Abba!Ni ce nake
cikin hadari?Ni ce Allah zai kona a wuta? ya ce,
umma bana nufin haka, ina fada miki ne ki kiyaye
da zuwa gurin Bokaye makaryata,macuta 6arayin
Imanin Jama'a. Na ranste miki da girmn Allah
umma Bokaye 'yan wuta ne,matsawar ba su tuba
ba. Ta ce, Kai ni rufe min baki,da za ka ce karya
ne sau nawa suna min asirn kuma yana ci. Ba
gashi nan da ya min na kada Ummi ta riga Fati
samun miji baga Fatin ta riga samun ba? ummi
kuma ba ta d masoya. Abba ya ce, Umma kin ga
karya ko? wa ya fada miki Ummi bata d masoya?
ta ce, To me yasa ba wanda ya tsaya? Ya ce, Ni
dai Umma ki bar zancan nan a wurina, Bashie zai
bar Ummi ko yana so ko baya so,dn haka na
hada ki d girmn Allah kada ki koma gidan
mishieikin Bokan nan. Ta ce, Ba zan koma ba in
hr zaka raba Bashir da alakakai din yarnyar nan.
Ya ce Na miki Alkawari. ta ce, Shikenan. Ya fice
jiki babu karfi.URFIN CIKI book 2 part 8
ZURFIN CIKI book 2 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:18
Kasa shiga gidan su Umma ya yi,haka nan ya
manta sam da batun motar da yazo da ita a
kofar gidan Umma. Ko Bishira bata san cewa ya
shigo gidan ba,tana can jarabar kallonta na
tsiya,ya rufe gidan ya nufi dakinshi. Ranar mu2m
5 bacci sai dai 6arawo,Umman Bashir kwana tayi
saka da mugun zare. Umman Abban ma juyi
kurum take yi hr Alhj ya gaji ya ce,Yau dai sai
juyi ki ke yi. ta ce Na kasa bacci Alhj. Ya ce,
Tashi to kiyo alwala kizo ki kama sallah,in kina
da damuwa ne sai ki fada ma Allah. Umma bata
tsaya ba,ta tashi. shi ko Abba wani matsanancin
ciwon kai ne ya hana shi sallah. Ya dai yi
nasarar yin alwala da ya shiga daki sai jiri. Dole
ya kwanta rigingine tare da dafe kanshi da
hannuwa guda 2,sunan Allah yake ta kira dan

neman dauki. Ita ko Ummi dirshan ta zauna tana
kuka,hr sai da hawayenta suka kafe,idanunta
suka shiga zafi,kanta ya soma sarawa gefe daya.
Ita ma ringingine ta kwanta tare da lumshe
ido,Istigfari kurum take yi tare da hailala,shi ko
Bashir mafarkai ne suka hana shi bacci,dk
mafarkan na Ummi ne. Da safe da matsannancin
zazzabi ya farka,dn haka bai iya zuwa Masallaci
ba,da kyar ya yi alwala.yana idar da sallah ya
kundundune cikin bargo. Matsanancin ciwon kan
da Ummi ta tashi dashi ya firgita 'yan
gidan,Musamman Umma wadda ta same ta
kwance a tsakar daki da safe. Ganin fuskarta a
kumbure ya tsorata Umma,hr sai da ta kira
Alhj.Nan fa Alhj ya dauko wayarshi ya shiga kiran
Abba,kan cewa yazo ya kaita asibiti. Sai dai tayi
ringing ya kai sau 10 amma ba a daga ba. Alhj ya
ce Ina yaron nan ya shiga ne?kuma ga motarshu
a kofar gidan nan,na ganta da asubahi da na fita
Masallaci. Umma ta ce,Tao Allah yasa dai lfy.
Har karfe 8 Alhj na neman layin Abba shiru ba a
dauka ba,ga Ummi rike da kai tana ta salati
Umma ta ce,Alhj ko Bashir za ka sa ya duba shi?
Alhj ya koma daki ya dauki hula ya nufi gidan
Abba. Gidan a kulle ya same shi,dn haka ya dinga
bugawa.Abba na jiyowa amma ba zai iya tashi
ba,haka dk ringing din da wayarshi ke yi yana ji
ya kasa tashi ne. cikin bacci Bishira taji bugun
gida ya yi yawa,ta tashi ta bude. Da Alhj suka yi
ido 2,ya ce lfy ba ku tashi ba? Ta ce Mun tashi.
ya ce Ina maigidan naki? ta ce Ina ga ya fita,bari
in duba. Ta juya ta nufi ciki. Alhj ya cika da
mmk,ya za a ce wai mace bata san fitar mijinta
ba? Anya wannan matar tasan darajan mijin?
Tunaninshi ya katse lkcn da ta dawo tana cewa
Alhj yana kwance ba shi da lfy. Alhj ya bita yana
cewa Ba shi da lfy,amma ke ba ki sani ba?Wanna
wane irin zama ku ke yi ace kina matarsa amma
ba ki san cewa ya tashi ba lfy ba? Bishira ta ce
To ai shi ne bai kira ni ya fada min ba. Alhj ya ce,
Allah ya kyauta. ya nufi dakin. Abba na kwance
ya kundundune cikin bargo sai rawar sanyi yake
yi. Alhj ya yi Sallama ya shiga dakin ya rusuna ya

daga daidai fuskarshi ya janye bargon ya ce,
Abbana ba ka ji dadi ba? Abba ya bude
ido,idanunshi jajir,ya ce Abba kaina ne tamkar zai
6alle. Sai zazza6i tun daren jiya. Alhj ya ce,Ikon
Allah Yau kuma abn da na wayi gari da shi
kenan? Ummi ma na can kwance da ciwon kan,to
tashi. Shi yasa nake ta kiranka don ka kaita
asibiti amma da ka daga ba. Yanzu tashi in za ka
iya ka kira Ahmada abokinka sai ya kai ku
asibitin. Abba ya ce To Wayar Ahmada din a
kashe don haka sai Alhj ya ce "Af, na tuno da
Bashir,kintsa bari in je muzo naga mator can
kofar gidanmu ko?Abba ya lulubo makullin motar
yaba Alhj., Zani kawai Umma ta daura ma
Ummi,sai ta zura mata hijabi,suka shiga bayan
mota su 3 da Umma da Alhj,sukaje gidan Abba
suka dauko shi. Bishira taso zuwa amma suka ce
ba wuri ta bar shi kawai. Asibitin kudi ne kuma
likita guda ne ya duba su. Ummi dai hawan jini
ne don ita a ka fara dubawa. Gado likitan ya
bata,sannan Abba ya shiga shima likitan ya ce
jininsa ya hau,amma ba kamar nata ba. Nan ya
roki likitan cewa kada ya fada ma iyayensu abnda
ke damunsa,ya rubuta mishi magunguna kawai.
Likitan ya ce Ba komai. Amma me ya ke
damunku kai da sister dinka ciwonku iri daya
kuma ya kama ku a lkc daya? Abba ya ce Ba
komai lalura ce kawai a ka kaddara ta same su
lkc daya.Da Abba ya fito sai ya ce ma su Alhj
Zazza6i ne. sai dai shi kanshi ya ji mmkn
ciwonsu iri daya. Yana jingine da bango a dakin
da a ka ba Ummi gado,yayin da Bashir ya tsaya a
gabn gadon Umma tana zaune a kan kujera. Alhj
krm d Bbba suka shigo tare da Likitan ya kalli
Abba Yarona kana bukatar bacci ga. Abba ya ce
To yanzun zan tafi gida. Ya iso kan Ummi wadda
a ka daura ma ruwa,ya ce ku barta ta huta bata
bukatar hayaniya,don haka ku rage daga cikin
dakin. Alhji ya ce, To mun gode. Suka tafi suka
bar Umma. A mota Alhj ya ce da Abba,ka fada a
wurin ainkan? ya ce, Eh abokin aikina ya kira ni
kuma na fada masa. Alhj ya ce,To shi
kenan,yanzun sai muje can gidanmu zaka fi

hutawa... .Yanayin aikinku ne ba ka samun bacci
ko? eh kurum Abba ya ce,amma shi yasan
tunanin Ummi ne ya ke hana shi bacci da
matsalolin da yake hangowa. Yinin ranar yasha
bacci,sai kusan 4 ya tashi ya yi Sallah,ya ji dadin
jikinshi. Bishira tana gidan Umman Bashir wai ita
da tazo jinyar miji,tana bata lbrn wai Abba bai
fada mata ba shi da lfy ba,ya kira Alhj yazo yana
ta min surutai wai mijina ya fita ban sani
ba,meye- meye? Umman Bashir ta ce, Da Allah
kyale su,don wani sabon iskanci ma wai Bashi ne
ke son Ummi. Bishira ta mike zumbur tare da
cewa, Bashir fa ki ka ce Umma? Hu'um,lallai da
wani abu. Bashi da ya tsani Ummi shi ne zai ce
yana sonta? Umma ta ce, Sannu 'yar albarja,ashe
kin fahimta,? Tabbas nasan ke za ki fahimta,to in
gaya miki Bashir ko yau da safe fa sai da muka yi
ta dashi. Dubi yadda Bashir ke min biyayya amma
yau ina fada yana fada. wai hr da ce min shi bai
ga wani mugun halin Suwaiba da nike fada
ba,tana min alkairi amma ni kullum ina binta da
sharri. Kai dai jin wannan zancan ka san ba yin
Bashir ba ne,don haka na ce masa ba komai
nasan ba yin ka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login