Showing 9001 words to 12000 words out of 46188 words

Chapter 4 - ZURFIN CIKI book 2 Complete by halima Abdullahi K Mashi .pdf

wulakanta
ki. Kuma game da batun sallah dk lkcn da bata yi
ba ka dakar min ita ni na saka,batun tsafta kuwa
kada tayi,ka nemi mata ka aura ka barta da
tsiyarta. kai dk lkcn da ka samu matar ma zan
biya maka sadakinta ko 'yar wanene.Sai a lkcn
Alhjn Su Abba ya yi magana. Hakuri za ka yi

ranka ya dade,Allah ya saka da Alkairi bisa
karamcin da a ka yi mana,kuma insha Allah ba za
su sake ba. Abba ma ya yi godiya,sannan suka
masa sallama.Ita ko Bishira mayafi ta dauko tana
kuka suka tafi. Hjy Zainu ranta ya 6aci,taso a
kashe auran don dama bata son Abba sam,kafin
zuwan iyayen Abba da shi kansa Abban ta
fadawa mijinta karairayi,kamu ransa ya 6aci. Ya
kuma daukar wa kansa alkawari in ya bincika ya
tarar haka ne dukanta da zaginta yake ba tare da
ta masa laifin komai ba?sai yasa an raba auran.
Amma da yaji batun Abba gata a gurin bata musu
ba,sai ranshi ya baci da ita, har dai batun sallar
nan.dn haka ya bincike yana da kyau ayi shi,kada
ka yanke hukunci da maganar gefe daya,wannan
shi ne adalci. Bayan sun dawo Abba ya rakata
gida ya zo gurin Alhj da ya ce ya dawo yana
jiranshi. Alhaji ya masa fada cewa dk in da tara
tayi to ya kansace a gida. Sannan fadan da ta ce
yana yi in ya shiga shi ma ya daina,haka ya
dinga zama yana cin abncin.Abba ya ce to.Umma
ma da ya shiga suyi Sallama nan dai ta kara
masa fada tare da nuna mishi hanyoyin da zai bi
ta ce kuma cikin satin nan yayo mata rijistar
Islamiya tunda da ita a kusa. Ya shiga ya same
ta zaune bakin gado tana ta fushi,ya zo ya zauna
kusa da ita.Yasa hannunshi ya kamo nata,sannan
ya kira sunanta bata amsa ba bata kalle shi ba
ya ci gaba da mgn. Kin san dai ina sonki ko??ta
dube shi Da ba kafin a zuga ka.Ya ce wa zai zuga
ni? ta ce Wa kuwa in ba Ummar taka ba. Ya yi
tsam ya ji haushin maganarta sosai,amma sai ya
danne kada ki zargi Ummata tana sonki kin ki
fahimta ne kawai.amma mu bar zancan kiyi hkr
akan abubuwa da nike miki. ki yafe min nima na
yafe miki. . Ya jawota zuwa jikinshi,hr gobe ina
sonki sosai.Ranta ya yi sanyi don mata na son
wannan kalma daga mazajensu. Ya kira sunanta
ta dube shi cikin ido suke kallon juna,ya ce kin ya
fe min?ta daga gira,kina sona hr yanzun?Ta kara
mannewa a jikinshi "Ina sonka sosai ma.Ranar
dakin shi suka kwana,kuma ranar ce rana ta
farko da suka soma kwana a dakin nasa. Washe

gari tunda ya dawo Masallaci ya soma akin share
gida,lungu-lungu ya gama ya wanke bayi kan su
sannan ya yako ta da kyar ta tashi ya ce tayi
sallah ta yiwa yaro wanka. Tayi Sallar,wankan ta
kuke wai akwai sanyu,sai ranar ta daga. Ya ce,To
t dafa musu ruwan zafi su karya.Shi kuma ya
fitar da wankinshi yana yi ya gama ya ce ta fito
da duk wankinsu ita da yaron.Tsawaya ya yi yana
kallon tilin kayan,amma gudun kada suyi rigima
sai ya yi shiru ya ci gaba da wanki. . Ya cire
kayan yaron da zannuwanta hr ma zanin gado
wadanda yaron ya yi kashi ta aje su suka
bushe,,wasu kayan hr da tsutsotsi. Ya kira ta ya
ce "To kalli kayanki hr da tsutsotsi,wanna n ya
dac fisabilillah?samo leda ki kwashe su,ba zan
iya wanke su ba,in kuma za ki wanke to. Nan ta
samo bako ta kwashe takai gurin bola,ya ce
Bishira tsafta cikin addini ce,Annabi (S.A.W)ya ce
Babu mai shiga Aljanna sai mai tsafta. Don Allah
ki dinga kula,ke kanki za ki ji dadi in har ki ka
tsaftace ko'ina na gidanki.Ta tura baki ta wuce.
Ranar haka ya yini wanki kayan yaron dk sun
dafe kaya masu tsada da kyau irin wadanda a ka
sai masa daga gidan iyayenta,ranar dai ko shago
bai je ba. Cikin satin dai babu laifi suna ta
shiri,kuma tana daurewa tana yin tsaftar
jikinta,haka nan yasa ta wanke kai tayo kitso. sai
dai ita gani take dk an takura mata,amma tana
jin dadin yadda ya sakar mata fuska kamar
farkonauresu. Mitar da take masa kullum ya
daina dadewa a waje,ita don Allah ya zauna a
gida suyi hira. Ranar dai saiya gwada zama tun
da ya dawo sallar Isha'i ya shigo gida. Tana
zaune ba riga ya ce,Wai Bishira kayan kwalliyarki
sun kara ne? ta ce,Me ka gani?ya ce,Rabon da in
ga kwalli a idonki tun kina amarya bare dan jan
baki. . Taja dan tsaki "kwalliyar me zan yi sai
kace wata budurwa?Da dai nayi.Ya ce kin ji wani
shirme kuma,ban da ke ai matar aure me miji a
hannu ita ce da yin kwalliya. Ta ce, To ko ma
nayi ba zama ka ke ba.Ya ce "To yau dai gani na
zauna,kuma ina son a sheka min kwalliya. Ta
dube shi Gsky sanyi ba zan iya yin wanka yanzun

ba.Shiru ya yi yana kallonta,can sai ta zame ta
kwanta,sai kuma bacci. Ya yi murmushi.Dubi
matar da ta ce wai ba na zama a gida. to yau na
zauna amma kalli yadda ta bingire tana shirgar
bacci. Ya mike ya fice.cikin takaici korafin banza
kenan take yi tunda ba ta san yadda za ta yi fira
da mijin ta ba. haka dai abba yayi ta hakuri don
baxai yiwu ya ce shi kadai zai dauke mata duk
aikin gidanta ba. sai dai yayi wanda zai iya,amma
duk wanda ya shigo gidan shi ko ba a fada ba
yasan matar gidan kazama ce ta bugawa a
jarida. ummi tana zaune gaban umma,fuska
shabe- shabe da hawaye.ta rikewa ummar
hannu."kinji don Allah umma kice wa ya Abba ya
dawo dani garin nan.wallahi bana son makarantar
kwana,ni dai bazan koma ba."umma ta ce "haba
ummi xuwa yanzu ya ci ace kin saba da
makarantar" ta ce,"umma bazan saba da rashinku
ba....."karaf a kunnen Abba. ya ce,"to sai ko ki
shirya sabawa,don wata rana ma aure zaki yi."
umma ta ce sosai kuwa. tsohuwa dake zaune a
kofarta,tana jinsu ta sako baki da cewa,"ku dai
lallasheta,karatun nan fa da ake ta matsanta
mata bana ganin manzo bane." Abba ya ce
mata,"in ji wa? kin ji ki,to ana neman aljanna da
karatun boko kuma ana neman wuta." ta ce,"kai
ni raba ni da shegiyar karya tunda bata so a
barta." Abba ya dubi ummi,"kada ma kiyi za ton
maganar tsohuwa za tayi wani tasiri,gara ma ki
shirya komai gobe da wuri zamu wuce." ta dube
shi,"don Allah ya abba." ya mike ki shirya da
yamma zanzo muje (sahad store). ya dubi umma
na tafi. . Ta ce,"abba bamu ko gaisa ba,ya mutan
gidan?" ya ce,"suna lafiya,sauri nake in karasa
wasu dinkuna,saboda gobe bana nan jibi litinin
zanje interview da gidan radiyo da talabijin na
(c.t.v) ta ce,"a'a ka samu anan din ne?" ya
ce,"eh bana fada miki ba da aka tura takarduna
can sai suka ce gurin da zasu saka ni akwai wani
wanda suke jin dadin aikinshi a gurin? don haka
zasu turo ni kano,suna ganin ana bukatar irina.to
shine mijin anty ya fada min to yanzu sun kirani
ranar litinin zasu min (interview).ummi dai na

jinsu bata ba kukanta ba.abba na ficewa umma
ta ce tashi kije kiyo kitso ummina,kin ji? dakyar
taje ta dawo.umma tana yankan kubewa wayarta
ta shiga ruri,ta dauka Abba ne.ya gaisheta ta
amsa,ya ce ummana ummi fa ta shirya? umma
takai duba cikin daki inda ta hango unmi nade
kan kujera tunda ta fito wanka. Tace can cikin
kujera,wai sanyi take ji.yace sanyin lfy kuma? ta
shirya ta sameshi gida,umma tace to gatanan
xuwa sukayi sallama.umma tace ke ummi fito
man in kin gama shirin.ummi tace umma nifa
sanyi nake ji,ina ganin xaxxabi ne xai
kamani.tace to ku biya ta kyamis kusai
magani.tsohuwa tace ke yi kwanci yanki, dole ne
fitan? umma ta miqe tana cewa, yanxu in ban je
ba da yaxo xai fara min masifan shi ne. ta shirya
ta fuce rai a bace.a nutse ta ke tafiya har daf da
qofan gidan ya abba. sallama taji anyi mata.wani
matashi ne suka gaisa, ya tambaye ta nanne
gidansu? tace a,a lafiya?ba tare da bata lkc ba ya
fara xayyane mata manu fanta,santa yake kuma
da aure,tace kaga mlm sai anjima.ta shige gidan
abba shiko ya kafe yaqi tafiya.da sallama ta
shiga gidan,qaran inji baisa aji sallaman ba,dan
haka ta jingina da rijiya tana kallan tsakar
gidan.mamakin daya yadda mace daya a gidan ta
kasa gyara gidan.sai kace gidan namiji, namijin
ma qaxami. . abba ne ya fita wanka sanye da
jallabiya fara.ya aje bokitin ya dube ta. yace ki
siga ciki mana, ai tana falo.tayi
sallama,bishiratana xaune da baso tana kalan tv,
ganin umma ta daga labule sai ta hada rai tare
da cewa lfy? ummi tace ina wuni. bishira tace
lau, nace lfy? ta fada hadi da xare ido. ummi tace
ya abba ne ya ce na xauna anan na jira shi. tace
baxa a xo nan adame ni ba, ehe dan kallo nakeyi.
ummi ta ja tsaki tare da sakin labulan, ta koma
ta jin gina da rijiya.bishira ta fito.ke sarkin rashin
kunya wa kike ma tsaki? ummi ko kallanta batayi
ba.sannan tace baki isa kixo min har gidana
ba,kice xakimin rashin kunyan da kika saba.abba
ya jiyo hargowanta ya fito, yana qoqarin saka t-
shirt baqa akan faran singiletin shi,wandan jeans

ne mai laushi blue.yace,menene? tace, wannan
mara kunyan yarinyan nanne xata sameni har
dakina tamin tsaki.oa dubi ummi dake kallan
qasa tamkar bata san me akeyi ba. yace ke
ummi, ta dube shi da sauri,xan bata maki rai
kinsan bana san raini ko? tace nifa ya abba
banfa yi mata komai ba kawai fa.ya daga mata
hannu,yace banasan ji. yace na fada maki dai
bana san raini. takaicin duniya ya isheta,ta
sunkuyad da kai cikin qunan rai.wanna shine
gaba kura baya damisa.bishiqa kam sai ci gaba
da mita take, shiko abba tuni ya koma dakinsa da
qarasa shiri. ya fito fes, sam baxaka ce mijin
bishira bane.qamshin turaransa ya karade gidan
ya daga labule.ni na fita. tace sai ina? xan kai
ummi ta sai duk abinda xata nema dan gobe xata
koma mkrt. ta tabe baki. ya dubi ummi wadda ke
cika tana batsewa,sannan ga sanyi alamun
xaxxabi yana damunta.yace muje ko? ta dube shi
sannan ta bishi.a qofar gida ya iske wannan
saurayin,yace lfy, ko kana jiran wanine? saurayin
ya ce wata yarin....sai ya hango ummi,dan haka
ya katse batun da cewa yauwa gatanan. . abba
ya kalleta ke uwar rore rore wannan ke yake jira
ko? ummi tace oho mashi, bina yake tayi.abba ya
ce, kayi haquri dan samari,ba aure xa a mata ba,
krt takeyi. yace nima din bawai ina nufin yanxu
bane.ya ce na fahince ka.to ka bari sai nan
gaba,ina nufin in auran yayi sai kaxo ko???? Ya
dubeta ranshi bace,ke kuma wuce muje.suka bar
shi nan tsaye yana kallansu.yaga kishi qarara a
idon abba.yace wannan ba wanta bane shima
santa yake.ya raya aransa shima yayi gaba abin
shi.shi kam abba suna tafe yana yi mata fada,wai
tabi ta sakar ma maxa fuska kowane gaja sai ya
xo yace yana santa.maimakon ta tsaya tayi
krtnt,xamani na ilimi,ita dai ta qi kula shi,har
yanxu takaicinta abin da matarshi ta mata,kuma
ya nuna ya goyi bayanta.wayarshi tayi ringing,ya
kalli ummi muje shago na mashin din
nacan.sannan ya daga wayar,ita tana tafe ne
amma sam bata jin dadi.da yake tafiyanta yanxu
tamkar tana jin tausayin qasa take yinta,sabanin

da da sai dai tayi gudu,shi da ke tafe yana waya
ya riga ta isa.gefe ta tsaya ya shiga shago bayan
ya gama amsa wayar.ahmad abokinsa yaxo xai
shiga shagon ya ganta tsaye.tace ina yini ya
ahmad? yace lfy lau yar daru.daman haka ya kan
ce mata.ya shiga shagon yana
waiwayanta,abbana barma yan shagon sallahu
wasu kayan da xa a xo dauka,ahmad ya shigo.
suka tafa,sannan suka gaisa.ahmad yace naxo ne
in fada maka anjima xamu shiga gidan su hafsa
dan gaida iyayenta,sai dai kuma ganin ummi ya
sani jin wani abu.anya ba xan dawo gida da
neman aurena ba?a rude abba ya ce wace ummi
kenan? ahmad ya ce qawarka mana.abba ya ce
dan Allah saki xancen nan kada ma ta jiyo ta
raina mu,me ka gani naso a gun ummi? dan Allah
kada ka cta min rai. . ahmad yace, allah in xai
yiwu, nutsuwan ta birge ni .abba ya ce to ba da
ni xa aci amanar hafsa ba.ummi kuwa dan Allah
ka bar xancenta.yaea ahmad yaga abba ya sha
mur ya tsare gida,dole ya saki batun.suka yi
sallama ya tafi,abba na cewa sai yaxo da
dare.yasa yaron shagon ya goge mashi mashin
din sannan ya tada,ya kalli ummi fuskarshi daure
xo ki hau.itama tata fuskar a daure take.tahau
suka tafi,iskar dake kadata tasa xaxxabin dake
san kamata ta qaru.ya kafe mashin dhn ya
kalleta,muje mana.ta bishi suka shiga cikin sahad
store din.tsaye tayi tana kallanshi yana diba
kaya.da alama na iyalanshi yake diba,dan taga ya
soma da pampas. Hannuwanta harde a qirjinta
tana kallan shi,kome nashi yana birgeta.ya
waiwayo ya dubeta, tsayuwarme kike yi a nan da
ba xaki dauki abinda ya kawo kiba? ta rasa me
xata dauka,sai kurun ta dauki makilin ta riqe a
hannu,ya gama diban abin da yake so,sannan ya
aje gaban masu amsar kudi.ya dubeta,bakya
buqatar komai kenan? ta nuna mishi makilin din
hannunta,tana murxa shi.ya harareta baxa ki
dauki komai ba,kina da kayan tea dasu complex?
tace a,a.y2e to ki tsaya kada ki dauka.ya soma
dibo mata saitin sabulan nan daya taba sai mata
na aloe vera,dan yaga duk kananan qurajen sun

mutu.sannan ya hada mata da audugar mata
guda biyu.ya kai table.lkcn ta dauki madara da
milo ta kawo.yace wawiya,dalla matsa ki bani
gu.yaje ya qara tsinto mata ,sanna akayi musu
total ya biya.suka fita.kafin sukai gida haqoranta
sun s6a haduwa,gashi tana ta takurewa,yace
lfy,wani irim xama kika yi haka?tace,sanyinake
ji.tana magana muryarta na makyarkyata.wani
dan asibiti ya nufa da ita nan kusa da unguwansu
aka dubata. Wurin allura,nan fa a ka soma
daga.Ta ce,ita kam bata san allura.Abba ya daka
mata tsawa da cewa,Allurar ce abn tsoro?Na
gane sam ba ki son ki koma mkrnt,a gobe ne
kuma sai kin koma duk abnki. Ta ce, Naji zan
koma amma yanzun kam dn Allah Ya Abba kada
amin allura.Nurse dai sai kallonsu take yi tana
dariya. kwai Ummi sai ta soma hawaye ita fa har
ga Allah bata son allura.Nurse ta ce,To ka rike ta
mana ko ba Amarya ba ce?Naga shagwabar tayi
yawa. Abba ya ce,Me? cikin tsawa ya yi
maganar,hr sai da Nurse din ta tsorata,ya ce
kanwata ce fa,kin ga wannan kucakar tayi kama
tayi kama da Amare? Nan take Ummi taji ta
muzanta,sannan km ta tsorata da irin tsawar da
ya yi,ba ta san lkcn da ta shige a ka yi mata
allurar ba. Ta fito tana sharar kwalla suka koma
gida. Sai dai tana hada kayanta a Jaka,Sannan ta
ga wadannan sabulun da kuma audugar,kenan shi
ne dama ya sai mata wancan?ko me yasa ya sai
mata kuma hr da augugar mata? . wata zuciyar
ta ce,kila dn yaga Umma bata san kan abubuwan
zamani ba sosai.A fili ta ce,kai umma tasan
audugar mana. Haka dai ta ci gaba da tufka tana
warwarewa,hr ta gama shirya kayanta. Yau kuma
a bayan Tsohuwa ta za6i kwanciya,da dn komai
ba sai dn suyi hirar yaushe gamo. Sai dai
Maimakon hira sai ta tsunduma a tunani,ta bar
Tsohuwa tana ta zance ita daya. Fitarsu da Ya
Abba ta tsaya mata a rai,ita tayi ta tunowa tana
murmushi.Sai dai bata Son tuna lkcn da ya yi wa
Nurse din nan tsawa dn ta ce ko ba amarya ba ce
kom me yasa zai mata Tsawa? ita kam kalamn
Nurse din nan sun birgeta,shi kuma daga ganin

yadda ya yi tsawar nan kalamn ba su masa dadi
ba.......... wai takwara bacci ki ka yi ne?Muryar
Tsohuwa ta katseta,ta ce,Idona biyu Tsohuwa.Ta
ce, Tunanin me ki ke yi ne haka?Ummi ta ce
"Um" ina tuna gobe yanzun ina can.Tsohuwa taja
tsaki,Ai mai sunan Malam ya san takan mugunta.
UMMI dai ta ce "Um.Tsohuwa kuwa sai yi take
da mai sunan Malam.Tun Ummi naji tana "Um",
hr zcyrta ta soma tsanar kalaman Tsohuwa. Sai
dai bata da damar ta katse Tsohuwa tunda dn ita
take yi,bata da mafita da ta wuce ta bar
dakin,don haka ta suri butar Tsohuwa,wai zata je
kewaye(bandaki). Shi ma Abban da ke kwance a
tsakar dakinshi kan kafet ya tada kai da
katifarshi,ban da tunanin fitarsu ta dazun ba abn
da ya keyi. Sai dai damuwarshi daya,me yasa
samari da dama suke kawowa Ummi hari?Me
yasa ya ke jin zafin haka?Zuciyarshita amsa da
cewa,ka so ko ka ki kana Son UMMI."a fili ya
furta "Haba dai so,Allah ya tsare ni." Tun misalin
tara Ummi ta gama shirinta tsaf,cikin kayan
mkrnt mai ruwan hoda,mai gida-gida.Da kuka ta
bar gidan yau ma. Haka nan kuka take hr suka
isa mkrnt,ta samu Khadija hr tazo,dn haka tare
suka kwashe kaya.Kafin Abba ya tafi sai da ya yi
mata fada kwantankwacn wnda Umma tayi
mata.Waton ta kula d kanta,kuma tayi abn da ya
kawo ta,waton krt.Sannan ba ya son tayi
kawance d yaketa shari'a.irin wanda wasu
watsatstsun yaran ke yi.(Allah ya shiryesu).
Sannan ya jadadda mata batun ibada,sannan ya
kawo kudi ya bata,ta ce Umma fa ta riga ta bani.
Ya ce,"Ki kara."ZURFIN CIKI book 2 part 5
ZURFIN CIKI book 2 part 5
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:12
Umma fa ta riga ta bani. Ya ce,"Ki kara."
Rayuwarta a mkrnta wannan karon ba laifi,sai dai
fa hr yanzun ta tunu da gida sai tayi kuka. Su
Safiyya suna mmkn yadda Habiba take da
matsanancin nacin gida. ******** Abba ya shigo
gidanshi dauke da ledajin kayan miya,da sauri ya
dire su kofar kicin ya nufi Bishira da ke kofar
bandaki tana shara amai. Ya kama ta,"lafiya?Me

ki ka ce? Sai da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login