Showing 42001 words to 45000 words out of 46188 words

Chapter 15 - ZURFIN CIKI book 2 Complete by halima Abdullahi K Mashi .pdf

Bishira
ta ce, Na gode Anty, amma don Allah ki barni na
dan huta a nan gidan duhunsa nake gani, don ba
ki ji yanda ni ke ji ba ne Anty ko da dana Walid
ya rasu ban ji kunci irin wannan ba. Ta sake
rushewa da sabon kuka wiwi, Anty kallonta kawai
take ta ma rasa me zata ce. Wayarta ta ciro
daga chaji ta shiga kiran layin Abba, lokacin ya
kira kananan kannanshi su Kamal suna ta fito da
kayan dakin Bishira saboda ayi fenti har an gama
nashi dakin. Wayarshi da ya ajiye a kan windown
dakinshi ta shiga ruri, ya duba, Anty ce. Ya daga
tare da sallama, ta amsa ya gaida ta cikin
girmamawa da mutuntuwa, ta amsa da fara'a
sannan ta ce, "Abba ga Bishira nan tazo tana
kuka, kuma ta ce min ba ka san ta fito ba". Ya
ce, "Eh haka ne, ta ce don Allah in baka wani abu
ina son ganinka. Ya ce To zan zo Anty, amma
yanzu ina aiki ne kayan dakin ta muke fita da shi
za a yi mata fenti ne, ta ce To ko da dare ne
haka, ya ce to zan zo. * 68.... Ummi tana ta zuba
ido ganin Abba amma shiru har a ka yi Magriba
tayi wanka tayi sallah. Tana zaune har Isha'i tayi
daga Masallaci shima ya nufo gidan su Ummi,
lokacin Ummi tana bakin gado tana 'yan shafe-
shafenta.Ta juyo Abba suna gaisawa da su
Umma, ta shirya cikin leshi mai ruwan lemun
tsami, da dan mayafinta fari haka takalminta. Ta
fito tana zaune kan kujera, ta ce "Sannu da zuwa.
Za ka ci abinci?" ya ce, "Da sauri haka ba muko
gaisa ba?" Ta zauna ina yini? Ya ce, lafiya lau. To
na kawo abinci? Ya ce, daga gida fa nake, ina da

kuma mata. Ummi ta ta6a baki, oh, haka ne ashe
kana da mata, gani nayi da matar taka ka ke
zuwa cin abincin daga nan ta lafe a kujera tare da
hada rai. Ya mike muje ko? itama ta mike, ya
kalle ta da wannan mayafin za ki? Ta ce, eh, ya
ce a'a dauko hijabi ba zan lamunci yafa wannan
dan mayafin ba. Ta kalle shi kamar ta ce ai
matarka tana yafa irin shi sai kuma tayi shiru ta
nufi uwar daki don dauko hijabi. Shi kuma ya nufi
waje, ta yi wa su Umma sallama sannan ta fito.
Yana tsaye jikin mota ya ce, ina wayar nan? Ta
ce, "Gata nan a hannuna ya yi dan murmushi
yace mayyar waya dama nasan sai kin dauko har
yanzun cikin haushin maganar shi ta dazun take
yi. Don haka bata kula shi ba, ya shiga motar ya
bude mata gefen kusa da direba ta zauna cikin
fushi. Lura ya yi da hakan, don haka sai ya ce ba
ni tamata ta ce so nake in loda mata kudi. Ya
guntse baki don kada yayi dariya, ganin yanda
tamiko mishi wayar cikin hanzari gata Allah yasa
bacewa nayi a bani ba. Ta juyar da kai tana
kallon titi, shima bai sake cewa kala ba har suka
shiga cikin gari. Ya dube ta, wane shagon zamu?
Ta ce, duk wanda kaje, ni sanin wani saloon nayi?
Shagon wata mata ya kaita kusa da inda yake
aski, sun samu shagon Musulma ce 'yar
Maiduguri.Shamsy belloRFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 3 part 9
ZURFIN CIKI book 3 part 9
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:40
nayi? Shagon wata mata ya kaita kusa da inda
yake aski, sun samu shagon Musulma ce 'yar
Maiduguri. 69.... Abba ya ce mata ga Amaryata a
gyara mata kai duk da ba wai gashi ne da ita ba
ya yi kyau sosai ko nawa ne zan biya. Mai
shagon tayi 'yar dariya, zan mata yanda ka keso
ya dubi Ummi wadda ta samu kujera ta zauna
fuska daure. Ya ce, "Kanwata zan tafi nayi aski
nima, daga nan sai na dauki matata daga unguwa
na kaita gida, sannan ta san in har ta bude baki
to kuka ne zai kwace mata, don haka sai ta yi
shiru. Ya fita yana 'yar dariya, mai shagon
Yagana saloon ta ce, "Kai kanwata kun dace fa,
kuma da alamayana sonki sosai.Ta kalli mai

shagon hawayen da take makalewasuka zubo, ta
ce "Anty ina so a nan, dubi fa abinda yake
min.Komai sai ya ce min matarsa, matarsa, ko
inaruwana da matarsa? Yagana ta ce, "Yana da
matane? Sam bai yi kama da mai mata ba.Ummi
ta ta6a baki ta ce, "Yana da mata da yakeso ni
bana sonshi, baya sona, iyayenmu ne sukahada
mu.Yagana ta ce, in ma ke ba kya sonshi shi kam
yanadauke da tsantsar sonki a idanunshi n
fuskancihakan. Ummi ta ce, "Anya kuwa? Bana
zaton yanasona ne, in kin ce yabi iyayenmu ne
zan fi yardadon shi din mai biyayya ne.Yagana ta
tura mata kujera, zauna in soma miki,sai da ta
fara gyara mata kai sannan ta ce, "In mamijinki
ba ya sonki to kuwa ba za a yi wuyarshawo kai
ba.Ummi tayi murmushi tare da kallon fuskarta
tamadubin da suke fuskanta, ki ke gani Anty? Ta
cesosai kuwa, ki tarairaye shi da kyau, kin san
shinamiji dai dan shauki ne da son nishadi.
(((KWARAI KUWWA!!!)))Ga kuma son tarairaya
kamar jaririn yaro, ummi tace, "To zan yi hakan in
har yin hakan zai sa ya soni.Yagana ta ce, "Zai
so ki, zan so kiyi gyaran jiki dafata, Umi ta ce,
kamar ya ya? Yagana ta ce, kayanmata zuwa
gyaran fata, wanda za ki sha don 'karinni'ima.
Ummi tayi shiru, don bata son irin
wannanzantukan.Ta ce, "Kin yi shiru, Ummi ta ce
Ummana ta ce bata son in sha komai, tunda ni
budurwa ce, in je wamijina da ainihin halittata.In
yaso daga baya sanin saboda 'yan garinmu sunzo
da shi daga Zamfara. Yagana ta ce, Hakan
mayana da kyau, domin Amare da yawa suna
shanwahala sosai kasancewar ba su saba
ba.Sannan mazajen ba su bambance ainihin
yandamatan suke. Ummi cikin gundira ta ce, Gara
ma nagyara fatar.Yagana ta ce, "Wancan ma za
ki neme shi, ko nangaba Ummi ta ta6a baki, ni
dai fada min na gayarnfatar.Ta ce, "Ina sai dawa
in kina so zan baki kije gida kihada kiyi zan hada
ma angon lissafi da shi Ummita ce, ba ni sai da
suka gama a ka gyara matagashi fes, sannan ta
dauko kayan ta shiga lissafamata kamar haka:-1.
Man Zaitun2. Lalle3. Kurkur4. Madara ta ruwaZa

ki hada su guri daya ki kwa6a, sannan ki
shafejikinki da su kafin shiga wanka, in ya bushe
idan zaki shiga wankan sai ki murje shi tas,
dukwadannan 'yan kurajen na fuskarki za su
mutu,jikinki ya yi laushi da sheki.Ga kuma wani.1.
Sabulun Ghana2. Dettol3. Zogale4. Farar
AlbasaZa ki hada Sabulun Ghanada da Dettol da
garinzogale, da farar albasa, ki hada su ki kir6a
kimurmule shima a jikin za ki ringa shafawa.Da
fuska kafin ki shiga wanka, zan bar ki da biyunin
sun amshe ki ma sun ishe ki. Yanzun ko inwanke
miki kafa? 39. 70.... Ummita ce, "Ina tsoron kada
yazo kuma kudin shi ba su kai ba, Yagana tayi
'yar dariya, kina tausayinsa ne? Ki daina tausayin
mijinki shi ne zai amfana da gyaran da duk za ki
yi. Ummi ta ce, "To wanke mini".Ta hada kayan
wankin kafa ta ce yarana ke yi amma zan miki da
kaina. Sai kuma taga zanen fulawa. Ta ce, "Au,
an riga an yi zanen fulawa ma ba dama ayi,
Ummi ta ce, Ohi ni na manta ma, to ki fada min
yanda zan dinga gyara kafar, ta ce To bari in ba
ki mai sauki ma. 1. Man kwaka 2. Man shanu 3.
Man Zaitun Ki samu man kwakwa da man shanu
da man zaitun ki hada man kwakwa da man
shanu guri daya, ki shafa da dare da safe. Ki dan
gasa kafar sannan ki wanke ki shafa man zaitun,
za ki ga yanda kafafunki za su yi tamkar ta jariri.
Ko ki yi na ruwan ko kumba, lalle ki hada su guri
daya ki shafa a kafafunki da dare. Da safe ki
wanke ki shafa man ridi, wadan nan kurum in kin
rike su za ki ba wani labari, Ummi tace zan
kiyaye in sha Allah. Shi kuma Abba yana fitowa
daga shagon aski kai tsaye gidan Anty ya nufa,
ya samu Bishira Anty ta matsa mata tayi wanka
ta bata kaya ta saka. Ta kira mai kitso tazo tayi
mata ta sata ta shafa turaruka. Tunda Abba ya
shigo yake kallon Bishira, sun gaisa da Anty,
sannan ta ce dama dai na ce kazo ne don Bishira
ta baka hakuri. Sannan in maka tuni da yin adalci
a tsakanin matanka, kuma na yi wa Bishira fada
sosai. Ta dubi Bishira, ki ba shi hakuri, Bishira ta
hada rai tare da turo baki, ta kalle shi cike da
tsananin jin haushin shi. Kayi hakuri ya ce ba

komai dama ni ban yi fushi dake ba, a zuciyarta
ta ce, ba ka isa in baka hakuriba, albarkacin ina
son zuwa Makka ne da kuma canjin kayan dakin.
Ya yi wa Anty godiya ta ce ma Bishira gobe da
wuri kiyi parking din duk kayan ki a waje da mun
zo sai mu shirya miki. Bishira ta ce, Allah dai
yasa su yarda, Anty ta ce,"Za mu su yarda in
Allah ya yarda. Ta dauko wasu kayan sawa da
sabbin kuloli ta ce ma Bishiran je kisa a motarku.
Abba ya ce, "Kawo in kai, Anty na gode sai
anjima, ta ce To Abba ayi ta hakuri". Ya ce, Ba
komai, Insha Allahu. Suka biyo shi a baya tana
kara jawa Bishira kunne kan cewa in har ta
kuskura ta ji wata magana ta 6ullo ta rashin
mutunci sai ta fasa tsaya mata a kan maganar
aikin Hajji ko Dady ya amince sai tasa ya janye.
71.... Sun shigo mata Muhibba tana baya tana
'yanwutsil-wutsil dinta tamkar kurame, haka suke
tafiyar. Ta zaci su nufi gida sai taga sun nufi
cikin gari. Bata tambaye shi ina za su ba, har
suka isa inda yayi parking ya dubeta, Madam ina
zuwa, hum kawai ta ce. Ya bude baya ya dauko
Muhibba ya sa6a a kafada ya nufi shagon saloon
din. Daidai lokacin sun kammala komai, Ummi ta
zari hijabinta da niyyar rufe kanta, Yagana ta ce
a'a kanwata bari ya gani don ya biya ni 'yan
kudina. Abba bai zaci Ummi tana da gashi ba,
domin dai acikin Hausawa 'yan Arewa za a iya
saka Ummi acikin ma su gashi. Yayi laya-laya a
dokin wuyanta baki sidik. Yayi murmushi, lallai
kin gyara da kyau. Nawa ne kudinki? Ta fada ya
ciro ya bata, sannan Ummi tazari hijabinta.
Mamaki take, Gida ya koma ya dauko Muhibba?
Yamiko mata ita, Ga 'yarki. Ta amsheta. Yagana
tace, yarinyar tana kama da ku. Abba ya ce, "Ai
'yarmu ce, suka yi mata sallama suka fito. Ummi
da Bishira a tare gabansu ya fadi lokacin da suka
ga juna. Bishira ta kauda kai yayin da Ummi taja
baya daga mazaunin kusa da direban da ta nufa,
ya bude mata baya ta zauna tana rike da
yarinyar. Ya tada motar suka dauki hanyar tafiya
kowanne zuciyarshi da abinda take karantowa.
Ummi tunaninta Abba ya je ya zo da matarshi ne

don yanuna mata shi fa matarshi yake so. Ita ko
Bishira nata ganin wulakanci ne na karshe da ya
dauko ta yazo da ita gurin wannan karamar
yarinyar. Shi ko Abba addu'a ce a zuciyarshi
Allah ya hada masa kan matansa, sai kuma ya
soma tunanin ina zai soma zuwa? Nashi ganin in
ya kai Bishira gida ya sauke ya tafi kai Ummi bai
mata adalci ba. Amma ya kula Ummi tana fushi
kuma yaso ya lallasheta, yana cikin wannan
tunanin ya tuna dawayar nan. Ya kalli wayar a
gefanshi. Dan murmushi yayi da ya tuna lokacin
da ta dangwarar masa da wayar don ya ce ta
matarsa ce. Yanayin yanda Ummin ke nuna
kishinta yana birge shi, koda bata sonshi tana
kishinshi sannan bata masa raini ko rashin
kunya. Kofar wani gidan saida gasassun kaji da
ire-iren kayan kwalam ya tsaya. Ya kalli Bishira
Madam mu shiga ko? Ta ce, "A'a ni fa ba zan fita
ba, ya ce To bari in dawo, ya nufi ciki. 72.. Ta
waiwayo ta dubi Ummi, ta ce "Ba ni 'yata
fitsararriya. Ummi ta mika mata tare da cewa
nima ai ba cewa nayi a bani ba, ta ce "Kar dai ki
min rashin kunyaki bar ganin an jona ki da mijina
ki zata za ki hada sahu da ni. Ummi ta ce, "Sai
dai kada a kuma in dai batun hada sahu ne, kuma
ban damu don mijinki ba bai sona ba, tunda ni ina
sonshi. Bishira cikin daga murya ta ce, oho?
Dama sonshiki ke yi? Yanzun na gane da nufi aka
yi. To ki sani kin sai ma kanki masifa da bala'i.
Ummita ce, "Kin ga bala'inki can, daga nan
batakara magana ba ta bar Bishira na ta masifa.
Tundaki ka za6i ki auri mijina zan shayar da ke
ruwan dana sani. Sai kin gwammace zama a
kurkuku fiye da gidan mijina, daidai lokacin Abba
ya dawo da ledoji guda biyu. Bishira bata yi shiru
ba sai zagin Ummi take yi,"'Yar iska, 'yar daba...
tsawa Abba ya daka ma Bishira, tare da cewa ba
ki ji kunya ba da ki ke zaginta amma bata kula ki
ba? "Ta ce, "To ka ji abin da ta ce min ne? Tsaki
yaja tare da daukar wayar da ta aje yasa a ledar
Ummi, sannan ya tada motar. Kofar gidan su
Umma ya tsaya, Ummi wadda dama ta kosa tazo
gida, ta bude motar ta fada gida cike da takaici.

Ya kashe motar sannan ya dauki ledarta ya kalli
Bishira, Ina zuwa. Kala bata ce ba. Illa baki da ta
cije, kirjinta na yin wata irin suya. Ban da tana
tsoron Anty kada ta fasa zuwa gurin Dadynsu da
tuni ta shago Ummi ta nadi 'yan kayanta. Dakin
Umma ta shige, Ummar tana shirin fitowa Ummi
na shiga, ta ce kun dawo? Ummin ta hadiye 6acin
ranta."Eh, mun dawo Abba a ya shiga gaida
Umma sannan ya mika ma Ummi ledar, gashi kin
manta Ummi ta amsa tare da cewa, an gode.
Umma ta ce, "Me ku ka siyo in ce dai ka sai ma
Bishira? Ya ce, "Eh na sai mata, kaza ce fa
Umma ba wani abu ba". Ta ce, "To shi ke nan
maza ka koma gurin su, yace "To. Tana fita ya
kalli Ummi akwai waya a cikin zan kira ki, kuma
bana bukatar ki kashe min waya. Ummi ta ciro
wayar da sauri, ta dibe shi ba wayar matarka ba
ce? Ya ce, "Eh tata ce, ta mika mishi cike da
kunan rai, ga abinku ka kira ni da layin Umma. Ya
ce, "Ke ce za ki cigaba da rike ma mata
tawayarta, ba tare da ya jira jin me za ta ce ba
yana murmushi, Ummi ta kasa gane cewa ita ce
matarta shi. Ko kallon kazar bata yi ba illa dai
tayi duk wasu abubuwan da ta saba yi kafin ta
kwanta, sannan ta kunna wayar tana tsammanin
kira. 73..... Shi ko Abba koda yazo Bishira tana
ta mitar don tsohon wulakanci an zo da ita an
shanya ta, bai ce mata kala ba illa dai motar da
ya tada suka nufi gida. Gidan duk kaya saboda
bai maida ba da a ka gama fentin, ya dauki
tsintsiya ya share dakin, sannan ya shimfida
katifa ya fito inda take zaune bakin Rijiya.
Muhibba tayi bacci tana rungume a jikinta, ya ce
kawo ta, ta mike a fusace ta nufi dakin ba tare
data bashi 'yar ba. Ya bi bayanta, so kurum yake
ya lallasheta ba wai don tsoronta ba sai don
tausayinta, yasan mata kan kishi za su iya yin
'yar karamar hauka. Wasu ma sai sun yi babbar
kuma bai dace ana nuna kishinsa ba, shi kuma
yana nuna ko 'in kula a gare ta, gefen katifar ya
zauna ya lalubo hannunta ya rike cikin
nashi."Bishira!" ya ambaci sunanta cikin sanyin
murya, bata amsa ba kuma bata dube shi ba, ya

ci gabada cewa, "Bishira ban ga abin damuwa ba.
Ko damata uku a ka daura min aure da su bare
daya, inkin yi la'akari da irin son da nake miki ke
kin san Bishira ba kiyayya ta hada mu ba. Kina
manta wannan ne? Ta dago ta dube shi ta dan
soma saukowa, yayi murmushi har yau ban daina
sonki ba, ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta turo
baki sai kace 'yar yarinya. To ai na sha jin a ana
cewa so daya ne tak, ya cehaka ne, ta ce "To
tsakanin ni da Ummi wa ke keyi wa? Da sauri ya
ce ke, ta ce Allah?Ya sake tausasa murya, haba
Bishira ya ki ke wannan zancen kema kin sani,
kuma don Allah na roki ki in muna tare ki daina
min zancen Ummi, ke kadai ce za6i na. Bishira
taji dadin wannan kalamai, don haka sukaci
namansu suka kwanta, ya bukace ta a nan masai
da ta ce kaje gurin Ummin mana. Ya ce, "Na ce
in muna tare bana son kina min zancenta. Sai dai
in kina son ci gaba da horon daki ke min ne.
Haba Bishira, ko tausayina bakya yi?An fi wata
uku kina haramta min halas dina. Kullum sai dai
ina azumi sai ka ce gwauro? Yajawota jikinshi, ya
rungume da kyar dai ya samu yadan rage
matsala, sai dai ita ma ya lura tayi missing
dinsa. Suna kwance har kusan sha daya saura
tuni ita tayi bacci, shi kam daman so yake tayi
bacci yakira Ummi. Ya mike yaje yayo wanka
sannan ya nufi dakinshi. Yaja katifarshi ya kai
dakin, sannan ya kwanta akai, ya kira Ummi
lokacin bacci ya soma figarta. Ringing din ne ya
farkar da ita, sai da ta kusa tsinkewa sannan ta
daga, kafin ta amsa sallamarshi sai da tayi wata
doguwar hamma.Ya ce, "Ke baccin ki ma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login