Showing 24001 words to 27000 words out of 27847 words
Chapter 9 - KUCAKAR KISHIYA Hausa Novels By Aisha Muhammad Sani.txt
taji haushi bane sai dan taji kishi tayi tunanin yi maka abinda yafi hakaN.
Amaan yace, "Wooo er karama me kwakwalwar manya anya kuwa bana nemi su Auntynan naki ba daki bane labari Aunty Aisha,Aunty Ambeby,Aunty Walida dama sauransu domin nasan wannan duk darasun sune."
Ahlam ta galla masa harara tare da fadin, "Auntinane ni kadai bara kamin kwace ba eheee."
Amaan yace, "umm shine wato harda harara ta ko zan kamaki ne."
Ahlam ta tashi tana masa gwalo sannan ta shige daki da gudu tana dariya.
Amaan yataso yabita yana zaki sani inna kamaki yau ko zakamin indiancin yan rugarku.
*********************
Hamlat nazuwa bata bari dady yaganta ba ta nufi dakin Mumy ta zaiyanewA Mumy kome aiko mumy tafara surfa bala"i tana, "Ni Wallahi hamlat har kin fara bani kunya,bazakiyi kasa kasa da er matsiyantan nan ba iyee? ai wlh da kin kwara mata ruwan zafinnan ma ba iyaka yanka kadai ba maza maza kije ki kira maamah kuje gidan tare da kuma dukan tsiya bana son raini fa."
Hamlat tace, "mumy ba wani zancen duka yamzu fa ni burina kawai ta bar min gida ."
Mumy tace, "ok ga wata shawara in bata yi aiki ba ma gwada na dukan kawo kunnnenki kiji."
Hamlat tace, "Wooo mumyna shiyasa nke kara sonki wallahi kin iya kissa da kisisi na Amman kinsan miye ba yau ba sai randa kwananshi adakinta ma yakare abin zai fi sugar."
Mumy tace, "Yoo ai bakome hakan ma dabarace."
sai misalin karfe 6 takoma gida inda tA tarar da Ahlam da Amaan suna wasAn buya.
Amaan ido rufe ya fito yana , "sahibty wallahi nagaji ki fito fa inkikasa na fadi kukq zanyi wallau."
Ahlam tana ta dariya abinta.
Sai ga hamlat ta banko kwofa.
Amaan yace, "yess ysn sai nakamaki."
Juyowan da zaiyi ya chafko Hamlat....
*Urs preety xayeesheerth*
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬
*KUCHAKAR KISHIYA*
🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬
*ZAMANI WRITERS ASSOCATION🤝🏻*
__________________________
*we are here to educate,motivate, and entertain our readers.*
__________________________
*Story and Writing*
*by*
*Aysherth Mohammed Sani*
_(Preety Xayyeesherth)_
*BANCE KOME BA DOMIN NIMA SAI DA NAYI 😭*
*PAGE* 64
------------------------------------------------------------------------------------------
Ahlam tace, "umm nidai ba ruwana."
Anan suka manta da zancen Hamlat suka fara hirarsu.
Wunin ranar zubur Hamlat ta kasa fitowa waje kwata-kwata.
Yau Ahlam da Amaan sun cika sati chif dan haka yau zai fara zuwa office kuma in ya dawo kwanan hamlat neh.
Amaan ya shirya zai tafi office Ahlam sai shagwaba take ita fa bataso yatafi yabarta da kyar yasamu ta hakuri ya tafi harda kukanta.
Hamlat na kallonsu tana cizan yatsa.
Amaan na fita tadau waya ta kirawo mamah .
Aiko ba ayi minti talatin ba sai ga maamah ta iso .
Tana isowo Hamlat tace su shiga bangaren Ahlam.
Ahlam na ganinsu gabantA yafadi mussaman ma irin kallon da taga Maamah take yi mata hakan yakarasa mata tsoronsu ba abinda yafado mata arai sai lokacin da suka kwonata da mangyada.
Hamlat ta ce, "Ahlam wai bakiga nakawo miki bakuwa bane?"
Ahlam ta daure tadanyi murmushi sannan ta ce, "sannanku da zuwa aunty bara nakawo muku ruwa."
Hamlat ta ce, "A a ba ruwa mu ka Zo sha kinsan ba shi muka saba sha ba ruwa sai irinku."
Maamah kawai kallewa dakin kallo take azuciyarta tana, "Hmm Insha Allah ina dap da shigowa gidannan nima na mori arziki tare da samun gwarzon miji."
Hamlat ta ce, "Kawata tunanin me kike neh yakamata fa mu fara ai watar da aiki."
Maamah tuni ta mike ta nufi Ahlam tana," ke yar matsiyata kin samu guri ko , sai yadda kika yi da mijin kawata toh wallahi ina fada miki tun huri ki fita a idonmu inba haka ba zaki sha mamaki."
Ahlam sai baya baya take Hamlat na bayanta Maama na gaba .
Ahlam ta ce, "Innalillahi-wa'inna-illaihir-raji'un Dan Allah kuyi hakur.......
Bata karasa ba taji mari tassssss hamlat ma ta kara mata taaasssssss.
Gaba daya Ahlam ta gigice ta ko ina dukanta suke.
Hamlat nadukanta tana fadin"wai har er nan zata nama gwalo kuma na fada magana ta mayar min hmm yau maga bakin maganar da harshen gwalo."
Tun tana iya basu hakuri har ta daina sai numfashi kawai da take, Daga karshe ta daina numfashin.
Hamlat ta ce, "Ke Maamah ta mutu fa".
Maamah ta kara tabata taga dai ba alamun motsi.
Maamah tace kinga wallahi kuwa ta mutu toh nidai ba ruwqna sai natafi sai anjima.
Hamlat ta fara kuka tana fadin, "Maamah Dan Allah ki tsaya karki tafi ki barni."
Ko kallonta batayi ba tayi ficewarta da sauri.
Hamlat ta rasa me zatayi kawai sai kuka take.
Chan dai kawai ta dau waya ta kira Amaan awaya da dai har bazai dauka ba sai ya dauka.
Yna dauka tafara cewa, "Ahlam ta mutu wallahi bani na kashetq ba maamah ce kazo ka gani."
Amaan bai gama jin me take fada ba kawai yq katse ya hawo mota sai gida tuki kawai yake hankalinsa baya jikinsa.
Yana shiga ko ta kan Hamlat bai yi ba yadau Ahlam yana kuka ya nufi mota.
Cewa, "yake Ahlam dan Allah karki tafi ki barni inkika barni bazan iya rayuwa ba."
Ahaka har yakai asibiti.
suna isa likitoci suka karbeta .
Sai cewa, "yake wallahi bata mutu ba karku bare ta mutu inta mutu sai nqkashe kowa aduniyar nan."sai yasa kuka kawai
😰😰wannan page din ni kaina ya girgiza ni ba kai kadai ba Amaan.
URs preety xayyesherth
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬
*KUCHAKAR KISHIYA*
🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬
*ZAMANI WRITERS ASSOCATION🤝🏻*
__________________________
*we are here to educate,motivate, and entertain our readers.*
__________________________
*Story and Writing*
*by*
*Aysherth Mohammed Sani*
_(Preety Xayyeesherth)_
*Remain 5 pages to finish insha Allah*💃
*PAGE* 65
------------------------------------------------------------------------------------------
*WANNAN SHAFIN NAKINE AMARYA KHADEEJAERTH AHMED MUHAMMAD DEBERSH MARUBUCIYAR BADON SHI BA ALLAH YASANYA ALKAIRY YASA ZA AYI ASA"A TARE ZURI"AH DIYYIBA😍*
Dakyar likitan yasa Amaan yadan nutsu sannnan likitan yakirawo dadyn da hike likitan familynsu ne.
Ba jimawa sai ga dady,baba,dasu mama harda ma mumy.
Ita ko Hamlat tana gida ba abinda take sai kuka tayi nadamar rayuwarta gaba daya ta rasa meke mata dadi.
Da kyar likita yasamu ceto rayuwar Ahlam amman duk da haka bata farfado ba.
Dadyne yake tambayar Amaan , "wai meya faru ne."
Amaan yace, "Dady wallahi nima bansani ba kawai hamlat ce ta kirani ta fadamin amman ga dukkan alamu dukanta tayi."
Mumy najin hakan gabanta yafadi ras aiko suka hada ido da Dady.
Mama da baba dai basa cewa kome sai Allah yakyauta.
Hamlat ce tashigo cikin asibitin tana kuka."Amaan da Ahlqm dan ALLAH kuya femin wallahi mumyce tace mu ma ma ta duka ba kasheta mukuje yi ba."
Ta durkusa gabansa tana kuka mumy kuwa ta kasa sukuni.
Dady yajuyo ya kalli mumy rai abace yace, "Burinki yacika kin bata yarki da duk mugayan halayanki har ma tanaso ta fiki ke baki barni ba,baki bar yan uwa na ba
Naga alama kinaso hakuri na yagaza ko toh wallahi kibarmin gida nasake ki saki daya."
Yana fada ya ficewarsa a asibityn baba nakiransa ko juyowa bai ba.
Mumy kuwa tuni itama ta zube tana, "Dan Allah ku yafemin wallahi sharrin zuciyane daga yau nabar mugun hali ku basa hakuri dan Allah."
Mamace ta dagota tare da fadin,"karki damu yanzu afusace yake shiyasa kije gidan insha Allah zamu zo mu dauke ke."
Mumy tace,"toh nagode Amman dan Allah kuzo."ta tafi tana dan kukanta.
Hamlat ma haka mama da baba suka nuna mata cewa ai bakome amman duk da haka ta kasa sakewa jikinta na dar-dar.
Sai chan anjima dady yadawo inda yayi dai-dai da farfadowar Ahlam.
Hamlat sai kuka take tana Ahlam ta yafe mata.
Ahlam tace, "Aunty ki daina kuka ai ba wanda ya huce kuskure da tsautsayi kaddara tace dole sai hakan ya faru Allah ya yafe mana duka."
Gaba daya yan gurin Ahlam kara shiga ransu sai albarka suke sa mata.
Ba jimawa aka sallamesu tare da magunguna hamlat sai rawar kai take wa Ahlam shidai Amaan bayaso kawai kawaici yake dan da iyayensa agun.
Gidan Dady suka huce duka wanda kuwa baba ne ya bukaci hakan.
Salim ma sunji dan haka suka tawo tare da amarya Amrin.
Suna zuwa gida hamlat ce me hadawa Ahlam ruwan wanka harda taimaka matA taje toilet.
Kowa abin yabasa mamaki mussaman Amrin da Amaan suda suka fi sanin rashin mutuncin Hamlat.
Aha suka kasance har safiyar ranar.
Washe gari da safe.
Baba ya hada kowa da kowa a falo yayinda ya nemi da dady yadawo da Mumy domin bai ga amfanin hakan ba halinta dai inda sabo ansaba bare yanzu da tanuna alamum nadama.
Sannan yakoma ga Amaan,Hamlat,tare da Ahlam.
Yace, "banda abince wa gareka da yahuce kanunawa matanka adalci kar ka yadda ka fifita wata awajen watq nuna musu cewa duk kaunarsu kake,Hamlat kece Babba kamata yayi ki rike girman ki kinga abaya kinbarwa Ahlam girman ke kindau kankantar wamda bai kamata ba agareki yanzu inaso ki jajirce ki fito amatsayinki ta babba agidan miji tare da masa ladabi da biyayyah,kinga ita Ahlam banda abinda zance mata sai dai Allah yayi albarka sannan in muku fatam alkairy duka,domin tana da duk abin bukata ga mata ta gari sai sai dai ince ta kara,nadawo gareka Amaan kasani cewa yanzu matanka tarbiyarsu tana hannunka duk yadda ka tafi da su haka zasu tashi fan za akiyaye."
Bakaramin jin Dadi dady yayi game da maganar baba dan haka anjima mama da shi zasu je sudawo da mumy.
Hamlat ba abinda take sai kuka domin tasan ada tayi kucha kanci.
Hamlat tace, "Nagode sose ba sai yanzu nakara sanin cewa ni ce *KUCHAKAR KISHIYA* Ba Ahlam ba."
MAma tace, "aa ya'ta karki kara kiran kanki da wannan mummunan sunan domin ada ne kike haka amman ayanzu ke kamar kowace."
Tuni Hamlat ta rumgume mama tana mama nagode da ace ke nasamu amatsayin uwa tun farko da banyi kukan yau ba.
Baba yayi murmushi yace, "toh dai isa kome ma ya huce yanZu."
Ana gama tattaunawa dady da kanshi yamaida su Amaan gida .
Sannan yazo yadau mama domin adauko mumy.
Suna zuwa gidansu mumy iyayenta suka dunga basu hakuri itama ta kara basu tare da alkawarin ta chanja hali sannan suka nufo gida.
Su Amaan kuwa baki yakasa rufuwa sai washewa yakw wai yau shine da mata biyu kuma cikin farinciki.
Ahlam taki hutu suna zuwa tashiga kichin ai tuni Hamlat ta biyota tana nima gaskiya sai kin koyamin girki.
Ahlam tayi murmushi tace, "yoo ai aunty sai ma kinfini iyawa domin kinsam tsohon hannu yafi sabO."
Hamlat tace, "Ummm nice me tsohon hannun ko zaki sani."
Aha sulayi girkinnan cike da zolayar juna Amaan najinsu sai murmushi yake.
Bayan sun gama abincin rana sunci Ahlam ta nufi bangaren hamlat ta gyarasa tsaf sannan tace to aunty aje ayi wanka kinsan fa yau oga adakin ki yake."
Hamlat tace, "umm anya kuwa nifa kunya nke ji gaskiya kawai nabar miki shi yakara sati."
Ahlam ta rike baki tarw da fadin rufamun asiri ai sai yau oga yakaini kotu wlh bawani shima so yke yazo fa."
Hamlat tace, "haba dai?"
Ahlam ta girgiZa kai.
Hamlat tace, "bara nayi bani hanya kiga har ta shiga tace karki fita fa ki jira na fito kimin kwalliya."
Ahlam tayi murmushi ta jirata ta fito sannam ta dauko mata sabuwar abaya tasa ta mata daurin chakwai tare da simple make up dinta .
Hamlat ita kanta tasan tayi kyau sose kawai godiya tkewa Ahlam.
Ahlam tace, "yauwa toh aunty zauna yqnzu oga zai iso bara na fada masa munshirya."
Hamlat kawai murmushi tke domin ko ran aurensu batayi farinciki irin na yau ba.
Ahlam na fita taje ta durkusa gaban Amaan tana, "Kayi hakuri bansan ko na aikata abinda bai kamata ba agunka amman aguna dai dai-dai ne yau zaka koma dakN Auntyna Na fada matq kuma ta shirya kawai kai take jira."
Amaan yayi shiru yarasa mema zai cewa Ahlam .
kaji yaya plsss dan ni zakayi .
Amaan yace, "shikenan naji kuma nagode Allah yamiki albarka sahibty er aljannah."
Ahlam tayi murmushi ta riko hannuna tashi muje.
Amaan yatashi suna zuwa kwofar daki tasake shi ta kwankwasa sannan ta juyo da gudu domin tafiya dakinta hawaye ne fal a idonta kuma bataso Amaan yagani bare yadamu.
Dn Haka tana shiga ta fada kan gado tana kuka.
Shiko Amaan yashiga da sallamarsa...
*Preety xayeesherth*
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬
*KUCHAKAR KISHIYA*
🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬🥬
*ZAMANI WRITERS ASSOCATION🤝🏻*
__________________________
*we are here to educate,motivate, and entertain our readers.*
__________________________
*Story and Writing*
*by*
*Aysherth Mohammed Sani*
_(Preety Xayyeesherth)_
*PAGE* 66,67&68
------------------------------------------------------------------------------------------
*SADAUKARWA GA DUK MASOYAN HAMLAT*
Amaan yayi mamakin ganin Hamlat awannan yanayi hakan yasa kawai ya tsaya yana kallon ta,bai san cewa Hamlat kyakkyawa bace sai yau.
Hamlat tayi murmushi tare da kara sowa garesa da murmushinta ta ce, "Ayyah yayanah nasan dole zakaji wani iri yanayin da baka saba gani na ashi ba amman inaso kasancewa da , da yanzu ba daya bane."
Ta durkusa agabansa tare da riko hannunsa ta ci gaba da ce wa, "Dan Allah kayafemin ina me maka alkawarin cewa bazan taba komawa Hamlat din da ba yanzu A Amina ta nake Insha Allah baraka kara kuka dani ba ko na second daya."
Ta matukar ba Amaan tausayi mussaman da yaga hawayen da take zubarwa har yaji yamanta da rayuwarsu ada.
Hakan yasa yadago ta tare da share mata hawa ya rungumeta yana fadin, "Ai koda ace ke ba matata bace ke jininace bazan taba kinki ba Hamlat."
Ahaka suka kasance asabuwar rayuwa adaren ranar.
Ahlam tasha kukanta har ta gaji hakan yasa ta tashi ta dauro alwala tayi sallah sannan ta karanta Alqur'ani agurin barci yadauke.
Da asuba kuwa Amaan yazo ya kwankwsa mata kwofa ta tashi tayi sallah bayan ta idar bata koma barci ba ta gyara dakinta tsaf sannan ta nufi kichin.
Breakfast taje hada musu soyayyar doya tare da miyar kwai sannan ta musu farfesun kifi.
Tana gamawa ta shirya su tsaf akan dainin aiko ta gama shiryawa kenan sai kasu sun fito da murmushinsu.
Ahlam ta kasa hada ido da Amaan kawai murmushin dole take tace, "morning sahib and Auntyna."
Hamlat tace, "morning sister."
Amaan ya ce, "wai me gimbiyar ta shirya mana ne naji gidan duk ya dume da kamshi."
Ahlam tayi murmushi tare da fadin, "Umm kuzo muyi karya nidai inason nasha tea."
Tuni Amaan da Hamlat suka zo na.
Hamlat tace, "toh sister tunda ke kika girka ai kya bari ni yi saving din kinga anraba ladan."
Ahlam tace, "As u wish Auntynah."
Haka suka kasance cikin farinciki da begen juna hakan ya hana Amaan fita ko kwofar gida bare yaje office hamlat kuwa tadau hutun wata guda daman domin ta zauna Ahlam ta koya mata girki da gyaran jiki.
Ya kasance akullum yana cikin farin ciki da iyalansa har in yana office kullum burinsa kawai yadawo yatarar da gimbiyarsa Ahlam, Duk da cewa Hamlat ma tafara shiga ransa Amaan ba kamar Sahibtynsa ba.
Yau yakasance ranar asabar Amaan bai je aiki ba kuma adakin Ahlam yake hakan yasa Hamlat ta nemi alfarmar fita.
Amaan ko ya yarje mata domin kuwa intana gidan baya iya bajewa sahibtynsa asalin so da kaunar da yake mata domin gudun kar ta shiga damuwa.
Ba inda Hamlat ta nufa sai gidan su Maamah tana zuwa bata karasa shiga ba taji Mumyn Maamah na cewa, "Wai niko kwana biyu ina Hamlat neh."
Ai tuni hamlat ta tsaya chak.
Maamah tace, "Mumy ina zaki ga wannan matsiyaciyar ta nan ta kusa kisa,ai ni wallahi kawai ina daga mata kafa ne amman sai na auri Amaan domin tun randa nafara ganinsa nakamu da sonsa fatana kawai boko jum yadawo daga nema min maganin da yaje na aure abi nah."
Mumyn Maama tace, "Subhannallah wannan lamarin abun kunyan tare da shirka ba agidannan ba wallahi."
Hamlat ta rasa ta cewa sai yanzu abubuwa suke dawo mata daman ashe Maamah bason tsakani da Allah take mata ba?.
Ba ma bari tagama jin me suke fada ba tashige dakin tare da cewa, "Nagode da hallacin da kikamin Maamah kuma wallahi indai Amaan ne yafi karfinki sanin kanki neh."
Mamah tace, "mtswww aikin banza to se me?"
Hamlat ta yi murmushi sannan ta cewa mumy"mumy nagode da irin nasihar da kikemin da kuma nagyara hali Allah ya saka da Alkairi."
Tayi ficewar tah.
Bakaramin mamaki Hamlat taji bq hakan nr ma yasa ta kira mumy ta fada matA.
Mumy tace, "hmm Hamlat kenan ai gwada kema kingane da huri niko ina tare da makiyata kuma er uwata taji kusan shekara talatin da wani abu tana sani yin mummunan aiki ai kawai sai dai muce Allah ya yafe mana."
Hamlat tace, "Amin kam".
Suna gama wayar kuwa tayi gida.
Rayuwa ta cigaba da dadi agidan Amaan domin kuwa dukansu sunq bawa junansu kulawa yanzu har kwatance ake dasu domin hadin kansu tare da zaman lafiyansu.
Har yakasance duk inda zasu tare suke zuwa sai kuma an nemawa Ahlam admission a universty of jos tana digirin ta afannin computer science Hamlat kuma ta cigaba da zuwa gun aikinta.
Yau yakasance ranar monday kuma Amaan yanq dakin Ahlam tunda ya bugawa Hamlat daki da asuba bai koma ba dan hakq bai sani bsma ko ta tashi.
Har sungama shiri bata fito ba hakan yaSa Amaan yakara bugawa yaji shiru da karshe dai sai keyn gunsa yadauko yq bude dakin .
Hamlat kwance zazzabi ya riketa rawar sanyi kawai take.
Tuni Amaan ya kira doctor ba jimawa yazo.
Ya ma Hamlat gwaje gwaje alamu suka nuna cewa tana dauke da ciki wata biyu.
Ai ba wanda yakai Ahlam murna kin tafiya skul tayi ita zata kula da unborn babynsu .
Amaan ma yayi farinciki sose amman azuciya ynq fatan ganin jininsama daga bangaren Ahlam.
Hamlat kawai murmushi take.
Daga ranar kuwa kullum Hamlat sai sunyi fada Da Ahlam akan aikin gida .
Hamlat tace ai sai tayi , Ita ko Ahlam tq ce wallahi bazaki wahalar mana da baby ba kije ki hutA.
Amman duk da hakA Hamlat ba yarda sai tayi aikinnan bata bari ma Ahlam tazo ta tarar da aiki domin tasan farincikin Ahlam shine na Amaan shiyasa kullum koda bata jin dadin jikinta ta gwammace ta ta aiki dan kawai tasa mijintq farinciki.
Akullum in suna zaune ana hira sai Ahlam tace, "Auntynah karfa kizo kina min rowar babynmu domin aguna zai na huni sai barci da shan nono zai na kawoshi gunki."
Hamlat tayi murmushi sannan tace, "Ai babyn ma naki ne Ahlam bansan ran zan rani da ko yar da zan hafe ba."
Amaan ko yakance kullum dai maganar ku kenan.
Watan haihuwar Hamlat yakama kullum karatun Alqur'ani take tare da addu"o"in samu rahama .
Inko ana hira bata da abin fadan da yahuce yayana ka yafemin kanwata kema ki yafe min domin bansan ko zan tashi .
Tun Amaan da Ahlam suna maida abin wasa har sai yafara basu haushi.
Amaan yace, "indai ba so kike ki tarwaatsa mana farin ciki ba kidai na kawo mana zancen