Showing 75001 words to 78000 words out of 82249 words

Chapter 26 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf

ba kashe zhi za
tayi da.....
Malam ya katseta yace "Fatima khalifa ya rsu
kuma ba zai taba dawowa ba har abada, tunda
aka halicci duniya bbu wanda yataba dawowa
bayan ya mutu haka khalifa ma ba zai dawoba,
kin g kuwa idan hakane babu amfanin aci gaba
da tattaunawa da maganar, zai fi kyau miyi
hakuri, wannan al'amarin daya faru mu barshi a
matsayin kaddara, Dr. khalifa babu abunda za
muyi masa illa addu'a, Allah yaji kansa yakai
rahama kabarin sa, kuka da zaman damuwa ba
zai sa yadawo ba kuma ba zai goge abin da

ummi tayi ba, da ace zai goge ko yadawo mana
da khalifa da sai ai tayi, kiyi hakuri Allah yabaki
wani mijin.
*****
Tun a lokacin da kotu tagama yanke hukunci
ummi tafadi bata kara sanin inda kanta yake ba,
a bisa dole aka kaita asibiti tun tana numfashi
har ya kaance ba ta iya numfashi da kanta sai da
taimakon oxygen.
Kowa sai Allah wadai abinda ta aikata akeyi tare
da mamai mai tsanani, abinda yafi zama abin
mamaki shi ne yadda ummi ta tayar da hankalin
ta bayan mutuwar khalifa, ta fi kowa nuna
damuwarta akan mutuwar ta sa, tunda aka binne
dr. khalifa ummi take kuka ta rasa sukuni, kullum
ckin zirga zirgar masu taimakon ta don fidda
fatima daga zargi tare da binciko wanda yayi wa
khalifa kisan gilla, abin mamaki wai itace ummul
haba isin kisan, wannan shi ne a na zatom wuta
a makera sai ga ta a msaka.
Hakika fatima ta ba ma kowa mamaki ta bar ma
mutane abin tattaunawa kowa na fadin albarkacin
bakinsa ciki dai har da iyayan ita kanta ummin
ballantana wadanda suka haifi khalifa, mama ita
ke tare da ummi kullum tun kashe dr. khalifa har
yau ita tafi kowa sanin damuwar da ummi ke ciki
da irin kukan da takeyi a lokuta da dama ita
maman ce ke lallashin ummi amma ckin wani irin
yanayi ya bayyana cewa ummi ce ta kashe
wanda take kokawa mutuwarsa kukan da batayi
ba a lokacin da mahaifin ta yarasu, abin
tambayar anan shi ne shin me yasa ummi take
kukan mutuwar khalifa ? bayan ita takashe shi,
sbda bata son rayuwarsa a doron kasa a bisa
gurguwar hujja wai don ta rasa shi kowa ma sai
dai yarasa idan akace don ta yaudari mutane take
wannan kuka tana zargin daman asirin ta zai
tonu ne, kokuma ta yi abin ne don ya dameta,
shiyasa take kokawa kanta don ta san ta yi
babban kuskure da ganganci a rayuwarta. To
koma dai meye Allah kadai yasan dalilin kukan
ummi bayan kisan datasa aka yiwa dr. khalifa da
kanta.

Ga ta nan dai a bisa gadon asibiti batasan inda
kanta yake ba, karkashin kulawan jami'an tsaro,
likitoci sun bada sakamakon binciken dasukayi
akan ummi cewa damuwa tasa tashiga wannan
halin, akwai yiwuwar tadawo normal akwai
yiwuwar tarasa ranta, sbda tsananin damuwar
datake ciki yayi yawa.
Mahaifiyarta hajiya hauwa ce me jinyarta,
hankalinta a tashe sosai yake sbda yadda ake
yayata labarin a kafafen yada labarai na jihar har
da makota, tayi kuka ta yi kuka har ta ba uku
lada, ba a barin kowa ganin ummi sai dai tasa
ummin a gaba tana kuka, tunda aka kawo ummi
bata taba farkawa ba, numfashinta yahau ya
sauka sai dai wani lokacin tana motsawa kamar
za ta farka sai kuma tacigaba da barcin da in
barda ana ganin numfashinta sai kace ta mutu
,kunyar mutane yasa hajiya hauwa ba ta iya fita
ko ina batasan yadda za ayi ta iya hada ido da
iyayan khalifa ba, dansu kwaya daya ummi ta yi
sanadiyar barinsa duniya sbda wani hujjarta mara
tushe ballantana makama.
Tuni dai yan sanda sun sami nasarar chafke
matashin nan me suna yaya wanda ya tabbatar
shi yakashe dr. khalifa da hannunsa a bisa
umarnin ummi, bai wahalar da shari'a ba ya
amsa laifin sa har yayi magana da yan jaridu
cewa ai dama kawo kansa hukuma ne kawai bai
yi ba amma zaman jiran kamu yake tunda shi da
kansa ya bayyanawa duniya ta yadda al'amarin
yakasance kuma yabari aka ga fuskarsa to ai ya
yi talla da laifinsa knan.
A gdansu khalifa abin ya zamo tamkar na
jajantawa yadda jama'a suka dinga ta zuwa
bayan 'yan jaridu dake zuwa neman labari, Abba
na iya magana da 'yan jarida ita kam mama
wannan al'amari ya dawo mata da mutuwar
khalifa sabo fil a zuciyarta, tayi kuka ta yi kuka
kukan da bata taba irinsa ba a rayuwarta, jama'a
na bata hakuri tana fadin, "ku kyaleni in yi kuka
abin kukan ne ya sa mun, ummi ta cuci kanta me
yasa ta hau dokin zuciya.
Wasa wasa lamarin mama tadaina barci tsabar

takaici ne fal a zuciyarta, dan na su kwara daya
shi ne don masifa sai da aka salwantar.
Wannan daran ma zama tayi daram a dakin abba
tazuba tagumi tana kallonsa yana barci ita kuwa
ta kasa tayi juyi ta yi juyin shiru, ta gaji ta tashi
tazauna hawaye wani na bin wani, tadunga tuno
yadda al'amrin yakasance bayanmutuwar khalifa.
A DAREN FARKO
39
UMMI takan zauna tana kuka kamar ranta zai
fita, watarana mama ta isketa a zau? e a harabar
gdan tana sana'ar ta ta, mama tace "ummi ya ya
kika fito nan kina kuka? kowa yana kallonki duk
kukan na ki ya wuce ckin gida sai kinzo waje.
Ummi tace "mama wai ba ni da dalilin kuka ne?
duk wanda yashigo gdan nan abin mamaki ne
don ya ganni ina kuka? Wallahi mama tun daga
ranar da aka sa khalifa a kabari har yau har nima
in mutu ba zan daina kuka ba.
Mama tace "haba ummi a matsayimmu na
musulmi dole mu dogara ga Allah a bisa kaddarar
da Allah yadora mana, ni ce fa na haifi khalifa wa
ya fini sanin ciwon sa? a cikina ya rayu nayi
nakudarsa na raine shi, bbu wanda zai nuna min
son khalifa tunda na hakura na karbi kaddara ya
dace kema kiyi hakuri.
Ummi tadago jajayen idanunta tadubi mama tace
"na san da haka mama amma kin san wani abu
daya, kuna kukan rashin khalifa ne don ku kuka
haife shi nikuwa kukan danake daban ne da zan
iya bayyana miki wani gagarumin sirrin dake
zuciyata da daga yau na san ba za ki kara cewa
indaina kuka ba mama.
A wan? lokacin da ummi ta fadwa mama wannan
magana babu abunda tasa a ranta face sirrin da
ummi ke nufi bai wuce na soyayyar da take wa
khalifa ba.
Abba dake ta barci yamike zaune kamar an tashe
shi ya zubawa mama ido yace "maijidda wanan
tunanin zai ci gaba da hanaki barci a kowane
dare idan har ba za kiyi hakuri ba.
Mama tafashe da kuka tace "Alhaji ta yaya tunani
da damuwa za su fita daga xuciyata, wane irin

bakin ciki ne wannan?
Yace "kiyi hakuri Allah ne yakaddara kwanan
khalifa ya kare shiyasa suka samu nasarar kashe
shi, kuma da sukayi hakan meye meye ribar da
suka samu banda faduwa, tunda aka kai khalifa
kabari ummi bata sake samun natsuwa ba babu
abunda yaja mata hakan face hakki, haka shima
wanda tasa yayi kisan hakki ne yasa ya tonawa
kansa asiri da kansa.
To kinga lah za muyi wa godiya muyiwa khalifa
addu'a .
*****
Jiddah ce tadaga labulen dakin inna tare da
sallama, inna ta fadada fara'arta tace "maijidda
ke ce tafe da yamman nan, daga ina? zauna ga
kujera nan.
Bayan sun gaisa tace ina fati;a?
Inna tace "Tana daki shiga.
Ganin fati a kwance yasa tabata rai tace "wai don
Allah fatima sai yaushe za ki kwantar da hankalin
ki ki dinga walwala? dubi yadda kika rame kika yi
duhu kullum idanuwan ki ckin zubar hawaye har
sun zama jajaye fati me yai zafi haka?
Fatima tamike zaune tace "jiddah duk wadannan
abubuwan dakuke ganin laifina da rashin dauriya
na kune baku san ina dauriya akan su ba, jiddah
tun da nake rayuwa a duniya ban taba kwatanta
so ba sai akan khalifa, ko da cewa a baya na yi
niyyar auran musbahu na ami? ce ne sbda da
darajar iyayena amma ko sau daya ban taba jin
digon soyayyarsa a zuciyata ba, ni kadai nasan
asarar dana tafka wadda ba za ta taba mayar da
ko da kwatankwacin mijina ba ballantana fa
daidai dashi .
Jidda tadafa mata kafada tace "kiyi hakuri yadda
Allah yabaki khalifa ya amsa abinsa haka zai
musanya miki da wanda zuciyarki za taso,
lamarin na ubangiji ne babu abunda zai fi karfinsa
in dai bawa zai dogara dashi to ya isar masa.
Fati tace "jidda har ban san kalaman da zan yi
amfani dasu gun gode miki ba, kin yi namijin
kokari a gareni Allah yayi miki sakayya da
mafificin alherin sa na duniya da lahira.

Jidda tace "fatima godiyar nan ta isa na gamsu
Allah shi ne abin godiya daya nufeni da in yi
hakan da bai ba ni iko ba ban isa in yi ba, yanzu
wata alfarma nake son ki yi min.
Fati tace "ki fada jidda ko mene zan miki in dai
xan iya, kin fi karfin komi a gareni.
Jidda tace "sanin hakan danayi shiyasa nazo, a
safiyar yau din nan ne mahaifiyar ummi taxo tana
rokona in taimaka in zo in roke ki ki je asibitin da
ummi ke kwance ki dubata domin ta farfado
amma tana ta kuka tana rokon a kawo mata ke
da iyayan dr. khalifa za ta fada maku wata
maganar, dafarko nace da hajiya babu ruwana sai
nagata kama kuka tana rokon in taimaketa tace
wllhi jidda nima ba laifina bane ba ni da masaniya
ko ta kusa ko nesa game da abinda ummi ta
aikata,.
Fatima ta jinjina lamarin sosai a ranta, yanzu
kam a duniya ba ta da makiyin daya wuce unmi,
ji tayi kamar za ta hadiyi zuciya ta mutu sbda
bakin ciki me za tayi da wadda tarabata da
masoyinta, kai hakika ummi ta gama cutar ta har
me za ta gaya mata.
Babu yadda ta iya da jidda tana ganin kimarta da
yawa don haka ya amsa mata cewa za ta, ta
sanar dainna da malam suka mata izinin zuwa,
dogon hijjabinta me hannu da nikab tasa ravon ta
da fitowa waje tun ranar da aka sallamo ta daga
kurkuku, hawaye suka dinga zuba daga idonta har
suka iso asibitin., a lokacin taga mama suma
suka iso su biyu jidda takira hajiyar ummi a waya
tace dasu sun zo tafito tashiga dasu dakin da
ummin take.
Duk yadda zuciyarsu ke cike da tsanar ummi da
bakin ciki sai da jikinsu yai sanyi, sakamakon
yadda suka ga ummi ta yi wata muguwar rama
kamar an sauya ta, ta yi baki ta fita daga
hayyacinta, babu wanda yazauna sun kame ne
suna kallonta.
Ummi ckin rawar murya hawaye wasu na bin
wasu tace "Abba, mama, fatima na gode kwarai
da kuka danni zuciyarku kuka zo nan, na bukaci
zuwanku ne don kuga halin danake ciki kafin Allah

yakarbi rayuwata, domin ni tawa ta kare ba zan
kai labari ba ba kuma so nake ku tausaya min ba
don ni ba abin tausayi bace,
kuyi hakuri masu karatu a littafin babu page
47-51
Kwanan ummi goma sha shida a gadon asibiti
karkashin kulawar lokitoci da jami'an tsaro
tarasu, bayan aman jini ta hanci da baki data yini
tanayi saita dinga sai tadinga zabura tana gwara
kanta da bango tana ihu, "Na cuci kaina, shi ne
kadai abi? da bakinta yake furtawa har tadaina
numfashi, lokacin da labarin mutuwarta yazo
kunnan fatima ta yi kuka har sai da zazzabi da
ciwon kai suka rufeta..
*****
Wai shin masu karatu kutambayeni ina musbahu
yashiga mana? ku biyoni kuji.
Lokacin da musbahu ya tabbatar ya rasa fatima
sai ya kaddara a ransa cewa dama ba matarsa
bace, .
Musbahu gdan kawun sa malam habibu yafara
zuwa ya sanar dashi abinda yafaru, kawun ya ji b
dadi a ransa amma ba yadda za ayi in dai mutum
mai hankali ne da adalci babu yadda za ayi yayi
wani zargi akan malam da inna don sun rike
musbahu tsakani da Allah, Allah ne bai kaddara
fati rabonsa bace.
Musbahu ya shaidawa malam cewa zai tafi garin
bauchi gun yayar mahaifiyarsa ne sbda yana so
yayi nisa da kano a dalilin ba ya so yaga daurin
auren fatima.
Karfe biyar da rabi na yamma yashiga gdan
goggo mairo dake ckin garin bauchi tayi mamakin
ganinsa tace "ango na amarya kaine tafe?
Yace "Gwoggo ina wuni mun sameku lfya.
Tace "lfya kalau yashi kaje dakin au sagiru yana
nan yana barci kayi wanka kayi sallan xan aiko
ma da abinci idan kaci sai kazo mu gaisa sosai.
Sagiru kusan sa'an musbahu ne shi ne dan
goggo na biyar ya biyo mata biyu maza biyu,.
Tun a ranar yafara devewa musbahu kewar
damuwar dayake fama da ita, sbda mutum ne me
ban dariya, da alheri ga son mutane.

Musbahu ya bayyana masa abin da yarabo shi da
kano, sun tausaya mai sosai ganin damuwar
dayake cki yasa nan take goggo tace ga diyarta
nan hafsa in dai yana son ta ta ba shi, musbahu
yayi dan jim bai ce komi ba, goggo tace "ko bata
yi maka bane in dai ba ka son ta babu dole.
Yace "ba haka bane goggo ina tunanin yadda
malam yace ya bani fatima tace ta amince sai da
na saki jiki da ita nabata amanar soyayya ta
sannan tace ba ta so na, dr khalifa take so shi ne
ra'ayinta nikuma ra'ayin iyayanta, nayi mata
uzuri cewa ba ita ta zabeni ba niyyar biyayya ga
iyaye tayi .
Gwoggo mairo tayi murmushi irin nasu na manya
tace "musbahu duk wannan abinda yafaru
kaddara ne Allah ya hukunta cewa ba matarka
bace, idan xa ka lura duka kwana nawa yarafe a
daura maku aure khalifan ya bayyana, da ace
matarka ce ba zai bayyana ba ko ya bayyana
kuma ba zaiyi tasiri a zuciyarta takalle shi da
sunan so ba.
Ba wai ina gaya ma hakan ne don kaso hafsa ba,
in kana raayin hafsa ga ta nan in ba ka ra'ayi
kayi zamanka har Allah ya baka wadda kake so.
Musbahu yakara dukar da kai yace "wallahi
goggo hafsa tafi karfin namiji yaki ta, in ta
amince dani ma ta yi min alfarma domin ta girmi
ajina.
Goggo tace "karka sake fadar haka kaje gareta ku
daidaita kanku, Allah yatabbatar mana da alheri.
A cikin sati biyu musbahu da hafsa suka fahimci
juna, yasameta yarinya mai sauki da son mutane
kamar mahaifiyarta, ga ladabi da biyayya, kowa
ya yi farin ckin wannan al'amari a dangin su, nan
da nan aka tsaida magana babansu hafsa yace
zai ba musbahu aron gda su zauna kafin su koma
kano, ba wani kudi musbahu yakashe ba illa iya
abinda yayo sai da goggo tai masa fada cewa
daya suke dashi da hafsa a gdan nan.
Bayan wata guda aka daura aure sukayi biki
sosai suka kashe kudi, musbahu har mamakin
gatan da suka nuna masa yake, aka gama biki
lfya aka kai amarya dakinta, a ranar da zai shiga

dakin ne yadinga tunanin abubuwan daya tanada
zaiwa fatima a ranar da aka kai masa ita, ashe
ba matarsa bace yanzu haka tana chan da
angonta ta ma manta dashi shikuwa yana fama
da ita a zuciyarsa.
Sai da yadinga addu"a Allah yataimake shi
yarabashi da tunanin fatima kada ya cutar da
hafsa sbda ya lura hafsat ta yi dammarar zaman
aure dagaske tare da biyayya, ckin ikon Allah
yataimake shi yasamu natsuwa a zuciyarsa
yamaida hankali sosai gun kyautatawa matarsa
sukayi zamansu lfya kowa yana sha'awar auran
na su.
A DAREN FARKO
40
Kusan watanni shida knan da rasuwan dr. khalifa
an dan samu cgaba a rayuwar fatima sbda ta fara
rage damuwa har ta shiga wataislamiyya nakusa
dasu da akeyi alhamis da juma'a, ta kuma fara
tunanin komawa makaranta a halin yanzu ba ta
da aminiyar da ta wuce jidda koda yaushe suna
tare itama jiddan bata koma london din ba ta
dawo da karatu? ta BUK tana karanta mass
comm. kasancewarsu tare da jidda ya taumaka
kwarai gun debewa fatima kewa sai dai har yanzu
idan tatuno dr. khalifa takan yi kuka mai tsanani
sbda soyayyar da take masa tayi mata yawa a
zuci, shi yasa yau da jidda tazo mata da wata
magana sai da taji kanta yana mata tsawa.
Ta zubawa jidda iso kawai tana nazarin fuskarta
bata katseta ba sai da taji tayi shiru sannan
tamike zaune tace "jidda maimaita abinda kika
gaya min yanzu.
Jidda tabata rai tace "kina nufin baki ji abinda na
gaya miki ba?
"Na ji ina so in kara ji ne.
Jidda tace "cewa nayi yayana usman ya aikoni in
mika mai kokon bararsa gareki da fatan za ki
amsa mai bukatarsa.
Fatima tayi ajiyar zuciya tace "ni kam jidda na yi
mamaki danaji wannan maganar a bakin ki, na yi
zaton ko yaushe ke nake gaya wa cewa babu
wani namijin da zan iya sawa a zuciyata in haka

ne kuwa bai dace ki zo min da batun wani namiji
ba.
Jiddah tace "Fatima kin san dai ba zai yiwu ki
zauna babu aure ba don dr. khalifa ya rasu dole
sai dai kiyi hakuri ki amshi kaddarar da Allah ya
hukunta miki yarda da kaddara shi ne cikar
imanin musulmi mumini.
Ko kusa fatima ba ta jin dadin hirar don haka
tace "To na ji ba ni lokaci zanyi tunani.
Ganin yadda fuskar jidda ta nuna rashin jin dadin
maganar tasa tace "kiyi hakuri jidda ba cewa nayi
ba na son dan'uwanki ba wlh zuciyata ce ke cikin
matsanancin hali har yanzu karfin hali nake ni
nasan abinda nake ji game da ciwon kisan da
akayi wa khllifa, ,na kasa sabawa da wannan
damuwar, duk namijin danace xan aura a yanxu
na cutar dashi domin ba zan ba shi kulawar data
dace in bashi ba, wannan shi ne dalilin dayasa na
fidda batun aure a zuciya ta, zan yi zamana haka
har lokacin da Allah zai karvi rayuwata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login