Showing 18001 words to 21000 words out of 82249 words

Chapter 7 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf

bai sonki da kansa ita
za takalli kyautatawar da kike mata ta tursasa
shi ya aureki, kin san son uwa shi ne son d'a,
Hajiya hauwa tace "wannan shi ne hanya mafi
dacewa.
Zuciyar ummi fari kal san da tagama sanya
kayanta suka nufi gdansu khalifa, .
A bisa hanya hajiya sauda atana ta wassafa
mata yadda za tai amfani da damarta duk san da
take dashi don jan hnkalinsa.
Ummi jin ta kawai tana dura mata a zuciyarta,
daga alhajin har hajiya maijidda sun nuna jin
dadin zaman ummi a gdan daman fada ne ba na
so nayi a samu matsala in ba haka ba in ba haka
ba idan hauwa da duk yaranta sukace za su
zauna a gdan nn, rikesu xan iya insha Allahu.
Daki guda aka warewa ummi a gdansu khalifa
kusa da na mama, akwai gado da dressing mirror
da toilet acikin dakin, tun a ranar da taje gdan
aka gama wannan mama maijidda tace da ita

'"gdan nan gdanku ne kin sani ki dauki kanki fiye
da yadda kike rayuwa a gdan iyayanki, duk abinda
kkeso akwai su idan ma babu kada kigawa kowa
kigaya min in har da kudi za a siye shi zan saya
miki ummi.
Batazo gdan nan dan cutar da khalifa ko iyayansa
ba dan haka za ta nemi soyayyar khalifa a bisa
hanya ta gaskiya da tsakani ga Allah.
Ta tashi tabude kofar sakamakon kwankwasawar
dataji ana yi, daya daaga ckin yan matan dake
aiki ne tace da ita,
"Mama ta ce in zo in ce miki an gama sanya
abinci a tebur kifito kici.
Ummi tace "ki ce ina zuwa. Har yar aikin ta tafi
ta kirata tace "meye aikinki agdan nan?
Tace wanke wanke wani lokaci ina yin girki.
Ta jinjina kai tace "wa ye yakedafa abincin da
yaya khalifa yake ci?
Tace"yana da kyankyami bai yarda da abincin mu
ba shi da abbansa mama ke dafa musu abinci sai
dai mu tayasu shirya tebur kawai
Tace "yanzu ya dawo?
Tace "eh yana falon dasuke cin abinci shi da
iyayansa.
Cikin zumudi ummi takoma daki gaban katon
madubi ta tsaya tana kallon surar jikinta, daga
sama har kasa tana tmbayar kanta shin tana da
tagomashin da zata iya jan hnkalin namiji kamar
khalifa?
Tafito falo cikin yauki khslifa yana zaune kusa da
abansa kan kujerar zaman mutum uku sanye yake
da bakar kot, da wandonsu.
Zahiri da badini khalifa ya yi kyau ba na wasa ba
kamar yadda yake kyau a idon kowacce mace
ballantana ummi data mutu acikin soyayyarsa.
Ta gaidasu gaba daya, kallo daya shi ma khalifan
yayi mata yamaida kansa ga jaridar da yake
dubawa kafarsa daya tana kan daya, mama ce
tace dashi khalifa ga kanwar ka nan ummi ta
dawo gdan nan da zama.
A nan ne yadan ajiye jaridar akan cinyarsa yakalli
ummi suka hada ido yayi mata murmushi
takaitacce yamaida ganinsa ga mama yace "ya yi

dai dai hakan kinga kin samu mai tayaki zama.
Tsigar jikin ummi yadinga tashi sakamakon
murmushin khalifa da ta gani kuma ita yayiwa
murmushin.
Karfe taran dare khalifa yatashi yawuce dakinsa
ya kara yin wanka yasauya zuwa blue din jeans
da farar t shirt yazuba wani mai tsadar takalmi
ga farin gilash dan siriri ya manna ya fesa turare
yadawo falon da iyayansa ke zaune yarusuna daf
da abbansa yace"abba ba ni aron makullin
motarka za ni unguwa in dawo.
Ba musu yazaro key din ya damka masa yakalli
mama yace "mom sai na dawo.
Ta sha kunu sosai tace ina za ka a wannan
daren?
Yadubi agogo yace "mom wani abokina zan duba
a asibiti da asubahi za a tafi dashi egypt.
Tarasa abinda za tace sai kallo tabisa dashi har
yafice kamar yadda itama ummi ta lalace kan
kallon sa.
Tabdijam ashe jan aiki ne a gabanta
**********
Khalifa bai dawo ba sai biyu da rabi na dare,
yana shiga dakinsa yafada bisa gado bacci yai
awon gaba dashi .
Da sassafe ummi tariga kowa tashi agdan tayi
wanka tatsala ado za tashiga kitchen sa'ar da
tayi ita gwanar iya girki ce da kwalliya ta yi cos
din wadannan abubuwa guda biyu a gun
hajiyarta.
Mama tafito wurin karfe bakwai d rabi tana shirin
hadawa abban kayan tea sbda fitar da zaiyi
dawuri, sai taji kamshin girki ya game dakin.
tashiga kitchen suka hada ido da ummi tarike
baki tana murmushi tace 'oh sannu da himma
ummi irin wannan kamshi hka?
Ummi tatsuguna tana murmushi tagaida tace
"ummi ke za kidinga girki a gdan nan, girki ba zai
hanaki bacci ba a lkcn da kowa ke hutawa ko yan
aikin nan a yanxu haka suna chan suna bacci
idan ba abban ne zai fita da wuri ba sai karfe
gomaake gama abinci sannan aci.
Ummi tace "mama ai daga wannan rana dana

dawo gdan nan da zama insha Allahu ruwan
shayi ba za ki sake dafawa da kanki ba sai fa in
ba na nan, kuma yau ma na tashi da wuri ne jin
abban ya ce zai fita dawuri.
Mama tagyada kai tace "ya yi kyau lallai na san
za ku shirya da yayanki khalifa don yana son
abinci mai dadi.
Gabanta yadan fadi tayi murmushi kawai.
A kwanaki shida da ummi tayi a gdan kafin
tafiyarsa germany sai da tayi kokarin da khalifa
yake kulata a kalla yana amsa mata gaisuwa
cikin fara'a har yakan ja ta da magana a wasu
lokutan.
Ranar laraba da asuba ta kama tafiyar khalifa
germany a daran talata bai shigo ba sai sha biyun
dare yan can wurin abokansa da yamatansa da
sunan sallama.
Mama tana zaune a dakinta ita kadai bayan ta
idar da sallar shafa'i da wutiri da casbi a
hannunta, ummi tashigo da food flask a hannunta
tatsuguna gaban mama tace "mama yaya khalifa
ya ce amala yau yakeso da miyar kubewa ya ce a
gama da wuri, na yi masa tun magriba ga shi har
yanzu bai dawo ba.
Mama tace "na yi zaton ma kinyi bacci dama tun
dazu kina falo jiran khalifa? lallai baki san gararin
khalifa ba, idan yaga dama in yazo yaci idan
baiga dama ba cikinsa.
Tace "mama ko dai injira in ya ce bazai iya ci va
ya yi sanyi in dafa mai wani abun.
Mama tace "habadae sai kace kin zamo baiwarsa,
tashi ki mayar da abincin falo kitafi ki kwanta.
Ummi tadawo da flask falo maimakon taje
takwanta sai ta zauna tayi tagumi a daidai
wannan lokaci shi khalifa na daki tare da ramcy a
yau ta kare mai gida taviyo shi har gdan ubansa,
kamar yadda tasha gaya masa ta ce "duk abinda
zai faru in dai a kaina ne ta dauka ba gudu ba ja
da baya.
Khalifa ya rasa yadda zaiyi da ramcy yau ta rikice
msa yini guda yayi a gidanta tun safe har dare
bata barshi ya motsa ba amma da dare yayi bai
san yaya akayi ba har ta biyo shi a motarta ba,

sbda shi kansa a yau ckin natsuwa yake sbda
alhinin rabuwa da gda ba wasa bane tun safe
jikinsa yake a sanyaye dan hka yinin dayayi a
gdanta ma ba abinda ya iya aikatawa sai
kwanciya tana kallonsa kawai.
Sa'ar da yayi shi ne lokacin da zata biyo shi ta yi
shigar mutumci ta sa dogon hijjabi mai hannu
har kasa yana shiga da motarsa itama tasa tata
motar mai gadi zai mata hayaniya kasancewar
dare yayi kuma bai taba ganin motar a gdan ba
khalifa yace yakyaleta bakuwarsa ce.
Suna shiga daki yarufe ta da bala'i yace "ni za ki
walakanta haka? baki san uwata da ubana suna
gdannan ba? me kike son a daukeni dakika
biyoni, toh abinda xan gaya miki shi ne na barki
kin shigo nan dakinnan ne don kar inyi hayaniya
dake a waje wanda bai san abinda ake ciki ma ba
yasani, ki tashi kikoma inda kika fito...
Sai tayi wuf takamoshi tarungumeshi kam kam
tana masa kiss, wannan ne dalilin dayasa khalifa
ba ya hada ramcy da wata dan wata hanya ta
kan shawo kan namiji ta sani komi fushin da yayi
kuwa, tace "khalifa me na rasa ne? meye
mahaifina bazai iya mallaka min ba a rayuwa? sai
kai kai ne kadai mahaifina bai da ikon yamallaka
min sbda kudi bazai siye ka ba to yaya zanyi da
raina khalifa?
Jikin khalifa yayi sanyi kwarai da gaske bai taba
tausayin wata diya mace irin yau ba, musamman
yadda take me kuka da hawaye.
Dai dai wannan lokaci ummi ta gaji da zama a
falo tana takaicin ace khalifa bai ci wannan
abincin ba yadda tzauna ta tsara shi hakan yasa
ta kasa juriyar tafiya ta kwanta ta zuba abincin
ta jera a plate tanufi dakinsa tunaninta shi ne
tabar masa a dakin nasa tunda tana da makullin
dakin shi da kansa yabata sbda yanajin dadin
yadda take gyara masa komi a dakin a tsaftace.
Tana isa kofar dakin tasa makulli ta bude, abinda
tagani yasa gabanta mugun fadi, yaya khalifa
rungumeda mce tana sanye da hijjabinta, bayan
Runguma ba wani mummunan abu da ummi
tagani amma duk da haka sai da abincin

hannunta yasubuce ya tarwatse a gun takoma
ckin gida da gudu tana haki, wani abin takaicin
tahadu da mama a falo za ta sashen abba.
Gaban mama yafadi tatsare ummi da tambaya,
hnklin ummi yatashi tarasa abinda za tace wani
karya za tawa mama, mama tawuce tabarta jiki
na tsuma.
Khalifa ture ramcy yayi yace shkan hnklinki ya
kwanta kin tona min asiria gdan mu ko?
Za tayi magana yadaka mata tsawa yace, "kawai
kifita idan kikaci gaba da tsayuwa anan komi zai
iya faruwa dake tunda asirina ya tonu ba na
fargabar komi dn haka kama gabanki.
********
Karfwme dayan dare tayi khalifa ya kasa
runtsawa, ganin da umi tai masa rungume da
mace ya tayar mai da hnkli matuka bai san wani
irin kallo yarinyar za ta ci Gaba da yi masa ba a
yadda take ba shi girma shknan ta daina ganinsa
da kima bayan wannan za ta iya gayawa mama
daga nan maman za ta iyasa wa ai masa aure da
diyar da maman ke son ya aura itace 'yar
aminiyarta mai suna ummi.
Yamike cikin tsananin mutuwar jiki cikin sanda ya
kwankwasa dakin ummi a hnkli ya san dai da
wahala su abba su ji.
ummi tamike ckin tsoro tace waye?
A hankali yace ni ne khalifa, dasauri tamike ko
kayan bacci yau bata sa ba, kayan jikinta ne
hijjabin datayi sallah, ta tsaya jikin bango tana
kallonsa, cikin kakkausar murya ta jaruman maza
yatsare ta da idanunsa.
A wannn lokaci hnkalin ummi yai matukar tashi
yace "ummi
Murya na rawa ta amsa yace me ya kaiki dakina
dazun?
Tace abinci kawai naje kai maka na ga ka jima
baka dawo ba ni kuma ba na so yakasance baka
ci abinci ba sbda tun azahar na shiga kitchen
nahda maka shi.
Ya danna mata harra kamar zai shaketa yace
'damaa a dakina nasaba cin abincin?
Sai dai na zo ne dan in gargadeki dan kisani kada

wani yaji kinga wata mace a dakina.
Idan kuma naji ko da wasa wani ya furta ta ko
shakka babu na san ke kika fada, saiki saurari
matakin dazan dauka wanda ba zai taba yimiki
dadi ba.
Sannan maganar soyayya tsakani na dake bbu, ni
ba sa'anki bane, idan naji kince da mama ko
abba ko wani cewa kina sona xa kisha mamakin
matakin dazan dauka akanki, idan wannan ce
gulmar da kika dakko kikazo gdan nan da ita
sbda ni to kikoma don ba xa kiyi nasara ba, yaja
tsaki cikin hushi yafice daga dakin.
*******
Tabdijam su duka biyun bbu wanda yayi bacci a
wannan dare, abinda yadaga hnkalin kowa daban
kowa tunaninsa daban.
Bayan fitar khalifa ummi tatashi ckin tashin
hnkali tayi kuka kamar ranta zai fita tadubi agogo
karfe biyu da minti ashirin bata ga nisan dare ba
takitra mahaifiyr ta a wannan dare tana kuka
wayar a kashe, hajiya sauda itama a kashe, takira
babbar aminiyarta jiddh bata kashe waya ba,
jiddah tadauka a figice tana fadin "inalillahi wa
inna ilaihir raji'un. tadaga wayar abinda tace shi
ne "ummi waye yamutu?
Musanman kukan dataji ummin na rusawa kamar
ranta zai fita, tace ni ce na mutu jiddah mesa
kuka ban kwarin guiwar in so wanda ba zai so ni
ba?
Jiddah tayi ajiyar zuciya tace "ummi yau
kwananki nawa a gdansu khalifa?
Tace "shidda.
Ta j tsaki tace "gaya min abinda yasa kika kira
kanki matacciya gashi kina raye.
Cikin sanyin murya ummi tabayyanawa jidda
abubuwan dasuka fru a wannan daren, jiddah tace
"kin ban kunya da hushi ummi kuma kin kashe
kanki a wurin khalifa.
jiddah tace "ummi ita nasara tare suj tafiya da
hakuri, tunda khalifa tafiya zaiyi abu daya yarage
miki shi ne kiyi kokarin yin abinda zai matukar ba
shi tausayi tyadda idan yaje jamus abin zai tsaya
masa a rai, .

Khalifa na sanye da bakar kot ya tsuke sosai
fuskar nan ba fara'a ya sha kunu, mama tana
dakinta ko fita batayi ba, ummi ta bishi dasauri
ta tsaya daga baya a langabar da kanta a jikin
bango tana kallon khalifa yana taku dai dai.
Lokacin dazai shiga motar ne ya waiwayo sai
karaf kuwa suka hada ido da ummi, sai yayi cak
yana kallonta bai shiga motar bazuciyarsa
tashiga harba wa, ganin haka sai ummi tadaga
hannu sama da nufin tana masa addu'a kuma
tashiga yi masa bai bai da hannu tashiga ckin
gda da gudu.
Khalifa yafada mota abbansa na kusa dashi
direbansu yahaya yaja motar zuciyar khalifa ba
dadi abubuwa da dama suka cunkushe masa a
zuciya.
Tausayin ummi suka kamashi har suka isa filin
jirgin saman malam Aminu kano hannunsa biyu
tallafe a kumatunsa, abubuwa da dama suka
tsaya mai a rai, abokansa da yammatansa ba
wanda bai nunawa tsananin damuwa ba ama ba
wanda yatsaya mai a rai irin ummi.
Ya kwana yanajin zafinta a ransa a tunaninsa ma
yarinya karama dako secondary bata gama ba
tatsaya gaban namiji tace tana sonsa.
Lokacin dazai shiga jirgi yarike hannun
mahaifinsa yace "abba kayi min addu'a zan bar
kasar nan cike da kewarku zuciyata ba dadi.
Abban yarufe me baki yace "a duk lkcin da mutum
zaiyi tfya abinda yake tsirga mishi shi ne abinda
yafaru lkcn rabuwarku.
Kamar yau danazo maka rakiya insha Allah kamar
yau xanzo taryarka in dai muna raye.
Kazauna da kowa lfya kaji tsoron Allah gun
muamularka da mutane sannan kariki gskiya da
amana ba za ka tabe ba kuma ba za kayi asara
ba insha Allahu
Duk dauriyar xuciya irin na namiji khalifa sai da
yashiga jirgi yana goge hawaye abbansa yabishi
da kallo yana murmushi

A DAREN FARKO
10

Ummi tagyara zama tare da jan dogon numfashi
tace "jiddah khalifa ya tafi ba tare da na amfana
da zaman da nayi a cikin gdansu ba, face bacin
rai da mugun gani da idanuwa na suka gani.
Jiddah tabata rai tana yimata wani irin kallo tace
"wai me yasa kika fiye gaggawa ne ummi, anya
za ki rinka cimma nasara a kan abubuwa, idan
kika dubi tsarin khalifa gaba daya da yadda kike
ba abu ne mai sauki ba mallakar zuciyarsa sai
anyi da gasken gaske.
Ummi tace "to in banda abinki jiddah tawace
hanya zan samu nasara idan nayi hakuri, kada
kimanta fa shekaru hudu khalifa zaiyi a germany
kafin yadawo kasar nan, yana chan Ina nan zan
iya jan hankalinsa jiddah, dole xuciyata takaraya,
ke bari in gaya miki wani abu daya da ban yi
zaton zan gayawa wani ba, ina cikin gdan nan fa
ina kokarin jan hankalinsa na ganshi da mace
rungume a jikinsa a dakinsa, idan zan iya jan
ra'ayinsa zai kawo mace gdan nan ina cikinsa?
Jidda ta ja dogon tsaki tace "daman kina
tsammanin ko khalifa a karan kansa yake sonki
za ki rabashi da yammata ne, namiji irin khalifa
ko baice yana son 'yanmata, za su yi tabinshi tun
bai kula ba watarana sai ya kula, don hakama
shawarar da zan ba ki itace idan kinyi nasarar
mallakar khalifa to ki sanya hakuri mai yawa a
zuciyarki akan 'yanmatan da za suyi ta bibiyar
khalifa don ba namijin mace daya bane.
Ummi tajinjina kai tace "tabdijam hakika zan
girgiza kowa a kan khalifa ba zan hada miji da
wata ba, ba zan yi tarayya da wata macen a
dakin khalifa ba.
Jiddah takyalkyale da dariya tace "ummi manya
har khalifan ya zo hannu da za ki wannan cika
bakin.
Ta lumshe ido tace "kuma fa hakane maganar
dakika fada ne naji kamar har na mallake shi na
ji tsananin takaicin hadashi da wata da zanyi a
sunan kishiya .
*************
Malam musbahu yana cigaba da karfafa
zuciyarsa ga kaunar fatima tare da tattalin farin

cikinta sai dai ba ya samun hadin kanta sbda
tsananin kunyarta, ba ta iya sakewa dashi hakan
yasa tadaina sakewa a gidan duk abinda take
idan yashigo sai taji kamar za ta nutse a kasa
don kunya hakan na takura shi shima don ya fi
son tasaki ranta auyi soyayyar da za su fahinci
juna kafin lokacin auransu.
Ranar laraba da safe inna ta tursasawa fatima
kaiwa musbahu abincinsa a kokarin innar na
ganin sun shaku ta fuskar soyayya kamar yadda
tafahimci basu sake da junansu ba, fatima ba ta
son shiga dakin musbahu sbda maganar soyayya
da yake mata na daga mata hankali alhali bata
saba ba.
**********
Lafiya kalau khalifa yasauka a kasar germany
inda zai zaman karatun likita ,har yanzu damuwar
daya taho da ita daga nigeria yana makale a
ransa ga kewar iyayansa tamkar bai taba tafiya
ba sai a wannan lokacin, yana shirin shiga motar
dazata kaishi masaukinsa kamar daga sama yaji
an rike mai hannu, yajuyo dasauri yazu bawa
yarinyar ido, Anisa? Yafada cikin shakku dan ba
shi da tabbacin ko daidai yafada sunan.
Tayi murmushi tace "amma na ji dadi daka iya
kiyaye sunana.
Yace "nikam mamaki nayi dana ganki a kasar nan
yaushe kikazo?
Tace "sai mun zauna zan ba ka labari yanzu muje
naga masukinka ko za ka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login