Showing 21001 words to 24000 words out of 82249 words

Chapter 8 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf

fara zuwa ganin na wa
masaukin?
Yace "ah ba komi inga waya ba sai mun tafi ba.
ta langabe kai tace "kada ka sanyaya min jiki
bayan na yi farin cikin ganinka kayi murnar
ganina.
Yace "hakika na yi farin cikin ganinki domin ina
bukatar abokin debe kewa a wannan kasa da
nazo.
Tace"to kayi hakuri mutafi mana.
Yace "to muje.
Sashensa daban a gdan da zai zauna, falo guda
daya da bedroom ba dai wani girma bane amma
akwai kayatarwa, kitchen kamar na mace sbda

tsaruwar da yayi shi kansa saida yayi sha'awar
ace yanada matar aure wadda za tarika dafa
masa abinci irin na mamansa, wadda yayi mugun
sabo dashi, a zaman da yayi da mamansa bai da
matsalar komi ta fuskar abinci duk abinda yakeso
shi ake masa, duk yawonsa da gararinsa bai iya
cin kowani abinci sai a gdansu sbda shi mutum
ne mai kyama da kuma son cin abinci mai dadi
duk dadin abinci bai iya ci sai a gdansu ko a
halin yanzu yunwa sosai a cikinsa bai san yadda
zai yi ba tunda bai iya girki ba ko ruwan tea bai
iya dafawa ba, hakan yasa tunda ya zube akan
gado bai kara motsawa ba dan ko takalmansa
anisa ce tazare masa.
Tana zaune daf dashi tace "khalifa bayan gajiya
kana tre da damuwa kataimaka kagaya min.
Ya lumshe ido yace "Anisa ba za ki iya magance
min matsalata ba shi yasa nace kar ki biyoni, ba
za ki ga walwala ta ba a wannan lokacin.
Ta marairaice kamar za tai kuka tace "dan Allah
kafada min Abbakar.
Yace "Anisa yunwa nakeji kuma ba za ki iya dafa
min irin abincin dazai gamsar dani ba.
Ta bushe da dariya tace "Abbakar idan yau ban
dafa maka abincin daya gamsar dakai ba to mata
na rako duniya, kuma har yanzu bakasan wacece
ni anisa ba, ko ka san cewa sbda na ji labarin
kana matukar son abinci mai dadi na shiga
fafutukan koyon girki ko ta ina?
Ya fiddo ido yna kallonta, tamike tace banga
tazama ba kafin kagama nazarin maganata bara
in dafa ma abincin.
Ido yabita dashi har ta fice yamaida idonsa kan
rufin dakin.
A wani party suka fara haduwa wanda wasu
dalibai suka shiga sbda nishadi, a lkcn bata dade
dafara xuwa mkarantar ba, tana zaune tare da
kawarta nafisa, suna hira wasu samari suka
tskoanesu har nafisa za tayi magana anisa
tahanata tace "kyalesu dan mu kulasu ne zo mu
bar gun.
Za suci gaba da binsu shi kuma khalifa yana
kallonsu ya aika a gaya wa wadannan samarin su

shiga hankalinsu su kyale su anisa ko yasa a
musu tsirara a gun, samarin wanda sakon yafito
daga gareshi yasa sukayi nasu gurin, ya aika
akira mai anisa.
Mamaki yakamata jin ance wai wani ne yake
kiransu kamar wasu 'ya'yansa taduvi dan aiken
tace "kaje kace a za mu zo ba. ..
Nafisa tayi saurin rufe mata baki tace kinsan
waye Abbakar muhammad? zo muje kawai.
Anisa tace "to me zai mana da har zai ce muzo?
Idan wani abu yakeso garemu mai zai hana shi
yazo da kansa? kai je kace bazamu zo ba.
Dan aiken khalifa yace "idan kika kara furta kalma
mara dadi akan maigidana zanje in gaya mai idan
kuwa nagaya mai daga wannan rana kin daina
farin ciki a wannan makarantar.
Ga dukkan alamu ita kawarki ta san shi ke kuwa
bakuwa ce shiyasa nayi miki uzuri.
Anisa takara fusata sosai za tayi magana nafisa
tarufe mata baki ta ja hannunta tace zo muje.
Har anisa ta dage akan ba ta zuwa sai kuma taga
bara taje taga abinda wannan mai gadarar yake
takama dashi tabashi mamaki.
Khalifa na zaune kan kujera tare da abokansa,
Anisa da Nafisa sukazo gabansu, Nafisan ce tayi
musu sallama ita kuwa anisan bakinta ne yayi
nauyi duk abinda nayi niyyan fada masa ya
gagara sai ido data bishi da shi.
Yayi murmushi yanuna musu gun zama yace
"kuzauna 'yammata.
Bata san sanda tazauna ba, gayen ya gaji da
haduwa ya yi mata ya burgeta anya kuwa ta taba
ganin matashi mai kyaun wannan a rayuwarta?
Tun daga wannan rana suke gaisuwar mutunci da
shi da abokansa, zuciyar Anisa ko yaushe a cike
yake da kuncin son khalifa batasan yadda za ayi
tasamu soyayyar ta sa ba, hatta nafisa duk yadda
suke ba sa boyewa juna sirrinsu amma ta kasa
gaya mata .
Lokacin dataji cieon so na neman hallakata ne ta
sanar da nafisa halin datake ciki, tayi dariya tace
"haba sister na san halin dakike ciki boye min din
da kikayi ne yasa na nuna miki ban sani ba.

Tace ni dai na ji ina mafita? Anisa kai tsaye
zance ba za kisamu khalifa ba, ba za ki iya
mallakarsa ba sai dai in Allah ya sa ravonki ne
amma sai kinyi hkuri mai nisa kafin kicin ma
nasara, kada kifito kigaya mai kina sonsa saidai
kici gaba da hakurin bin wasu hanyoyi dan kija
ra'ayinsa.
Anisa taci gaba da binciken rayuwar khalifa daki
daki me yakeso da wanda bai so, har a gdansu,
abinda yatsorata ta shi ne mata dayake
mu'amula da su sannan ba shi da niyyar aure.
Lokacin daya kammala karatunsa na Bayero duka
shekararta biyu a nata karatun, anan ne
hankalinta yatashi sosai ganin bbu hanyar da
zata kara ganinshi kuma tashiga binciken ina
yasa gaba a rayuwarsa, aiki zai fara ko ci gabada
karatu, bata samu cikakken byani ba sai da aka
dade tana fama da azaban ciwon sonsa a
zuciyarta, tadagawa mominta hankali akan sai an
maidta kasar germany ta karsa karatunta acan,
momin tadube ta cike da mamaki tace "ke kuwa
sbda me?
Kasancewar nisa ce diya tafari a gun mahaifiyarta
kamar kawa da kawa haka suke bata iya boye
mata duk wani sirrin daya shafeta ko meye shi,
taciro wayarta tanuna mata hoton khalifa tare da
bayyana mata halin datake ciki a kansa, tace
"momi tsawon shekaru biyu zuciyata ta rayu ckin
azabtacciyar soyayyar har wani lokaci inaji a
raina kamar mutiwa zanyi idan ban mallakeshi
ba, mom ba zan iya rayuwa bbu khalifa ba ke
kadai ce za ki iya min wannan taimakon.
Hnklin mmin yatashi sosai ta tausaya wa Anisa,
ta jima tana kallonta sannan tayi ajiyar zuciya
tace, "Anisa ba zan ga laifinki ba dan kin kamu da
soyayyar wanda kikeso tunda ba mutum ne yake
dorawa kansa so ba kuma zan yi iya kokarin inga
burinki ya cika.
Zan sa abanku yashirya maki zuwa germany
kiriga khalifa zuwa, zanyi ta binciken tafiyar shi
da saukar shi a kasan, inaso ki kasance a filin
jirgin lkcn dazai sauka domin kibashi mamaki,
dan zai sauka ckin kewar iyaye da abokansa Na

gida tabbas sai ya yi farin ckin ganinki.
Abu guda daya zan rokeki Anisa shi ne kitsare
mutuncinki, kada kiyarda soyayyarsa tasa kibiye
mishi ya lalata miki rayuwa.
Ta gyara zama tace "mom ban taba kallon khalifa
da wata manufa ba mara kyau burina shi ne
muzama miji da mata, ba zan iya bata rawana da
tsalle ba akan khalifa.
Mom tayi murmushi tace "anisa duniya fadi
gareta abinda kika sani shi kika sani wanda baki
sani ba baki sani ba, na san mutumcin soyayya
kuma ina darajata, ni ce mace ta uku da mahaifin
ki ya aura kinsan da wannan ko?
To ina mai tabbatar miki da cewa ni ce mace
tafarko daya fara so a rayuwarsa".

ries
: A DAREN FARKO
11
anisa tafiddo ido tace "to momi me ya hana
yafara auranki har sai da ya auri su hajiya da
mama?
Momi tayi murmushi tare da girgiza kai tace
"Anisa tun ina 'yar shekara goma sha daya
mahaifinki yake so na, so ba na wasa ba tun
muna ganin d wasa yake har kowa ya amince so
yake min na gas*iya,yadinga hidima dani, duk
abinda yasami niyake ba mawa, hr na kammala
secondary dina lokacin aurena ya zo knan ba na
kula kowa.
Lokacin daya tuntubi babana da mganar aurenmu
lokacin na yi candy sai yace ydaka ta masa sai
ya yi shawara da 'yan uwansa, hnklin abbanku
yatshi yanuna min damuwarsa akan haka nace
yayi hakuri na san babana bazai ba mu matsala
ba.
Ahe kuwa matsala na tare damu domin babana
biris yayi har takai ga ya kira abbanki yace
yadaina zuwa guna dan kuwa ya yi min
miji,munga tashin hankali abban ki Ibrahim a
wannan rana domin kuka da hawaye yadi? ga yi
yana rokin abbana yayi hakuri yarufa mai asiri
kada yacuce shi da chan ba a hana shi ba sai

yanzun, ba afi sati ba babana yadaura min aure
dawani d'an d'an uwansa wanda yace shi yzaba
min a matsayin miji.
Wannan abu yajefa abban*u cikin matsanancin
tashin hnkli domin kuwa ba karamin so yake min
ba kowa ya san da wannan.
Hakan yasa yan unguwa akayi ta zagin babana
ana cewa bai kyauta ba anci amanar ibrahim,
wannan ne dalilin dayasa mahaifiyar ibrahim tayi
fushi tazo har gida tana gayawa babana bakaken
maganganu yace da ita ai ba maryam ce kadai
diya mace a duniya ba, bai ba wa ibrahim diyarsa
ba ai ba wani yahaifa masa ita ba, idan anyi
hushi ta aurawa ibrahim mata biyu koma hudu a
rana daya shi ne zai tabbatar ita mai zuciya ce.
Ai kuwa abinda yafaru knan, hajiyar ibrahim ta
nemo mai 'ya'yan aminanta biyu itace hajiya
hauwa uwar gidan abbanku ta yanzu da hajiya
hafsa dakike ce ma mama.
Ibrahim yayi namijin kokarin ba wa mahaifiyarsa
hadin kai dan kada yakunya ta ta a idon duniya
ganin walakancin da akayi mai a kaina,ya amince
da auran hauwa da hafsa wadanda aka daura
auransu rana daya aka fara kai hauwagdan da
hajiyar ta sa tagina mai daga bisani bayan sati
daya aka kai hafsa ,yayin da ni kuma bayan wata
daya da daurin aurena da Aminu aka kaini gdan
iyaynsa dake bayan layinmu.
Na yi kuka na yi bakin ciki mara misaltuwa sbda
ko ido ba na sn in buda in ga Aminu.
Sai daga baya zance yabayyana cewa mahaifin
Aminu ne yake bin babana wasu kudade masu
yawan gaske yabukaci yabashi abinsa ba shi
dashi, mahaifin aminu yace "tunda lokacin
damuka yi za kabiya ya yi kuma babu to sai dai
kabaiwa Aliyu auran maryam in ba haka ba kuwa
zaiyi kararshi ne kuma nan take dole yabiya sa
kudinsa, yace wadannan kudi in dai yabada
maryama to sune a matsayin kudin aure da
kayan lefe, sadaki kawai zai biya a daura aure,
hnklin babana yatashi sosai sbda ya san dai da
kunya yahana ibrahim auran maryam lokaci daya
yabawa Aminu bayan lokaci mai tsawo ibrahim

yadeba yana hidima da maryam tabbas ya san
sai duniya ta zageshi, yayi duk tunanin dazaiyi
dan yasamu mafita bai samu ba, kudi kuma bai
da hanyarsu, hakan yasa yarufe idonsa yana
takaici yaba Aminu aurena, lokacin daya ga
damuwar goggona ya yawaita ne yasa yagaya
mata yadda akayi shi ne nikuma tagaya min.
Hakan danaji yasa zuciyata tadan sosu tadamu
na tausayawa babana domin ko yaushe tunanina
shi ne yadda babana ke son ibrahim meyasa
yahana shi aurena rana tsaka ,bayan babana
mutumun kirki ne ba mutum ne mai kwadayin
abun duniya ba.
: Shekarata biyu a gdan Aminu kowatan bata ban
taba yi ba, shi da mahaifiyarsa suka shiga min
walakanci suna cewa ba na son Aminu shiyasa
naki yarda in haihu, ni kam ina iya kokari na duk
da ba son Aminu nake ba ina mai biyayyaya
shikuma yana wahalar dani kasancewar ba wani
mutumin kirki ne sosai ba halayyarsa ba masu
kyau bane.
Watarana ina kwance a dakina yace dani "in fita
inje gdanmu ya sakeni ba zai iya cigaba da zama
dani ba, ba ni da wani amfani sai inci inyi kashi,
natafi gda na fadawa babana daya tuntubi
mahaifin Aminu kan maganar sai yakama fada
yana cewa kar a gaya mai zancen banza mana
maryama ce tahura wa Aminu wuta sai ya saketa
gar da yi masa gori cewa ita ba shi takeso ba
kuma tunda an yi masa haka kudinsa dinnan dai
sai an biyashi tunda baiga amfanin auran
maryama ga aminu ba, babana yace bai isa ba
tunda dai yakafa sharadi kuma anyi auran a bisa
sharadin daya kafa zancen kudi kuwa babu shi
sai dai in kara zaiyi.
Momi tadan yi shiru tana kallon fuskar anisa
wadda tazuba mata ido tana mamakin labarin da
take ba ta tace,"to momi yaya akayi har kika auri
babana?
Momi tace "Anisa hakika abbanku ya san darajar
soyayya kuma ya mutunta kaunar dake tsakanina
dashi; ahaifin Aminu yayi karar babana yace sai
ya biyashi kudinsa tunda dai diyarsa maryam ta

ki zama da Aminu, kiri kiri alkalin nan yagoyi
bayan mahaifin Aminu bayan ni da baba na mun
bayyana a kotu yadda abubuwa suka kasance wai
sai alkalin nan yace sai na kawo shaidar mutum
daya kwakkwara wanda zai min shaidar cewa
Aminu ne yasake ni da kansa ba ni nace yasakeni
ba, nace banda shaida sai Allah dan shi ne
masanin dukkan abubuwan dasuka faru,, alkali
yace dole sai babana ya nemo kudin Aminu ya
biyashi lamarin daya tayar da hnklin kowa a
gdanmu har kuka sai da babana yayi, kwasam
Allah mai iko bayan kwana biyu dayin hakan sai
ga abbanku ibrahim ya zo gun babana yakawo
mai kudin da sukafi wanda baban Aminu yake
binsa, mamaki yakamashi da kunya yarasa
abinda zai ce, Ibrahim yace karka damu baba ni
fa kaunar dana kewa maryam Allah kadai yasan
iyakarta, duk abinda yashafe ni ya shafeku, Allah
ne bai kaddara itace matata tafarko ba shiyasa
abubuwan dasuka faru suka faru.
Babana yabiya baban Aminu kudinsa kuma yace
bai yafe masa ba, ina kammala idda aka daura
aurena da Ibrahim, ban cika shekara daya ba na
haifeki a cikin shekarata ta uku a gidan nan na
haifi kaninki mahmud, kuma a wannan shekarar
ne Allah yadaukaka arzikin mahaifinku wanda
izuwa yanzu shi da kansa bai san abinda ya
mallaka ba.
Har yanzu iyayena ba su da abin Kauna kamar
ibrahim kamar yadda nima ban iya hada shi da
kowa, abinda nakeso inkaiki gareshi guda daya ne
Anisa mahaifinki dani kaina mun san martabar
soyayya muna mutunta ta.
Mahaifinki ya nuna min kaunar da ban taba jin
wani da namiji dayai wa mace halacci irin wadda
ya min ba ko da kuwa a labari, shi yasa ban
wasa da duk abinda yasha fe shi.
Duk da kasancewarsa adali a tsakanin matansa
amma kowa ya san soyayyar dayake nunamin ba
karama bace shiyasa hajiya da mama suka
tsaneni to amma ba su da ikon komi akaina sbda
sanin halayyarsa.
Wlh Anisa ni kadai ce matar da zan tunkareshi da

kowace irin bukata yayi min ko baida ra'ayi don
hka zan umarce shi da ya shirya miki tfya xuwa
kasar germany don ki karasa karatun ki a chan.
Anisa ina rokon ki kiji tsoron Allah a wannan
tafiya da zakiyi kada kija min bacin rai,duk rintsi
duk wuya kada ki lalata rayuwarki idan ban gani
ba Allah ya gani ki min alkawarin tsare mutuncin
kanki.
Anisa tace "mom na maki wannan alkawari insha
Allahu.
Kowa yayi mamakin batun tafiyar anisa har kasar
germany da sunan karatu tun da babanta dai ba
shi da wannan ra'ayin ko babban dansa da hajiya
hauwa tafara haifa anan kasar yake karatunsa na
jami'a hakan yasa aka dauki hassada aka daura
akan anisa amma dan ita abin bai dameta ba
cikar burinta ne kawai damuwarta har a ranar da
za tabar gida nigeria zuwa jamus batun mominta
guda daya ne.
"Anisa kiji tsoron Allah kada ki zubar da mutuncin
ki baki da takamar data wuce budurcinki a gun
mijin da za ki aura duk abinda zai rudeki kiji
tsoron Allah kada ki biye masa bbu inda zai kaiki
face ga nadama wadda zai sa kiyi ta kunkan da
ba ki da ranar dazaki daina, duk abinda d'a namiji
zai aikata a rayuwarsa ado ne mace ce a cikin
hadari da bakin ciki idan batayi taka tsan tsan da
rayuwarta ba.
A cikin jirgin anisa ta hada kanta da guiwa ne
tana tunanin wadannan maganganun na
mahaifiyarta wadanda suka tsaya mata a rai,
hawaye suka dinga zuba a idonta wani na bin
wani, taji tausayin kanta da iyayan ta jikinta yayi
sanyi sosai batasan yadda rayuwarta za
takasance a wannan kasa ba.
***********
Jiddah zaria
Babban magana wai namiji dasuna Hajara, anya
kuwa Anisa za ta iya cika wannan alkawari na
mahaifiyarta???? ni ma dai jiki na ya yi sanyi
amma dai ga mai fili ga mai doki........ karku gaji
dai kukasance kuna biye dani a baya ganin yadda
za takaya.... Ni ce dai 'yar mutan zazzau.

Hawwa umar. a.k.a jiddah zaria.
A DAREN FARKO
12
Kamshin da khalifa yaji ya halarci hancinsa yasa
yamike xaune yana kallon Anisa, tace "ga abincin
nan tashi kaci kayi wanka kayi sallah.
Ya fubi abincin cike da gamsuwa yace "amma fa
nagode Anisa kin fara ragemin damuwata zauna
kigaya min dalilin zuwanki garin nan.
Tayi murmushi tace "karatu nazo yi nima, rakiya
nayo wa wata kawata za tayi tafiya kamar daga
sama na ganka.
Yajinjina kai yace "na godewa Allah daya kawoki
daidai lokacin da zama ya kamani a nan.
Farin ciki ya mamaye zuciyarta ta fara jiyo
kamshin nasara a cikin muradinta duk da cewa ta
san akwai aiki ja a gabanta.
********
Ruwan sama akayi kamar da bakin kwarya tun
safe har gab da za ayi sallar azahar sannan
yadauke, garin kano yadauki sanyi mai dadi
kasancewarba sanyin takurawa jikin bil'adama
ba. fatima tagama shiryawa cikin atamfarta
maroon mai adon ja da fari, ta yi mata kyau
sosai tadauki littafanta za tafara karantawa inna
tadubeta ta ce "Ajiye littafin nan za ki yi ki kaiwa
hajiya maijidda wamcan man shanun na soyashi
tun daren jiya naso akai mata.
Ta dan bata rai tace "nikam inna ba na son shiga
wannan godan.
Inna tarike baki tace "me mutanan gdan suka yi
miki mutane masu kirki da mutunci wai ke
meyasa ba kya son mutane ne fatima?
Tace "ba haka bane inna kin sani duk abinda
mutum

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login