Showing 24001 words to 27000 words out of 82249 words
Chapter 9 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf
yakeyi ana kallonsa idan ina yawan zuwa
gdan karshe ace kwadayi ne yake kaini.
To a fada din mana "inna tafada a fusace sannan
tadora da fadin "idan har za kibiyewa surutun
mutane ba abinda za ki aikata a rayuwarki dan
duk abinda ka aikata din mutane ba fasa magana
za suyi ba.
Fatima ta dakko hijjabinta tasa ta dauki bokitin
man shanun tanufo gdan abba.
Hannu bibbiyu mama ta amshe ta suna zaune ita
da ummi a falo suna hira, ta tsuguna ta gayar
dasu tamika mata bokiti tace "Gashi inji inna.
Tace "Oh Allah sarki inna da hidima take na gode
Allah saka da alheri zauna sai anjima kya tafi ke
in kin shigo gidan nan sai kace ana korarki na
rasa sanda za kisaba da mutane fatima.
A haka ta dan zauna a darare sai kace akan kaya
tazauna, ummi tadubi ta da fara'a tace "fatima
kin iya kitso ko rannan naga na kan kanwarki
Aysha tace ke kikayi mata yaushe zanzo ki min
irinsa?
Tace 'idan kin shirya yanzu ma sai in miki.
Tace "yawwa kamar kin san kan yadameni da
yawa ina kuiyar saloon, tadkko kibiya da mai da
komi tace "xo mu shiga daki kimin ma yi hira ma.
Mama tayi murmushi tace "Ayi hira ko gulma idan
ba gulma ba me zai hana a yi kitson a nan falon
sai an shiga daki.
Ummi tace "mama wannan hiran ai ta sirri ce.
Tace 'gulma dai knan.
Fatima na mamakin jin dadin da ake a wannan
gida ita kanta ummi ace an shirya mata
kasaitaccen daki irin wannan, tfara mata kitso
suna hira tana ba ta labarin makarantar ta wadda
saura shekara daya ta kammala, ummi tace
"fatima amma idan kin gama za kici gaba da
karatunki ko?
Tace "a'a aure za ayi min in barda ma inna ta so
inyi candy ai da yanzu anyi bikina da malam
musbahu.
Ummi tace "ba dai malamin ajinmu na islammiyr
yamma ba.
Tace "shifa ai dan gidan mu ne.
Ummi tasake kallon fatima tana rayawa a
zuciyarta yaya za ayi yarinya tanada kyau na
garari irin wannan takare gun wani malamin
islamiyya.,kwata kwata fati ba ajin malam
musbahu bace, domin kyaunta yasa wasu har ce
mata suke beauty, dukda cewa ba ta da sakin jiki
da mutane ba ta ayyanar da tsabar kyaunta ta fi
zama da nikab a fuskarta amma dukda haka
kallonta ake ana zuzuta kyaunta, sbda zahiri
Allah yayi mata kyakyawar sura tadaukar hankali
da ace fati irin wayayyun 'yan matan nan ne
masu budaddan ido ba karamin kudin maza zataci
ba sbda in dai batun kyau ake fati ta fi gaban
kwatance abin sai wanda yagani, ita kanta ummi
aduk sanda tadubi fatima ji take kamar takwace
kyaunta, tabbas ace tanada kyaun fati khalifa bai
isa yace ba ya sonta ba, hankalinta bai kara tashi
da fati ba sai watarana dataje gdansu fatima ta
isketa ba dan kwali ta fito daga wanka tana taje
gashin kanta, ummi taga yadda bakin gashin nan
ya kwanta lanban a bayan fatima yana daukar ido
kamar irin yammatan indiyawan nan, ga kirar
jikinta abin sha'awa irin wadda ake cewa coca
cola shape, ita kanta ummi datake mace saida
taji tanason fatima sbda kyaunta kyaunta yayi
mata ga tadai yar talakawa ba wani kayan ado
dazai fiddo da itatake samu ba hakanan ta ki
tawayar da kanta ,duk da haka fati ta isa abar
kallo, kyaunta gdan wani hamshakin maikudi inda
za ta jiku da jin dadi lallai za ayi kallon mace
anan.
Bayan ta gama mata kitson ummi taja hannunta
zuwa kan dressing mirror tarike kugu tana
kallonta tace "fatima kinga acikin kayan
kwalliyarmu mata babu nau'in kalar da babu anan
na baki dama ki zabi duk abinda kikeso wanda za
ki dinga kayatar da kanki dashi gun ado, don
Allah fati ki sani jikinki domin inason kizamo
wayayyar mace mai ado za ki zama abar kallo
fati, Allah ya yi miki baiwar kyaun sura wadda
duk wata diya mace za taso ta mallaki sura irin
wannan, dan banga abinda kika rasa ba fatima.
Fatima tace "Nagode ummi da kaunar da kike
nuna min, sai dai ina son kiyi hakuri ba zan dauki
komi ba anan dan idan nadauka narabaki da
abinki ba zan yi amfani dasu ba.
Ummi tagyada kai tace "fati na fahimci kyamar
dukiyar nan gdan kike yi.
Fatima tace "haba ummi kada kiyi min muguwar
fahimta mana.
Ta tareta dasauri tace "me zai hana in fadi haka
ba muguwar fahimta bane gskiya nafada miki.
Ta girgiza kai tace "kiyi hakuri ba haka bane.
Tace "to in dai ba haka bane zan hada miki kayan
kwallia dakaina dan Allah kidaure kidinga amfani
dasu.
Tayi dariya tace " to na ji ummi amma dai zan
tunasar dake abu daya wanda kwalliya ana yinsu
ne dan afita kinga dai ni babu inda nake zuwa in
banda makaranta,kuma ba wasu maza ke zuwa
guna ba kinga dai ba su da amfani a gareni.
Ummi tace "to in banda abinki fatima shi malam
musbahun ba ya da bukatar yaga kwalliyarki,
gskiya kanki a duhu yake dayawa kibani hadin kai
in wayar miki dashi kada kiyi aure a cikin wannan
yanayin dukda kasancewar malam musbahu
malami ne amma xa ku iya samun matsala acikin
zaman auranku idan kika cigaba da tafiya a
wannan tsarin na ki, namiji dakika ganshi ko wani
iri ne yana bukatar matarsa tayi masa ado yana
bukatar matarsa takasance wayayya mai iya lura
da abubuwa na jan hankali, idan akace mazan
suke waje kadai za ayiwa ado banda na mazajen
aure hakika kwalliya bata biya kudin sabulu ba
knan, mace in har ta amsa sunan mace to tattalin
rayuwar mijin auranta take domin shi ne na ta,
wata kila kina ganin misbahu malami ne kuma
dan gdanku ne ba ya bukatar sai kin masa wata
kwalliya ta jan ra'ayi, wannan kuskure ne idan
ma ra'ayinki ne haka to kisauya domin misbahu
namiji ne kamar kowa rayuwar da zakuyi ta aure
tanada banbanci mai yawa da wadda kukayi a
gida, dole sai kin ajiye wannan kunyar da kke
fama da ita domin tuni na fahimci kunya itace
tahana ki sakin ranki ki zama wayayyiya mace,
idan nace wayewa ba ina nufin kizamo mara
kunya ba a'a kizamo mai wayewa ta fuskar
rayuwa, matukar baki bin wannan hanyar dana ke
son doraki a kanta ba, za kisamu matsala ba za
kiji dadin zaman auran ba.
Fatima tayi shiru tana tunanin abinda ummi
tafada mata, ummi taci gaba da fadin "kiyi nazari
sosai za kiganoinda nasa gaba, kinada kyau
fatima kyaunki kadai ya isa yamallaka miki da
namiji to amma fa masu iya magana kan ce in
kanada kyau ka kaara da wanka,, dan Allah kisaki
ranki da misbahu kidinga tsala ado sosai kina
tsayawa kuna hirar soyayya za kiga yana dada
rudewa akanki, a tunanina babu wani abun
Burgewa ga mace wanda yawuce mijinta na aure
yayi ta sonta ya kasance kullum hankalinsa na
kanta, matukar kuwa bata bi hanyoyin dazata rike
shin ba ba zata samu yadda takeso ba daganan
sai kiga anata samun matsalar rayuwar aure a
dalilin a dalilin hakan za kiga aure ba ya danko
kiyi taganin kananan zawarawa a gari, wadannan
abubuwan da matan mu na hausa ba sa kulawa
dasu suna taka muhimmiyar rawa gun lalacewar
zamantakewar aure.
******
A DAREN FARKO
13
Har fatima tadawo gida tana tunanin
maganganun ummi wadanda suka jefata a wasi
wasi amma tana karfafa kanta dacewa gaskiya ne
mamakinta shi ne yadda ummi tasan wadannan
abubuwan ba tare da ta yi rayuwar auren ba
ballantana tasan matsalolinsa da abubuwan da
ke haifar da matsalolin, koda yake kallo daya
inkayiwa ummi za kasan kanta a waye yake sosai
ta fuskar rayuwa haka karance karancen datake
na littafin hausa suna taimaka mata sosai nagano
abubuwa da dama da suke ckin rayuwar auren.
Fatima na zaune a dakin da suke kwana ne a
wannanlokaci da bai wuce karfe takwas na dare
ba sallar isha'i ta idar tadauko kayan da ummi
tahada mata na kwalliya tana dada kallonsu har
da kayan sawa materail ne kala biyu da
mayafinsu da fashions da agogi ga turarruka har
kala uku, kuma taroke ta idan gari yawaye
tadawo daga makaranta tazo zata rakata saloon
u gyara mata gashin ta, a dazun da wayo da
wayo sai da ummi taja hankalin fatima takai
la'asar a gdansu tana cusa mata maganganu na
jan ra'ayi don dai ta samu ta aminta da
maganganunta har sai da taci nasarar da fatin
tasaki jikinta take ba ta labarin yadda shi kansa
malam musbahu yake nacin son tadinga sakin
jikinta suna hirar soyayya tadaina gudunsa, tace
wani lokacin har tausayi yake bata idan yafaye
mata magiyar tayi mai hirar soyayya ko kaka ne
dan yaji sanyi a zuciyarsa, amma ina tsabar
kunya yasa ba ta iyawa, ko hada ido ba ta yi
dashi, ummi tace "kinji ko ? "
Tace "wannan idan baki bar wannan halin ba idan
anyi auran yagaji zai dinga kula wasu yammatan
ko yadaina baki kulawar dakike bukata kema.
Lokacin data dawo gida innarta rike baki tayi tace
"Tabdijam kece kika yini yau a gdan hajiyar ?
Tace "uhm ummi ce tatsareni da magana kinga
kayan ma data ba ni.
Inna taduba tayi godiya.
Fatima ta san cewa ummi na kaunarta kawai don
Allah, don haka tasaki jikinta da ita sosai tana
kokarin kwatanta abinda take gaya mata, tadaina
dari dari da ummin zama take suyi hira sosai
tazamo tazamo kamar irin aminan nan dasuka
jima da shakuwa da juna, ita kanta fatin ko
dayaushe idan takalli irin alherin da ummi take
mata da yadda tadamu da ita tana nuna mata
tsantsar kauna sai ta dinga mamakin kaunar da
take mata, yakasance ko yaushe ummi na gdansu
fatima ko ita tana gdansu suna hira, malam
musbahu yana matukar jin dadin kawancen
fatima da ummi sbda ta samu cigaba mai yawan
gaske a cikin rayuwar fatima, hakan yasa yake
mutunta ummi tazamo abokiyar shawararsa kan
abin da shafi fatima, duk abinda yataso ita yake
fadawa. ,kuma ckin ikon Allah sai ta nusar da
fatima hanyar data dace nan da nan abubuwa
suka dawo daidai kunyar nan ta fati duktazama
tarihi har tana iya caba ado tatsaya suyi hira
sosai da malam musbahu.
********
Yadda Anisa tashiryawa khalifa abincin safe hka
ta tsara mai na dare wanda yafi na safen dadi
yana can yana baccinsa ya iske an shirya tebur
sai kamshi mai dadi ke tashi tana zaune kan
kujera tana kallon wani fim da ake haskawa ya
dubeta yana mur. mushi yace "godiya nake ranki
yadade.
Tace "na fika farin ciki da yabawarka Abbakar dan
haka ni yafi dacewa in yi godiya gareka bisa
karbar bakunci na dakayi a gdan ka, idan ka
kammala zan koma masauki na abokaina na
karatu suna jirana yanzu muka gama waya dasu.
Ya rausayar da kai har yanzu da murmushi a
fuskarsa yace "bakiyi laifi ba idan kin tafi dole in
barki ki tafi domin bansan zan sameki ba na hadu
dake amma dai va zan ji dadin tafiyarki yau ba
me zai hana ki daure ki tayani kwana.
Ta lumshe ido tare da ajiyar zuciya takwantar da
kanta tana kare mai kallo lokacin daya zauna
yabude abincin yana fadin "A bisa ra'ayinki za ki
kwana a hidan nan idan gari yawaye sai muje
nima inga na ki masaukin, amma idan kinga da
takura sai muje yanzu ba na son inyi abinda xan
matsawa mutum.
Bai jira abinda za tace ba yafara cin abincinsa,
idanunta a lumshe taje tunanin abi ? da kwananta
a gidan zai haifar, har yau idan sunyi waya da
mominta rokon da take mata shi ne tarike
mutuncin kanta kada tayarda wani ya yaudareta
ya lalata mata kuka yaja mata abinda za tayi
kukan da ba ranar karewa., ance idan mace da
namiji suka kebenta a wuri daya su biyu na ukun
su shaidan ne, soyayyat da takewa khalifa ita
kanta har tsoro yake ba tazuciyar ta ta tsananta
da ciwon so mai zafi da tsanani shin akwai
abinda zai nema a gareta ta hanashi.
Bayan ya kammala cin abincin ya wuce dakinsa
ya zuba wasu kananan kaya da suka kama
jikinsa kam kam sun mai kyau abin har ba a
magana, kamshin turarensa ne yafara baibaye
Anisa kafin yabayyana gareta, hawaye suka taru a
ido? ta Allah ya taimaketa suka koma ba tare da
sun zubo ba amma duk da haka idanuwan ta
sunyi jawur zuciyarta ta kuntata tunda take
rayuwa da ciwon sonsa dake hana zuciyarta
sakat bata taba jin abinda taji yau yana mata
yawo a zuciyarta ba, hakan ne yasa tamike
dasauri tace "bari in dakko jakata muje in wa
sisters di na bayani sai mudawo.
Yanayin muryarta yakarantar dashi wasu
abubuwan game da ita, ko da yake yana sane
dacewa tana son shi duk wasu alamu ta nuna
masa ya dai ki nuna mata ya fahimci inda tadosa
ne sbda tausayin ta yakeji.
Ganin bata fito ba yasa yazauna kan kujera
kafarsa daya kan daya yana tuna watarana a b.
u. k aboki? sa bukhari ke ce masa "khalifa kafito
kanunawa yarinyar nan anisa ce ba ka ra'ayin ta
don tadaina wahalar dakanta son da take maka
ba kadan bane.
Ya ja tsaki yace "wai ku mesa ba kwa rabuwa da
gutsiri tsoma, ita anisan ce tace ma tana so na?
Buhari yace "kai da Allah kar ka raina min wayo
ka fi kowa sanin son da take maka idan kuma za
ka iya ba ta soyayyarka to kabata fuskar da za
ta bayyanar ma da abinda ke ranta.
Yayi murmushi yace "Buhari tausayin anisa nakeji
sosai a zuciyata, ban shirya batun aure ba ba ni
da ra'ayinsa idan nayi soyayya da ita naravu da
ita wahala za tasha gara tayi hakuri dani a yanxu
akan ta shaku da soyayya ta a gaba ta rasa ni,
shiyasa nake nuna mata kamar bansan abin da
takeyi ba.
Anisa ce takatse mai tunani lokacin data murda
kofar dakin tafito rataye da yar madaidaiciyar
jakarta tace "inaga ba sai mun fita ba na yi masu
waya sun taho nan din yanzu.
Yace "ba laifi.
Suka zauna shir7 kowa tunanin dayake kara kaina
a zuciyarsa, lokaci zuwa lokaci takan kalleshi
tashare kwallan dake taruwa a idonta, ta kagu
sisters dinta su zo tahuta anya za ta iya kwana a
gda daya da khalifa?
Namijin data kwallafa rai akansa take masa son
da batayi tsammanin anawa wani d'a namiji ba,
suka kirata a waya sukace ga su a kofar gdan
tamike dasauri taje tashigo dasu.
Fadilat da Ramat su ne abokan anisa wanda take
ji dasu komi na su tare suke aiwatarwa gida daya
suke zaune wanda yake kusa da makarantarsu,
amincewar da iyayanta suke nuna mata yake
tsoratata yasa take matukar kiyaye rayuwarta,
Fadilat da ramat suna rayuwar dasuke so da
samari? su yayin da ita ba ta da sakewa da
mazan.
Ita kanta anisan bata ji dadin irin tarbar da
khalifan ya yi wa su Ramat ba, ta dai daure
tagabatar dasu a gareshi sannam taya musu
cewa za ta taya shi kwana ne, basu jima sosai
ba sukace xa sukoma tabiyo su don yi musu
rakiya, suna fitowa fadila datake ta fi ramat zafin
kai ta hau ta da fada tace "dama haka Abbakar
din yake kika gayyato mu gdansa? kina sane da
cewa a rayuwata babu ab8nda natsana kamar
walakanci, meye dalilin na nuna mana isgilanci
haka?
Tace "kuyi hakuri nima banji dadin abinda yyi
mukun ba haka halinsa yake bai da son magana.
Ramat tace "halinsa yake bai da som magana
kuma to haka kike tsammanin za ki iya
mallakarsa, gskia anisa jikina ya yi sanyi da
yanayin khalifa dole ki sassautawa zuciyarki burin
da kika ci akansa.
Jikin anisa yayi sanyi tace "ina bukatar ku tayani
da addu"a xuciyata ba wanda za taso bayan shi,
fadila tayi tsaki tace "aikin banza wai dole sai kin
rayu da khalifa?
Suka tafi suka barta tsaye, ta jima a gun daga
bisani takoma ckin gdan, a nan falom data bars&i
ta tadda shi yana magana da iyayensa a waya
har sai da barci ya dauketa, bayan ya gama da
iyayansa yai tunanin ckin yammatansa wa zai
kira tadebe masa kewa, yanajin wani iri ne a
ransa zaman anisa a gdan ya taimaka masa
amma hakanan yake jin tausayinta ba zai iya
maidata abokiyar debe masa kewa ba yayin da
kudirin datake dashi a kansa ba zai yiwu ba.
Yakoma cikin daki yafidda kayan jikinsa yabar
gajeran wando kawai yahaye gado sai kuma
ummi tafado masa yayi murmushi yakira laila
daya daga cikin yammatan na sa, wayarta a
kashe, yaja tsaki yakashe wayar ya kama barci.
*********
Posting a yan kwanakin nan sai hakuri a dalilin
muna ta hidimar biki, duk yadda aka gani a
hakura da hakan.
A DAREN FARKO
14
GIDAN ainihin iyayan ummi yau hajiya saude tayi
ma tsinke ta iske hajiya hauwan tana shirin fita
tace "yanzu kuwa nake shirin kiranki a waya inji
ko kina gida in biyo ki min rakiya.
Saude tace "ai zuwa nyi inji labarin inda aka
kwana da batun ummi da khalifa, wai shin har
yanzu babu wani labari?
Hauwa tace "uhm wani labari ne ban da na
takaici saude? wannan yaron zai wahala mu
cimma nasara kansa yana da jin kan tsiya.
Saude tace "shi din banza, ke fa yadda uwarsa
taraba mu da dan uwanmu haka za mu rabata da
danta, ba za mu samu wannan damar ba har sai
khalifa ya auri ummi.
Hauwa tace "to tana can dai tana faman bautar
girki a gdan idan yadawo ma san abin yi, yanzu
kam sai hakuri tunda ba ya nan.
Saude tace '"duk da haka bai dace muyi kasa a
guiwa ba da safe ake kama fara idan mukayi
sakaci wankin hula yakaimu dare bazamu samu
yadda muke so ba.
Hauwa tazauna gefen gado tace "to me za muyi
yanzu?
Tace "gun boka za muyi duk abinda yadace a yi a
ja ra'ayin khalifa ga ummi idan ma ta kama
muhana shi zaman jamus din gaba daya yadawo
ya aureta ba