Showing 78001 words to 81000 words out of 257774 words

Chapter 27 - MUHIBBA Book Complete by Sameena Aliyou.txt

da kad’an idan muna bijiro mata da zancen har Allah zaisa mu dace ta bud’i baki ta sanar damu...!”
Ta k’arashe tana mai kuma k’ank’an da kai gaban Giwa...

Badon Giwa taso ba Ta mik’e tana mai ci gaba da duban Izzatu dake sakin murmushi cikin yanayin fuskarta da ya cika da datti da kuma daud’a....

Duban Jakadiya Giwa tai ta mata alama da cewa su fice... Babu musu Jakadiya tabi umarnin uwar gijiyarta...

Sam Muhibbah bata ankara dasu Giwa da tuni sun nufo k’ofa gadan gadan ba, hankalinta da tinaninta yayi nisa wajen tunanin shin wacece wannan mahaukaciyar, maiyasa Giwa ta ajeta a wannan sunk’urumin d’akin sannan mai take zuwa yi wajen wannan mahaukaciya... Ya kamata tasan wacece wannan mahaukaciyar....

Kaman daga sama taji alamun tab’a k’ofa babu shiri tai saurin komawa da baya k’irjinta naci gaba da bugu...

Giwa ce ta d’anja ta tsaya sanda taji tamkar akwai alamun mutum a wajen... Jakadiya ta d’ago tana dubanta, lokaci guda Giwa ke furta “Jakadiya, kin tabatta mu biyu ne a wajen nan bamuda wani d’an rakiya...?”

Jakadiya Ta waiga gefe da gefe kana tace “Rankishi dad’e mu biyu ne rak saiko Izzatu dake cikin d’aki...!”

Giwa Ta d’anyi Jim tana mai kuma karantar wajen.... Lokaci guda ta kaikaito sosai tana mai k’arewa d’akin Izzatu kallo... Babu shiri Muhibbah ta zame daga jikin k’ofar ta shige cikin d’akin dan tabbas idan Giwa ta matso sosai zata iya ganinta jikin k’ofar...

Giwa ta dubi Jakadiya tace “Jakadiya ban yarda babu kowa a nan ba mu koma da baya...!”

Babu musu Jakadiya tabi umarnin uwar gijiyarta...
Duk addu’an da yazo zuciyar Muhibba yinta kurum take.... Ta sadakar shikenan Giwa da Jakadiya Sun kamata, kaman daga sama taji an janyota Ta baya... Zuciyarta ta kuma tsinkewa sanda taga mahaukaciyar nan ne Ta rik’eta sosai ta b’oyeta k’asan gadon katakon da aka d’aureta bisa....

Tana jin sanda su Giwa suka dawo da baya suna masu k’arewa d’akin kallo na wasu dak’ik’ai... Giwa taceda Jakadiya ta bincika ko ina har k’asan gadon Izzatu...
Zuciyar Muhibbah ta kuma tsinkewa shikenan Sun kamata an gama... Tai saurin rintse idanunta had’ida toshe bakinta da duka hannayenta biyu...

Jakadiya na k’ok’arin duk’awa Izzatu tai tsalle Ta mak’uro Jakadiya tanai mata wani irin duka wanda da kaga mai yinta kasan babu hankali a tattaredashi...

Giwa ta Wato ido waje don basusan Izzatu likamau tayi ba ashe dai ba d’aure take ba... Bugun Jakadiya take tamkar wacce aka aikota bataji bata gani...Jakadiya na sakin k’aran azaba...
Giwa kanta saida ta firgita da irin bugunda Izzatu keyiwa Jakadiya tasan ko shakka babu idan ta gama da Jakadiya kanta zata hauro tunda ba hankali bane jikinta...

Ai tuni Giwa ta soma jada baya Jakadiya na fad’in ta ceceta... Inaa Giwa ko takan Jakadiya batabi ba ta fice da baya da baya tana waige waige... Da k’yar da mak’yark’yata Jakadiya ta samu ta k’waci kanta hannun Izzatu ta fito a guje babu shiri amma kam ko shakka babu Ta daku irin bugun da akewa dawa idan an ciro daga gona...
Haki kurum Jakadiya take d’ankwali a hannu haka ta nufo waje tana gumi da haki had’ida d’ingishi...

Suna ficewa Izzatu ta duk’a ta yaye mayafin k’asan gadon nata yanda Muhibbah ke b’oye ciki....

Jikin Muhibbah ya d’auki rawa ganin irin bugunda taiwa Jakadiya kardai itama ta lallasa mata nata bugun... Saidai ga tsananin mamakinta murmushi ta sakar mata kana ta mik’a mata hannu alamun tana jira ta mik’o nata hannun ta fito da ita...

Dukda rawa da jikin Muhibbah keyi hakan bai hanata jarumtar mik’awa mahaukaciyar nata hannun ba... A hankali take janyota har Ta fito da ita daga k’asan gadon... Sukaima juna K’uri su duka biyun... Sai yanzu ne Muhibbah ke iya tantance mahaukaciyar da ko shakka babu Dattijuwa ce sannan da alama ta jima a wannan yanayi sabida daud’a da jikinta yayi sosai, data k’urawa mahaukaciyar idanu sai ta fahimci farar fata ce ba bak’a bace dan ga alamun asalin kalarta Ta ramin idanunta da kuma k’ark’ashin kunnuwarta ashe bak’in datti ne ya rufe mata fata har ya zamto tamkar wani layer....

“AUDOTU” (SAUDATU) abinda mahaukaciyar kenan Ta fad’i cikin kalamanata da basa fita sosai...

Gaban Muhibbah ya yanke ya fad’i jin wannan mahaukaciya tamkar sunanta taji Ta ambata...

Muhibbah ta d’ago firgitattun idanunta tana duban mahaukaciyar wacce tuni ta kuma sakar mata murmushi....

Hannun Muhibbah taci gaba da janyowa har suka isa jikin shirgin kayanta, itada dai Muhibbah bata dawo daidai ba har wannan lokaci saima bugu da k’irjinta Ke ci gaba da yi... Tana gani mahaukaciyar ta soma bincike kayayyakinta... Can k’asan kayan ta ciro wani zane mai yanayi da zanen dake lank’aye parlon su Umaima... Gaban Muhibbah ya kuma yankewa ya fad’i... Mai wannan zane yake nufi....?

Batakaiga samo amsa ba taji sauk’ar takardan a hannunta mahaukaciyar ta mallaka mata ta dunk’ula mata sosai cikin hannunta tana mai ci gaba da sakin murmushi... Lokaci guda kuma Ta koma mazauninta Ta zauna, Ta rarumo ledar bredin da jiya Jakadiya da Ubandoma suka kawo mata Ta barka ledar ta hau mamuk’ar bredin kaman mai tsoron kar wani ya k’wace...

Muhibbah ta tsaya daga yanda take tai mata K’uri don ba kowa ta tina mata ba face Mahaifiyarta... Haka mahaifiyarta Ke tsananin k’aunar bread shine abincin da yafi soyuwa a gareta a lokacinda take raye.... Ta lumshe idanunta a hankali sanda take jin wasu hawaye daga can k’asan idanunta suna yunk’urin fitowa...

Jin kaman alamun tafiyan mutane ya sanyata saurin saita kanta kana ta nufi k’ofa sauri sauri wannan zanen na damk’e cikin hannunta ta fice daga cikin d’akin tana mai kuma waigowa tana duban mahaukaciyar nan itama mahaukaciyar idanunta k’yam akan Muhibbar har Ta fice...

A haka Muhibbah ta nufi d’aki, har lokacin bata dawo daidai ba, abubuwan da suka faru suna kuma dawo mata... Musamman da Ta tuna taji kaman matar nan Ta ambaci sunanta... Toh wacece mahaukaciyar nan...? Ya akai ta santa...? Shin wacece ita..? Ta k’arashe tunanin nata tana mai bud’e wannan taswira da mahaukaciyar ta damk’a mata... Tai k’urima zanen ginin tana mai kuma k’are masa kallo... Lallai ya zama dole tasan yanda za’ai tai comparing wannan zanen da wanda Ke lank’aye parlorn su Umaima, idan har sun zmato iri guda toh ko shakka babu akwai wani b’oyayyen sirri tattareda zanen...! Ta k’arashe tinaninta tana mai kwanciya rigingine saman gado... Ta janyo wayarta tana mai k’ok’arin neman layin Ansar... Saidai kira kusan sau uku tai bai d’aga ba... Sai sannan ta duba time taga dare ya d’anja sosai dan haka bata kuma kiran nasa ba barshi har sai zuwa safiya...

**

Kafin Washe gari iyaka buguwa Ubandoma yayi laushi a hannun Majidad’i... Idan Kaga Ubandoma dole ya baka tausayi irin yanda bugu ya sauya masa halitta... Kankace mai labari ya bazama Fada cewa an kama Ubandoma a gidan Wamabai... Wannan labari ba k’aramin d’aga hankalin Giwa da Waziri yai ba... Mai yakai Ubandoma gidan Wambai... Shin kodai munafuntarsu yake... Shin kodai shid’in ya amintada Mahmood ne...? Bacin haka ma Uban wa yake aiki Tunda dai sunsan su basu aikesa gidan Wambai ba..
Shi kuwa Mahmood mamaki abin ya dinga basa... Shin mai yakai Ubandoma gidan Wambai..? Shin kodai yasan cewa shine bak’on Buzu...? Ya zaci Ubandoma aminatccen hadiminsa ne, kenan Ubandoma na munafuntarsa ne..? Yayi daidai da bai aminta dashi ya bud’e masa wasu sirrika nasa... Tabbas zarginsa ya tabbata wannan gida ba kowa ba abin yarda bane... Kenan zata iya yuwa wasu sunyi amfani da kusancin dake tsakaninsa da Ubandoma dan yai masu aiki.... Lallai ya zama dole ya k’ara taka tsantsan kuma Ubandoma zai fad’i abinda ya kaisa gidan Baba Wambai da kuma wanda ya turasa...
Da wannan tunanin Bawa guda ya k’araso ya zube gabansa yai gaisuwa kana ya k’arada “Allah shija zamaninka an tafida Ubandoma Gidan Yarin wucen gadi dake nan cikin Masarauta Dan a tsaresa...!”

Jinjina kai Yarima Mahmood yai a hankali alamun amsawa... Lokaci guda ya haura sama domin shiryawa dan ya zama dole ya gana da Ubandoma a yau d’in....

****


A daidai k’ofar shiga masarauta Yazeed da Majidad’i suka had’u...

Yazeed ya fad’ad’a murmushinsa sanda yake k’ok’arin k’arasowa dab da Majidad’in... Bayan sun gaisa ne Yazeed yai gyaran murya cikeda k’asaita “Ashe an kama b’era... Bravo gaskiya kayi k’ok’ari Partner... I’m so proud of you..!” Ya k’arashe yana mai tafe hannu a hankali shu’umin murmushi kwance saman fuskarsa...

Murmushin Majidad’i ma yai kana yace “Idan nasa abu a gaba bana fasawa har sai naci nasara domin ni d’in mai sa’a ne a koda yaushe...!” Ya k’arashe cikeda ziga kansa...

Shu’umin murmushin bai bar saman fuskar Yazeed ba ya d’an kwanto da fuskarsa kad’an saitin kunnen Majidad’i “Kar kayi gaggawa Abokina domin tafiya ce mai tsawo a gabanka...!”

Majidad’i ya murmusa kad’an yana mai duban Yazeed yake furta “At least yanzu na nuna maka what I’m capable of....Kai kuma fah shin ka nuna wani jarumta...?!”

Murmusawa kad’an Yazeed ya kumayi kana yace “Ta yuwu a idanunka kaga kaman ka fini k’arfin jiki... Amma saidai ni inada k’arfin tunani wanda zan iya yak’an tawaga guda da wannan tunanin nawa...!!”

“Ban gane mai kake nufi ba...!” Majidad’i yace yana duban Yazeed d’in...

Kafad’arsa kad’an Yazeed ya buga kana ya kuma matso da fuskarsa dab kunnen Majidad’i “Waye kake tunanin ya umarci Ubandoma da ya shiga Gidan Wambai...?!”

Majidad’i ya dubesa shaye da mamaki yana nazarin maganar.. Lokaci guda yake girgiza kai yana mai furta “Ta yuwu shi yakai kansa babu wanda ya turasa tunda wannan gida namu kowa ba abin yarda bane... kuma babu irin bugun da banyi masa ba dan ya fad’i Waye ya turo shi amma ya sanar dani babu wanda ya turo shi..!”

Yazeed ya kuma sakin wata murmushi yace “And you believe him...?” Yai tambayar yana mai tsare Majidad’i da idanu.... Lokaci guda ya kuma sakin murmushi ganin ya jefa Majidad’i cikin shakku da kokonto, Yazeed yaci gaba da fad’in “Ubandoma Hadimin waye... Waye Ubangidansa...?!”

Majidad’i na tsananin sakin huci ya d’ago yana duban Yazeed... Lokaci guda cikin karaji yake furta “Yarima....Mahmood..!!!”




SameenaAleeyou 📚
[7/16, 5:34 PM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*


*034*



*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*




Yazeed ya kuma sakin murmushi yana mai jinjina kai “Tabbas Mahmood is behind all this, shine silan ciwon mahaifinka... Zai iya yin komai dan yaga ya mallaki sarautar nan Ta ko wacce hanya ce, gashi ya soma da mahaifinka... Wannan dama ce ta samemu muyi amfani da ita wajen kaisa k’asa...!” Ya k’arashe yana sakin huci a hankali...

Majidad’i ya d’anyi shiru tamkar mai nazari sai kuma ya nusa yace “Toh amma kan wane dalili Mahmood zai cutar da mahaifina... Da ni da kai munsan cewa tun daga fari mahaifina is being very supportive to Mahmood, Toh kan mai zai nemi rayuwar mahaifina bayan shid’in ya zabi ya goyi bayansa yayi sarauta sama dani da nake d’ansa....?!”

Yazeed ya daidaita tsayuwarsa hannayensa hard’e ta gaba ya d’an turo k’irjinsa gaba kad’an irin tsayuwar da masu mulki keyi... “Da alama har yanzu baka fahimci yanda al’amara Ke gudana cikin gidan nan ba... So tari a gida irin namu mafi kusanci dakai shine mak’iyinka, wanda ka aminta dashi can easily betray you... Correct me if I’m wrong..!”

Jinjina kai Majidad’i yai yana mai kuma karantar Yazeed lokaci guda yace “Kana tunanin Mahmood could be behind my father’s illness..?!”

Yazeed ya saki murmushin cin nasara yana mai ware hannayensa “Isn’t it obvious..? Ai a bayyane yake Mahmood shine sila, da umarninsa Ubandoma ya shiga gidan Wambai... And believe me idan bakai komai akai ba sai Sun kashe Wambai har lahira...!”

Majidad’i yace “Toh yanzu miye abunyi Ta yaya zamu kama Mahmood da laifin idan har ba Ubandoma bane ya fad’i cewa da umarninsa ya kutsa gidan Wambai kuma shine bak’on Buzu...?!”

Yazeed ya murmusa a hankali kana yace “We make him talk... We gonna make sure he rats Mahmood out... Dole mu tabbata ya fad’i cewa Mahmood shine yai masa umarni da ya shiga gidan Wambai... After all, haka zancen yake tunda Ubandoma Hadiminsa ne...!” Ya k’arashe babu alamun jin k’ai ko imani cikin k’wayan idanunsa...

Jinjina kai kurum Majidad’i yake cikeda tsanani tsanar Mahmood “Zan d’auki fansar ciwon mahaifina zan tabbata Mahmood bai zama sarki ba sannan sai ya tafi gidan Yari har tsawon lokacinda mahaifina zai kwashe a kwance....!”

Yazeed ya saki murmushi yana mai furta “Impressive..!! Yanzu abinda ya kamata muje muga Ubandoma musan ta yanda zamu b’ullo masa..!”

Babu musu Majidad’i ya jinjina kai kana yabi bayan Yazeed suka shige cikin Fursuna...
**

Dogari guda ne ya k’araso cikeda risinawa ya bud’ewa Mahmood gark’amemen k’ofar fursunan da aka rufe Ubandoma ciki wanda sai ka shige manyan k’ofofin k’arfe har kusan guda uku kafin ka cimma d’akinda Ubandoma Ke ciki.....

Ubandoma na hango Yarima Mahmood ya shiga sanne kansa ya zube gwiwoyinsa ya had’e hannayensa waje guda yana fad’in “Rankaidad’e dan Allah ka ceceni kamin rai ka fitar dani daga wajen nan... Wllhi banida laifi sahun b’arawo na ta...!” Hango tsagwaron b’acin rai saman fuskar Mahmood wanda bai tab’a ganin irinsa ba tattaredashi tsawon zamansu tare ya sanyashi saurin had’iye zancensa gumi naci gaba da tsartsafo masa...

Yazeed da Majidad’i da k’arasowarsu wajen kenan tin daga k’ofa Yazeed ya umarci dakarun dake tsare da fursunan da su bud’e masu suga Ubandoma...

Dogarin ya risina yace “Allah shi taimakeka Mai Girma Yarima Mahmood yana ciki bazamu iya barinku ku shiga ba...!”

Wani jahilin duba Yazeed ya watsa masu “Kun kuwa San ko ni wanene...? Kun kuwa San da waye kuke magana..?!”

Dogaran suka kuma risinawa d’ayan na fad’in “Umarnin Yarima Mahmood ne kuma zab’ebb’en sarki na gaba Allah shi taimakeka... Wannan ba umarninmu bane...!”

Yazeed da Majidad’i suka dubi juna... Yazeed dake tsananin huci yana k’ok’arin damk’o wuyan Dogarin Majidad’i yai saurin taresa kana ya d’aga bakin rigarsa kad’an zarkwad’ed’iyar wuk’a mai tsananin shek’i sabida kaifi Ta bayyan...
Dodagarin ya had’iyi miyau da k’yar dan tsoro yana mai k’ifta idanu... Lokaci guda ya matsada baya yana mai basu hanya...

Yazeed ya dubi Majidad’i yace “Zaifi kyau idan ka jirani a nan... Shiganmu a haka mu biyu zaisa Mahmood ya zargi wani abu....!”

Majidad’i ya jinjina kai kana ya koma da baya ya bar Yazeed ya soma shigewa...

**
Mahmood ya girgiza kai yana duban Ubandoma lokaci guda ya d’an gyara tsayuwarsa yana mai fad’in “Kai nake saurare, ka sanar dani gaskiyar Al’amari idan har kanaso na taimakeka..!!”

Ubandoma ya kuma goge gumin dake ci gaba da karyo masa, Ta ya zai soma sanar da Mahmood ga abinda ya kaisa gidan Wambai, Ta yaya zai soma sanar dashi zancen Giwa da Waziri yaji har ya jefasa a ukun da ya tsinci kansa... Sanar da Mahmood gaskiya na nufin tono komai na Masarautar kenan... Idan har ya sanar dashi ga shirin Giwa da Waziri komai ya riga ya lalace kuma yayi imani hakan na iyayin sanadiyan rayuwarsa tinda yasan wacece Giwa ballantana Waziri...

“Kai nake saurare Ubandoma..!!! Wai ma tsaya tukuna, who are you..? Wanene Kai..? Ka sanar dani idan akwai wanda kake munafunta dashi cikin Masarautar nan..!!” Ya k’arashe cikin tsananin zafin rai...

Ubandoma ya shiga girgiza kai yana furta “Allah shi taimakeka BillahilAzim bani ha’intarka da kowa... Ka yarda dani Rankaidad’e, ka min rai ka cireni daga wajen nan..!” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya yana mai k’ank’an da kai...

Girgiza kai kurum Mahmood yai kana yace “Had’in kanka shi kad’ai zai bani damar taimakonka Ubandoma... Amma a halin yanzu ni kaina ban yarda dakai ba, inada kokonto da tarin shakku akanka... Zan baka nan da kwanaki Uku Ubandoma, ka gama dik tinanin da zakai... Idan ka zab’i ka fad’i gaskiya watak’ila ka tsira da mutuncinka amma idan ka zab’i akasin haka... Kafi kowa sanin zaka dawwama cikin k’ask’anci a gidan Yari har lokacinda Allah zai baiwa Wambai lafiya ya bud’e bakinsa ya fad’i komai...!”

Daga haka juyawa yai da niyya ficewa Yazeed dake mak’ale daga gefen gini ya gama sauraren duk abinda suka fad’i, shiru yai yana nazari... Kenan Ta tabbata ba Mahmood bane ya tura Ubandoma..? Kenan akwai wani wanda Ubandoma yafi aminta dashi a Masarautar sama da Mahmood... Idan ya fahimci wani abu tabbas akwai wanda yake son ganin bayan Mahmood cikin Masarautar fiyedashi... Toh wanene wannan wanda Ubandoma kema aiki... Waye mak’iyin Mahmood har haka..? Lallai ya zama dole yasan ko wanene wannan...?! Ya k’arashe tinanin yana mai juyawa da baya shiga wajen Ubandoma da baiyi ba kenan... Dole yai shiri ya kuma San takunsa da alama Kuraye sunyi yawa a Masarautar tasu... Mahaifiyarsu tana cen tana fatan Mahmood ya d’ale Karaga ashe akwai wani wanda Ke cin dunduniyarsu basu sani ba.. Yayi imani Giwa batasan Ubandoma na munafuntar d’anta da tafi so da sarauta ba...!
Shafa hab’arsa yake a hankali yana nazarin waye ke son ganin bayan Mahmood sama dashi irin haka a cikin Masarautar..!?

**
Mahmood yana fitowa yaceda Dakaru masu tsaron Fursunan kar su bari wani ya gana da Ubandoma har nan da tsawon kwanaki uku, dan yasan idan aka bari kowa yana shiga munafukin da Ubandoma ke masa aiki zai iya tsoratasa har ya canza niyyansa na fad’in gaskiya tinda ya kula kaman Ubandoman ya soma karaya da alama zai fad’I gaskiya bayan kwanakin da ya d’ibar masa cewa yai shawari da zuciyarsa....

**

Wayar mak’ale kunnenta na b’angaren hagu ta kuma sauk’e huci a karo na biyu, saida ta canza wajen zama kana taci gaba da fad’in “Ansar I’m quite certain matar nan sunana Ta kira... She knows me Ansar... Duk yanda akai ta sanni... Tambayar a nan shine wacece ita..?!”

Daga d’aya b’angaren Ansar ya fuzar da fuci a hankali kana yaci gaba da fad’in “Hiba kiyi tinani maybe kin tab’a saninta a shekarun baya, watak’ila tun tana cikin hankalinta kafin lalurar hauka ya sameta... Kiyi tinanin mutanen da kikai rayuwa dasu a shekarun baya...!”

Shiru tai tamkar mai nazari sai kuma tace “Ansar bazan iya tunawa ba, bazan iya tuna sanin wata mace mai yanayinta ba... The only thing da na sani shine inajin wani babban al’amari gameda matar sannan inaso na taimaketa bayan haka inason sanin asalin labarinta da kuma yanda akai Ta k’are rufe a cikin wannan masarauta..!” Ta k’arashe maganar cikin rawar murya..

Shiru na d’an dak’ik’ai suka gifta kana Ansar yace “I have faith in you Hibbah... Nasan duk wad’annan abubuwan da kika saka gabanki da izinin Allah zaki Kai k’arshensu... Addu’ata da soyayyata na taredake ko yaushe kinji koh, dan haka Koda wasa kada Ki karaya...

Jinjina masa kai tai a hankali tamkar yana ganinta kana sukai sallama cikeda kewar juna... Takardan zanen da mahaukaciyar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login