Showing 198001 words to 201000 words out of 257774 words

Chapter 67 - MUHIBBA Book Complete by Sameena Aliyou.txt

kufce mana ba... Muje muyi sauri mu mik’ataga Tal’udu ya cika aiki Kaga matarka Umaima ta tsira..!!”

Jamal na girgiza kai yake furta “But Maami Zahra tana nan a wajen nan, Ta b’ace min ban ganta ba, yanzu haka ita nake nema..!!”

Giwa Ta zaro idanu waje tace “Jamal Zahra kuma..! Zahra fah kace..? Mai ya kawota nan.. Ya akai tazo nan..?!”

Girgiza kai yake yana furta “I don’t know Maami..! She followed me..!”

Giwa tace “K’yale batun Zahra ka shige muje kafin damarmu na k’arshe ya kufce mana..!”

Jamal ya girgiza kai yace “Maami don’t underestimate that girl.. What if taje ta fad’awa Mahmood..?!”

Giwa Ta buga Uban tsaki tace “Idanma ta fad’a masa bazai samemu ba dan muna Fadan Sarauniya tareda ita yarinyar, sannan abu ne mai matuk’ar sauk’i yanzu da muka samu k’ofar makullin Mulkinmu zai rufu ruff sai mu kashe Mahmooda harma da d’iyarsa kaga mun cire bare cikinmu tinda daga shi har d’iyar tasa ba jina bane.. Dama na gaji da pretending..! Shige muje.. Muyi sauri bamuda lokaci..!!” Ta k’arashe tana turasa Jakadiya na biye dasu...

Hankalin Zahra yakai k’ololuwa wajen tashi...! Tana jin Sun wuce ta bud’e bakinta data toshe Ta fitar da kukan da ya kuma taso mata tin daga k’irji..! Kuka take tana mamakin badak’alan zalunci da aka jika anayi cikin Masarautar su... Babu abina yafi tsaya mata kaman jin muryar Giwa da tayi tana fad’in Mahmood da d’iyarsa ba jininta bane..! Ashe ba ita ta haifi Paa d’inta ba shisa tun can basa wani son juna irin yanda jika da Kaka Ke son juna... Wasu hawayen suka kuma gangaro mata tsananin tausayin Paa d’inta na kuma kama Ta....! Tunowa da halinda Muhibbah Ke ciki ya sanyata Saurin mik’ewa Ta nufo waje babu shiri tana kuma neman hanya... Allah kurum take ambato tana rok’onsa ya fitar da ita ta isa ga mahaifinta..!!

**
K’iris ya rage bai had’ada masu tsaron k’ofar Masarautar ba, saida ya shige har tsakiyar farfajiyan Masarautar kana yaja wani irin burki... Zuciyarsa bata daina bugawa ba ya finciki marfin motar ya fito... A guje ya nufi b’angaren da ya ajeta, jama’an masarauta sai zubewa suke suna basa hanya cikeda mamakin yanayin da suka gansa ciki... Turaki da Barde harmada Ansar suka k’araso cikin Masarautar suma hankali tashe...

D’aya daga cikin Kuyangi masu kulada b’angaren Muhibbah itace Ta soma hango Rankaidad’e cikin wane irin yanayi da bata tab’a ganinsa ciki ba...! Ta shige a guje tana fad’in “Hasiya..! Hasiya ki shirya ga Rankaidad’e..!!”

Gaba d’aya Kuyangin sun rikice duk sun zuzzube a k’Asa zukatansu naci gaba da tsinkewa...

Babu kaman Hasiya wacce Ke zaune saman gadon Muhibbah ta janyo alkyabba ta rufe fuskarta da ita, zuciyarta sai tsinkewa yake sanda taji Rankaidad’e ya turo k’ofar d’akin ya sako k’afafunsa ciki...

Kai tsaye ya nufeta zuciyarsa bata daina tsinkewa ba, lokaci guda yakai hannunsa ya janye Alkyabban... Zuciyarsa tai wani irin tsinkewa sanda yaga ba Muhibbah bace..!! Fuskarsa Ta kuma rinewa zuwa ja haka nan idanunsa... Ga wane irin gumi da ya wanke masa fuska gaba d’aya sai d’iga yake...
Ita kaw Kuyangar sai karkarwa jikinta keyi sabida tsananin tsoro tamkar zata had’iyi ranta...

Mik’ewa yayi ya dafe kansa da duka hannayensa biyu dai dai lokacinda sauran kuyangin suka shigo kawunansu a k’asa... Shugabar tasu ce ta soma duk’awa tana furta “Rankaidad’e kai mana aikin Gafara...!”

Cikin wane irin yanayi yake dubanta kana yace “Where’s my wife..?! Ina matata nace..?!!”

Kuyangar jiki na rawa take furta “Allah shi taimakeka.. Munyi iyaka k’ok’arinmu ganin mun dakatar da ita amma tak’i tsayuwa..!”

Bai daina huci ba yake dubanta lokaci guda yake furta “Wannan shine umarnin da aka baku..?! Nace wannan shine umarnin da aka baku..?! Wacece take nan sanda hakan ya faru..?!”

Hannu na rawa d’aya ‘yar matashiyar ta nuna Hasiya da tuni ta silalo ta zube k’asa daga saman gadon..!

Tana jin ya soma takowa zuwa gabanta Ta soma fad’i cikin tsananin rawar murya “Rankaidad’e kai min gafara wllhi babu yanda banyida Gimbiya ba amma ta had’ani da Allah tace rayuwarta na cikin had’ari a Masarautar nan ya zama dole ta gudu shiyasa mukayi musayen kaya ta saka nawa na Bayi gudun kar azzaluman da suke nemanta su kamata..! Rankaidad’e Gimbiya tayi nisa da Masarautar nan dan tun jiya bata nan..!”

Zuciyarsa taci gaba da tsinkewa, kenan da gaske su Giwa suna nemanta zasu halak’ata..! Ina Ta tafi..?!
Bai tsaya nemo amsa ba ya nufo waje yanda ya tadda Ansar da Turaki.. Ansar na ganinsa ya k’arasa yana tambayarsa Ina Muhibbah.. Ko kallon arziki Ansar bai samu daga Mahmood d’in ba.. Saima duban Barde da yayi yace a rufe Kuyangin nan har sai an sami Muhibbah... Hakan yasa suka fahimci Muhibbah bata a cikin gidan...!

Bai kuma bin takan kowa ba ya nufi b’angaren Giwa kaman zai kifa k’asa..! Saidai koda ya nufi b’angaren Giwa bata nan babu Jakadiya babu Zahra ma sai taron ‘yan karb’an gaisuwa irinsu matan Waziri Talba Madaki da dai sauran masu sarauta harda iyalan Wambai...!

Cikin sauri ya fito ya nufi b’angaren Jamal tinda harda shi a case d’in..!

Nan ma bai tadda kowa ba, yayi tunanin ko yana waje can wajen maza su Talba da su Liman da dai sauran masu sarauta dake cike a Fada dan karb’an gaisuwa da jajen abinda ya sami Yarima Yazeed...

Yana k’ok’arin sa kai da niyyan ficewa ya sinkayo muryar mace daga upstairs alamun tana neman taimako...

A hankali ya furta Muhibbah... Babu shiri ya nufi saman yana bud’e k’ofofi yake ambato sunanta...!

Can saman gado ya hango Umaima ta gama jigata maganan ma da k’yar take..! Cikin tsananin sanyi jiki had’ida mamakin ahalinsa ya isaga Umaima ya hau kwanceta..!

Yana kwanceta yake tambayar “Who did this to you.?!”

Cikin kuka take sanar dashi duk abinda ya faru tin daga kan abubuwan da Muhibbah ta sanar da ita gameda Jamal har kamasu da Jamal d’in yayi ya d’aureta.. Bata kuma San ina yakai Umaima ba... Har kawo kiran Zahra da tai a waya duk saida Ta sanar dashi..!

Cikin kuka daidai sanda ya ida kwanceta take fad’in “Yaya please you need to go after Zahra..! You need to save them both.. I’m sure idan Jamal ya ganta itama bazai barta ba..!!”

Umaima bata ida magana ba Mahmood ya mik’e ya soma jada baya zuciyarsa na barazanar fitowa waje... Mutane biyu da sukeda matuk’ar mahimmanci a rayuwarsa suna hanun mahaukacin k’aninsa... Matarsa da kuma d’iyarsa suna hannun Jamal..!

Lokaci guda yake girgiza kai yana kuma jada baya..! Take ya nufo downstairs yana ambaton sunan Jamal da k’arfin gaske..!

Duk wanda yaci karo da Mahmood cikin Masarautar sai yasan babu lafiya.. Hanya kurum ake basa ana risinawa, duk wanda ya giftasa kuwa sai ya bisa da kallo....

Yana fitowa babban haraban Masarautar yayi wani irin k’ara cikin muryarsa mai amon gaske yana ambato sunan Jamal...! Can ya hangi Zahra ta nufosa a guje sai layi take alamun Ta jigata.. Fsukarta shar shar da hawaye take furta “Paaaa!!!”

“Zahra..!” Ya furta zuciyarsa naci gaba da tsinkewa..!
Zahra tana isowa ya tarota ta fad’o hannunsa dan k’iris ya rage bata zube k’Asa ba sabida tsananin tangad’i da take..!

Mahmood ya shiga jijjigata yana kiran sunanta yana tambayarta Ina Jamal da Muhibbah..!

Cikin kuka Zahra Ke. Furta “Paa you need to save her..! Her life is in great danger Paa..! Maami and Uncle Jamal zasu kasheta..! Paa I don’t want to lose her..!”

Cikin tsananin rawar murya yake furta “No Zahra bazamu rasata ba kinji.. Tell me ta ina suke..! Talk to me Zahra... Fad’a min yanda suke..!!” Ya k’arashe yana jijjiga Zahra da har lokacin bata gama dawowa daidai ba..

“Paa bazan iya ganewa ba...! All I know kawai daga ta can ne yanda na fito..! Paa you need to hurry..!”

Bai kuma tsayawa sauraren Zahra ba ya nufi yanda take nuna masa.. Turaki dasu Barde harma da Ansar da k’arasowarsu kenan sukabi bayansa... Turaki yaceda Barde yaje yazo da Dakaru a bazama nema cikin Fada...!

Umaima da itama bata jima da k’arasowa ba suka rungume juna itada Zahra suna kuka sosai..!

**

Bata kuma sanin meke faruwa ba tinda taga Giwa da Jamal a gabanta sai bud’e idanu tayi ta ganta cikin wani d’aki a wane irin waje... Ta ware idanunta da sukai matuk’ar mata nauyi tana k’arema d’akin kallo..! Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un.. Ta fahimci wannan d’aki, bayan shekaru goma sha hud’u da suka shud’e Ta fahimci d’akin.. Shine d’akin da ta farka ta tsinci kanta ciki bayan yaran Giwa sun lalata mata rayuwa.. Allah ya taimaketa Ta kub’uta daga hannun wani azzalumin mutumi mushiriki mummuna wanda sam baida kyaun gani...! Yau Gata nan Ta kuma tsintar kanta cikin d’akin bayan duka wad’annan shekaru..! Ta yuwu wannan shine K’addararta.. Koda ta gudu a baya yanzu gashi ta kuma dawowa bayan shekarun nan..! Ta lumshe idanunta a hankali hawaye suka gangaro mata..! Ta yunk’ura zata tashi taji inaa gaba d’aya a zarge take, irin d’aurin da akema abin yanka idan za’a yanka irin d’aurin akai mata..! Aka had’e hannuwanta da k’afafunta aka d’aure waje guda..!

Bud’e idanun da zatai Ta hangi Giwa, Jamal harma da Jakadiya tsaye daga k’ofar d’akin suna dubanta..!

Giwa ta kece da wani irin dariya yau d’in sanye take da bak’ar lkyabbarta na tsafi ga wani bak’in tulu gabanta harda wani jan fitila maici da jan wuta...



SameenaAleeyou 📚*MUHIBBAH*





*74*




*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*





Cikin zuban hawaye take dubansu d’aya bayan d’aya zuciyarta na kuma karaya da tinanin watak’ila itakuma tata K’ADDARAR kenan ta mutu cikin wannan d’akin hannun wad’annan azzaluman... Ta lumshe idanunta hawaye suka kuma gangaro mata.. Cikin zuciyarta take furta “Ya Allah kada ka k’addara mutuwata hannun wad’annan azzaluman bayi naka..! Ya Allah ka kub’utar dani da buwayarka kar ka basu nasaran cutar dani..!” Bata ida ba taji Giwa tasa k’afa ta shureta...

Tayi tsaye gaban Muhibbar had’ida k’ura mata idanu, lokaci guda ta shiga jinjina kai tana furta “Tabbas ke ce..! SAUDATU..!” Ta kuma sakin murmushi kana taci gaba da fad’in “Na tabbata kin gane d’akin nan..! D’akin da ya shekara goma sha hud’u a bud’e yana zaman jiranki, yau gashi kin dawo cikinsa kuma zaki dawwama cikinsa domin kuwa wannan d’aki Naki ne wanda aka ambacesa da sunanki Saudatu aka kuma rubuta saman Farin k’yalle, Ked’in kyauta ce ga Sarauniya, a yau Zata cika k’udirin ta ta kuma cika min Mulki na da gudan jininki..!!” Ta kuma kecewa da dariya..!

Muhibbah da hawaye Ke gangaro mata take Ta soma furta “Allah bai baku nasara shekarun baya ba, Maiyasa kike tunanin zai baku nasara yanzu..? Maiyasa kike tunanin zaki tabbata kina zalunci..! Barin tuna miki idan kin mance.. Ni ce nan wacce na shigo rayuwarku na tarwastaku ba tareda kun ankare ba..! Kuma ni ce nan zan zamto silan tonuwar asirinki dake da muk’arabbanki... Zaki gani da sannu Ubangijina zai kawo min d’auki ya kawo wanda zai fiddani daga sharrinku..!!” Batakai aya ba Giwa ta d’auketa da muguwar mari.. Lokaci guda take furta “Babu wanda zai fitar dake daga wajen nan Saudatu, duk duniyar nan babu wanda yakeda mabud’in wannan gini... Mutum guda yake da mabud’in wannan gini kuma ya mutu.. Mabud’in wannan gini guda d’aya ne tak kuma an bisneta cikin K’undi da jimawa... Saudatu bazaki tab’a ficewa daga wajen nan ba... Nima kaina banida wannan mabud’in wanda ya adana wannan mabud’in har ya bar duniya bai mallaka min ba... An busnesa tareda k’undin cikin turb’aya....Tal’udu shi ya bani karatun tsafi da zanke biyawa ginin ya tsage min na shige.. Sannan ko Jakadiya da a kullum take min rakiya bata iya wannan karatun tsafin ba.. Gata nan ga Jamal ki tambayesu ya akai suka shigo wajen nan... Bud’e idanu kawai suma sukai suka gansu cikin wajen nan kaman yanda Kema bud’e idanu kurum kikayi kika ganki ciki..! Har abada babu wanda zai iya fitar dake Saudatu..!!” Ta kuma kecewa da wani irin dariya..

Muhibbah na murmushi take furta “Wanda ya fitar dani daga farko inada tabbacin shi zai kuma fitar dani..! Dashi nayi imani dashi na dogara, kuma na tabbata shine zai taimakeni..! Da sannu zai tona miki asiri, sannan ya k’asak’antar dake, zaki koma bakida wani daraja ko matsayi ta yanda k’ask’antaccen bawa sai ya fiki daraja cikin Masarautar nan..!” Bata kai aya ba Giwa ta kuma kwashe ta da wata mari.. Tana huci take nunata tana fad’in “Ke k’aramar maras kunya..! Na gama da iyayenki na gama da kaf zuri’arki balle ke..Tin daga Kan Kakanki Sarki Jamaluddeen na k’asar Benin wanda shine ya haifi mahaifinki Yarima Alfah d’an uwa ga Gimbiya Turai matar Sarki AbdulJabbar wacce na maidata Kuyanga a gidan Mijinta, mahaifiya ga ‘ya’yan Sarki guda biyu Yarima Mahmood wanda na maidashi nawa tin yana jariri domin na cika k’udirina akansa, da kuma Ja’afar wanda na maidashi d’an Bawa ya girma cikin k’ask’anci da bauta a gidan mahaifinsa a Masarautar Sa.. Dan haka ki sani gamawa dake abu ne mai matuk’ar sauk’i a gareni k’aramar Alhaki..!!” Ta k’arashe tana mai d’ago fuskar Muhibbah wacce ta shige rud’u sosai.. Bata fahimci mai wannan matar take fad’i ba gaba d’aya ta zama lost and confused..! Cikin wane irin yanayi take duban Giwa da idanunta da suka firfito waje tana jin kanta na juya mata...

Giwa ta kuma kecewa da dariya tace “Nasan duk bakisan wad’annan labarun ba, bakida masaniya amma bazan bari ki tafi ba tareda kin sani ba... Zan baki labarin duk abubuwan da nayi ma zuri’arki tin daga tushe... Idan kika tafi a haka ba tareda kin sani ba kinci banza..! Gwara ki San komai, kisan duk abubuwan dana aikata kafin k’ofar d’akin nan ya rufe dake rufuwa ta har abada..!!” Ta kuma kecewa da muguwar dariya...

Take Giwa Ta shiga labartawa Muhibbah duk abubuwan da suka faru tin daga farko, Dik wani k’ulli da makirci da tayi da lokutan da abubuwan suka faru da komai da komai..!

**

A can asibiti wajen Yazeed kuwa bore da hauka yake ci gaba da yi, an masa alluran baccin ma kaman a banza don yana somawa allurar zata sakesa ya farka yaci gaba da ihu yana fad’in a dawo masa da hannayensa da yaransa... Ya dubi Waziri dake zaune gefensa dan tinda ya farka bai bar gefen Yazeed d’in ba...! Cikin wane irin huci yake ceda Waziri “Kai Old Geezer, Take me to the palace..! I want to see Mahmood, I want to rub it to his face... Ina so naga fuskarsa idan yaji cewa shid’in ba kowa bane d’an Baiwa ce k’ask’antacciya mai k’wacen mijin Uwargijiyarta..! Ka d’aukeni ka kaini Masarauta na sanar da Mahmood haka, ya daina jin kansa shid’in wani ne ko shi d’in yafi wani... Baifi kowa ba shid’in k’asaitacce ne d’an Baiwa... Baiwarma Ta wani Masarautar wacce aka sadakar da ita...! Ka d’aukeni Ka kaini nace... I can’t be the only loser..! Mahmood ma dole ya d’and’ani irin k’uncin dana d’and’ana... Na tabbata yana can yana murnan abubuwan da suka sameni..! Amma idan yaji asalinsa da tushensa zai fahimci cewa shid’in k’ask’antacce ne... Bawa bai dace da sarautar Masarautar mu ba... Gwara nakasasshe ya zamto Sarki akanka D’an Baiwa ya gaji sarauta..! Ashe abin a jini yake shiyasa ya k’are ya auri d’iyar bayi...! Toh yau d’in nan wllhi zaiji asalinsa koda zai had’iyi zuciya ya mutu ne..!!” Ya k’arashe yana mai ci gaba da fidda huci..!

Waziri dake faman muzurai zuciyarsa na tsinkewa ya soma fad’in “A’a Yazeed kai hak’uri dai har ka k’ara samun lafiya...!”

Baikai aya ba Yazeed ya katsesa da fad’in “Kai Dattijo kayi abinda na umarceka idan kana son kanka da lafiya.. Har gobe nid’in sama dakai nake domin ni d’an Sarki AbdulJabbar ne... Ko a mafarki kada ka tab’a zaton zan kalleka matsayin mahaifi..! Tashi ka kaini masarauta idan baka so na k’arasa kashe kaina yanzu a asibitin nan..!!”

Waziri ya had’iyi miyau da k’yar yana sab’a babbar riga cikeda daburcewa yake fad’in “Toh..Toh.. Toh ai Wato ai gani nayi ciwonka d’anye ne dukda cewa na rufe cikin bandeji..!”

Yazeed ya katsesa da fad’in “Zakayi abinda na umarceka ne kokuwa...!!”

Waziri ya kuma mik’ewa zunbur yana furta “A’a ba za’ayi haka ba Rankaidad’e..!!” Lokaci guda ya mik’e ya nufi k’ofa yana fad’in bari ya kirawo malaman asibiti su kwance ruwan da aka d’aura masa...! Bai kuma tsayawa sauraren Yazeed ba ya fice...!

Yazeed ya shiga k’walla masa kira, inaa Waziri ko juyowa baiba dan ko kusa bazai biyema Yazeed su tapka wannan rashin hankalin ba... Domin kuwa ba asirin Mahmood zai tona ba asirin mahaifiyarsa zai tona...!

Yazeed yaji zuciyarsa kaman zata buga Dan babu abinda zai iyayiwa kansa... Ya shiga shure shure da k’arfin gaske har dai ya samu ya finciki drip d’in dukda tsananin azaban hannayensa da yakeji... Amma dole ya daure koda jini zai b’alle a jikinsa ne sai yaje ya tunk’ari Mahmood ya tarwatsa zuciyarsa kaman yanda nasa rayuwar Ta tarwatse... Haka ya lallab’a ya sauk’o daga saman gado babu hannaye... Taimakonsa d’aya Waziri ya mance k’ofa a bud’e nan yabi ta k’ofar yana tafe yana ciza labb’a sabida tsananin azaban da hannayensa ke masa, zafin zuciya irin nasa da tsanar Mahmood bazai bari ya zauna a asibiti Mahmood yana can yana jubilating nakasan da yayi ba...
A haka ya fito yana bin garu yana satan idon mutane har ya samu ya fito haraban waje... Nan ya iske Waziri na k’ok’arin shigewa Mota... Cikin sauri Yazeed ya nufi Waziri yana furta “Kai Oldtimer..! Kai Dattijo..!!”

Waziri na k’ok’arin kutsa kai Mota dan baiyi zaton zaiga Yazeed ba, Yazeed ya k’araso yana hakin azaba lokaci guda yake furta “Kana jina wllhi ko ka d’aukeni ka kaini masarauta ko kaima na tona maka asiri kaci amanan amininka ka nemi matarsa har kun haihu... Kasan ni a halin yanzu I’ve got nothing to lose..! My whole life is already ruined... Abokin tafiya nake nema shiyasa zan fuskanci Mahmood na sanar dashi asalinsa..! Idan kana son kanka da lafiya, idan baka so ka tafi k’asa taredani da Mahmood, Toh ka d’aukeni ka kaini Masarautar nan,.. Kuma Kai banda abinka, idan naje Masarauta na tona asalin wanene Mahmood ai Kasuwarka ce Waziri, kaga watak’ila sarauta ta fice daga ahalin AbdulJabbar ta har abada Kaga shikenan ka samu tsuntsu a sama gasasshe... All thanks to your Bastard Son, at least ko ban maka noma ba na baka abinda yafi Gonakin ka da ‘ya’yanka suka jima suna noma maka..! Na baka sarautar k’asar baki d’aya...! Ko ya kace Old geezer.. Kaga watak’ila nayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login