Showing 99001 words to 100116 words out of 100116 words
kake? Ya kwana biyu?
"Lafiya Lau UMMIE ya biki?
"Alhmdll! Ta amsa tana murmushi! Addu'a yayi ma ta sosai sannan sukayi sallama.
Washe_gari
Karfe 11 na safe aka daura auren Farooq da Ummie a kan sadaki naira 200k, daurin auren d'aya tara daruruwan mutane.
Ummie tayi kyau cikin lace din da Sa'adah ta ba ta.
Light make up akayi ma ta. Ansha hotuna kafin amarya ta fito.
Tun da ya dora idanunsa a kanta ya kasa daukewa.
Tana dagowa ta hangoshi, kashe masa Ido tayi tana dariya.
Yusuf na kallonsu! Sam Ummie bata jin kunyarsu har wani kashe masa Ido take!
Ya fada a fili Yana kallon Farooq.
Sai wajen karfe 1 sannan suka koma gida aka cigaba da gudanar da shagalin bikin.
Karfe 6 saura aka shirya Ummie cikin lafaya me kyau da tsada zuwa gidanta na aure.
Tasha fada sosai da nasiha. Ko digon hawaye batayi ba. Ummanta na gama yi ma ta fada ta bude fuskarta ta ce " Zan dinga zuwar Miki kullum Ina wanke Miki nama!
Dariya suka saka gaba d'aya dan sunsan halin Ummie da tsokanar Ummanta, ita da umman nata sun zama tamkar *KAWAYE* shiyasa Ummie bata boye ma ta damuwartw Dan Zarah tajata jiki sosai Kuma hakan besa Ummie ta Raina ta ba sai da ma gudun bacin ranta.
Rungumeta Zarah tayi ta ce " Allah yayi Miki albarka Mamana!
"Amin Ummana inasonki sosai!
Zayd ne ya shigo Yana fad'in "wai baku tafi ba?
"Inafa suna ta rungume²" Cewar Sa'adah tana dariya.
"Ga Shehu chan sai Fada yake kunsan halinsa!
Tasowa Ummie tayi tana isowa inda Zayd yake ta riko hannunsa ta ce " Thanks for everything Uncle Zayd! Allah ya biya maka bukatunka! Zan dinga zuwa duk Friday Ina yanke maka farce"
Kumatunta yaja Dan tana son ya fara feeling so emotional. Rungumeshi tayi tana runtse idanunta hawaye suka biyo kuncinta, tabbas irinsu uncle Zayd kadan ne a zamanin nan!
"Lokaci na tafiya! Zayd ya fada yana Dan dukanta alamar rarrashi.
Sakinta tayi tana goge fuskarta ta ce " Zan dinga zuwa fa!
"Waya hanaki? Khaleel dake bakin kofar falo ya fada. Yana guduwa. Dariya tayi ta sake juyawq ga Ummanta.
"Allah yayi Miki albarka UMMIE ya kawo Miki haske a dukkan lamuranki ya baki zaman lafiya na har abada"
Da Amin suka amsa gaba d'aya.
Sa'adah! Zainab da Kuma yar k'anwar Aunty sune zasu rakata dakinta. Hannunta Zayd ya riko suka fito.
A tsaye jikin Rolls Royce phantom dankareriya sabuwa fil baka wuluk me tinted glasses taga Abbanta a tsaye ya cika yayi fam dan sun bata kusan 30mins saboda har an fara kiran sallar magariba.
"Ku tafi! Ya fada yana kallonsu. Karasawa tayi ta rungumeshi tana fad'in " Nagode Abbana Allah ya kara budi dayawa ya rabaka da asara! Zan dinga zuwa kullum kana bani kudi!
Ta fada tana dagowa ta kalleshi.
Murmushi yayi kadan ya ce "Lashe Money!
Dariya tayi tana kara rikeshi sosai.
Shima riketa yayi yana shafa kanta tare yi ma ta addu'o'i sosai.
Daga bisani ya saketa ya ce " Wannan motar taki ce UMMIE! Wannan motar taki ce! Ina ta jiran wannan ranar tazo na baki! Kinsan kudinta?
Karewa motar kallo tayi kafin ta girgiza kai alamar A'a.
"No need just for you my darling! Ya fada yana murmushi.
Shima Zayd murmushi yayi Ashe kudin da Shehu yake ta fafutar hadawa kenan! Motar over 200m a kudin Nigeria! OMG! Lallai Shehu ya canza! Kuma tabbas yayi kokari sosai.
Mukullin motar ya bata Yana fad'in " A ita za'a kaiki!
Cikin farin ciki ta kara rungumeshi. Zarah nata kallonsu ta taga zuciyarta fes.
Zayd ne ya shiga motar, sannan amarya, sai Aunty Zee a gaba sannan yar k'anwar Aunty da Sa'adah tare da amarya a baya.
Har compound din gidansu Farooq Zayd ya kaisu sannan yayi parking suka firfito, sai kallon motar ake Dan ta gaji da haduwa.
Sai da Mama tayi nata nasihan sannan aka nufi gidan UMMIE.
Da kafar dama aka sa ta shiga tare da Bismillah.
Bude fuskarta tayi ta fara kalle ².
Dukanta Aunty Zee tayi kadan a baya tana Jan lafayar ta rufe ma ta fuska.
Sai kusan 10pm sannan ango ya shigo tare da abokinsa! Dan uwansa kuma Yayansa *YUSUF*
Aunty Zee da Sa'adah ne kawai suka rage a gidan. Dan duk yar k'anwar Aunty ta hada kansu an Kara gyara gidan sannan suka tafi.
Su ma Aunty Zee basu Dade ba suka tafi aka bar Ummie da Farooq daga su sai halinsu.
Lafayar ya sauke Yana kallonta. Murmushi tayi ta kalleshi ta ce " Yaushe rabo?
"Uhm an min rowar ganinki! Amma yanzu Babu Wanda zai hanani"
Dariya tayi tana dan juya idanunta.
Tashi muyi sallah. Da toh ta amsa sannan ta tashi dan alwarta Bata Dade da yin sallar ishai ba.
Sun gudanar da komai kamar yadda Sunnah ta koyar.
Tunda suka gama cin kaxa ta koma gado ta lafe sai a lokacin gabanta ya fara dukan tara² sosai take tuno irin azabar da tasha lokacin da Shege Saleh yayi raping dinta.
Farooq murmushi kawai yayi dan yaga kamar jikinta yayi sanyi! Yasan dama za'a rina....
"Ummie ki canza kaya mana!
Ya fada yana kokari rike dariyarsa.
"A'a ni a haka zan kwana" Ta fada tana juya masa baya. Bai ce komai ba illah murmushi da yayi ya shiga toilet.
Ya jima sannan ya fito yayi Shirin kwanciya ya dawo gefanta ya kwanta yana janyota jikinsa.
Numfashi ya sauke a hankali yana jin wata nutsuwa na zuwar masa! Nikuwa nace ance maka aure wasa ne😜 Nima ji nayi fa lol....
Shuru Ummie tayi ga dakin yayi duhu.
"Nifa bana iya bacci idan ba fitila" Ta fada tana kokarim tashi. Rikota yayi yana fad'in "Shiiiiii!
Hadiye maganarta tayi zuciyarta na bugawa kamar zata fito waje.
Duk da cikin duhu ne hakan be hanashi ganin tsoran dake fuskarta ba! Amma zai cire ma ta shi a yau insha Allah........
Ni kuwa ganin abinda ya fara yasa na kwaso alkalamina da silipas dina da nake sawa tun Zarah na budurwar har yanzu na fito da gudu kar inga abinda yafi karfin kaina lol....
*Alhamdulillahi Alhamdulillahi Allah Kaine abin godiya! Allah na gode maka! Kuskuren da nayi a cikin littafin nan Allah ka yafe min, Allah ka Kara mana basira ka cigaba da kiyaye mana alkalamin mu! Ka tsare mu da rubuta abinda bazai amfanin al'umma ba! Allah nagode Maka. Wad'anda na batawa a littafin nan kiyi hakuri! Ina godiya ga goyan bayan Dana samu daga gareku tun daga farko littafin nan har zuwa karshensa Nagode*
*Sai Kuma Allah ya kaimu bayan sallah Ina Nan tafi da labarina me taken BAKAR SAKAYYA! Ina fatan zaku nuna min kauna ta hanyar siyansa nagode*
*Number na 08142904255, kira ko Whatsapp*
Autar Mama ce.