Showing 42001 words to 45000 words out of 81464 words
Chapter 15 - MATA'UL HAYAT HAUSA NOVELS BY SAKINAT USMAN.txt
'yar Najeriyar ce tunda har kika san kanwata?
Mamaki ya sake bayyana a fuskar shuhuda Ibn Khaddab. Ta mayar da kallonta ga shuhuda Sagir Rabi'u tace: wannan kuma waye a gare ki? Shuhuda ta dubi Isah, tukunna ta maido da duban nata ga dayar shuhudar tace:
Yaya na ne Isah, wanda nake fada miki?
Shuhuda ibn khaddab tace: Auhi, Allah sarki yayanmu, barka da yini?
Kin amsawa ya yi, saboda ya ga ta raina masa hankali zahiran, in bacin rainin hankali su hadu da ita sannan yanzu ta nuna masa ba ta ta6a saninsa ba? Shuhudan ma ya dauke ta a wadda ta raina masa hankali, kuma MAKARYACIYA, ya tambaye ta shuhuda ibn khaddab ta nuna masa ba ta ta6a sanin mai sunan ba, sannan shuhuda ibn khaddab ta nuna masa shuhuda kanwarsa ba ta santa ba, hasalima ba su ta6a haduwa ba.
To ta ya kuma suka san juna bayan ya ji shuhuda kanwarsa ta yi ikirarin shuhuda ibn khaddab kawarta ce? Wannan salon rainin hankali ne da yawo da tunaninsa, abin da kuwa ba su sani ba shi ne, hankalinsa ya wuce nasu bare su sa shi a RUDANI, sa6anin haka ma sai dai shi ya saka su.
Shuhuda ibn khaddab tace gaba da cewa: Na yi ta neman yadda za a yi mu hadu na sanar da ke auren Sa'adatu ban samu ba. Shuhuda tace: Ayyah, ashe anyi auren Sa'adatu? Makaranta? Ta fasa ci gaba?
Isah ya ga za su dauke shi shawaragi sun share da shi sun ci gaba da hirarsu, saboda haka ransa ya sake 6aci, yace:
Shuhuda ina yayanki Abdallah ibn khaddab? Ta juyo da sauri alamun mamaki, sai ba tace komai ba, ta dubi shuhuda, tace:
Takwara wai don Allah ina yayanki ya sanni hat yasan Ya Abdallah?
Shuhuda tace: Ni ma mamakin da nake yi ke nan, saboda ba a nan ya yi rayuwarsa ba, kuma lokacin da ya dawo muna jarabawa har muka gama bai je makarantarmu ba, bare na ce ko a can ya sanki, yasan kuma yayanki da yake kawo ki makaranta.
Isah ya shiga RUDANI matsananci da wannan bayani da ya ji suna yi, anya kuwa shuhudan da ya hadu da ita ce a Misra yanzu a gabansa? Idan ba ita ba ce me ye alakar sunanta da sunan yayanta da waccan shuhuda? Idan ita ce me yasa ta ke son yawo da hankalinsa?
Tun ranar da ya soma ganinta da salon yawo da hankalinsa ta fara, tunda ita ta soma yi masa magana cewar ta ganshi kamar yayan Shuhuda Sagir Rabi'u, wannan kuwa idan ba kana da alaka da sanin hakan ba babu yadda za ayi ace bincike na sanadin suna ya kasance idan sun hadu ta shaida shi.
.
Ci gaban labari.
.
Bayan basu ta6a haduwa ba.
Abin tambayar a nan shine me yasa suka yi amfani da wannan salon gare shi? Shin kowaccensu sonsa ta ke yi ne shi yasa suke son juyar masa da kwalwa? A'a ba sonsa suke ba, so suke su juya shi kai-kai ce, su rikita shi, su sanya shi cikin RUDANI, Su kuma tsotse ruwan kansa bisa jagorancin shuhuda kanwarsa, don ita din ma ta nuna masa abubuwan RUDANI da yawa, saboda ranar da ya ce yana sonta kin amincewa tayi, daga baya kuma ta zo masa da amincewarta.
Tunda ya gane manufarsu kamata ya yi ya bi su da yadda suka zo masa. Murya a taushe kuma yana murmurshin da yake kara masa kwarjini, murmushin da yake fito da cikar HAIBARsa( Asalin sunan littafin)
Yace: Kada ki damu shuhuda ibn khaddab, haka nake na kasance mai binciken duk wata mace mai sunan kanwata, don haka ne ma zan iya cewa na sanki, na san yayanki Abdallah Ibn Khaddab.
Yanayinta ya nuna bata gamsu da bin da ya fada ba, amma jin karar hon din da ake ta doka mata wanda ke nuni ta tsarewa na bayanta hanyar fita, sai ba ta samu damar tankawa ba. Ta dubi shuhuda, tace: Don Allah minti daya na dai-daita tsayuwar motata.
Kafin ta amsa mata tuni har ta shige mota, Isah ya lura da zoben da ke yatsanta, wanda iri daya ne sak da wanda ya sa yowa shuhuda kanwarsa da shi lokacin da ya tsaya a kasar Misra.
Da sauri ya dubi yatsan shuhuda kanwarsa inda ya saka mata zoben, yana nan daram, saboda haka kama ce, ita ma ta sayi irinsa. Sai ya koma motarsa ya matso da ita, ya kasance motoci biyu ne yanzu a gabansa.
Kafin ya baro jikin motar har an sanyawa daya daga cikin motoci biyun da ke gabansa mai, saboda haka sai bai yi garajen barin gurin ba, ya tsaya. Cikin sa'a kuwa ita ma motar dake gaban tasa ba wani mai yawa aka zuba mata ba, sai shi. Ya fadi adadin yawan da yake so, aka zuba masa sannan ya iso gurinsu da motarsa.
Yana isowa shuhuda ibn khaddab ta cewa shuhuda.
To takwara sai gani na biyu, da fatan zaki cika alkawari idan bikin ya tashi ki kawo mana katin gayyata, da dai nace bazan kara zuwa bikin class mate dinmu ba, amma tunda ke ce da yayanmu ba ji, zan zo.
Shuhuda ta rusunar da kanta kasa saboda kunya, tunda Isah na tsaye a kanta.
Shuhuda ibn khaddab ta dubi Isah tana murmushi tace:
Yayanmu Allah ya sa yadda ka binciko ni saboda ina da sunan kanwarka, idan lokacin aurenku ya yi ka iya binciko ni ka kawo min katin gayyata. Kuma idan na koma gida zan sanarwa Yah Abdallah na hadu da abokinsa ISAH SADA RABI'U.
Tana kammala fadar haka ta bude murfin mota ta shige.
Isah tsaye ya yi sararo yana kallonta, ya kasa koda motsin kirki ne, ambatar cikakken sunansa da ta yi ya kara jefa shi cikin rudani.
Koda yake a wani 6angare bai kamata ya yi mamakin jin haka ba tunda ya ba su dama wata kila a cikin lokacin shuhuda ta samu sararin fayyace mata cikakken sunansa, ko kuma dama ta dade da saninsa,idan ya yi la'akari da maganganun da suka tattauna, wai makaranta daya suka yi.
Ta gabansa ta zo ta wuce yana kallonta tana kallonsa, tamkar tana son fada masa wani abu amma ba ta tanka ba, illa murmushin da ya ki 6acewa daga fuskarta.Shuhuda tace: Yaya mu tafi ko?
Ajiyar zuciya ya soma yi, kafin daga bisani ya girgiza kai ya nufi mota.Ta bi bayansa, duk suka shiga cikin motar ya soma jansu zuciyarsa ta gaza nutsuwa, haka kuma ya kasa daurewa, yana son cikakken bayani game da alakar da ke tsakanin shuhuda kanwarsa da shuhuda Ibn Khaddab, don haka yace
Amma kun sakani a RUDANI sosai. Ta dube shi tace: Wane irin rudani kuma yaya?
Yace: Wannan shuhudar ita ce muka hadu fa da ita a birnin Misra na tambaye ki kika ce baki santa ba, ita ma ta ce ba ki santa ba, amma ita ta sanki ta hanyar bincike a dalilin sunanku ya zamto daya, sai ga shi na ganta a Najeriya wanda a can ta tabbatar in ba ta ta6a zuwa Najeriya ba, a yadda na lura na kuma fahimta a cikin kalamanku kun dade da sanin juna, kamar ma a makaranta daya kuka yi, to mutumin da yace bai ta6a zuwa Najeriya ba ta ya kuma ya yi karatu a Najeriya har yasan wasu mutane da ke rayuwa a cikinta? Thats my question (wannan ita ce tambayata)
Shuhuda tace: Kai yaya anya kuwa ita ce wadda kuka hadu kuwa? Ita fa wannan a nan katsina ta ke, karatu ya kaita kano ta zauna gidan yayan mahafinta. Da farko ba ma shiri, saboda lokacin da na yi karatu ina rayuwa da hankali ne na awa biyu, sai gab da zamu soma jarabawa muka soma shiri har ma muke zama mu yi hira. A nan ne ma ta sanar da ni ita 'yar katsina ce, su uku mahaifanta suka haifa, daga ita sai yayanta Abdallah wanda yake karatu a Misra, sai kaninta Yusufa su ke nan mahaifinsu suka haifa. Mafarin ke nan suke samun ingantacciyar kulawa daga mahaifan nasu...
Har muka gama makaranta ba tasan gidanmu ba, ni ma haka dama kuma ba zuwa bikin kawaye nake ba, shi yasa tun da muka gama makaranta ba mu sake haduwa ba sai yau.
Ya gama sauraronta ne kawai, amma bai gama fahimtar inda kalaman nata suka sa gaba ba, shi dai ya yarda ya kuma amintar ma kansa, wannan shuhudar da suka hadu a Misra ce, wadda ke bin kasashe yawon majalisin malamai, shuhudan da ta sanar da shi iyaye da kakanninta dukkansu 'yan asalin Misra ne. Ya fi amincewa lokacin da suka hadu a Misra wani sanadi ne ya kaita, amma ta 6oye masa saboda sun shirya hakan da kanwarsa shuhuda, wannan shi ne hakikanin abin yarda.
Tammat bihamdillah
Gare ku fa makaranta? Kun yarda? Anya kuwa? Kai ko ni ban yarda ba, akwai dai yadda akayi.
Shin ina Uncle Hamza da zuwairiyyarsa?
Kada fa a yi danyen kasko mana? Ai kun fahimci labarin MATA'UL HAYAT ko? Idan ma ba ku fahimta ba, zaku fahimta ne idan kuka ji muhimmin sakon da ya kunsa.
Kada dai ku manta da tarin abubuwan da suka faru tun daga littafi na farko zuwa na biyu. Musamman rayuka uku da aka rasa saboda shuhuda, da sauran abubuwan da suka biyo baya?
Izra'el,Libhas,Tanzif me ye alakarsu da shuhuda? Ina aka samo keken doki da ta ke zuwa Misra kamar yadda ta fawa uncle Hamza?
Yakub, Abdallah ibn khaddab, da shuhuda ibn khaddab duk me ye alakarsu da shuhuda.
Kai-kai-kai!!! Akwai fa yawa abubuwan, amma dai mu yi hakuri,juriya zuwa MATA'UL HAYAT-3 don jin yadda zata kaya.
Shin Hamza ko Isah? Akwai dai sadaukarwa, waye mai sadaukarwar? Kuma ta ya ya?
ada Hausa Book stories
MATA UL HAYAT(JIN DADIN RAYUWA)Book 3
¤¤21¤¤
.
KUSKURE.
.
Idan aka duba littafi na biyu page na 150 sakin layi na karshe an yi amfani da sunan Abdallah Ibn Khaddab a maimakon Abubakar Ibn Khaddab har zuwa karshen littafin a haka ya kare.
Matsalar ta faru ne daga gare ni ne, da parko Abdallah shi ne asalin sunan, bisa wani dalili na maida Abubakar, na ci gaba da bi ina replace da Abubakar, tuun daga page din da aka samu matsalar gaskiya ban duba ba, lokacin ba ni da lafiya, kuma har aka gama aikin ban ga kuskuren ba, sai da na yi nisa a 3 sannan ma na fuskanta.
.
A gafarceni bisa wannan kuskure.
Zahra u Baba Yakasai.
.
Allah ya jin kanta da rahama ya saka mata da Aljannah.....ameen.
.
Ci gaban labari..
.
Shuhuda ta dan dube shi a kai kaice, tukunna ta ci gaba da cewa. 'Shuhuda tana da mutumci, ta na da kaifiyya da bincike akan abin da ya shafi harkar taimako. Ka ganta dai yarinya ko, amma wallahi idan ka ji irin mutanen da ta binciko ta taimaka musu abin sai ya ba ka mamaki matuka. Shi yasa a rayuwa duk wanda ya kasance yana da kaifiyya ya ji dadi'.
Wannan kalma ce da Shuhuda Misra ta yi amfani da ita a lokacin da ta ke sanar da shi yadda aka yi tasan kanwarsa Shuhuda, ta ce tana amfani da bincike ne gami da kaifiyya. Wannan ma kadai ya isa ya zamo hujja agare shi, Shuhudan Misra ce ya yi tazali da ita a Nigeria.
Ya so ta ba shi lambarta, gami da adireshin gidansu a can Misra ta goce masa, kuma babu amfanin da ba shi lambarta don gudun kada idan sun hadu a Nigeria ta nuna ba ta sanshi ba ya kira wayarta ta yi kara a gabansu asirinsu ya tonu, shirin da suka yi ya ruguje.
Lallai idan haka ne ya ci a jinjinawa wannan kaifin hankali nasu, tunda har suka iya wannan tufkar ba tare da an samu rauninsu ba kasancewarsu MATA masu tarin rauni, da kuma kuruciya. Domin mace mai shekaru sittin a duniya ba ta kai namiji mai shekaru ashirin kaifin hankali ba, su dama mata haka suke, rauni ne da su. Abin da suke tunanin idan sun yi dai-dai ne, amma idan maza suka tace sai aga abin ba dai-dai ba.
.
(Sadin Mama yar Anty, ni dai na ce what a man can do, woman can do far much better )
.
Ku yi hakuri yan uwa na mata, kada kuce na yanke mu, gaskiya ce idan kuwa gaskiya ta zo ana son fadarta komai dacinta.
.
Shiru ya yi bai kuma tanka mata ba domin ta gama yawo da hankalinsa, ta gama kunce masa duk wata jijiya ta tufka da warwarashi.
.
BABI NA GOMA
TABDIJAN!
Shagari low-cost nan ne unguwar da Haj Asmo ta ke, a kofar gidan suka tsaya suna jiran maigadi ya bude musu get. Koda ya bude Isah ya sulala da motar cikin harabar gidan, Shuhuda ta bude kofa ta fita ta nufi hanyar shiga cikin gidan.
Isah ya sanya baki ya kirayi sunanata. Ta juyo tana dubanshi ba tare da ta tako ba.
Ya ce, "ki tsaya mu shiga da tsarabarsu mana".
Cikin shagwaba ta ce masa, "mu tara shiga mana, ba sai a samu wadanda zasu shiga da tsarabar ba?"
Yana kyabe baki ya ce da ita.
"Shi ke nan".
Yara kusan su shida suka tarar a falon suna kallo, da ya ke sun san Shuhuda don haka suna ganinta suka mike da sauri suna mata oyoyo-oyoyo.
Ta dauki Sajida 'yar shakara hudu ta saba a kafadarta.
Hayaniyar yaran ce ta fito da Haj.Asmo daga dakinta. Ita ma tana ganinsu ta washe fuska.
"Ni kam na yi fushi, yanzu saboda Allah Isah sai yau kake zuwar min?"
Yana sosa keya irin na maza, ya ce,
"Ayi hakuri Goggo".
Ta ce "idan ban yi hakurin ba ai da ba zaku ma gane gidan ba, duk da kuwa ka dauko wannan marar son zumuncin. Ta hana min 'ya zaman lafiya, kullum kuka wai ita akaita gurin Aunty Shuhuda".
Su duka suka yi murmushi, Shuhuda ta dora da cewa.
"Ki yi hakuri Goggo, dama karatu ne yake hana ni zuwa, to yanzu kuma an gama kafin a tafi wata".
Haj.Asmo ta ce.
"Idan an daura aure ko? Ai ni an fada min kun hada kanku....."
Kunya ta lullube Shuhuda har shi kansa Isah, aka rasa wanda zai ce wani abu.
Haj.Asmo ta lura da hakan, sai ba ta ja zancen ba, ta dubi Sajida da har lokacin ta ke makale a kafadar Shuhuda ta ce.
"To a sauka a bar Aunty ta zauna ko?"
Ba musu yarinyar ta soma kokarin sauka, Shuhuda ta sauke ta, ta zauna akan kujera. Haj. Asmo ta ce da daya daga cikin matasan matan.
"Nafisa a kawo musu abinci da ruwa ko?".
Nafisa ta nufi kicin don hado musu abinci.
Isah ya dubi sauran yan matan, ya ce.
"Ku taso mu je ku kwaso tsarabarku".
Sun kwaso kayan tsarabar wanda suka ware na gidan, sauran kuma suka barshi a mota.
Sai da suka soma gaisawa sannan suka ci binci, aka shiga hira.
Karfe shida na yamma, Isah da Shuhuda suna zaune a falon Haj. Asmo da ita kanta Haj. Asmon suna hira, Musabahu ya shigo falon hannunsa rike da waya yana murmushi ya ce.
"Afuwa, wani uzuri ne ya tsayar da ni".
Isah ya kawar da kai, ya ce.
"Ba ni zaka bawa hakuri ba, kanka zaka baiwa, domin yiwa wani yiwa kai ne, kuma duk wanda ya gyara ya sani".
Musbahu yana kokarin zama akan kujera ya ce.
"Kin ji shi ko Sister?"
Shuhuda ta kawar da kai, ta ce.
"Ni kyale ni, bani da lokacinka. Bayan tunda muka zo aka sanar maka isowarmu, amma ba ka tashi zuwa ba sai yanzu da ka ga dare ya yi, don kada mu fita zaga gari ko?"
Musbahu ya saka dariya, ya ce.
"Shi yasa ina shigowa na soma neman afuwa, kuma sha kuruminki tunda dai kwana zaku yi ai magana ta kare, gobe idan muka dinga yawo sai kin ce kin gaji".
Haj. Asmo ta saka musu baki.
"Ai sun ce da safe zasu wuce. saboda zasu karare. Kuma a goben zasu koma kano".
Ya ce "shi ke nan, sai a yi min uzuri".
Bayan sallar magariba Isah da Musbahu su ka fito daga masallaci. Wayar Musbahu tayi kar. Yana dubawa ya ga wande ke kiransa, kafin ya duba ya dubi Isah ya ce.
"Ina ji se ka rakani wani guri saboda wannan kiran da aka yi min nasan mafita".
Kafin Isah ya magantu, Musbahu ya kara wayar a kunnansa, yana cewa.
"Ya aka yi ne Malami?"
Ya dan saurara kadan don jin abinda ake fada masa, sannan ya ja fasali ya ce.
"Malami ni a ganina ka baiwa Allah zabi idan Zuwai din ce alkhairi. Allah Ya tabbatar, idan kuma Dodoridon ne.... Don Allah tsaya.... Na daina.. Kana jina? Ba na son ka sanya kanka a cikin taskun rayuwa, ka yi hakuri...."
Ya sake saurarawa na wani lokaci, sannan ya ce.
"Kai kasan yadda ta ke, mu kam ba ka taba nuna mana hotonta ba, don haka maganar musun kyawunta ko kwarjininta bai taso ba.... Kuma yarinyar da aka tabbatar maka da MAYYA ce na me zaka....... No! Wallahi na fi kowa son ka, son da nake maka din ne ma yasa nake nusar da kai tarin kalubalen da kake neman fadawa.... Shi ke nan, zan shigo, baki muka yi ma ai da tuni ka ganni.... To sai na shigo din".
Ya kashe wayar cike da alhini. Isah a tun soma wayar ya tsurawa Musbahu ido, mamakin kalaman da suka tattauna yake, don haka Musbahu na kashe wayar ya ce.
"Me ya ke faruwa?"
Musbahu ya yarfar da kai, ya ce.
"Wallahi wani aboki na ne yake cikin rudani. Wata yarinya ce Allah Ya hada su da ita, yana matukar sonta amma matsalar ne barkatai, ka ga dai na farko wani yayanta Yakub ya same shi ya fada masa auren zumunci za a yi mata, amma shi ya kasa hakura da ita, kuma fa akwai wata kanwar mahaifinsa da ta ce yarinyar mayya ce, shi kansa yana tunanin kasantuwarta jinsin mutane, saboda kana kallonta zaka ga tsabar kyau kamar aljana.
Amma sonta ya makantar da shi kana ji yanzu har an kai fagen da yake tunanin tuburburewa lallai sai ya aure ta".
Isah ya girgiza kai cikin tausayawa.ya ce.
"So ke nan! Kasan idan mutum ya na son abu hankalinsa ba zai taba kwanciya ba har sai ya ga ya mallaki abin"..
Musbahu ya ce. "Ai ko dai, amma wani lokacin yana da kyau mutum ya dinga ragewa kansa kaifin son abu idan har ya soma katari da matsalolin da abin zai saka shi".
A dai-dai lokacin suka karaso gidan.
Sun gama cin abinci, Isah da Musbahu suka mike zasu fita. Tsam! Shuhuda ita ma ta mike tana cewa.
"Ina zaku?"
Musbahu ya yi murmushi, tukunna ya ce.
"Zamu je wani guri ne mu dawo".
Ta ce, "Ai kafarku kafata".
Nusaiba kanwar Musbahu wadda