Showing 132001 words to 135000 words out of 143522 words
Chapter 45 - DAHUWAR 'KAHO BOOK COMPLETE Hausa Novels By Ameera Adam.pdf
da kuka kwaso
Allah Ya jarabce ni da shi." Tana gama maganar ta shige ciki. Kamar Yaya Inu zai ɗora hannu a
ka, haka ya fice daga sashen Inno abin duniya ya haɗe masa.
Yamma ce sakaliya, sanyin la'asar tuni ya riga da ya sauko. Fadar Mai gari cike take da
mutane ana zaune ana zaman fada. Mafi yawan mutanen da suke zaune gulma ce ta kawo su,
a kan abin da ya faru da Mai gari. Shi ma da yake ya fahimci haka sai ya tsuke fuska, ya dubi
su Mahmud da suke takure kamar zakarun da aka tsamo daga ruwa ya ce. "A madadinmu da na talakawan yankinmu muna yi muku barka da zuwa. Muna buƙatar
ɗayan bayan ɗaya, ku gabatar da kanku a gaban mutane. Mudassir ne ya ɗan muskuta zai yi
magana, Mai gari ya yi wa Mahmud ƙuri da ido ya ce.
"Kai yaro, kamar na san fuskar nan taka?"
Cikin Mahmud ya karta, amma sai ya yi ta maza ya ce. "A'a ranka shi daɗe, sai dai idan mai
kama da ni ka sani. "
Jin Mai gari ya yi shiru ya sa Mudassir ya furta, "Ni dai sunana Mudassir Najib, ɗaya daga cikin
ɗaliban da aka turo daga babbar Jami'a yin bautar ƙasa (NYSC)." A fili Mai gari ya faɗaɗa
fara'arsa yana jinjina kai, saboda ya ji ya ce bautar ƙasa suka zo don haka sai ya ci banza. Har
ya fara lissafa kansa, a sahun mahajjatan da za su sauke farali a bana. Duba da irin aikin gonar
da ya ayyana zai jibga wa su Mudassir. Shi ma Mahmud ya gabatar da kansa, sannan Mai gari
ya fara baza babbar yana haɗe rai ya ce.
"Tun da har Gwamnati ta aiko ku garin nan, na tabbata babbar Masarauta ƙasar nan ta san
irin gudunmawar da nake bayarwa a ƙasata. A don haka, ya zame muku wajibi ku zage damtse
ku yi mini noma yadda ya kamata." Mai gari ya zaro ido waje cike sa barazana ya sake dubansu
ya ce.
"Ku dube ni nan, bautar ƙasa ba wasa ba ce yara ina fatan kun gane. Domin shinkafar da kuke
miƙe ƙafa kuke ci, ita ma sai da aka gama bauta mata sannan ta bauta muku a cikinku.
"Ammm amma ina ganin kamar ba ka fahimce mu ranka shi daɗe. Service muka zo fa, ga
wannan takardar za ka iya karantawa." Mahmud ya ƙarasa maganar yana miƙa masa takardar.
Gaban Mai gari ya faɗi, da ya ga ya miƙa masa wata zungureriyar takarda mai cike da rubutun
turanci. Sai da ya fakaice su ya sharce gumin fuskarsa, sannan ya riƙe takardar yana ɗan
matse idanu ya fara karantawa.
"Assalamu Alaikum. Ni Mai girma gwamna, na aiko waɗannan jajirtattu kuma haziƙan ɗaliban
nan, domin su zo garin nan su taya Mai gari aikin gona wanda muke kira da bautar ƙasa. Kuma
a don haka, muke jan kunnensu domin su jajirce wurin yin aiki tuƙuru. Idan ba haka ba, za mu
zartar musu da mummunan hukunci." Mai gari ya ɗago yana muzurai, daga can ƙasa ya ga
wani rubutu da lambar waya har da saka hannu, sai ya ce.
"Ga lambar wayata nan ni mai girma gwamna, duk wani ƙorafi da kuke da shi kai tsaye za ku
iya tuntuɓa ta. Kuma duk wanda ya yi ba daidai ba a cikinsu, muna bayar da umarnin Mai gari
ya saɓa masa. Idan da hali ma ya ci tararsa."
Tun da ya fara jawabin Mahmud da Mudassir, suka yi zuru suna kallonsa cike da mamaki.
Mutanen da ke wurin suka ɗauki sowa cikin kambaba Mai gari suka ce. "Allah Ya ja zamaninka
mai martaba. Haƙiƙa gado ba karanbani ba, duk wanda ya san gidanku ya san mane ne mulki."
Mai gari ya fara zuba doro yana kalle-kalle cikin izza. Hambali da yake gefe cikin tsananin jin
kunya ya ce.
"Allah Ya taimake ka, idan na fahimce su fa kamar ba haka suke nufi ba. Duk da dai ni ma
ba karatu na yi mai zurfi ba, iya ka ta diploma. Idan aka ce an tura ɗalibi NYSC wato bautar
ƙasa, ana nufin ya hidimtawa ƙasa ta hanyar bunƙasata da ciyar da ita gaba. Kuma kamar wani
ƙarin horo ne, da ɗalibai suke sake gogewa; domin su zama shugabanni ko al'ummar da za a yi
alfahari da su a gobe. Amma a gafarce ni ranka shi daɗe, idan na faɗi ba daidai ba."
Tun bai gama magana ba Mai gari ya fusata. Rai a ɓace ya nuna Shazali ya ce. "A
kanannaɗe shi a hukunta shi, mu zai kawowa raini a gaban fada? Shazali, yaron nan yana nufin
fada ba ta san me take yi ba ne?"
"Allah Ya taimake ka, abin da bawan Allahn nan ya faɗa fa haka ne. Ba aikin gona muka zo
ba, kamar yadda ka faɗa..."
Da sauri Mai gari ya katse Mahmud.
"Kai yaro ka iya bakinka. Shin ya bari mun gama fesar da maganganun bakinmu ne? Ko
numfashinmu ya tara? Abin da muke shirin faɗa kenan ya yi mana katsalandan, don haka dole
a hukunta shi." Kallon tsaf Mahmud ya yi masa, yana jinjina ƙarfinsa. Bayan Mai gari ya
sallame su, suna tafe a hanya ya ce.
"Na lura da Mai garin nan tsaf, ashe duk burgagin banza yake yi. Ba abin da ya sani wallahi,
kawai su yake naɗewa."
Mudassir ya yi murmushi ya ce, "Ai kuwa sai dai su ya naɗe su, don idan ya shiga tawa gonar
sai na yi masa naɗin da ya fi na huhun goro." Gabaɗaya suka saka dariya.
Baba Sale shi da Uwale ba su suka dawo daga asibiti ba sai yamma liƙis, saboda bayan likita
ya gwada Ɗan Bishir sai da aka ba shi gwaje-gwaje. Bayan sakamakon ya fito aka yi masa
dressing, sannan aka rubuta musu magungunan. Duk soyayyar da Baba Sale yake yi masa
haka ya danne shi da ana wanke masa, saboda likita ya tabbatar masa da matuƙar bai samu
kyakkyawar kulawa ba komai zai iya faruwa, tun da har wurin ya fara ruwa yana ɗan wari.
Likitan ya gargaɗe su sosai, wurin kula da tsaftar sabon gyambo koda ba na kaciya ba ne,
sannan ya ce bayan kwana uku su koma a sake duba jikin nasa. Bayan sun koma gida, ko
zama bai yi ba ya nufi gidan Bala wanzan. A ƙofar gida ya tsaya ya ce a yi masa sallama da shi,
yana nan tsaye yaron ya dawo tare da wani ɗan matashin saurayi.
"Kai Tasi'u, ina mahaifinka yake?"
Baba Sale ya furta fuska babu walwala. Matashin da ba zai wuce shekara goma sha uku ba,
ya rausayar da murya cike da neman tausasawa ya ce.
"An tafi da Baba ofishin 'yan sanda ɗazu."
Da sauri Baba Sale ya ce, "Ofishin 'yansanda fa? Me ya yi aka kai shi can?"
"Ban san takamaiman abin da ya yi ba, amma an ce wai Idi Naira ya yi wa aska, kuma wai ana
zargin yana da cutar ƙanjamau!"
"La'ilaha'illa'illahu Muhammadur Rasulillahi, Sallallahu alaihi wasallam. Ɗan Tasi me
kunnuwana suke zuƙo mini? Kada ka ce mini Ɗan Bishiriri ya kamu, wayyo Allah Tasi riƙe ni da
ƙarfi duhu nake gani."
Baba Sale ya yi maganar yana jin wata irin hajijiya tana yin ɗiban karan mahaukaciya da shi.
Da sauri Tasi'u ya riƙe shi yana kiran sunansa da ƙarfi, "Baban Ɗan Bishir lafiya." A hankali
Baba Sale ya ɗago duk da ba ya gane abin da Tasi'u yake faɗa sosai ya ce, "Tasi'u maza kai ni
ofishin 'yansandan."
Kamar sabon ɗan maye haka suka tafi Tasi'u yana riƙe da shi, don har suka ƙarasa wani irin
layi yake yi idanunsa suna yi masa gizo. Su Baba Sale suna zuwa, suka samu Bala Wanzan a
tsaye yana bayani.
"Wallahi tallahi yallaɓai ban taɓa sanin Idi Naira yana da cutar abar nan ba, ni ko sunanta ba
na son faɗa. Kuma babban tashin hankalina yaran da na yi wa shayi, a ranar da wannan
tsautsayin ya afku. Domin su ne masu tasowa ba su mori ƙuruciya ba..."
Wata irin ƙara suka ji gijiiiiiif Baba Sale ya faɗa ta saman kanta, saboda tun a bayanin farko da
ya ji Bala wanzan yana yi, ya ji ƙafafuwansa ba za su iya ɗaukarsa ba. Kalaman Bala na ƙarshe
suka sa ya ga wani baƙin duhu ta lulluɓe idonsa, numfashinsa ya ɗauke.
"Subhnallah! Waye wannan? Lafiya?"
Wani kurtun ɗansanda ya ƙarasa kansa yana tambaya. Tasi'u ne ya yi musu bayanin abin da
ya faru tsakaninsa da Baba Sale, har zuwansu cikin station ɗin. Ruwa aka ɗebo aka zuba
masa, a hankali ya farfaɗo yana daga kwance yake kallon mutane ɗaiɗai. Ya yunƙura a hankali
ya zauna sai a lokacin komai ya shiga dawo masa.
"Yallaɓai Ɗan Bishir, kun bincika mini Ɗan Bishiriri."
Wani Sergent da ya fahimci Baba Sale, ya dubi Bala Wanzan ya ce, "Kai Wanzan ka yi wa
yaron wannan mutumin kaciya ne?"
Da yake a lokacin an mayar da Bala cikin cell, yana daga ciki ya ce. "Eh na yi masa yallaɓ..."
Tun Bala bai gama magana ba Baba Sale ya sake sumewa a wurin, haka suka sake zuba
masa ruwa ya sake farfaɗowa. Sai dai su kansu abin da ya fi ɗaga hankalinsu, yadda Baba
Sale yana farfaɗowa zai sake suma. Har sun lura ko ya farfaɗo ba ya zama cikin hayyacinsa.
Don haka suka tattarashi hankali a tashe suka yi asibiti da shi, sai bayan sun je suka saka
Tasi'u ya yi musu rakiya har gida aka sanar da Uwale da su Baba Ibrahim halin da ake ciki.
Tun da suka fito daga asibitin yake zabga sauri, cikin sassarfa ta rufa masa baya ganin ya
fara yi mata nisa ya sa ta fara ƙwala masa kira.
"Masoyi! Masoyi don Allah ka jira ni saurin me kake yi kamar za ka tashi sama."
"Ya muke da jirgin sama? Na ce ya muke da shi?"
Baba Labaran ya furta a zafafe.
Sororo ta yi tana kallonsa don har tsoro-tsoro ta ji, ganin yana yi mata faɗan da ba ta saba
gani a tattare da shi ba. Hasali ma ba ta ga abin faɗa a maganarta ba.
"Asibiti na uku kenan a yau muna zuwa suna yi miki gwaji, amma duk maganarsu ɗaya kamar
haɗin baki. To magana ta gaskiya na fi son mace a haihuwar fari, saboda magaji nake nema.
Haka kawai duka asibitocin sun ce mace suka gani. Wallahi da sake an ba wa mai kaza kai." Da
mamaki ta dube shi ta ce. "Da sake fa ka ce Masoyi? Shin butulci za ka yi wa uabangiji ne? Mutane nawa ne suke
neman haihuwar ba su samu ba, mace ko namiji mai albarka ya kamata ka roƙa."
Maimakon ya ba ta amsa sai kawai ya saki tsaki ya yi gaba yana faɗin.
"Kanki ake ji, ni na gama faɗar ra'ayina."
Daskarewa Rahinatu ta yi, ta ɗora hannunta a kan ƙaramin cikin jikinta da bai fi wata uku da
satika ba. Cikin sanyin murya ta ce. "Dama duk soyayyar da mutumin nan yake yi mini ta fatar
baki ce? Haƙiƙa Labaran ya cika butulu."
Daga haka ta fara takawa a hankali, ta rufa masa baya tana jin zuciyarta na suya.
Damuwa haɗe da tarin ayarin tunaninnika ne suka cunkushe masa kwanya, saboda Indo da
su Hansatu sun nemi mayar da shi kamar mahaukaci. Don da sun kalle shi sai kowacce ta
gimtse fuska, yana bada baya sai su kwashe da dariya. Rumfar Tsalha mai kayan miya nufa,
yana zuwa ya yi sallama amma babu wanda ya amsa masa. Kamar haɗin baki, lokaci ɗaya
mutanen cikin rumfar suka watse . Turus Yaya Inu ya yi, yana shirin magana ya ji Tsalha ya ce,
"A gaskiya malam Inusa ka dakata da zuwa cikin rumfata, saboda ka da ka kawashe mini
albarkar cinikayyata. Ba zan ɓoye maka Inusa ka san dai ni abokinka ne, maganar haihuwar
zabiyar nan fa ya karaɗe ciki da wajen garin nan don haka ka yi hattara." Daga haka Malam
Tsalha ya koma kujera ya zauna yana haɗe rai, don kada Yaya Inu ya samu fuskar zama.
Kamar zakaran da aka tsamo daga cikin ruwa haka Yaya Inu ya fito ya nufi hanyar gida,
tunanin Zuly matashin kai ce ta faɗo masa. Ya saki murmushi ya nufi ƙofar gidansu. Ƙaramar
wayarsa ya ciro ya kira ta, ba a ɗauki lokaci ba ta fito tana taunar cingam.
"Haskena ashe kaine da yamma haka?"
Yaya Inu ya saki murmushi ya ce, "Takanas na shiryo na zo na ganki domin na huce takaicin
zuciyata, saboda ke kaɗai ce hasken da ke yaye duhun da ke ɗanfare a ciki."
Sai da ta hura kwai da cingam ta ce, "Wani zance nake ji yana tashi, wai an haifar maka
zabiya 'yan gidanmu har sun fara bala'i. Ni kuwa na ce duk bala'insu ba zabiya ba, ko rabi
mutum rabi aljan aka haifa maka babu wanda ya isa ya han ni aurenka." Farinciki ya sa ta Yaya
Inu ya zaro rafa kuɗi har dubu goma ya miƙa mata.
"Ki sha lemo da wannan, masoyiyata kuma hasken zuciyar Inusa."
Alewa ta buɗe ta wurga a baki ta tsotsa, sannan ta zaro ta miƙa masa cike da kissa. Cikin so
da ƙauna Yaya Inu ya karɓi alewar, ya jefa a baki ya yi mata sallama. Yana gab da shiga gida ya
hango wani mai magani, yana tafe da wata ƙatuwar Mp3 da wani faffaɗan kwando mai ɗauke
da magungunan maza a ciki.
"Ina mai matsalar kuzari? Ina namijin da ya rako maza? To ya hanzarta ya zo ga adamalmala.
Maganina rabo ne, maganina sa'a ce. Alhaji sai mai tsananin rabo ne zai dace na ba shi, ina
mazan da basir ya jima da yi musu illa? Alhaji ba ka nisan zango wurin tuƙa sitiyarin mota? Don
Allah ka zo, ga mai adamalmala ya dawo. Idan na bar garin nan ba zan dawo ba, maza kaɗai
nake ba wa magungunana domin na fi kishinsu a kan mata. Alhaji ko Malam kada ka ji kunyar
karɓa, indai matsalarka a ɓangare iyali ne ta kau. Sabon aure za ka yi ne? Ko kuwa ka rasa
gane kan matanka ne? To maza gangaro ka karɓa sadakar ƙalilance, ni dai ba na rowa domin
burina na kankaro mutumci a wurin maigida."
Yaya Inu ya tsaya a jikin bishiya ya yafito shi da hannu, Mai maganin ya ƙarasa wurinsa
adaidai lokacin Na Balaraba ya ƙarasa ta wurin zai wuce.
"Kai wa nake gani kamar Gambo, ko idanuna ne?"
Cewar Gambo.
Mai maganin ya ɗago yana kallon Na Balaraba da sauri ya ce, "Kai! Wa nake gani kamar Na
Balaraba? Dama rai kan ga rai?"
Yaya Inu ya washe baki, "Na Balaraba ka san shi ne?"
Na Balaraba ya furta, "Na san shi farin sani, yanzu ne dai zumunci ya zama yanda ya zama,
shekara biyar zuwa shida rabona da shi."
Yaya Inu ya washe baki ya ce, "Ka ce faɗuwa ta yi daidai da zama, dama kiransa na yi zan
sayi magani."
Mutumin tun da ya yi tsaye yake ƙarewa Yaya Inu kallo, har sai da gabansa ya faɗi. Amma jin
Na Balaraba ya ce ya san shi ya sa ya saki jikinsa.
"Haba ba ka da damuwa Inusa, ka sayi maganinka wannan da kake gani ba na shakku a
kansa."
Yaya Inu ya nuna wani magani ya ce yana son saya, Mai maganin ya yi zaraf ya ce. "A'a mai
gida bari na ba ka wannan, ai wannan shi ne gagara-badau an buga da kai an barka." Ya
ƙarasa maganar yana miƙa masa wata roba ƙarama ya ɗora da cewa.
"Yanzu kana komawa gida tun da magariba ta ƙarato ka shafa shi, sai bayan minti talatin ka
wanke da ruwan ɗumi. Ka zuba wa sarautar Allah ido za ka ba ni labari idan na sake dawowa."
Jiki yana rawa Yaya Inu ya zaro kuɗi ya biya. Bayan Mai maganin ya tafi Baba Ado da yake
gefe ya ce masa.
"Yanzu Allah Yaya, ba za ka raba kanka da gabzawa kanka waɗannan magungunan barkatai
ba? Haka kawai maganin kare da doki kowa na ka ne, ba ka duba inganci ko ka je wurin masu
magungunan gargajiya waɗanda suka san kansu ka saya..."
A sheƙe Yaya Inu ya katse shi.
"Kai dakata kada ka yi mini rashin kunya, tuzurun banza da wofi. Wai har da su kaza a cin
danƙo? Kai da ko arzikin auren ba ka samu ba, shi ne har za ka zauna kana yi mini fi'ili? Tun da
kai 'yan mata aljanu sun gama tsuƙe jijiyoyin jikinka, ai sai ka bar masu raya sunnar Annabi su
yi. Da uwar kuɗina nake saya babu wani ƙato da yake saya mini, don haka kada ka sake shiga
hurumina."
Yaya Inu yana gama magana