Showing 6001 words to 9000 words out of 112612 words

Chapter 3 - BABBAN GORO BOOK COMPLETE HAUSA NOVELS BY SUMAYYA TAKORI.doc

lokacin. Sai dai ita Safah din babu wani tunanin hakan ko wani abu can soyayya a gabanta, face karatunta. Ita bata sani ba bata san wannan ba. Ita abinda ta rike a ranta kawai Ya Imam Yayan ta ne, da suke ciki daya. Bayan wannan ba wani abu duk da tana ji kowa ce mata yake matar Imam. Wata irin miskilar yarinya ce da dawuya ka fahimci inda tasa gaba, domin fuskarta bata nuna abinda ke zuciyarta.
Ta iya danne abu cikin zuciyarta komin girmansa da muhimmancinsa, koda dannewar zata cutar da ita. Ta dage da son cimma burinta na son zama cikakkiyar likitar hakori (Dentist). Ko don ta gyarawa Marwah cinyayyun hakoranta da chocolate ta cinye, ta kuma likawa Hajiya hakoran roba biyu da suka fice daga bakinta na kasa. Yayin da Marwa ke da burin zama cikakkiyar mai harhada magunguna (pharmacist), ko don ta harhadowa Hajiya magunguna masu inganci ta daina shan jike-jiken data ke sha duk sanda wata lalura ta sameta don ita bata yarda da maganin asibiti ba.
Suna son Kakarsu sosai yadda take son su, domin rabin rayuwarsu tareda ita suke yi, su sata a tsakiya su kwana tare sai in sun koma makarantar kwana ne Hajiya zata kwana ita kadai, sun damu da ita har fiye da Uwarsu don yadda take kula dasu, kuma rikon da take yi musu ba rikon Kaka bane, riko ne na gangariyar tarbiyyah da cusa musu kyawawan dabi u a zukatansu tun suna kanana.
Mami kowa ya san Imam ta fi so kuma a gaban kowa bayyanawa take, Shahida ce dai gata nan halinta sai Allah domin tanada son girma, bata wasa dasu kada su rainata. Suma kuma tsoronta suke fiye da Mami don haka ne Hajiya bata shiri da Shahidah tace tana takurawa kannenta, don bata san yaya sukayi ta addua kafin Allah Ya basu su ba.
Suna da bambancin ra ayi a abubuwa da dama, basu taba hada ra ayi a kan son abu guda ba, kamar ba  yan biyu ba.
Kamar yadda suke da bambancin ra ayi a al amuran rayuwa, haka suke da bambanci a akida da halayya.
Safah shiru-shiru ce bata son hayaniya, bata son shiga jama a, bata da wani buri da ya wuce karatunnan nata. Takarda da biro sune manya-manyan abokan hirarta. Kowa nata ya san hakan, don haka ba a fiya shiga shirginta a gidan ba, in zata kwana uku ba a ganta a falo ba ba wanda ya damu, ta zabi rayuwar kadaici da goal attainment (cimma buri) fiye da komai.
Duk wasu abubuwa na debe kewa da zamani ya kawo Safah bata da sha awa a kansu, kamar yanar gizo da abubuwan da ta kawo, waya da sauransu.
A ganin Safah, duk da karancin shekarunta a lokacin, wadannan duk ababene na asarar lokaci irin na bature, a kokarinsa na nakasa kwakwalwar matasan mu su ki karatu, don yadda mu muka mallaka rayuwar mu a kansu (social networks), shi ba haka yake amfani dasu ba, yana amfani dasu ne kawai a lokacin da bukatar hakan ta taso ba kamar mu ba da muke kwana mu wuni muna amfani da ita, kuma ba za su amfane ta ko su kareta da komai ba, illa su karar mata da abu mafi daraja a rayuwar dan adam wato LOKACI.
Babu yadda Imam bai yi da ita ba ta rike waya ko don su dinga gaisawa amma ta ki, don haka yake yi mata e-mail, wanda bai san sau dubu ya aiko da sakon ko gani bata yi ba. Shikansa email ID din Marwah ce ta bude shi da combination na sunansu, itace kuma ke karantawa ta bashi amsa, cikin yi masa dariyar mai son alhuda-huda bata san yana yi ba, da dadadan kalamai masu taushi da tausasa zuciya da take koyowa a karance-karancenta na zamani, ita kanta bata san dalilinta na damuwa da Ya Imam ba yadda ba a zato.
Yayin da abokiyar tagwaitakarta ta kasance akasin ta. Marwah Aliko Dan Kasa, fara ce sol mai siririn hanci irin na Hajiya Zainab, ba ta da yalwar suma, sai dai ba ta rasa na kullewa cikin  ribbon ba.
Yarinya ce mai son hulda da jama a, tana da wayewar kai fiye da  yar uwarta, sakamakon huldar ta da mutane daban-daban tana da kawaye sosai a makaranta, don haka tafi Safah sanin zamani da halin da yake ciki.
Tana da son sarrafa  yanar gizo da shiga duk wani sabon abu da zamani ya kawo; su facebook, bbm, whatsapp, android, twitter da sauransu.
Marwah ta san tun tana karama Yaya Imam bai damu da ita ba, ita kuma nan duniya babu wanda ta damu da shi irin sa. Ba ta iya kwana bakwai ba ta tura mishi sakon gaisuwa ba, amma da sunan Safah.
Marwah ta sha zama ta yi tunani a kan-kanta, me yasa Yaya Imam bai damu da ita ba? Duk da kowa ya san Safah yake so da aure, wannan ba hujja ba ce da ita zai watsar da ita a matsayinta na jininsa,  yar uwarshi ta jini.
Safahn da yake so ba ta damu da shi ba, karatunta kawai take. Shin idan ya san ko sau daya Safah ba ta taba yi mishi e-mail ba tun tafiyarshi yaya zai ji a ransa?
Zai ji irin ciwon da itama take ji na yin biris da al amarinta da yake yi. Tunda cikin sakonninsa gaba daya da yake aikowa Safah, bai ko taba cewa a gaishe ta ba.
Duk da ba kalaman soyayya yake cika Safah din dasu ba. Galiban, gaisuwa ce da karfafawa a kan karatun ta. Sai dai in ka nutsu sosai cikin karatun sakonninsa, za ka fahimci kwantacciyar kauna mai sanyi da motsa zuciya cikin kalaman nasa.
Har take cewa a ranta, ina ma ita ce Safah? Safahn ba ta san bikin da suke yi ba.
Akwai ranar da ta tari aradu da ka, ta yiwa  yar uwarta nasihar ta dinga duba sakonnin Yaya Imam. A kalla ko bazata bashi amsa ba. Safah ta rufe ido ta yi amfani da mintocin da ta girmi Marwah din dasu ta balbale ta da fada, fadan da bata taba zaton cewa ta iya ba, idan akayi la akari da shiru-shirun ta. A fusace take fadin
 Miyid a kongatta, miwatta tegal joni, midalimo yauti amo Ni na ce miki ina da lokacin shirme? (Ta fada cikin fulatancin Mami, wanda Mamin ta fi yi musu magana dashi). Amma Safah bata yi sai ranta ya baci. Marwah kuma bata iya mayarwa amma tana ji.  Wannan tsagwaron shirme ne (soyayyah). Ni kuma duk wani shirme, to bana cikinsa.
Ke dai tunda baki da aikin yi ki je ki yi tayi, ko an ce da shi aure zan yi yanzu? Ina amfanin soyayyar tunda ba aurenka zan yarda nayi ba? Ni da aure ma ina jin nan da shekaru goma nan gaba albarka! Mijin auren ma ba a haifeshi ba. Don haka kada ki kara damu na da zancen Ya Imam. Shirmammiya kawai!
Marwa ba ta yi fushi ba, sai ta langabar da kai, tayi murmushi ta kwantar da murya cikin lallashi,
 Ki yi dai tunani Safah, Yaya Imam Yayanki ne kuma mai sonki, tun kina cikin mahaifa, har aka haifo ki, har zuwa girmanki bai daina hidima dake da son ki ba.
Idan kika ce bakya sonsa baki yi adalci ba. Kuma na rantse da Allah kika yi saken da ya kubuce miki, zakiyi nadamar da bazata yi miki amfani ba. Gara ka auri wanda ke son ka, akan ka auri wanda kake so!
Ban ce bazaki samu mai son ki bayan sa ba, amma ba kamar sa ba. Ratar da ingancin da yawa.
Na ji ni bani da aikin yi, zan ci gaba da amsa mishi sakon gaisuwa da kaunarsa gareki, tunda dan uwana ne, bazan iya ganin irin wulakancin da kike mishi ba, balle in taya ki, ba kuma zan taba bari ya gane ba ke kike amsa mishi ba, sai in ke da bakin ki kika gaya mishi tunda na lura baki da hankali, a bit lunatic& .!!! . Ta fada cikin dan daga sauti saidai ba yadda Mami zata jiyo ba, har ido ta zazzaro mata sabida takaici da bacin ranta karara (Fadansu na farko kenan a rayuwa).
 Ni ce bani da hankali Marwah, lunatic? Ni??? Ta fada tana nuna kirjin ta, tareda kallon kanwar tata cikin ido. Fuskarta dauke da tsananin jin mamakin kalmar.
Gyada kai ta yi, cikin tabbatar da kalamanta.
 Babbar mara hankali kuwa, kuma mara kirki, sannan marar tunani da kara. Ai in da alkawari ruwa bazai dafa kifi ba. ALHERI na binki kina gudu. Domin auren Ya Imam alheri ne a gareki. Muhimmi shine iyayenki zasu dawwama cikin farin-ciki dake har karshen rayuwarki, amma kina so ki janyowa kanki bacin ran iyaye da asara& .. Dube ki da Allah (ta nuna ta sama da kasa tana mere baki)  & & Me kika fi Ya Imam? Baka-kirin dake, siri-galau kamar karan raken-takanda, ban da so gamon jini ai baki ko ishi Ya Imam kallo ba, banza mai kama da  yan kauyen Chikun.
Kina tunanin ranar da Daddy ya san abinda kike ciki zaki kai labari? Safah ta jinjina kai, takaicinta ya kai intaha, sannan ta harare ta, ta ce,
 baki burge ni ba, sai kin gayawa Ya Imam din haka. In ya so sai ya gaya miki dalilin sa na son karan-raken takanda. Ki kuma yi aniyar zuwa gayawa Daddyn, tunda kin zama munafuka, ko baki fadaba rana na zuwa da zan fada da kaina; mihed aki hitkimo, awattayan dole miyid amo, tunda na an ha b bata tegal, yitki god d o wala ye so an (ban taba son sa ba, kuma bazaki tursasani ba, tunda ba ke zaki daura min auren ba, ke kije ki aure shi mana?) ta kara da cewa  I don t habe time for stupidity, mara aikin yi kawai . Ta tattara takardun dake gabanta ta mike ta bar mata dakin tana cigaba da cewa
 Ki yi da wani kuma, ba dai da ni ba .

Kwanan su biyu basa Magana da juna, ko hanyar da daya ya bi, daya baya bi. A rana ta uku dukkansu sun jigata, kasa jurewa suka yi, sabida abu ne da basu taba yi a rayuwarsu ba.
Suka yi ta kuka a daki su kadai, dole suka nemi afuwar juna da alkawarin daya ba zai kara yiwa daya abinda baya so ba.
Tun daga ranar Marwah bata kara yi mata zancen Yaya Imam ba. Email dinma rufeshi tayi, don fita daga abinda ba nata ba. Da gudun bacin ran  yar uwarta.
****

Sun shiga hutun kirsimeti, wanda in sun koma za su shiga ajin karshe a sakandire. Taron yaye su Imam ya zo.
A satin gaba daya Alh. Aliko, Haj. Zainab da Hajiya Maama basu zauna ba, ana ta shirye-shiryen dawowar sa. Kama daga muhallin da zai zauna cikin gidan da kayan da zai yi amfani dasu.
Hatta sittirun da zai sanya Daddy ya dinka masa namu na hausa, kasancewar Imam da son shaddah haka Daddy ya bayar aka yi ta dinka su, dakakkun shaddodi kala-kala dinkin Mohammed. Da yake suna da shaidar residence permit (takardar shaidar mallakar muhalli a kasar Birtaniya) basa neman bisa. Booking din jirgi kawai suke yi.
Mami ta gaya musu su hada kayansu, gobe zasu wuce UK yaye su Yayansu.
Safah ta yi kicin-kicin da fuska ta ce,  Ni dai Mami ba zan samu zuwa ba, akwai assignment din da nake yi .
Hajiya Zainab ta dan zuba mata ido tana nazarin ta, akwai wani boyayyen bacin rai a idanunta wanda ba ta fahimci ko na mene ne ba. Don bata ga abin bacin rai cikin kalaman da ta yi ba.
Ta ce,  Ba sai ki tafi da assignment din ba in munje can sai ki yi?
Kamar za ta yi kuka ta ce,  Don Allah Mami ki yi hakuri ni kawai bana son zuwa .
Hajiya Zainab ta rike baki cikin mamaki ta ce,  Ke kadai za ki zauna a gida kenan?
Ta ce,  Ba ga su Dije ba duk suna nan babu abinda zai dame ni .
Da Daddy ya shigo Haj. Zainab take gaya masa sakon Safah. Ya yi mamaki sosai, domin ya yi zaton kafin kowa ya ce zai je ita Safan ce za ta fara cewa za ta.
Ya ce,  Kirawo min ita .
Ta shigo cikin doguwar riga kirar Bahrain ruwan gwaiduwar kwai (beig) a jikinta. Ta daure gashinta da wani tafkeken bakin ribbons. Can kusa da Daddyn ta zauna fuskarta ba walwala.
Cikin hikima da tausasawa ya ce,  Safah yaya ne? Na ji an ce kin ce ba za ki je graduation ceremony din Yayanki ba?
Yadda ya yi mata maganar a tausashe, sai ta ji ya tausasa zuciyarta, ta yi shiru bata bashi amsa ba har sai da ya sake maimaitawa.
Cikin sanyin murya ta ce,
 Dama inada assignment ne, amma zan tafi da shi na yi a can Daddy tunda kana so in je .
Ya ce,  To ko ke fa? Assignment din da har sai an koma hutu sannan a karba? Amma in baki je ba ai ba zai ji dadi ba, mu duka ma ba zai yi murna da zuwan mu ba, kinsan Imam dai .

Saukar sassafe suka yi a London, daga  national-rail suka bi jirgin kasa zuwa Loughborough.
Safah tana ta kumburi na babu gaira babu dalili tun saukarsu a  Gatwick . Sanye take da tafkekiyar rigar leda baka har gwiwarta asabili da  snow dake sauka yaf-yaf kamar yayyafi har a jikinsu, daga cikin rigar ledar bakin wando ne  cherokee jeans a jikinta da farar  shirt mai dauke da bakin rubutun  dolce&gabbana , hannayenta cikin bakaken  hand-socks haka takalmin dake kafarta (snow resistant) ne, da safar kafa din suma bakake. Fuskarta kawai kake gani data zagayeta da dan karamin farin mayafin pashmina.idan ka ganta a lokacin saika tuna da fitacciyar jarumar fina-finan kudancin Najeriya Geneibiebe Nnaji.
Hatta kwayar idonta cikin bakin gilashin da aka fi sani da  FF (fitnessfirst) take. Shigar da tayi haka Marwa tayi, sai banbancin kala amma duka  design daya ne, ita Marwa tayi amfani da  red & white ne maimakon baki da farin da Safah tayi amfani. Ita kuma saita tuna maka da jarumar finafinan kasar Hindu (Diya Mirza).
Sabanin Safah dake kumburi mai nuni da an takura mata tafiyar da ranta baya so, ita Marwa cike take da dokin son ganin Yayan nasu.
Tana son ganin wanne irin ci gaba ya samu a shekarun da ta yi ba ta ganshi ba? Tun fil azal Imam na da wasu ilhamomi da bata taba ganin kowa dasu ba. Ko addu a take a kan miji na gari, cewa take  Ya Allah kamar Ya Imam! .

Cikakken matashi dan shekaru ashirin da tara. Ya zama katon gaske. Kai ka ce dan shekaru talatin da biyar ne. Yana da wata irin halitta da kalar fata mai daukar hankali da fizgo zuciya zuwa gare shi. Musamman daga fitinannun matan da suka san kirar namijin duniya. Girman da ya kara ya basu mamaki dukkannin su matuka; dogo sosai, mai ginannen jikin da babu kiba, babu rama a jikinsa. Ba kamar yadda yake a da ba.
A yanzun idan ka kalle shi mayuwaci ne ka bambance nationality dinsa, kasancewar Hajiya Kaltume Shuwa, yayin da mahaifinsa yake cikakken Bahaushe. A da yanada kala irin ta Alh. Aliko da mahaifinsa, amma a yanzu ya fisu haske ya su murjewa, kalar shuwa ta fito sosai a jikinsa, duk da duhun hausawan bai barshi yayi tasiri sosai ba. Sai maida shi kamar Egyptian bakaken cikin su.
Kamannin Uwa da Uba ne suka cakude suka bada surar wannan giant mai sanya zuciyar diya mace cikin soyayya ta babu gaira babu dalili. Idanunshi kadai sun narkar da zuciyar Marwah, cikin wata irin masifaffiyar soyayya ba Imam din baki dayansa ba.
Ita kanta Safan da ta kalle shi ta ji yayi mata kwarjini ainun, ya kuma burge ta, burgewa ba kadan ba. Irin wadannan mazan da Allah Ya hadawa komai na rayuwa, tsiraru ne a cikin al ummah. Tace cikin ranta
 ashe haka Ya Imam ke da kyau?
Sai dai hakan bai sa ta ji soyayyar shi ta aure ba, ko wani abu makamancin haka, ko kadan bata bari zuciyarta ta raya hakan ba, bata ji wani abu daban da na baya ba, wato kafin ya tafi. Tunda ta riga ta sawa ranta hakan.

Marwah ba ta taba ganin wanda hular ilmi ta yiwa kyau, ta tsaya kyam a kansa, ta dace da zubin halittarsa, ta fiddo haiba da kamalarsa, ta maida shi  choculate-bature irin Ya Imam ba. Da da ne, rungume su yake yi, amma a yau baki kawai ya rike cike da mamakin girmansu, yana satar kallon kwayar idon Safah, a lokacin da Daddy ya rungume shi.
Fuskar Safah ba yabo ba fallasa ta ce,  Congratulations Yaya Imam!
Kwayar idon shi ta yi nauyi a cikin kallonta ya ce (idanunshi a lumshe)
 Godiya nake Safahn Mami! .
Marwah dake rabe a bayan Safah, tana lekensa, yana ta hira da Daddy, a lokacin da zuciyarta ke ragaita. Ragaita cikin soyayyar da ba a san tana yi ba. Ta lalubi hannun Safah ta sanya mata wata leda da aka sunke wani abu a ciki cikin  wrapping-sheet , (cikin abin nade kyauta) mai kyan gaske. Ta rada mata cewa ta bashi, (a zuwan ita Safahn ce ta bashi).
Kallon rashin fahimta Safah ta yi mata, ta kada mata kai ta rausayar, kana ta langabar, cikin kallon lallashi, alamar kada ta watsa mata kasa a ido ta bashi.
Ta gatsina baki ta ce,  Ke kin fiye fi ili wallahi .
Sannan ta mikawa Aunty Shahida dake gefensu tana waya ta ce,  Ki bawa Ya Imam in ji Marwah .
Shahida sai ta dauka kunya ce da kara, don haka ta yi murmushi ta ce,  In ji ki dai . Ta murguda mata baki tace  sai kuyi kuma .
Shahidah ta kama baki  ni kike zobarawa baki Safah? Kamar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login