Showing 48001 words to 51000 words out of 95666 words

Chapter 17 - MASIFAR SO COMPLETE BOOK by Rahamat Muhammad .pdf

11 Mar 2025

7221

shiga tashin hankali


.
[10:56AM, 04/10/2016] Rahamat Nalele💋: Yanxu haka wayarta ta kurama ido tana kallan
hotan sah. Wanda ta tura awayan XARAH batama sani bah
Hawaye ne yake xubah mata kamar famfo
Rukayya tashigo ta tsaya akanta na tsawan minti biyar
Kana ta xauna tare da dafatah
Tace kidena kukan nan LABEEBAH haka mana Danko XARAH bayin irinsa takeba. Ta hakura
da KAMAL dan binshi da addu'a kawai take

Amma ke kinbi kinsa damuwa aranki kin tsan gwami kanki Bayan mutuwar nan muma jiranta
muke
Tace Aunty Rukayya dole inyi kuka dole ne in shiga damuwa dole in tamgwami kaina

Da fusata Rukayya Tace Toh kodai shine KAMAL 'dinki
LABEEBAH takalleta ka'dan Tace meyasaki min tambayar nan
Tace hakka dai dan naga tashin hankalin da kowa ya shiga naki na musammanne
Tace hmm nidai ki tayani da addu'a kawai.
Miqewa Rukayya tayi Tace toh Allah ya yaye mana matsalolinmu. tafitta.......

Wayan LABEEBAH ce tayi qara tana dubawa taga YUSUF ne
Share hawayanta tayi ta 'dauka da gyara muryarta Tace hello
YUSUF Yace ina 'kofar gidanku kifitoh. Tace toh da kashe wayan
Kyara kanta tayi da qara feshe jikinta da turare taje gareshi

Tunda tafitoh YUSUF ya xubah mata ido harta iso gareshi
Yace kinyi kuka ko
Tawaro ido Tace aa meka gani Yace abu buwa da yawa
Tace kwaro ne ya shigarmin ido
Yace ba mamaki kam. Dama naxo ganinki ne ko nasamu nutsuwa axuciyata da kuma
maganar bikinmu kinga anqara wata 'daya saboda rashin da mukayi na Ya KAMAL
Tace eh Hakkane
Yace toh yanxu ya kike san ayi

Ta kalleshi Tace duk abinda kayi MeeNi 'dayane
Kayi abunda ya dace kawai
Yace koda gobe jumma'a in mallakeki a matsayin matata
Tayi Murmushi Tace eh
Yace toh Ki saurari 'yan xuwan 'dau karmin ke gobe
Tace toh ina jira

'Dan 6ata fuska yayi ka'dan Yace axahirin gaskiya idan naganki kinyi kuka xuciyata xafi takeyi
min hankalina na tashi. Plx kicire rashin Ya KAMAL mugina wata gantacciyar rayuwa. Wacce
xanji da'dinta kiji da'dinta kema
sun kuyar da kanta qasa hawaye nasan xubu mata Amma tayima kanta gata dan tasan yanxu
ita da YUSUF bada bane tasan ya jure abubuwa da yawa abaya
Amma yanxu baxai iya jurewa ba. Tace kayi hakuri insha Allah baxan qara saka wata damuwa
bah
Yace gud✅
Ina buqatar ganin murmushinki
tayi murmushin Tace saidai dariya....
Yayi saurin katse da cewa nafi buqatarta
Aiko takalleshi suka sheqe da dariyar gabaki 'dayansu



Shuru XARAH tayi tana kallan LABEEBAH dan tagama fa'da mata maganar Auran nata da
YUSUF

LABEEBAH ta xungureta Tace azahiri kallona kike Amma a ba'dili damuwace tayi saurin
shigarki yanxu nan meya faru

Ya akayi kika gane XARAH ta tambayeta da kalar tausayi

LABEEBAH tata6e baki Tace ayanxu damuwa ko yaya take agangar jikin mutum ko fuskarsa
ina ganewa dan jina nake bawanda yafini Sanin kanta
Saboda me. Xara taqara tambayar

Saboda Ni kullin bana rabo da ita LABEEBAH ta fa'da da kafe XARAH da ido

Tashi XARAH tayi Tace hmmm
ba shakka
Amma Wlhi ayanxu nafiki kusanci da damuwa da tashin hankali
Ya xanyi da munafukar xuciyata. Yaxanyi da abin kunyar da tajaji6omin. Ya xanyi da raina
Na shiga uku ni XARAH yaxanyi da ~*MASEEFAR SOO*~
Saiga wani kuka ya kub cema mata fa'di take LABEEBAH kiyafemin
Ina so abinda kike shirin mallakarsa
Xuciyata ciwo takemin. Jinake tamfar in kashe Kaina dan ba'in cikin abinda xuciyata tamin

Cikin tashin hankali LABEEBAH Tace me yake damunki XARAH meya kawo miki
~*MASEEFAR SOO*~ a al'amuranki
Me kikeso wanda ya kasance ina gab da mallakarsa
XARAH tayi shuru
LABEEBAH ta dafatah Tace karki damu abuna nakine. Naki kuma nawane. Nayi miki alqawarin
duk abinda kika so indai mallakinane Wlhi xan baki shi yanxun nan. Kitemaki xuciyata ki
gayamin dan Allah dan inyi saurin faranta miki

XARAH takalleta qasa qasa cikin wani salo Tace nakamu da soyayyar *YUSUF*........
Shin xaki iya lamincemin ya aure mu mu biyu.
Na sani xaki amince Amma koda xan mutu bayan yarda da hakan ba

Ahankali LABEEBAH tayi baya hankalinta ya tashi hawaye ya xubu mata
Amma tayi saurin maida tashin hankalin tare da saka bayan hannunta tagoge hawayan nata
Tace Dan wannan xuxiyarki take miki ciwo
Dan wannan kikeji kamar kikashe kanki
Dan wannan hankalinki ya tashi

Hmmm Karki damu nasan ciwan ~*MASEEFAR SOO*~
Na bar miki YUSUF har abada
Cikin nuna tsoro XARAH Tace me ne.....

Abinda kunnanki yajiye miki shi na fa'da.
tunda narasa KAMAL bawanda xanji ciwan rabuwa da shi. Eh da gaske inasan YUSUF Amma
XARAH kinfini sanshi tunda har kika iya furtamin
Naji da'din hakan dan burina in faranta miki.
Inasan Ki da YUSUF dan harna hangoku a ma'aurata
LABEEBAH tabata amsa da hakan hawaye na xubar mata

XARAH ta qaraso kusa da ita cikin kuka tadur 'kusa tace Ki fahimceni LABEEBAH soyayyar da
nakema YUSUF bashi xaisa na tauye miki hakkinki bah
Wlhi baxan iya xaman Aure da YUSUF bakya tare da shiba
Wlhi saidai in mutu da ~*MASEEFAR SONSHI*~ indai baxaki aureshi bah
Menayi kenan nayi xalinci
LABEEBAH ta girgixa kai Tace baxan iya ha'da kishi dake ba XARAH baxan iyaba

Abin tausayi XARAH kuka LABEEBAH kuka

Candai XARAH Tatashi Tace nikuma Wlhi da in auri YUSUF inyi rayuwa ni dashi bake gwara in
kashe Kaina....

Ya isa haka
LABEEBAH ta katseta da fa'din hakan.

Tace ya kikeso ayi
Tace yanda nakeso shine inhar xuciyarki ta amince da Kin barmin YUSUF toko saidai ya
Auremu mu biyu baxanyi xaman kishi dake bah Wlhi LABEEBAH yanda mukesan junanmu
baxamu bari kishi yaci galabah akammu ba

Saboda Son da nakema YUSUF xaki juyani yanda kikeso

LABEEBAH Tace toh naji shikenan

XARAH ta girgixa kai Tace ba shikenan bah
YUSUF beta6a yimin kallan so bah
Kuma baxai a mince da hakan bah
Ki barmin Komai xanji da Komai LABEEBAH Tafa'di hakan da 'daukar SAUBAN Wanda
yaxame mata jinin jikinta saboda tana kallansa kamar KAMAL dan tsantsar kamannin KAMAL
daya bayyana a gareshi
ko yaushe LABEEBAH na tare da SAUBAN dan har ya ganeta sosai fiye da XARAH
LABEEBAH tasan XARAH bata bashi nono Amma tayi shuru da bakinta dan ganin madarar ta
kar6e shi
Amma abin na mata ciwo hakan nawasa tanajin bala'in haushin XARAH. Dake bayanda xatayi
shiyata kawar da fuskarta akan hakan

Tana shiga gidan nasu taxube kan taburma
Rukayya dake wanke Wanke Tace Innah da Sumayya sun dawo ne
Shurun da LABEEBAH tayi mata ne yasata juyowa
Aiko ganinta tayi tana xubda hawaye tana kallan SAUBAN
Rukayya ta tsame hannunta daga ruwan wanke wanken taxo gareta Tace habah LABEEBAH so
kike hawayanki yaqare
Ba ranar da Allah xai wayi gari bakiyi kukaba
Me yasa haka yake faruwa dake
Goge hawayan nata tayi Sannan tayi Murmushi ha'de da kissing 'din SAUBAN Tace wannan
na dabanne Aunty Rukayya
Nan takwashe yanda sukayi da XARAH tagaya mata
Rukayya ta furgita da wannan batu cikin baqin ciki tare da tausayin LABEEBAN Tace tab
Amma ke wawiyace
Shawarar daxan baki anan itace tunda kunyanke haka shine Ki hakura YUSUF 'din kawai kibar
mata shi.
Xaman Aure fah xamuyi ba xaman wasa bah
Wlhi kishi ya shiga tsaninki da XARAH kedai kinasan YUSUF
Abinma Takaici plx ki barmata shi ai Bashi ka'dai bane 'da namiji aduniya da xata nuna miki
wani alaye akansa
LABEEBAH ta kalleta nan ta hango 6acin rai a tartare da ita Tace Karki damu Aunty Rukayya
abun bai kaini nan ba
Inasan YUSUF kuma xan yarda ya ha'damu dukka ya Aunremu dan nariga na yardar mata da
hakan

Da fusata Rukayya Tatashi tayi 'dakinta xuciyarta nayi mata xafi
LABEEBAH tabita da kallo. Kana tadawo da kallanta kan SAUBAN ta rungumeshi tsam hawaye
bai bar xuba mataba

XARAH LABEEBAH na fitta tasheqe da dariya Tace Ashe xan iya buga wasan haka

Toyanxu yaxanyi da YUSUF dan ban san ya xai 'dau lamarin bah
Shuru tayi nawani 'dan lokaci can kuma ta'dauki wayanta takira Hajjiya Turai ringing biyu
ta'dauka Tace ...........



shegiya yane
XARAH tagyara zama Tace Turai ke dai bari yau nafama LABEEBAH MASEEFAR SON da
nakema YUSUF
Tace ke habah kuma da gaske kin iya fa'dan
Tace mamakin dana yima kaina kenan Ashe xan iya buga wasan
Turai tasheqe da wata dariya Tace tunda kika iya kashe mijinki XARAH wane wasane baxaki iya
bugawa bah.
XARAH tajah numfashi Tace ina tsoran randa xan buga game over
Turai Tace bana tunanin ranar xata xo danke 'din shegiyace me fuska biyu
Tace naji dai ai wasu halayan ke kika koyamin Su kika 'dorani akan hanya
Plx barwan nan mah yaushe xamu aha'dune
Tace ina abuja yanxu Amma jibi xan shigo kano
Tace plx Ki shigo ban san ya YUSUF xai 'dauki lamarin ba
Turai Tace koda yaji lamarin Karki sake dashi afuska koda kun ha'du kinuna mai bakisan
xancan bah
Kinga sai yayi tunanin ha'din LABEEBAN ne kinga baxai rainaki bah
Tace wow hakane fah
Amma Kinsan inyaxo ganin SAUBAN bana iya 'dauke idona akansa
Tace toh yanxu kidinga 'daukewa plx
Tace Xanyi qoqari


Wannan dare XARAH tayi baccin farin ciki
Yayinda LABEEBAH tayi na Baqin ciki
Tasaka aranta koxa dauwama cikin Baqin ciki sai YUSUF ya auri XARAH ya ha'dasu dan da
gaske ta hango MASEEFAR SON Sa acikin idan XARAH

Koda ya kirata bata mishi xanxan bah tafisan saigata gashi



Haka abin yake yau yammacin jumma"a YUSUF yaxo gidan nasu

Gidan su XARAH ya shiga ya gaida innah Sannan ya kalli XARAH wacce takasa jurema
kallansa Yace saina roqa xakiban 'dana
Tayi Murmushi Tace Nina isa yanacan gun mamansa
Ya tabe baki cikin muryar qasa qasa wacce Innah baxata jiyo shiba Yace na kusa 'dauke matata
ai dan gaskiya nagaji da
Wahalar da kike bata ta raino baji ba gani
Tace hmm indai LABEEBAH CE munanan dakai tana gidan nakama baxata fasa kar6ar wannan
wahalar bah
Tashi yayi Yace xan baki mamaki dan xan shagwa6ata yanda gyaran kanma saidai namata bare
tasamu damar 'daukar wata wahala
Tata6e baki da galla masa harara yayi Murmushi da yima innah sallama.

Yana fitowa ko LABEEBAH tafitoh
Ta sakar mai Murmushi da cewa kayimin xuwan baxata
Ya kar6i SAUBAN Yace nasan xakifijin da'din hakan
Tace eh najikam da'din fiye da tunaninka
toh ya hanya
Ya kalleta yayi Murmushi dacewa muje motah kiji
Haka suyi Cikin motar tana gaida shi Yace.baqaramin nisha'di nake jiba idan ina tare dake
Tace nimafah haka inban gankaba har wani xaxxa6ine yake caf kata.
yace gud
Kinsan dasu Momy mukaxo
Da murna Tace ayya momyna xanso in ganta
Yace xaki ganta yanxu dai bani labari Tace aikwai labari kam Amma bansan yanda zaka 'dauke
shi bah
Gabansa ya fa'di yaja numfashi Yace tunkan kice ga labarin naji gabana ya fa'di plx karkice
Komai dan Allahí ½í±í ¼í¿»
Tace hmm ka yimin afuwa ince ko ka'danne
Yaqara jan numfashi Yace inaji toh

Tayi kalar tausayi Tace dan Allah dan Annabi karkiqi abinda xan fa'da
Yace Wlhi koma miye ba alkairi bane tunda naji banasan ji

Tasunkuyar da kanta qasa Tace dama inaso ne ka.... Auremu....
mu biyu
Ya kalleta da kyau Yace ban gane in aureku Ku biyu ba keda wah
Ta'dan Sosa qeya Tace Ni da_________ XARAH

Waro ido yayi waje 😳 Yace what
Me kikace Tace sunake ka Aure mu Ni da XARAH......
Sumayya CE ta kwankwasa mishi gilashin motarsa yaxuge. Tace ina wini ya YUSUF 'daxu
najika lokacin ina Sallah Yace ayya lpy lau Sumayya ya gida
Tace lpy da kallan LABEEBAH Tace mata xanje gidan Ya Bashir ne Aunty LABEEBAH in jiraki.
LABEEBAH Tace aa jeki Tace toh nan ta'dauki SAUBAN Tace Ya YUSUF sai anjima 'daga mata

hannu kawai yayi tayi gaba
Sannan ya dawo da kallansa kan LABEEBAH da binta da wani mugun kallan da batasan ya iya
yin shiba. takoyi saurin sunkuyar da kan nata qasa

Yace Wlhi nutsuwata kinada Takaici yanxu ji nayi tamkar in miki dukan tsiya kona hucce wannan
takaicin naki Tace aiba Takaici ne
Yace ko
Tayi shuru.
Yaci gaba
Ba shakka abin xaiyi kyau ga Fatima-zarah ga Aisha-Labibah ko

Ta kalleshi ka'dan da cewa bakaji da'din hakan bama a bakinka
Kawar da fuskarshi yayi Yana rayawa aransa bai ta6a ganin wawiya sha-sha-sha me abin
Takaici irin LABEEBAH bah. Haushinta ya cikasa danjin kukanta da yaji tana cewa
Ka temaken MeeNi ka Auremu mu biyu dan Allah.
Tah qarashe da qarama kukan nata volume
Ya kalleta cikin bala'in takaici Yace ke fita min amota
Ta kalleshi Tace dan Allah kayi hakuri kakar6i rokona
Yace ko
Ta gya'da mishi kai
Yace Kinsan Allah in baki rufemin baki kin fita daga motar nan ba saina tsinka miki mari

Fitta tayi tana binshi da kallo ha'de da hawaye ya gallah mata harara dajan tsaki yaja motar
kamar xai tashi sama

LABEEBAH ta'dura hannu aka xata rushe da kuka sai kuma tafasa tashige gidansu
Rukayya ta kalleta da ta6e baki Tace baiyarda bane. Dan 'daxo na leqo naganki da YUSUF
LABEEBAH tamata shuru
Saiko tasheqe da dariya Tace damarki xatayi kyau yarinya tunda kinada kyakkyawar xuciyar da
xakiso amiki kishiya tunkan kisan meye Auran
Kallanta LABEEBAH tayi taci gaba da sharar hawayanta......
XARAH CE tashigo ganin LABEEBAH na kuka taqarasa gareta da sauri tana tambayarta
dalilin kukan Tace ba komai
XARAH Tace yaxakice ba Komai bayan gashi kuka kike
Tace cikinane yake min ciwo
XARAH tayi Murmushi dan tasan ba hakan bane Amma dake dama tasan hakan xata faru
bataqi kar6ar qaryar tatabah
Tace koda naji bara in baki magani
Shuru LABEEBAH tayi harta 'dauko maganin tabata
Da gaske ko LABEEBAH takar6a Tasha
Rukayya tajinjina kai
XARAH Tace dama wai Su Sagna ne xasuxo anjima sunkira wayarki basu jikiba
Nan farin ciki yacika xuciyarta Tace toh Allah ya kawosu

Bayan isha ko sai gasu farin Cikin LABEEBAH yaqi 6oyuwa dan harda Momy
Sagna da Safna Suna manne da ita Suna fa'din sunyi missing 'dinta
Bayan sungama gaisawa Momy Tace anya ba tafiya Xanyi da SAUBAN ba
Innah tayi Murmushi Tace da yau LABEEBAH baxatayi bacci bah dan kuka
Momy tayi Murmushi da kallanta Tace toh kwantar da hankalinki 'Yata dan ko 'dakinki kikaje
bame rabaki da SAUBAN
LABEEBAH tayi Murmushi kawai
Momy tabasu tsarabarsu sannan ta suka fitoh dan tafiya

LABEEBAH ko ganin hankanin kowa yayi gaba Tace dama Momy inasan magana dake
Tace toh gobe xan turo YUSUF ya kawomin ke sai kifa'da minko ina yayi Tace eh yayi
Momy tace yauwa toh Allah ya kaimu
Hakako suka tafi abinsu Sumayya da LABEEBAH basuso tafiyar tasu bah


Washe gari kusan sha 'daya YUSUF yaxo ya kira LABEEBAH ta wayanta yana cemata Yana
jiranta. Yana fa'din hakan ya kashe wayan
[1:14PM, 05/10/2016] Rahamat Nalele💋: LABEEBAH Murmushi tayi dabin wayar da kallo
Tace wannan fushi yake dani. Saita girgixa kai Tace 'Yar uwata xan temaka akanka dan baxan
kasance dakai bah. Ita tanacan tana kuka

Saka qaramin hijabinta tayi akan doguwar rigarta tayima Rukayya sallama
Yana kallo ta shiga gidansu XARAH tayima inna sallama suka fitoh da Sumayya dan tare xasu

Koda suka shiga motar kallan Sumayya YUSUF yayi suka gaisa baibi takan LABEEBAH ba yaja
motar

LABEEBAH tayi Murmushi Tace fushinka balaqine a gareni
Kayi hakuri mijina
Kamar xaiyi magana sai kuma yafasa
Itama shuru tayi har suka isa gidan Kakah Yana yin faking saiga Sagna taqaraso da sauri. Tana
murna. Dai-dai nan Sumayya tafitta Sagna ta rungumeta taleqa cikin motar Tace toh saikin
shigo Aunty
LABEEBAH ta'daga mata hannu alamar toh. Sukayi ciki

YUSUF ya harareta Yace kibisu
Tace haba MeeNi fushi kake dani Yace inkun gama da Momy kiyi sauri namaida Ku
Wato baxai bama xancan nata mahimmanci bah
Ta fita ya bita da harara itama tagalla mishi hararar
Yayi kwafah da cewa xaki fitone
A falan taga momy da Kakah nan taje har qasa tagaidasu
Momy tayi Murmushi Tace toh gani 'Yata

LABEEBAH tagyara xama yayinda Kakah Tace ina zuwa ta ficce daga falan
yarage daga LABEEBAH sai Momy afalan

Tace dama Momy so nake Ki roqi Ya YUSUF ya Auremu mu biyu nida XARAH
Shuru Momy tayi yayinda LABEEBAH tasunkuyar da kanta

Kamar Momy baxatace Komai can tajah numfashi wai ance ta yaro kyau take Amma bata qarko
Tace meyasa keko kikesan YUSUF ya Aure Ku kubiyu
Tace banasan rabuwa da XARAH ne

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login