Showing 18001 words to 21000 words out of 148964 words

Chapter 7 - DINGISHIN KWADO 3 & 4 COMPLETE BY HADIZA DA AUTA.txt

zai amsa ba, ko da kuwa ta bar samanta ta sauko. Idan da safe ya gaishe ta bata amsa ba, Babansa ya yi fadan yaro yana girmamata tana yada girman. Idan ta ce ai baya mata magana sannan ko mai zata ce masa ba zai nuna ya ji ba bare ya tanka. Ya kuwa ce mata ai yaro ne, sannan tunda yana gaishe ta ai ya kyauta kada ta sake ta biye masa watarana ba zai yi ba, bata ga Amrah ma hak'uri take yi da halinsa ba.
Bak'inciki kan bak'in amma ba yadda ta iya haka take hakuri tare da amannar yaran sune jarabawar gidan aurenta.
Da zai kaisu ya yi kwalliya irin wadda Hawwah ta dade bata ga ya yi irinta ba.
Ta kasa hak'uri ta ce "To ko dai kome zaku yi ne Baban Amra?".
Ya yi murmushi ya ce "Idan zaman bai k'are ba sai a yi".
Duk da zuciyarta ta buga amma da murnarta ta ce "Allah ya nufa gara ta dawo d'akinta ko Faruk ya janye kiyayyar da ya d'ora mini haka siddan."
Bai ce komai ba. Don kuwa ya riga yasan Bilki ta yi masa nisa har sai idan aure ta yi ta fito. Da kansa kuwa ya tabbatar matuk'ar ta had'u da namijin da zai biyar da ita ta samu gamsuwa ba zata yi marmarin sake zama da shi ba.
Ya dauki d'auki d'iyarta data ke zaune akan gado ya daga sama tana yi masa dariya sannan ya ajiye ta ya ce "Zan tafi daga can Zan wuce d'aurin aure kinsan yau asabar su kuma zan barsu a can sai ta tafi zasu dawo".
A sanyaye ta ce "A dawo lafiya".
Ta fito ya same su a falon sun Tisa jakar kayansu a gaba. Suna ganinsa suka mike. Ya ce ",Oya ku je ku yiwa Antinku sallama".
Ba musu suka hau k'afar benen yayin da shi kuma ya dauki jakar kayan ya fita zuwa wajen motarsa.
Amrah ce kawia ta hau ta yi sallamar. Amma Faruk nokewa ya yi daga k'afar benen.
Suka sauko a tare Amrah na yi masa fadan ya dinga jin maganar Dady Menene dan ya yi sallama?
Uffan bai ce mata ba. Ya shiga gaban mota Amrah ta shiga baya.
Har k'ofar gidan ya kaisu sannan ya ce su ce yana gaishe ta, haka nan su gaida Alti da Farha.
Ya ja motarsa ya tafi yana jin wani irin nauyi da nadama suna sake mamayarsa tabbas har ya mutu ba zai daina jin ciwon asarar da ya tafka ba.
Da gudu Faruk ya hau saman yayin da Amrah ta hau a hankali tana rike da jakar kayansu.
Alti ya tarar a kicin dan haka ya shiga ya rungume ta yana fad'in "Altina!
Itama ta rungume yaron tana jin dad'in yanayin da ta ganshi tabbacin basa cikin takura.
Daga haka ya sake ta da hanzari ya doshi d'akin da zai ga Mahma.



Mkbees Perfumery*
*Mopping liquid, Air freshener, Body* *mist ,Khumrah,Kulaccam,Hair* *Mist Carpet Spray,Linen Spray *
*Oil perfumes Kano*
*Sirrin gayun mace k'amshin*
07032456061


A bakin gado ya tarar da ita tana gyarawa Farha zaman hularta. Ai tana ganinsa ta ruga suka rungume juna. Save Restricted Contents Bot, [Sep 12, 2025 at 22:02]
Sakwanni goma suna haka kafin ya sake ta yana fad'in "Farha ya Abuja?"
Ta ce "Lafiya lau ina Yaya?"
Daidai lokacin Amrah ta shigo d'auke da jakar kayansu.
Itama ta rungume ta.
Yayin da suka zauna gefen uwarsu suka sanya ta a tsakiya.
A nutse Amrha ta gaishe ta shi kuwa Faruk jingina ya yi a jikinta. Bilki ta yi matuk'ar sanya jarumta ta karbi gaisuwarsu da sakakkiyar fuska. Amma k'asan zuciyarta tausayinsu fal yake yagalgala ta.
Da sanyin murya Amrha ta ce "Dady na gaishe ki, ke ma Farha ya ce yana gaishe ki ".
Farha da take zaune kusa da Faruku tana tambayarsa k'awayenta na makaranta.
Bilki ta ce "Ina amsawa ina kanwarku? Ya ma sunanta?"
Faruku ya yi fit ya ce"Lubaba".
Bilki ta ce "Sunan Hajiyar ne haka gatsal a bakinka?".
Amrah ta ce"Yana ji fa ina ce mata Ifrah amma dan iskanci indai ya ganta a hannuna ko wajen Dady sai ya wani ce mata Lubaba kullum ya fad'a haka sai Dady ya ce masa baka jin nauyin baro mini Faruk? Amma ba ya dainawa. Gaskiya Mamah ki yiwa yayanki fad'a baya jin magana kullum da abin da zai yi na rashin ji".
Bilki ta rungume shi sosai ta ce "Yayana da dai nasan ba ka neman fitina amma me yasa yanzu ka canja?"
Ya yi murmushi ya ce "Ba na neman fitina har yanzu amma bana son a takura ni ne, Yaya Amrah da Dady sai su dinga takura ni sai na shiga hanyar matar gidan ni kuwa ba zan shiga ba, ta yi harkarta na yi tawa".
Amrah ta ce "To me yasa kake mini sababi idan na je sama ko Idan na dauko Ifrah?"
Ya galla mata harara ya ce "Tunda Mamah bata tare da mu dole ki dinga kula da ni sosai. Akan me za ki tafi ki bar ni? Ki dinga neman shisshigi ai dama zan fad'awa mama ba ki rik'e amanata da kyau ba".
Dariya ta subucewa Bilki don ta lura da gaske yake maganarsa ba wai wasa ba.
Sosai suka hi hirarsu cikin nutsuwa duk da yawan hirar k'orafi Faruk yake ta gabatarwa akan Amrah tana takura shi wanda duk na shagwaba da iyashege ne kawai don uwar tasu da kanta ta gane Amrah ce take hakuri da shi tare da lallaba shi. Da azahar ta yi Alawiyya ta iso. Gidan ya sake kaurewa da murna suna tuna rayuwar da suka shafe tsawon lokaci tare tamkar ba za'a rabu ba, yanzu kuwa had'uwa gabad'aya irin haka zai dinga yi musu wahalar gaske. Wannan kad'ai ya isa a gane ba abin da ba zai wuce ba sai ikon Allah.
Da taimakon Bilki da Amrah Alti da Alawiyya suka shirya dukkan kayan da Bilki ta ke so wajen d'aya . Duk abin da su Amrah suke so ku suke da bukartarsa ta bar musu. Babban gadonta Amrah ta ce ta bar mata tunda yanzu itace a d'akinta Kuma Dakin babbane gadonta da wadirof sun yi kankanta da yawa.
Faruk ya yi tsalle ya ce ",Ba za'a bata ba, na d'akin baki ya ishe ta tunda suma set ne."
Ta harare shi ta ce "Kai ka d'auki na d'akin bak'in tunda nasan ce wa zaka yi kai ta baka."
Ya girgiza kai ya ce "A a ni nawa sun ishe ni. Alawiyya zata barwa ita kuma ta siyar da nata ta fara business da kudin, ba ki ga yadda take yi mana kirki ba har yanzu? Duk sati sai mun je gidanta mun yi abin da muke so, haka nan ita take zuwa ta yiwa wajenmu general sanitation duk karshen wata. Har firizar can ma ita za'a bawa ".
Amra ta yi maza ta ce "Hakane a bata to".
Bilki ta yi shiru tana nazarin hukuncin da Faruk ya yanke kaitsaye ba tare da neman shawara ba. Amma ta sani gaskiya ya fad'a. A ranta ta ji yafi dacewa da ya amsa sunan Sulaiman don kuwa halayyarsa rabi irin tasa ce.
Dan haka duk ta barwa Alawiyya kayanta har kujerun falon, yayin da Alawiyya ta dinga kuka tana hodiya tare da mamakin yadda ta mallaki kayan alfarma tashi guda. Tuni kuma ta amince zata siyar da nata kayan wasu kuma ta aikawa kanwar Babanta da ta rik'e ta tunda marainiyace ita.
Alti ta dinga taya ta godiya a wajen Bilki.
Da yamma Basma ta je mata suka yi hira ta yi murnar ganin Bilki ta samu nutsuwa zuciya sannan ta ji dad'in auren da zata yi. Ta jaddada mata zata kula da su Amrah iyakacin iyawarta. Itama Bilki ta bata warmers sabbbi sannan ta ce ta duba duk abin take so na amfani ta dauka. Gaf da magariba ta yi sallama suka ta tafi. Save Restricted Contents Bot, [Sep 12, 2025 at 22:11]
Sai dare mijin Alawiyya ya zo daukarta a mashin d'insa wanda dan kasuwane yana siyar da kayan vegies da yake sarowa daga Raudatul Jannah foods Jos.. A zuwan da Alawiyya take yi siyo kayan snacks da na amafanin gida suka hadu.
Har saman ya hawo ya gaisa da Mahmah tunda dama a gidan ya san Alawiyya sai da suka amince da junansu sannan Bilkin ta tura shi K'afur garinsu Alawiyya ya gana da wakilanta.
Ya dinga yin godiya alherin da aka yi musu tunda Alawiyya waya ta yi masa ta fad'a masa kyautar bajinta da aka yi mata duk kuwa da kayan d'akinta na yanzu Bilkin ce ta yi mata su sabbi Sai dai ai Basu kama k'afar wanda aka bata ba yanzu.
Kafin ta tafi Bilki ta ja ta d'aki ta fad'a mata zata yi aure a cikin sati mai kamawa ta taya ta da addu'a. Farinciki har cikin ran Alawiyya don kuwa bata yiwa uwardakinta sha'awar yin kome. Ta dinga yi mata addu'o'i masu sanyaya zuciyata tare da sake yi mata alkawarin matuk'ar tana cikin garin Katsina to Faruk da Amrah suna da Yaya tamkar uwarsu d'aya ubansu daya zata kula da su irin yadda ta kula da ita. Hankalin Bilki ya sake nutsuwa don kuwa ta gasgata Alawiyya. Ga su Faruk sun sake bada shaidar ba abin da bata yi musu.
Suka yi sallama suka rabu cikin sanyin jiki da fatan alheri.
*Na ce kina yiwa masu aikinki adalci da sassauci kuwa?*
*Ba ki san ta yadda zasu taimake ki a gaba ba. Kowanne dan adam akwai ranarsa, da ace Bilki bata yi mata adalci ba, da bata kular mata da yaranta a lokacin da babu idonta a kusa ba*.
Sai da daddare bayan sun kammala cin abincin dare tuni kuma Farha ta yi barci.
Ita da Alti suka faɗawa yaran batun auren da zata yi. Dukkansu yaran jikinsu ya mutu ba karsashi suka ce "Allah ya sanya alheri".
Amma k'asan zuciyarsu sun ji wani iri shike nan ta bar gidansu da dadynsu for ever?
Murya ba amo Amrah ta ce "Mahmah waye shi sannan a ina za ki zauna?"
Ba walwala ta ce "Uncle Asad ne sannan a Abuja zan zauna".
Amrah ta yi shiru ta rasa me take ji a ranta. Amma dai zuciyarta sai ayyana mata take yi mai kudine fiye da dadynsu amma kuwa Babansu ya fi kyau yafi kirki tunda shi ba ya dariya.
Kafin ta ce wani abu Faruk ya ce "Mahmah uncle police wai?"
Kai kawia ta daga masa tabbacin eh.
Ya rik'o hannunta ya ce "Amma takwarana ya fi shi kirki da kyau Mahmah".
Murya ba amo ta ce "Ba kyau na duba ba, sannan haka k'addara ta zaba mini kawai ku dinga yi mini addu'a".
A sanyaye suka ce to don hatta Faruk da yake ganin gara ta tafi inda ba zata dinga kuka ba, batun auren nata ya yi awon gaba da kuzarinsa. Wato kishi bala'i ne, ba ga yara ba, ba ga manya ba.😄Ba ga mazan ba, bare kuma mata masu duniya. Allah kasa mu wanye lafiya.
Washegari suka bar Katsina wanda su Bilkine suka kai yaran gidan Alawiyya akan da yamma su wuce gidansu tunda da sassafe suka tafi a dalilin zasu tsaya a Kano wajen Yaya Hamida.
Suna nisa da Katsina kewar ya'yanta na sake kama ta. Akan dole ta yi hak'uri mussaman da yara basu tayar da hankalinsu sosia ba, amma dukkansu sun yi kuka.
Haka Farha har suka kusa isa Kano kuka take yi akan a barta a wajensu ba zata koma Abuja ba. Sai da barci ya sure ta sannan ta yi shiru.
Taran safiya a gidan Yaya Hamida ta yi musu, suka karya sannan suka shiga daki Bilki ta sanar mata batun aurenta da Yaya Asad.
Take Hamida ta fara kuka tana fad'in tabbas na huce dan ke na ji wa'azi akan illar gaba mussaman ace jini guda ke yin ta. Amma ki sa ni sai da kwakkwarn dalili za ki ga k'afata a gidanki. Me za ki yi da wannan mugun marar mutunci dattijo da shi zai dage sai ya aure ki. Allah ne ya rufa miki asiri bai lalata ki tun kina yarinya ba, masu kakin nan fa kad'an ne na kirki amma wominzers ne na k'arshe. Ai ni tunda bai zo ta'aziyar uwarmu ba, sannan ya daurewa yar iskar Abidan nan gindi akan Yaya Sulaiman Wallahil Azim ba ni ba shi. Dan haka soyayyar da zan nunawa ya'yanki sai na nunawa su Amrah da Farha amma nasa kam kadaran kadaran hakan ma saboda ta jikinki suka fito." Save Restricted Contents Bot, [Sep 12, 2025 at 22:13]
Sai dare mijin Alawiyya ya zo daukarta a mashin d'insa wanda dan kasuwane yana siyar da kayan vegies da yake sarowa daga Raudatul Jannah foods Jos.. A zuwan da Alawiyya take yi siyo kayan snacks da na amafanin gida suka hadu.
Har saman ya hawo ya gaisa da Mahmah tunda dama a gidan ya san Alawiyya sai da suka amince da junansu sannan Bilkin ta tura shi K'afur garinsu Alawiyya ya gana da wakilanta.
Ya dinga yin godiya alherin da aka yi musu tunda Alawiyya waya ta yi masa ta fad'a masa kyautar bajinta da aka yi mata duk kuwa da kayan d'akinta na yanzu Bilkin ce ta yi mata su sabbi Sai dai ai Basu kama k'afar wanda aka bata ba yanzu.
Kafin ta tafi Bilki ta ja ta d'aki ta fad'a mata zata yi aure a cikin sati mai kamawa ta taya ta da addu'a. Farinciki har cikin ran Alawiyya don kuwa bata yiwa uwardakinta sha'awar yin kome. Ta dinga yi mata addu'o'i masu sanyaya zuciyata tare da sake yi mata alkawarin matuk'ar tana cikin garin Katsina to Faruk da Amrah suna da Yaya tamkar uwarsu d'aya ubansu daya zata kula da su irin yadda ta kula da ita. Hankalin Bilki ya sake nutsuwa don kuwa ta gasgata Alawiyya. Ga su Faruk sun sake bada shaidar ba abin da bata yi musu.
Suka yi sallama suka rabu cikin sanyin jiki da fatan alheri.
*Na ce kina yiwa masu aikinki adalci da sassauci kuwa?*
*Ba ki san ta yadda zasu taimake ki a gaba ba. Kowanne dan adam akwai ranarsa, da ace Bilki bata yi mata adalci ba, da bata kular mata da yaranta a lokacin da babu idonta a kusa ba*.
Sai da daddare bayan sun kammala cin abincin dare tuni kuma Farha ta yi barci.
Ita da Alti suka faɗawa yaran batun auren da zata yi. Dukkansu yaran jikinsu ya mutu ba karsashi suka ce "Allah ya sanya alheri".
Amma k'asan zuciyarsu sun ji wani iri shike nan ta bar gidansu da dadynsu for ever?
Murya ba amo Amrah ta ce "Mahmah waye shi sannan a ina za ki zauna?"
Ba walwala ta ce "Uncle Asad ne sannan a Abuja zan zauna".
Amrah ta yi shiru ta rasa me take ji a ranta. Amma dai zuciyarta sai ayyana mata take yi mai kudine fiye da dadynsu amma kuwa Babansu ya fi kyau yafi kirki tunda shi ba ya dariya.
Kafin ta ce wani abu Faruk ya ce "Mahmah uncle police wai?"
Kai kawia ta daga masa tabbacin eh.
Ya rik'o hannunta ya ce "Amma takwarana ya fi shi kirki da kyau Mahmah".
Murya ba amo ta ce "Ba kyau na duba ba, sannan haka k'addara ta zaba mini kawai ku dinga yi mini addu'a".
A sanyaye suka ce to don hatta Faruk da yake ganin gara ta tafi inda ba zata dinga kuka ba, batun auren nata ya yi awon gaba da kuzarinsa. Wato kishi bala'i ne, ba ga yara ba, ba ga manya ba.😄Ba ga mazan ba, bare kuma mata masu duniya. Allah kasa mu wanye lafiya.
Washegari suka bar Katsina wanda su Bilkine suka kai yaran gidan Alawiyya akan da yamma su wuce gidansu tunda da sassafe suka tafi a dalilin zasu tsaya a Kano wajen Yaya Hamida.
Suna nisa da Katsina kewar ya'yanta na sake kama ta. Akan dole ta yi hak'uri mussaman da yara basu tayar da hankalinsu sosia ba, amma dukkansu sun yi kuka.
Haka Farha har suka kusa isa Kano kuka take yi akan a barta a wajensu ba zata koma Abuja ba. Sai da barci ya sure ta sannan ta yi shiru.
Taran safiya a gidan Yaya Hamida ta yi musu, suka karya sannan suka shiga daki Bilki ta sanar mata batun aurenta da Yaya Asad.
Take Hamida ta fara kuka tana fad'in tabbas na huce dan ke na ji wa'azi akan illar gaba mussaman ace jini guda ke yin ta. Amma ki sa ni sai da kwakkwarn dalili za ki ga k'afata a gidanki. Me za ki yi da wannan mugun marar mutunci dattijo da shi zai dage sai ya aure ki. Allah ne ya rufa miki asiri bai lalata ki tun kina yarinya ba, masu kakin nan fa kad'an ne na kirki amma wominzers ne na k'arshe. Ai ni tunda bai zo ta'aziyar uwarmu ba, sannan ya daurewa yar iskar Abidan nan gindi akan Yaya Sulaiman Wallahil Azim ba ni ba shi. Dan haka soyayyar da zan nunawa ya'yanki sai na nunawa su Amrah da Farha amma nasa kam kadaran kadaran hakan ma saboda ta jikinki suka fito." Save Restricted Contents Bot, [Sep 12, 2025 at 22:17]
Hawaye a fuskar Bilki ta ce"Ni ma ba sonsa na ke yi ba, Yaya Faruku ne ya matsa mini amma ko Baba ma ce masa na yi bana sonsa".
Yaya Hamida ta ce "Ni dai tunda kun shirya ke da su ba zan ce komai ba, amma ki sa ni Wallahi mu ba ruwanmu da su mussaman ma Asad mugun mutum mai bak'ar fuska da zuciya.".
Kan dole suka goge idonsu suka yi hirar sannan aka yanka cake din d'iyar Hamida ta biyu wanda ranar take yin birthday da sai yamma za'a yanka amma Saboda ayi hotuna da su Bilki da Farha aka yanka a lokacin.
Duk da Bilki harkar snacks ta k'ware Sai da ta tambayi wacce ta yi cake din tare da su samosa da springrols saboda dad'insu sannan da aka fad'a Mata Farashin sai da ta jinjina tare da karɓar lambar dan ta had'a ta da kawayenta na Kano da suke ta fad'in har yanzu basu samu wacce ta iya snacks irinta ba.

Deenah cakes and more -Kano
09038055790
IG @Deenah cakes and more
Snacks such as :
Birthday cakes
Cupcakes
Samosa
Springrolls
Meatpie
Frozen snacks
Event snacks.

Sai azahar sannan suka kama hanyar Abuja bayan Yaya Faruku ya azalzale su.
Shi Yaya Faruku har yanzu ba wanda yake fishi da shi tunda dama tun filazal na kowa ne.
Sai dare sosai suka isa gida.
Kushen Yaya Hamida akan Asad ya sake tsananta kinsa a zuciyarta sai dai ba zata iya ce wa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login