Showing 102001 words to 105000 words out of 197906 words
lokacin kuruciya da san da take masa duk ya rufe mata ido ta ce taji ta gani.
Sai gashi Balaraba ta sa ya kasa rike alkawari ya kasa mata hallaci ban da wahalar da ta Sha a gidansa da duk a yanzu ya gane makiricin Balaraba ne wai Kuma ya saketa.
Ba zai tab'a yafe wa kansa idan har wani Abu ya samu kudirat ta silarsa ba.
Rashin Sanin halin da kudirat ke ciki bayan barin gidansa da tayi da Dan binciken da yayi na bata gidan iyayenta da Mahaifinta ya zama Mai kudin gaske dan har fastocinsa ya gani alamar ya zama wani dan siyasan na matukar daga masa hankali.
Bacci sai dai barawo ya sace shi saboda tashin hankalin da yake ciki da Fargaba.
Na farko na rashin sanin inda kudirat take na tana rayye ko a macce.
Na biyu iyayenta idan suka gano Yana garin wane irin Mataki zasu d'auka akansa idan suka nemi sanin ma inda kudirat din da bai san inda take ba.
Na uku bai San inda Siyama da Hisham suke ba bai San suma a wane Hali suke ciki ba.
Abinda kawai ke dan kwantar masa da hankali bai wuce Ishama da Allah ya rufa masa asiri ta rabu da Balaraba da yake Jin ba zai iya tab'a yafe mata ba
Kasan zuciyarsa kuwa igiyar aurenta kawai yake so ya tsinke ya Yar Amma Abu ya gaggara.
Sai gashi a lokacin da Sam bai tab'a kawowa zaa ce masa an ga daya daga cikin wayanda yake yawan yiwa Addu'a sai gashi Ishama ta kirashi cikin ihuun murna wai an ga Siyama
Sam bai kawo ba mafarki yake ba sai da ya rufe idonsa ya Kara budewa
Inda ya hau kabbara tare da sakin wayar yayi sujjadar godiya ga Allah.
Halin da ya tsinci Kansa a ciki yasa ya zama Mai rauni kuka bai masa wahala kamar mace.
Hawaye ya ringa zubarwa yana jerawa Ishama da ita kan ta kukan take tambayoyi da ya akayi aka ga Siyama.
Anan Ishama ta dan bashi labarin da Saleem ya bata.
Inda ya nemi Ishama ta tura masa lambar da zai samu magana da Siyama .
A Kuma tura masa lambar Saleem din.
Haka ya ringa gwada layin Ammu a daren bai shiga ba.
Farin cikin da yake ciki yasa ko bacci bai iya yi ba sai rayya daren yayi Yana addu'ar yadda Allah ya sa suka ga Siyama cikin sauki Allah yasa yaga Hisham da kudirat haka.
A daddafe ya bari gari ya danyi haske ya Kara Kiran lambar da Ishama ta tura masa dan muryar Siyama kawai yake so yaji.
Baa irin mafarkin da ya Saba yi ba sai ga muryar Siyama ya ratso wayar cikin kuka tana Kiran sunansa.
Dak'yar ya samu tayi shiru inda ya hau ce mata ta bar kuka haka zai zo ya sameta har can Cameron din da Kansa zai zo ya d'auketa.
Dak'yar ya samu ta bawa Ammu wayar dan ya Mata godiya.
Ammu kuwa tace masa ba komai duk an zama daya
Yana Jin Siyama na cewa Ammu ta bata wayar zata masa magana yaji an kashe wayar.
Sanin Siyama na rayye a cikin koshin lafiya yafi masa komai.
Lambar Saleem da Ishama ta tura masa ya kira
Bugu daya yaji ya d'auka.
Sai da suka gaisa yace masa mahaifin Siyama ne.
Inda ya kwara masa godiya da addu'a.
Saleem kuwa yace masa ba komai an zama daya.
Alfarma daya kawai yake nema a wajen sa kar ya biyewa Siyama akan ta dawo yanzu ya bari ta gama makaranta dama babban burinsu bai wuce su San inda danginta suke ba.
Jafar kuwa har ga Allah kamar Saleem ya shiga zuciyarsa rokonsa yake so yayi akan Siyama ta dan zauna dasu kafin yazo ya d'auketa da Kansa.
Dan ba zai tab'a iya barin Siyama ta Kara zama da Balaraba ba.
Kuma ba zai so ta zauna a gidan Ishama ba.
Addu'a yayi wa saleem sosai inda yace zai na kiransa akai akai.
Da haka suka yi sallama.
A ranar Jafar wuni yayi cikin farin ciki.
Koda Ishama ta kirashi akan d'auko Siyama ce mata yayi ta bari da Kansa zai d'aukota.
Ishama dai ba haka ranta ya so ba dan ji take kamar tayi tsuntsu ta ganta a Cameron din so kawai take ta ga Siyama.
Saleem
Koda ya bar garinsu Siyama
Katsina ya nufa sai da ya kwashi sati Yana zaryar neman inda zai samu Wanda ya San mahaifinsa da dan Karamin passport din ya ringa yawo.
Amma Sam bai dace da samun Wanda ya san mahaifin nasa ba.
Address din bayan hoton kuwa da yabi wasu ya samu daban bama su San mahaifinsa ba balle su San Wanda ya San shi.
Siyama kuwa sai takura masa take ta wayar Ammu sai da ya rufeta da fada ta daina takura mi shi da waya akan yaushe zai dawo ita Nigeria kawai take so ta koma har da kukanta
Ammu ma da alama ranta ya b'aci dan itama kiransa tayi akan Siyama ta dage tunda an ga Yan uwanta ita Nigeria zata koma inya so zata cigaba da karatu acan kar su takura mata akan lailai sai ta zauna.
Saleem kuwa cewa Ammu yayi ta share Siyaman sai ya dawo tukunna ai mahaifin Siyaman ma yace da Kansa zai zo ya d'auketa.
Ganin ya Tafi sati biyu Babu alamar zai dace da samun labarin mahaifinsa ko ganinsa yasa ya fara shirye shiryen komawa Cameroon Dan akwai ayyuka da yawa da zai yi kafin ya dawo da aiki Nigeria gabad'aya.
Balaraba
Fuskarta dake a kumbure take tattabawa tana kallon mudubin da ta d'auko daga dakinta tana kallon yadda shagari ya canza mata kammanin fuska.
Ba mai kallonta bai yi tunanin hatsarin mota tayi ba.
Har ita Shagari zai yiwa irin wanan bugun dan kawai taje wajen Ishama
Har Kuma wuyan Ishama ya Isa yanka ta kaita asibiti ta baro ta a can.
Cije lebbenta tayi saboda azabar daya ratsa hannunta da take Jin kamar karyewa yayi ta ajiye mudubin hannunta ta hau girgiza kafarta tana tunanin yadda zata kawo karshen shagari da Ishama Koda kuwa za tayi yawo tsirara.
Idan har akan Ishama shagari yayi mata irin wanan dukan sai inda karfinta kuwa ya kare wajen raba su.
Yanzu Jinyar kanta za ta danyi ta samu kwari in ta kama ma ta siyar da gidan wajen Samun cikar burinta siyar da gidan za tayi.
Haka ta ringa tunanin hanyar da zata bi wajen haukata shagari ko Ishama.
Dan ba zata tab'a samun nutsuwa ba sai taga Shagari ko Ishama sun zama Abun tausayi.
Ko Yaya ta rufe idonta katon gidan Ishama kawai take gani da irin daular da Ishama ke ciki.
Bayan ita gata nan a cikin Karamin gida ko abincin da zata ci bata dashi.
Jafar kuwa yadda ya tafi haka zai dawo ya sameta saukin kawai take so taji ta ba zama kauye wajen Wanda ya Mata aiki a baya
Nisan da kudin da yake cazarta yasa ta kasa zuwa wajensa
Amma wanan karon dole idan tana san ta samu biyan bukata ta je wajensa.
Hajiyar Shagali
Akan dole ta fara cire rai da ganin Siyaman dan ba cigiyar da ba tayi ba amma Babu alamar zaa ta ga Siyama
Duk Kuma Yan Matan da aka sake kawo mata ba wacce ta shiga ranta kamar Siyaman.
Takurar Kuma da Saleem ya fara mata yasa ta fara k'ok'arin canza takunta dan ba zata so Saleem ya tab'a Sanin tana lesbian ba.
A Rana daya yazo duk Ladabi da biyayarsa haka ya murzawa idonsa toka ya kora duk Yan Matan dake gidanta.
Koda tazo magana haka Saleem ya sa mata kuka da roko da magiyar Rayuwa da take yi.
Ya Kara da hadata Allah da Annabi akan ta fada masa inda zai ga dangin mahaifin sa dan ba zai zo Aure ace za'ayi bincike ace bashi da Uba kamar yadda wasu ke zargin shi dan gaba da fatiha ne.
Tunda ta haifi Saleem bai taba mata tijara ba irin ranar.
Hakane yasa taji jikinta yayi matukar sanyi dan tasan Saleem nada matukar hakuri da biyayya tunda har ya fara mata irin haka hakurinsa ya fara karewa.
Idan akwai abinda ta tsani tunawa bai wuce mahaifin Saleem da take ganin ba zata iya yafe masa abinda ya Mata ba
Idan har zata tuna Abunda ya Mata sai tayi jinya.
Shi ya Saka ta tsani Nigeria dan danginta ma a lokacin basu yadda da ita ba haka suka korata ta shiga duniya da cikin Saleem.
Hawayen da ya zubo mata ta share tace Saleem ya tafi ya bata lokaci zata bashi labari a yanzu bata shirya ba.
Saleem bai tashi ba sai da ya hada da mata wa'azi da rokon ta ajiye wanna rayuwar da take zai tsaya Mata duk abinda take so zai mata.
Inda yake fada mata zuwan da zai yi Nigeria da can da yake tunanin komawa da aiki.
Addu'a kawai ta masa dan ba zata cigaba da amfani da karfin uwa tana takura shi ba amma da da yadda za tayi da ta ce ya ajiye aikin indai sai an maida shi Nigeria.
Duk da kowa nata na Nigeria Amma bata tab'a sha'awar zuwa ba ko taji tayi kewar wani nata.
Tunda har lokacin da mahaifin Saleem ya rufe ido wajen Yi Mata sharri basu yi bincike ba suka juya mata baya itama.
Har bata san tuna wahalar da ta Sha Kafin ta haifi Saleem.
Kwana biyu da tafiyar Saleem hajiya Mardiya tazo gidan da yamma tana zaune a palon ita kadai tana waya dan duk wani Mai kudi da yake ji da kudi yake harkar bin mata yasan ta Yana Kuma da lambarta
Dama ta bar Yan Matan ne a gidanta saboda kar su ringa cutar ta idan ta hada su.
Amma tunda Saleem ya koresu.
Ita zaa ringa bawa kudin tana biyansu da kanta
Waya kawai zata yi kije sai ita ta biya ki.
Wayar hannunta ta ajiye cikin murmurshi tana amsa sallamar hajiya Mardiya da ta ganta a hargitse
"Allah ya sa lafiya ya na ganki haka"?
"Dole ki gani haka yarinya nan tana neman samin hawan jini kinsan yadda Rafia ta raina ni kuwa wallahi ba Zaki yadda ni na haifeta ba yanzu saboda ita kinsan bana iya fita ko na bari azo gidan wallahi bibiyata take na rasa yadda zanyi da ita Assadiq kuwa har bugunta yake idan tamin wani Abu duk bai san akwai dalilin da yasa take min haka ba"
Hajiyar Shagali tabe baki tayi tana "Baki tab'a mata mugun duka bane tunda yarinya nan takura ki za tayi ki Mata Aure kawai tunda ta gama makaranta amma idan har ba aure kika mata ba haka zata cigaba da sa miki ido ni nayi mamaki ma da bata fadawa Babanta halin da kike ciki ba"
Tsaki Hajiya Mardiya taja tana "Wallahi ba zan damu dan Dr yasan halin da nake ciki ba naga duk shi ya jawo min halin da nake cikin ni fa Allah ban da nayi girma da zawarci Allah da sai nemi saki a wajensa yanzu dai ba wanan ya kawoni ba taimako nazo nema a wajenki"
Hajiyar Shagali gyara zamanta tayi ta bawa hajiya Mardiya duka hankalin ta tana tunanin wane irin taimako zata mata
"Dan Allah Saleem nake so kiyiwa tayin Auren Rafia nasan ba macen da Saleem zai je wajenta bata so shi ba"
Yarinya nan yanzu bani da burin da ya wuce naga ta bar gabana bama zan iya bari ta cigaba da makaranta ba"
"Kai Kai Hajiya Mardiya ai kin Makaro Saleem ya samu matar Aure tuntuni yanzu haka ma maganar da nake gaya miki shirye shiryen Kai kudi ake wallahi da tuntuni kika fada min da na masa magana"
Hajiyar Shagali tace tare da dan Kau da fuskarta saboda ba Karen hauka ne ya cijeta da zata bar danta daya tilo yaje ya auri Yar gidan Dr da ya kware a neman mata har ita kanta hajiya Mardiya da a yanzu bata da aikin daya wuce Neman kananan yara ba tsaurin ma idon hajiya Mardiya ta gani.
Taya Saleem da take cin buri ya auri yar gidan Mallamai zata bari ma ya auri Yar gida Dr Allah ma ya kiyaye tana nan tana cin burin nema masa matar Aure da kanta.
Hajiya Mardiya kuwa Sam bata ji dadin matar da aka ce Saleem ya samu ba dan nauyin baki kawai tayi amma taso ace Rafia Saleem ya aura.
Rokon Hajiyar Shagali ta Kara yi akan ta dai gwada yiwa Saleem magana ta taimaka mata .
Inda hajiyar Shagali tace mata kar ta damu zata masa magana da haka suka dan tab'a hira ta tafi
Inda hajiyar Shagali ta fara tunanin nemawa Saleem mata da kanta.
Siyama
Birikice wa Yaya Saleem da nayi da ya dawo da kukan kawai da na ringa yi ba dare na rana yasa ya kira Abba da bansan tsawon lokacin da zai dauka kafin yazo ya d'aukeni ba
Jina nake kamar akan kaya burina kawai na Gani a Nigeria a cikin yan uwana.
Yadda na matsu da San ganin Ishama haka itama ta matsu.
Abla da Waleeda su suka Kara samun tsanar zaman gidan Ammu da Cameroon din gabad'aya
Tun kafin ma Yaya Saleem ya dawo su kadai su ka cigaba da zuwa makaranta.
Inda ni Kuma nake zaune ni kadai a gida da Ammu.
Ammu tace sai ya Saleem ya dawo zaa canza min wata makarantar tasan Mai zata fadawa Saleem idan ya tambayeta dalilin da ya sa take so ta canza min makarantar.
Ni kuwa a yanzu bata makarantar nake ba yadda kawai zan gani a Nigeria nake dan nima Ina so na gani da Yar uwata naga Abba da Hisham.
A yanzu kuwa bana Jin tsoron zama da mama.
Sai gashi wai da Yaya Saleem din ya dawo sai cewa yayi Abba yace na cigaba da zama a Cameron da Kansa zai zo ya d'aukeni.
Ai tuni na birikice na ringa kuka akan ba zan iya zama ba ni Nigeria kawai nake so na tafi.
Yadda na ringa kuka yasa Ammu yiwa Yaya Saleem magana akan ya barni kawai na koma gidan tunda na dage a kira Abbana a waya a fada masa naki yadda na zauna.
Yaya Saleem kuwa ransa yayi balain b'aci ban ko damu ba nidai kawai Cameron nake San bari gani nake barina kasar zai sa na binne irin rayuwar da nayi da mahaifiyar Saleem da Muhseena da bana kwana biyu banyi mafarki da ita ba.
Cikin bacin rai Yaya Saleem ke fadawa Abba yadda na tubure akan sai na dawo inda Abba yace a bani wayar yamin magana.
Cikin hade rai Yaya Saleem ya mikomin wayar na karba.
Abba ya fara magana Yana "Siyama idan kika bar Cameron yanzu a Ina zaki zauna bayan ni bana nan?kinfi so ki zauna da Balaraba ta Kara gana Miki azaba?ko gidan Ishama Zaki je ki takura mata da mijinta?
Ki bari nan da wata hudu zan zo na duake ki da kaina ko Dan ke sai na ajiye aikin nawa dan ba zan Kara yadda balaraba ta cutar da ke ba"
"Abba a yanzu na girma mama ba zata iya cutar dani ba Abba Ina so naga Ishama da Hisham Abba Ina so na gani a cikin Yan uwana ba zan iya Jira har sai kazo ka d'aukeni ba wallahi zan iya jure komai ma mama zata min balle ma nasan yanzu ba abinda zata iya min Abba Dan Allah ka barni na tafi wallahi zan iya kula da kaina"
Yadda na dagewa Abba da magiya yasa yace min bari ya kira Ishama zai Kara kirana.
Haka na rike wayar a hannuna sai da ya Kara kira na dauka inda ya fara magana Yana "na kira Ishama nace Mata ki zauna a gidanta kafin ki dawo Amma ban yadda ki zauna da Balaraba ba dan ba Imani gareta ba zata iya kasheki kafin na dawo"
Ji nake kamar na zuba ruwa a kasa na Sha Rabon da najini cikin farin ciki haka har na manta.
Ina Jin sadda Abba ya kira yaya Saleem yake fada masa tunda na dage ya taimaka masa ya kaini Nigeria zan zauna a wajen yayata kafin ya dawo.
Yaya Saleem toh kawai yace inda naji Yana ta Ameen da alama addu'a Abba ke masa.
Yana kashe wayar na shige daki
Naji Ammu na Allah yasa komawa na Nigeria shi yafi Alheri.
Ai tuni na hau hada kayana dan banki a yau na dau hanya ba.
Haka Ishama ta ringa kirana cikin Doki da murna.
So kawai nake na barwa Abla gidan taje ta karata ita kadai dan bansan Mai na mata ta tsaneni haka ba har murna naga tana yi.
Washegari kuwa Yaya Saleem kirana yayi naje na same shi a waje.
Inda ya hade rai Yana murna nake zan tafi na bar shi ko
Hakan da ya fada yasa na dago na kalle shi na Maida kaina kasa batare da nace masa komai ba dan wani irin Kallo naga Yana min.
Magana ya cigaba da min da shi ma nan da wata daya zai dawo Nigeria gabad'aya kar na sake na kula samari na tsare mutuncina ya hau dai min waazi.
Ni duk ba ta naganar da yake nake ba ranar da zamu Tafi kawai nake so naji dan nasan shi zai kaini.
Kamar yasan abinda ke Raina yace na shirya jibi zamu Tafi.
Ai sai naga kamar na jawo jibin
Na matukar matsuwa da San barin Cameron.
Washegari kuwa na Kara gyara kayana
Inda na tsafe Kaina a ranar ba makaranta su Abla ma na gida.
Ammu ce ta bani kudi akan naje na wanke kaina.
Inda nayi kasa da kaina Ina Jin idon Yaya Saleem dake zaune a gefen Ammu a kaina.
Bansan Mai yasa yake San Kallona haka ba ko Yaya na dago sai na Hada ido dashi.
Takalmi nasa Ina Jiran Waleeda ta fito mu tafi dan ammu cewa tayi ta rakani naje nayi wankin kan na dawo.
Sallamar da akayi da muryar wacce naji yasa gabana mugun faduwa.
Jikina ya d'auki rawa da naga muhseena ce ta shigo cikin shigar hijabi da sallama.......
6/25/24, 10:42 - SADNAF: MATAN GIRMA MATA MASU AJI
MACEN DA TA SAN KANTA ITACE TAKE GYARA
A&Z COLLECTION TA KARA DAWO MUKU DA ZAFINTA MASOYA KAYANMU.
A&Z COLLECTION TA ZO MUKU DA ZAFAFFAN KAYAN GYARAN FATA,GYARAN JIKI CIKI DA WAJE MAI DA TSOHUWA YARINYA WANAN KARON A&Z TA SHIRYA TSAF DAN TA GYARA AURE GYARA BUDURWA,GYARA MATAR AURE,HAR DA BAZAWARA.
Wa.me/2349037870422
A&Z COLLECTION TA ZO MUKU DA ZAFAFFAN SUPPLEMENT KALA KALA
HAJIYATA IDAN KINA DA KYAU KI KARA DA WANKA GYARA DUNIYA NE A YANZU AN BARMU A BAYA KARKI SAKE DA KURUCIYARKI KI JERA DA SAARKI A RINGA MIKI KALLON TSOHUWA SABODA