Showing 3001 words to 6000 words out of 62407 words

Chapter 2 - SAKATA COMPLETED WRITING BY SAYYID (LEGENDS PEN).txt

naji zuciyata ta karye, nafasa yin abinda ya kawo ni.





Abinda ya faru kuma, jiya da daddare har yaja Yaya ilyasu ya mareni. Mun dawo daga makarantar magariba, sai wani dan ajinmu Walid ya tareni a lokon baya. Yana tambayata a kan buduruwarsa, wacce take awata. Muna cikin magana, Mus ab yazo wucewa, da sauri Walid yace.  Salma ga yayanki. kallon Mus ab nayi nace.  Naganshi, yayi kyau kamar rago. gyaWa kai yayi yahuce, kasancewar lokon da mutane. Shi kam bazaiyi abinda xai zubda mai da mutunci gaban mutane ba.



Ina shigowa harabar gida, naganshi yafito daga bangaren Hajja. Da sauri na nufin Sangaren nata, amma yarikemun hannu, juyowa nayi zan mai masifar da nasaba. Naji ya tsinkeni da mari.



"Allah ya isa, Allah yagamaka da masifar duniya. addu ata  yar kullum gareshi, wacce shi kan shi ya haddace ta.  Zaki ci gidanku. ya fada tare da jana ciki, ihu na fara kur mawa, ko Allah zaisa maman ciki tajiyo ni, amma Allah bai nufita ba. Kai tsaye inda Yaya Ilyasu yake yakaini.



 Yayana, nagaji da abinda yarinyar nan keyi. Har ta kai ga abokaina sun fara mun magana a kan rashin kunyar da takeyiwa mutane a waje.



Da sauri na Wago, tare da faWin. Wallahi karya yake, Mus ab kai azzaulumi ne. Yaya iliyasu ne ya tare ni da cewa.



Legends pen.



(08165383931/ 08129553971).





*SAKATA*d'&



<;Stroy and written<;

By

Sayyid writer (Legend)
'





*FUTURE WRITERS ASSOCIATION*



*(FUWA)=؋=*





(3E 'DDG 'D1-EF 'D1-J



SHAFI NA UKU

(P.03).



 Tabbas kuwa, wanan ba rashin kunya bace. Salma mai yasa kike haka?. Cike da jin haushi na sake buWe baki nace.  Wallahi, karya yake min. Kawai ya tsaneni ne. ban rufe baki ba naji, an Waukeni da mari.



Tabbas marin ya shigeni, domin har wasu taurari nagani. Suna yawo a sama, daga nan Waki na huce. Ban san mene zanyiwa Mus ab na huce wanan kayan haushin, sai dai kuma Waukar fansar duk kusanci dashi ne, nikam ina neman tsarin ubangiji da zuwa kusa dashi, ni ko a laira idan za ayi mana Hisabi so nake tazarar mu ta kasance nisan sama da asa. Idan kuwa har akace sai nuna gab da juna, ni mai iya yafeshi ce.



Duk lokacin da Mus ab, ya matso kusa dani wani irin turnuui nakeji daga cikin zuciyata. Wani irin zafi kamar ana soyata. Idan nace na tsani Mus ab, to na tsaneshi, bana fatan ko da rana daya naji na samu sasssuci daga tsanar da nayiwa Mus ab.



Yau ta kasance Lahadi, babu makarantar boko sai islamiyya. Muna zaune a compound muna wasa, har yanzu zuciyata cike da Wacin marin da Yaya ilyasu yayimun jiya, kamar ance Salma fita waje haka naji zuciya na na fusgata.



Kyawawan samari ne guda biyu, suna tsaye daga gefen gidanmu. Kyawawa ne sosai da sosai, cike da nutsuwa na fara tafiya zuwa inda suke, kamar wacce aka saka.  an mata barka. Daya cikinsu ya faWa fuskarshi da murmushi.  Ina wuni. na faWa kasancewar sha-biyu ta kawo kai.



 Lafiya alau, dan Allah ko kin san gidan Alhaji idi me mai. Waga kai nayi sanan nace.  Ai kuna kusa ma, gida na uku daga gidanmu.



 To inane gidan naku?. Wayan da baiyi magana ba tun dazu ya faWa, cikin wata murya mai sanyi da zai.  Kaji mazan arzii, ba irin su Mus ab masu maganar mata ba. na faWa a raina, a fili kuma nayi murmushi na ce.  Wan can mai jan get Win shine namu, to daga na kusa da mu mai ofa, sai wancan mai Sakin get na farko, to mai bain na biyu shine.



 Mungode an mata. nayi murmushi, kamar an cemun juya idanuna suka faWa cikin na Mus ab, Ya harWe hannye a irjinsa yana kallonmu. Irin kallon da yakemun naji zuciyata ta buga da arfi, da sauri nashiga gidansu Nana.



Sai dai ko minti biyar banyi a gidan ba, iki tazo tace wai nazo inji kawu Mudi.



 Innullahi, mai wanan mutumin yaje yace nayi kuma ni. iki dai ba tace mun komai ba ta huce, na bita jikin a sanyaye. A tsakar gidan mu, na tarar dashi hannunsa rike da bulala ga Mus ab can tsaye.  Kawu gani.



 Tsugunna asa.



 Kawu mai nayi.



 Bazaki tsugunna ba. ban kai ga tsugunnawar ba ya fara dukana, da iya arfinsa, babu imani ko tausayi. Yana dukana yana faWin.



"Ke mara kunya mara tarbiyya ko, kina yin rashin kunya a gida ana kyaleki. Yanzu abun naki yakai harda fita waje, kiga mutane tsaye suna magana ki hau yimusu rashin kunya ko?. zallan mamaki ne ya hanani cewa komai, wacce irin tsana Mus ab yayi mini, mai nayi masa haka da zafi?, haka kawu mudi ya ci gaba da zabgamun bulal, har kuka shigo farkon labarin.







*Cigaba*



Nanata addu a ta nakeyi. Allah yagama Mus ab da masifar duniya. na jiyi sautin Walida, tashigo bangaren mu tana rusa kuka, Abinda ya fara zuwa raina shine. Mus ab ya mutu, afili na furta.



"Allah ka tabbatar. shigowa tayi Wakin mu tana faWin.



 Ummah, Yaya Mus ab ne ya faWi, ciwon kansa. wani sanyi naji ya ratsa zuciyata, wanda kwata-kwata yau banji shi ba, tun bayan haWuwata da wanan samari guda biyu. A gigice Ummanah ta fito, kamar wacce a ka ce mata, ni ko Yaya Asma u sun faWi.



 Innullahi wainna illahir raji un, Allah ka kawowa yaron nan saukin wanan ciwon kan.



Ummanah ta fada tana ficewa, da ido na bita ina taSe baki.



 Allah yasa har mutuwarsa.



na fada tare da kwanciya abuna, ban farka ba sai kiran sallar asuba. Tashi nayi na shiga toilet, na daura alwala nayi sallah.



 Ummah ina kwana?. Na fada daga inda nake, amma naji shiru.  Ina kwana. still shiru, tashi nayi nafito falo tunda ita Ummanah na anan take zama lazimi, tun sallar asuba har bakwai. Rashin ganinta a falon yayi matukar razana ni, dakinta ta nashiga kai tsaye nan ma batanan.



A kid imi na fito xuwa b angaren Abbanah, dakinshi na shiga na tarar dashi xaune da carbi hannunsa. Kallo Waya yayimun yasan da damuwa a tare dani.  Salma lafiya?.



 Abbanah, ina Umma?. Murmushi yayi sanan yace.  Yayanku ne ba lafiya a asibiti suka kwana. A jiyar zuciya na sauke, ni kam na ma manta da wani Mus ab ba lafiya. Hanya na kama zanfita yace.  Ki hada musu breakfast, kuje ke da walida. cuno baki nayi gaba, tare da ficewa.



Kitchen na shiga na fara hada breakfast, cikin ananin lokaci na soya doya da wai, zuciya ta nayi mun tuui. Nasan yadda Mus ab ke mugun aunar doya da wai, domin ko a baya a ka kaiwa Hajja ba taci sai dai ta ajiye masa, har na zuba a plast sai kuma na tuna Mus ab bai cin yamboll (osan doya), cikin hanzari na jawo doya nashiga ferayewa. A gaggauce na dadatsa ta na Wora ta a kan gas, tare da balbala uwar wuta. Zuba doyar nayi a plast tare da tea na miawaya Abbabah, na Wibi iya cikina, na Wibawa Hajja sai kuma wani bangare na zuciyata ya rayamun kar na kaiwa Hajja, domin ita ke daure masa gindi. Amma fa inason Hajja ko ya ne, fita nayi zuwa Sangarenta hannuna rie da doyar. Tana zaune jigom kamar wacce aka yiwa mutuwa, ina kyautata zaton jiya batayi bacci ba. Ina kwana?. na faWa, ina shiga dakin.  Lafiya.



 Gashi. na fada tare da miamata.  Babar taki ta dawo ne?. girgixa kai nayi, sanan nace.  Nina soya.



 Menene kika soya?.



 Doya ne da wai. Murnushi tayi sanan tace.  Kin Wibi na Asibiti. a da kile nace.  Uhm. daga haka na juya na fice. Ina zuwa na tarar doya ta tayi, aikuwa na sauke na fara dakawa, cikin ananin lokaci na dake ta. Na yanka albasa da attatuhu na zuba a ciki, na kawo maggi da kuri na zuba a ciki, nasan baicin kifi hakan yasa na dakko kifin gwangwani na zuba a ciki, na hau mulmulawa. Cikin ananin lokaci na mulmule ta tas, na kaWa kwai na hau soyawa.



Ina gama soyawa na juye a plast, nasan duk masifa yana shan ruwan zafi hakan yasa naki da fawa dasu. Zuba tea din nayi a kofi, na zuba doya da yamboll dina, na hauci. Sai dana oshi, na hade ragowar doyar na juye a baar leda, na jefe a kwandon shara, zuciyata fari tas.





Abbanah ne ya kirani Wakinsa, bayan na zauna ya kalleni yace.  Salma, kije ki shirya kuje asibitinan yanzu.



 Abba wallah, afata ciwo takemun sosai&  wani kallo da ya watsamun yasa na haWiye yawon bakina, da ragowar maganar tas, na tashi na nufi daki, dogon hijabin Ummanah na dauka na zura, aikuwa yazo mun har asa ina jaa. Ban ko damu ba, nashiga kicin na dakko plast din nasa a leda, a bakin ofar dakin na tsaya nace.  Kudin mota.



 Tasowa zanyi na kawo miki?. a jiye ledar nayi, nashiga dakin ya bani dubu biyu, ba godi ba nagode na kadai na tafi, tunda dai bani na tambayeshi ba.





angren su Walida na nufa, na sameta tsaye. Mai kike jira?. na tambayeta.  Lami nake jira ta gama abinci na tafi dashi; ina zaki ke?. ta tambayeni , donin kowa zaiyi mamaki idan nace, Mus ab zanje kai wa abinci. "Abba ne yasani girki, wai na kai asibiti, amma tunda ga wanan kawai kizo mutafi." na faWa da biyu a raina, domin banason ya zamana abinda Ummi zata tafi dashi, Mus'ab Win nacin sa, anyi ba'ayi ba kenan.



aki tashiga ta saka Hijabi itama, mu ka fice. A bakin titi mu kasami napep muka shiga, kasancewar kowa yasan asibitin da ake kai Mus'ab, ba ma shi kaWai ba, kowa da kowa na gidan Galadima.



A bakin asibitin mai napep ya sauke mu, naira duba daya na bashi ya Wau Wari biyar, yaban Wari biyar. Muka rankaya cikin asibitin, har zuwa bakin Wakin. A dai-dai na naja na tsaya, namia wa Walida ledar nace."Shiga da'ita, idan kinfito ina bakin nan."



"Haba salma, kishigo mana."



"Wallahi walida ba zan shiga ba, ko da ace dubashi da xanyi, itace hanyar samun saukin shi da huri.



Ba tak ara cewa komai ba, ta amshi ledar ta shige dakin ni kuma naja na tsaya, kamar wata mai gadi.



Ina tsaye kusan mintina biyar, Ummanah ta leo sai ji nayi ance. "Sannu tabbatacciya." da sauri na juya, domin banma ji sanda aka buWe ofar ba, da ruguwa zanyi a guje. "Ummah ina kwana."



"Bansani ba, zaki shigo ko sai nazo nan na tsinke ki da mari." ta kowa na farayi a hankali, har zuwa bakin ofar Wakin, a raina ina faWin. "Lallai Walida da ni take zancen."



Yana Kwance idanunsa na kallon ofa, aikuwa cikin rashin sa'a muka haWa ido, aikuwa na murguWa masa baki, tare da maka mai harara, game da yi masa gwalo a lokaci guda. Karo na farko a rayuwarsa da yaga nayi abu ya burgeshi, a cikin zuciyarsa yaji hakan.



"Maman ciki ina kwana."



"Lafiya alau Wiyar waje." kamar kullum dai dariyar mukayi, na matsa kusa da walida ko zama ban arasa yi ba na maka mata mintsine tare da faWin."Wallahi kinyi da ni." da sauri tace. "Wallahi bani na ce kinzo ba, Yaya Mus'ab ne."



"Wallahi Walida arya kike, aina yasan nazo."



"To nima bansani ba, daga Mama ta tambayeni ya mutan gidan, nace lafiya. Sai ta ara cewa ke ya kike, nace ke kikayi girkin ma, shine Ummah ta ce mai yasa baki biyoni ba, ni kuma nayi shiru. Sai ji nayi yace tare kuke, na girgixa kai amma yace wai tare muke Ummah ta duba." Hararar ta nayi na ce. "Ni ban yarda ba."



an minti na kaWan na mie tare da cewa. "Zamu tafi." dai-dai lokacin shikuma ya buWe baki ya ce. " Abinci..." Wani murmushi nayi tare da zama, Ummanah kuwa ta sakko tana faWin. "Walida kun manta da tea."



"Wallahi umma ba ni nayi komai ba, ko ledar ma sai a bakin Wakin nan ta bani na rie."



"Ai shikenan, Ummanah ta faWa tana kwance ledar.



Legends pen.

(08165383931/08129553971).





Daga page 10 zamu gama free pages, mu shiga paid pages, 500 kacal ne sai kuma masu buatar complete 1000.



Payment via.



8129553971

OpaY

Sani Muhammad lawan.



Shaidar biya.



08165383931.



*SAKATA*d'&



<;Stroy and written<;

By

Sayyid writer (Legend)
'





*FUTURE WRITERS ASSOCIATION*



*(FUWA)=؋=*



SHAFI NA HUU

(P.04).



(3E 'DDG 'D1-EF 'D1-JE





"Wallahi umma bani nayi komai ba, ko ledar ma sai a bakin Wakin nan ta bani na rie."



"Ai shikenan, Ummanah ta faWa tana kwance ledar.



Bude idanu tayi, ganin yamboll kuma ta tabbatar wanan din aiki na ne, domin kowa ya kwana ya tashi da sanin cewa. Mus'ab bai cin yamboll.



"Yunwa na keji." Mus'ab ya fada, wata dariyar mugunta ta tawomun wacce da kyar na iya tsaida ta, har sai da shi kanshi yaga alamun ina dariya.



"Salma, mene kikayi haka, kinsan baya cin yamboll ko?."



Hade rai nayi, sanan na ce. "Ummah shi ka dai ne damu."



"Eyh shi dake ba da doya akeyi ba ko?."



"A'a Ummah, yafi saui ne."



"Ke zanci gidanku wallahi, a gama dafa doyar azo a daka shine zakice yafi saui?."



"Wai menene?." Maman ciki ta tambaya, "Yamboll ta yo." Ummanah ta ba ta amsa, " Ai shikenan mu bari mu ci, ku kuma ku fita ku nemo mana tea, da kayan madara." Tashi nayi na amshi kudin, walida ta biyo ni har mun kai bakin kofa, Ummanah ta ce. "Saura ki siyo ruwan sanyi." Dariya nayi na fice, Mus'ab kam zuciyarsa kamar ta fito waje, ji yake kamar ya makeni da duka.



Mun siyo kayan shayin mun dawo cikin asibitin naji ana cewa."an mata." kamar nasan murya, amma duk da haka naki tsaya wa, duba da yanayin yawan mutanen dake wajen bai zama lallai ni din ake kira ba. "an mata, bakya jina wai." a ka sake fada kusa dani, da alama mutumin yazo inda muke. A hankali na waigo idanuna suka sauka a kansa, daya cikin matasan da suka zo layin mu jiya, suka tambayi Gidan Alhaji idi me mai. Wanda baiyi magana sosai ba, ina tuna lokacin da yace. "To ina ne gidan naku?." Murmushi nayi masa sanan nace."Ina yini." shima murmushin yayi, cikin zazzakar muryarsa yace. "Lafiya kalau anwata; me kikeyi anan?."



"an-uwan mu ne ba lafiya, aka kwantar dashi anan."



"Ayyah, Allah sarki muje na duba shi." Wani irin abu naji a zuciyata, amma kuma baxan iya masa musu ba, hakan yasa na ce. "Toh muje." jerawa mu kayi muka fara tafiya, Walida ta shige gaba mu kuma muna baya, duk naji nayi wanan fiyau. Ya cika wajen baki daya, a raina na ce. "Idan wanan yace yana so na, wallahi sai nayi sadaka, sabida yana da kyau, gashi Wan gayu, mai aji, murya mai zai. Nipa an gama tashin kai na." A haka muka ara so dain, walida ce ta ce. "Bari na sanar da su." gyada kai yayi, ni kuma naji ni a ta kure. Ban yarda da abinda Walida za ta ce ba, hakan yasa na ce. "Bari na bi ta."



"A'ah ki jira mana." kallonshi nayi, idanuna sunyi wani kala na ce. "Ban san me za ta ce ba."



"Mai kike tsoro to?."



"Za fa ta iya ce musu, Saurayina ko wani abu." Murmushi yayi, sanan ya ce. "To menene a ciki, ko ki na da wani saurayin ne?." asa nayi da kai na, ba tare da na ce komai ba. Shi kuma ya ara cewa. "Ko akwai ne." girgixa kai kawai nayi, dai-dai lokacin da Walida ta fito. Sai a lokacin na fahimci cewa, kofar bata yin ara idan a ka bude ta, shine yasa dazo banji lokacin da ummanah ta buWe ba. "Ku shigo." ta faWa, ni kam kamar munafuka haka na zama.



Idanunsa a rufe yana kallon sili muka shigo, Maman ciki ce ta. "Ga waje mana basai ka xauna a asa ba."



"A'a Mama bari na zauna anan; ina kwana, ya mai jikin."



"Lafiya alau, mai jiki da saui." su ka amsa tare. "Allah ya ara lafiya."



"Amin, Mus'ab ga bao fa." Mama ta faWa, a hankali ya buWe idonsa ya sauke su akan mu, kasancewar ya tsugunna kusa da inda nake zaune. Kallo daya ya gane fuskar gayen, wa'yanda yaganni dasu jiya, tasowa gayen yayi zuwa idan gadon yake, tare da mi awa Mus'ab hannu sukayi Musabaha."Ya arfin jikin?."



"Alhamdulillah." Mus'ab ya fada a da ile. "To Allah yaara afuwa."



"Amin."



"Zan huce, Allah yakara lafiya."



"Amin-Amin, an gode." Su Umma suka fada, shi kuma ya nufi ofa. Walida ce tayi magana da arfi yanda kowa zaiji."Salma kije ki raka shi mana." kamar mara laka haka na tashi, ina raba idanu nayi waje.



A bakin ofa na tarar dashi. "Salma..." ya faWi sunan, tare da ja cikin wani irin salo mai dadi. Sai naji kamar shi kadai ya iya kiran sunana. "Zan tafi, ngde da kulawa. Sunana Masrur, sanan wanan asibitin na mahaifina ne, kuma yana karkashin kulawata saboda haka, an dauke muku komai."



"Mun gode, amma da ka barshi dan wallahi ban san ta yadda zan fadawa iyayena haka ba."



"Salma..." ya ara kiran sunan na, a nutse na Wago na kalleshi. "Ina sonki." Kara Wagowa nayi na kalleshi, idanunsa suna kaina, da sauri nayi kasa da nawa a raina na ce."nima ina sonka." amma afili kuwa shiru nayi na kasa cewa ko uffan."Bazan ta kureki ba, zanbaki lokaci kiyi tunani. Ga lambata nan." ya faWa yana miomin wani kati, hannu nasa na amsa sanan nace. "Nagode." ka Wa kai yayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login