Showing 36001 words to 39000 words out of 121560 words
ta fahimci Ayanah ta kafe komai a tsakiyar zuciyarta Wanda illar da hakan zai mata tasan mai yawa ce sbd ta riqe baqin cikin da quncin gam a cikin rai ta kasa fitarwa amma ganin bata nuna ba tana komai na rayuwarta a natse ya saka bata ce komaiba sai itama ta sake sbd tinanin insha Allah lokaci na tafiya quncin kila zai ringa wankewa yana ficewa daga ranta.
Zuhrah da farko mamakin Ayanah ta ringa yi ta yanda ta Dena maganar su Abaas kwata kwata da iyayensu ta nutsu duk da tayi sanyi sosai kaman ba ita dinba ko dagowan magana bata iya yi yanzu Wani irin miskilanci da son kadaici ya aureta,
Zuwa yanzu kusan sunsan koina a bangaren nasu na bayi da yawan bayin da suka taho tare sun sake sun karbi wannan rayuwar dari bisa Dari farin cikinsu sukeyi da walwala tareda jin dadi,
Suna Sauran sati daya a kwashe su zuwa cikin asalin masarautar subar daular bayin hankalin Zuhrah ya tashi sbd tsananin tsoro da fargaban shiga BOYEM palace take dan abu daya ne akace a cikin biyun matiqar Kafarka ta shiga gate din masarautar aka rufe to tabbas gawarka ce kadai idan lokaci yayi zata fito bauta ce zakai har tsawon ranka sai kuma idan Ka zamo daya daga cikin bayin da zaa riqa kwanciya dasu Ka zama abar kwanciya kenan a duk lokacinda aka ga dama har tsufanka shima kokuma idan an gama jin buqatar kusantar taka zaka koma tamkar fankon da baida Sauran amfani a duniya shikenan.
Wannan tinanin ne yake saka zuciyar Zuhrah shiga mafi girman tsoro da tashin hankali harma firgita takeyi a cikin baccinta duk tabi ta firgice ta rasa nutsuwarta ga yawan mafarkin Abaas da Nurat datake suna zuwar mata cikin yanayi na tsananin tausayi.
Yanayin ya saka ta fara kasa maida hankali Akan karatun da ake musu ta fara zama yanayi na kaman tana Neman fita hayyacinta,
Yau ma cikin damuwa me tsananin yawa take zaune ta kasa saka Kayanta daya fito wanka ta qurawa guri daya ido hannuwanta qanqame da uniform dinta kanta bai ma San tinanin dayake ba.
Ayanah ce ta fito wankan daure da abin wankanta me tsayi da kauri fatar jikinta ta samu lafiya sosai haskensu kusan duka ya kusa dawowa,
Cikin sanyinta da rashin hayaniya ta dauko uniform dinta zata saka Zuhrah daya zuba mata idanuwanta da sukai jajir zuciyarta na Wani irin zafi da quncin dayake lullabe dasu ta bude baki idanuwanta na cikowa da hawaye tace,
‘Ayanah kin samu sabuwar rayuwar data mantar dake abaas na can wata duniyar yana gararin da zai iya rasa rayuwarsa koma ya rasa din?
Ayanah kin manta komai ne kin zubar da komai?
Sakinah data fito wanka ne ta iso gurin Zuhrah din da sauri tana riqe hannunta cikin tausasawa tace
‘Kar kice haka Zuhrah’
Fizge hannu Zuhrah tayi tana Miqewa tsaye idanuwanta na gangaro da hawaye tace iso gaban Ayanah din wadda bata iya juyowa ba ta kalleta cikin wani irin radadin zuciya tace
‘Maye a cikin wannan sabuwar rayuwar daya mantar dake yan uwanki da halinda muka shiga?
Daman damuwarki Akan yan uwanki na dan lokaci ne?
Daman akwai jin dadin da zai taho miki ki manta dan uwanki dake can duniya cikin garari da qunci?….
Riqota da karfi sakina tayi tana cewa
‘Ya isa haka Zuhrah,kinfi kowa sanin Ayanah ba haka take ba karki Bari Batan tinani yakaiki ga aikin dana sani’
Sake fizge wa tayi tana kallan Ayanah wadda ta dago ta zubawa Zuhrah idanuwanta da sukai wani irin jajir tsananin qunci da radadi me ciwon gaske yana cikesu amma bazata iya cewa komaiba Bayan kallan zuhran dake fada mata maganganu masu ciwo da radadin gaske.
Zuhran ma cikin tsananin jin ciwo da radadin ganin idanuwan Ayanah din taci gaba da fada mata maganganun da itama suke sosa zuciyarta tace
‘Ayanah su Amma sai sunyi Allah wadai dake da zasu dawo duniya su ga yanda kika zabi jin dadin duniya kika manta amanar da suka bar miki a lokaci dan qanqani,
Abaas zaiyi baqin cikin zabar sonki fiyeda Sauran yan uwansu idan yaga yanda kika zabi wata rayuwar akan tinaninsa,
Ayanah inama ace Nurat ce aka bar mana dan ita bazata taba manta yan uwanta ba koda bata cikin hankalinta…..’
Wasu irin hawaye ne masu tsananin dumi suka gangaro daga cikin idanuwan Ayanah a karo na farko Bayan tsawon lokaci mai nisa,
Silalewa qasa take kokarin yi sakina tayi saurin riqeta tana fasa kukan kalaman Zuhrah itama sbd tsananin tausayin Ayanah wadda har lokacin ta kasa furta komai sbd rabata da ranta ne kawai kalaman Zuhrah basuyi ba amma sun gama ratsa zuciyarta sun yayyankata,
Kalaman sun qarasa karya duk wani kuzarin daya rage mata na rayuwa,
Kalaman sun yanka mata sabon Raunin da shima har abada bazai warke ba…….
Wasu irin hawayene ke gudu sosai a fuskanta ta kasa iya tsayuwa duk riqon da sakina tayi mata silalewa qasa tayi tana Dora tafin hannuwanta biyu a fuskanta ta rufe wani irin kuka mai qaramin sautin daya saka Zuhrah yin tsit yana zuwar mata jikinta na wata irin rawa sosai wadda ta saka sakina zubewa qasa tana rungumeta da sauri,
Zuhrah ma sautin kukan ya ringa sosa zuciyarta ta durqushe itama a gurin tana fasa kuka sosai zuciyarta na dana sanin saka Ayanah kuka irin haka.
Shiru dakin ya dauka babu sautin dayake tashi saina kukansu mara sauti sosai amma babu dadin Ji ko kadan.
#MAMUH
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_
Mamuhgee
22
*JEWELRY JUNCTION*
08039440312
Ina macen datasan Yar kwalisa ce ko kuma wadda ke son zama cikakkiyar Yar kwalisa da zata kece Reni a cikin yan uwanta mata harma da maza ma,
Ina macen dakeson ta shiga mutane a kalli wuyanta da hannuwanta a sake kalla batareda an tantance asalin gwal da diamond ne a jikinta ba ko kuwa me Kama dashi ne??
To tazo ga inda dukkanin wani burinta zai cika gameda son hakan,
Mata Da Ado da Kwalliya Akasanku JEWELRY JUNCTION shago ne Na kayan Kawa Na Mata Manya DA Qanana,
✅duk wani nau'in design Na Sarka, 'Yankunne, Awarwaro, Zobe, Agoggo DA sauransu akwai su kala daban, daban. Sayen daya Ko sari👌
✅Munda ready to wear Na Adire dana materials daga kan boubou gowns zuwa palazzo DA tops dinki Na zamani👌
✅Idan ke ma'abociya son Kamshi ce munada turaruka kala daban daban masu Kamshi da rike jiki👌
✅Gefen inner wears din Yara ma ba'a barmu a bayaba, bra tops, half vest,vest, boxers DA pants Duk akwai masu kyau da inganci😍
🛒Shagonmu na nan a kan tanki road, guiwa low-cost a cikin garin Sokoto. Muna tura kaya ko wace jiha cikin Aminci DA Amana In Sha Allah.
WhatsApp 08039440312
Tiktok :@sokoto jewelry seller
Instagram: jewelryjunction23
*********
Sun jima a wannan yanayin kafin Ayanah ta taqaita kukanta data jima bata samu yi ba sai yau ta miqe tareda sake komawa toilet.
Acan ma wani irin sabon kuka ta durqushe tana yi Wanda dukkaninsu suna jiyota daga bandakin sai data jima tayi ta gama ta wanke fuskanta da ruwa ta fito ta goge fuskanta ta shirya cikin uniform dinta tana jin kirjinta da zuciyarta na Wani irin ciwo amma batada abin yi musu kawai qarasa shirinta tayi ta koma gefe ta zauna tareda kallan Zuhrah dake kuka har lokacin ta taso ta rankwafo kawai ta sumbaci tsakiyar kanta da gefen fuskanta ta bude baki da tsananin sanyin murya ta bude baki tace
‘Ya isa haka ki wanke Fuska ki shirya mu fice’
Ajiyan zuciya Zuhrah ta sake tareda dagowa ta kalli Ayanah din zata bude baki tayi magana Ayanah ta girgiza mata kai tana cewa
‘Ba komai ya wuce kije ki shirya din’
Miqewa Zuhrah tayi ta fada toilet duk ta zama kalar tausayi.
Tana fitowa sakinah ma ta shiga suka gama shiryawa tsaf suka fito su ukun suka wuce zuwa hall din karatun.
Wannan sabanin da suka samu ya sake ruguza Ayanah ta qarasa rasa walwala da kuzarinta sbd damuwan datai mata yawan gaske a cikin rai dan haka ta sake zama tamkar qanqara sbd sanyi da rashin magana sosai,
Komai Zuhrah takeso shi kawai take mata bata iya hayaniya ko magana koyaushe indai suna daki Zuhrah na jikinta kwance zata rungumeta tana mata addua da shafata dan bata nutsuwa sbd tsoro da firgici na Neman taba kwakwalwan Zuhrah din tsoro mai tsanani kawai take samun kanta sbd ganin kaman suna shiga palace din sun rasa kansu kenan har abada kila ma harda junansu,
Tsananin tsoron rabuwa da Ayanah take ji fiyeda komai ma daya faru a baya,
Idan har zata rasa Ayanah so take Allah ya dauki ranta ta mutu,
Koba komai mutuwar ma take tsananin so sbd rashin nutsuwan datake ji a zuciyarta.
Ana gobe ne ranar tafiyarsu zuwa cikin palace a zaune suka kwana rungume da juna Sai a Daren Ayanah ta bude baki tayi doguwar magana da Zuhrah din tareda tinatar da ita babu abinda zasu iya yi a duniya yanzu su samu damar haduwa da Abaas wata rana irin su jajirce su rayu har zuwa lokacinda Allah zai sake kawo musu wani sauyin rayuwar,
Babu abinda zasu sakawa kowane dan GHAZ dashi Bayan su rayu su kai labari dan haka matiqar tanason Allah ya kawo mata ranar haduwa da Abaas ko jin labarinsa to tabbas zata jajirce ta rayu zuwa lokacinda Allah zai dauki ranta.
Zuhrah da Sai a lokacin ta fahimci karfin halin da Ayanah takeyi jin tayi jikinta ya sake mutuwa dan kuwa kaman ita bazata iya ba takeji amma ko bazata iya ba zatai kokarin bawa Ayanah karfin gwiwan rayuwa sbd itace kadai a raye wadda take saka zuciyar Ayanah bugawa daidai,
Ita dai kam bazata iyaba da gasken gaske duniyar take son Allah ya dauketa daga cikinta ta tafi ta huta amma kuma idan babu ta Ayanah zata zama mara amfani a duniya sbd bazata taba moruwa ba.
Koda asuba tayi suna tsaye sbd tin kafin asuba aka tadasu aka tarasu a babban guri,
Anan aka sake rarraba musu uniform da abubuwan amfani a jaka aka bawa kowa nasa,
Sallar asuba kawai suka koma daki sukai aka sake buga qararrawa kira suka ringa fitowa kowa dauke da jakarsa fes dasu,
Jikin Ayanah dana Zuhrah a sanyaye sbd Sai yanzu ne Ayanah take sake fahimtar tsoron Zuhrah na zaa iya rabasu a gurin aiki ko gurin kwana dan haka itama jikinta ya tsananta sanyi.
Motoci ne masu tsayi bus bus aka zuba su a ciki aka fice dasu zuwa cikin palace din.
A mota ma hannuwansu na riqe dana juna qamqam sakina na gefensu,
Ficewa akai dasu daga babbar gate din daular bayi aka miqa zuwa mahaukacin gate din shiga BOYEM palace wadda securities dinta suka mugun baci sbd tsananin tsaro,
Shi Karan Kansa gate din shiga Masarauta kashe idanuwansu sukaga kaman yana yi sbd kyansa dayake tamkar na zinari,
Scannin komai nasu dasu kansu akai daya bayan wuni guda Ana abu daya kafin Ana gap da kammala wa aka zo kan wasu su biyu wainda sunan mahaifinsu Yazo irin daya komai da komai.
Dakatar dasu akai tareda zagaye su da wasu irin securities da suka sakasu saurin durqusawa kasa kansu a qasa jikinsu na wata irin rawa cikeda tsoron dake Neman rabasu da bugawan zuciyarsu.
Chief security ne Yazo gurin da Kansa ya kallesu dakyau kafin ya kalli sunayen nasu
Akan wadda tafi girma ya tsaida idanuwansa ya bude baki yace
‘Meye alaqarku da sunanku Yazo daya??
Wani yawu babbar ta Hadiye kafin cikin sanyi kanta na qasa tace
‘Alaqar jini ce……
Ko rufe baki bata gama yi ba akai sama da ita tamkar ba Mutum ba aka jefa cikin wata motar da batai Kama da mota ba sbd tsarinta dayafi Kama da motar yaqi.
Wani ihu taje yi tana kokarin riqo qanwarta a lokacinda ake janta tana jin kaman ranta zai fita amma ko imanin kallanta babu take aka buga kanta da karfen motar ta zube a cikin motar jini na fitowa gefen fuskanta kadan.
Qanwar tata ma Wani irin kuka me karfin gaske takeyi tana ambatar sunan yar uwarta kaman ranta zai bar jikinta take aka sumar da ita da wata shocker a gurin akace a dauketa a maidata daular bayi.
Ganin hakan ya saka wainda ke bayinsu suma su uku fara rawar jiki sbd suma yan uwane uwa daya uba daya.
Suma Ana duba sunayen su take aka rarrabu su ukun aka soke lasisin biyu aka bar daya Sauran zaa rabasu zuwa dauloli daban daban ga Wanda yayi rashin saa kuma ciyar da dabbobi namansu kawai akeyi sbd tin farkon shigowa qasar baa karban bayin da suke da alaqa da juna,
Doka ce da kaida me tsananin karfin gaske baa barin masu alaqa a masarautar matsayin bayi duk lokacinda aka Kama masu alaqa kai tsaye hukuncinsu a kashe daya abar daya tin asalin asali wannan dollar take sbd a shekarun baya sosai da suka gabata akwai bayi uku da suke uwa daya uba daya da suka kulla shirin guduwan juyin mulkin daya haddasa fitina mai tsananin gaske a masarautar boyem wadda baa taba maimaita irinta ba dan haka tin kakannin kamanninsu aka tsauranta dokar tareda kafata mai karfin gaske kai tsaye duk bawan daya kasance yanada ahali to kai tsaye hukuncin Kisa ne ga ahalin gabaki dayansu sbd kawar da kowace irin barna,
Bayi da yawa tin shekarun da suka gabata sun rasa ahalinsu akan hakan,
Duk bawan dayake boyem Sai an tabbatarda baida kowa a duniya Bayan Kansa sbd Kaucewa fitar sirrin masarautar Shiyasa ko Ka samu yancin Ka baka taba barin qasar boyem sbd bakada kowa a duniyar sedai Ka Gina sabuwar rayuwa.
Dan hakanne yasa duk wainda suke kawo bayi qasar sai sun tabbatarda bayinsu basuda kowa a duniya ko sunada Sai a tabbatarda basa duniya an kawar dasu sbd Ka zama na masarautar ita daya,
Kusrawa tin a farkon shigowa qasar sun tabbatarda bayinsu basuda kowa a duniya dan hakanne kai tsaye a yanzu duk Wanda aka samu yana tareda wani nasa zaa kawar da daya a bar daya.
Doka ce da tsananin karfinta babu Wanda zai taba wucewa kai tsaye ba tsayawa tinanin komai ake kawai da daya dan haka yanzu dinma hakanne zai faru akan wainnan sabbin bayin.
Cikin masifaffiyar azaba suna tsananin fita hayyaci suke kasa rabuwa da juna inda daga karshe suka zabi a dauki ransu su duka ukun wainda suke Bayan na farkon dan hakan babu bata lokaci take aka jasu su ukun kai tsaye akai baya dasu sedai kawai yaji qarar bindigar cika musu burin abinda suka zaba amma babu Wanda yaga inda aka fito ko yi da gawarsu.
Zuhrah da Ayanah dake kusan qarshe dagowa sukai a Wani irin slow suka kalli juna dukkaninsu jikinsu na qarasa sakewa gabaki daya da sabuwar mummunan kaddarar dake gabansu wadda basuda ma tinanin yi akanta.
Jajir idanuwan Ayanah sukai Zuhrah kuwa gangarowa nata hawayen suka fara da idanuwanta da suka kasa daukewa daga kan Ayanah tanajin tin yanzu tamkar ruhinta na barin jikinta sbd rabuwa da Ayanah na nufin mutuwarta,
Ita zata zabi a kasheta abar Ayanah sedai kuma basuda masaniyar waye zaa Bari a cikinsu kuma waye zaa bari,
Ita tanason Ayanah ta rayu sbd tanada dauriya da tawakkali hakama zata rayu a cikin aminci anan din amma kuma tasan Ayanaah zata zabi a kashesu gabaki dayansu kaman yanda na gabansu suka zaba sbd bazata iya barin a rabasu ba.
Wasu hawayen ne masu zafi suka gangaro mata tana sake kallan Ayanah tanason rungumarta taji dumin jikinta na bankwana amma daman hakan ta gama qare musu har abada dan haka zata zabi su rayu sbd Ayanaah kawai koda hakan na nufin raba jininsu har abada indai tana ganinta hakan ma ya isheta.
Sakinah dake gabansu dan juyowa tayi ahankali ta shiga tsakiyar su itama idanuwanta na cikowa da hawayen tsananin tausayinsu musamman Ayanah dake girgiza kai ahankali idanuwanta na tsananta ja hannuwanta na fara rawa ahankali ta bude baki tana kallan Zuhrah dake kallanta tana hawaye masu tsananin rauni da ciwo tace
‘Zuhrah bazan iya rayuwa babu ke ba,
Zuhrah na zabi barin duniya tareda dake mu tafi mu huta…..
Girgiza kai Zuhrah tayi hawayenta na tsananta jikinta a sanyaye tace
‘Abaas fa?’
‘Allah zai zama gatansa amma a yanzu da kike tare dani bazan iya rayuwar da babu ke ba Zuhrah’
Kuka Mara sauti Zuhrah ta sake tana kokarin zare hannunta daga na Ayanaah din tace
‘Sbd ki rayu tare dani din zan zabi hakan,
Inason ki rayu Ayanah ki samu rayuwan da zai baki nutsuwa dan hakanne dole zamu zabi raba jini,
Kina raye Ina raye muna Masarauta daya muna shakar Numfashi guri daya insha Allah zamu samu yancinmu wata rana mu tafi tare’
Girgiza kai Ayanah tayi da karfi tana sake riqe hannun Zuhrah tace
‘Zuhrah idan muka zabi hakan mun rabu kenan har abada,muna guri daya amma bazamu taba nuna mun san juna ba bare Hadin jini,
Bazamu taba sake jin dumin juna ba,
Bazamu taba kallan juna ba,
Bazamu taba dawowa Ayanah da Zuhrah GHAZ ba shikenan mun rabu har abada sai kuma ranar da Allah ya bamu yanci Kinsan da hakan?
Wannan shine doka da qaidar kuma taka hakan a bakin rayuwarka kenan,bazan iyaba Zuhrah.’
#MAMUH
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_
Mamuhgee
23
FREE CLASS ALERT
07068433198
Kinason business dinki ya zama tamkar kamfani me zaman kansa,
Kina da kaya ko sabis Amman tallanki baya Jan hankali?
Mutane suna ganin tallanki Amman basa saye?
Lokaci yayi da Zaki koyi yadda ake vedio advert mai daukar hankali da kawo kwastomomi🥳🎉
Shiga wannan FREE CLASS ki koyi yadda ake hada vedio da zai juya masu kallo zuwa kwastomomi🎉
**********
Sakinah data yadda da indai zasu rayu gwara su hakura din matiqar sunsan suna guri daya yafi a san sunada alaqa tin anan gurin a kashesu a banza kokuma a rabasu duniya daban daban gwara su tsaya guri daya koda babu abinda zai sake hadasu har abada dan haka hannuwansu ta Kama da hannuwanta biyu ta rabasu da karfi Zuhrah na Wani irin kuka Mara sauti zuciyarta na mutuwa a matakin karshe na shikenan.
Ayanaah ma wani irin kuka takeyi mata sautin tana kasa dauke idanuwanta daga Zuhrah wadda itama ita take kalla sakinah ma hawayen takeyi tana sunkuyar da kanta qasa.
Layi na zuwa kansu sunansu AYANAAH GHAZ da ZUHRAH GHAZ Ana tambayan alaqarsu Ayanah ta dago jajayen idanuwanta da suka rine gabaki daya ta zubawa Zuhrah wadda ta goge fuskanta tas ta bude baki tace
‘BABU ALAQAR JINI sunan ne iri daya’
Tana fadar haka take aka buga stamp a sunayensu tareda wata irin stamp ta daban wadda take bada tabbacin ko a toilet daya tsautsayi ya hadasu a