Showing 117001 words to 120000 words out of 121560 words
BOYEM aka daura musu aure sbd hanasu gurin zama da akai koina garin sbd basada aure dan haka suka daura aure Wanda har cikin zuciya da ransu suna tsananin son junansu hakama sun shirya rayuwa da mutuwa a tare,
Aurensu ne ya kawo wata yar nutsuwar rayuwa a rayuwarsu data cikin tsananin duhu da qunci tareda kadaici,
Kusanci da sabuwar shaquwa da kauna tareda so me tsananin gaske sukewa juna suna sake Jin karfin gwiwan fuskantar rayuwa.
Bayan wata uku suka bar BOYEM sakamakon cikin daya bayyana a jikin Ayshaah,
Cikin ya taho mata da rashin lafiya sosai dan haka tafara wata irin rama taba kofewa alaman jininta yana yin qasa dan haka Abaas ya sadaukar da rayuwarsa da kudirin sa dan bata nutsuwan rayuwan daya kamata kodan abinda zasu haifa kafa suyita yawon duniya dashi dan haka suka juya inda suka fito,
Shima kirgen garuruwan da suka Baro a baya tsawon shekaru lokacin da aka dauko su daga garinsu ya fara yi dan komawa qasar sa garinsa gidansu da iyalinsa sbd matiqar Ayanah tana raye to tabbas yasan zata je nemansa a cikin duniya kokuma anan gidan mafarinsu dan haka zai jirata daga yanzu har ranar da Allah zai dauki rayuwarsa.
*****tafiyar watanni sukai nai cikeda wahala da ukuba da tsinkewan zuciya ga yanayin ayshahh kafin Allah ya iso dasu dajin garinsu daya sha matiqar wuyar gaske kafin ya gane hakama dukiyarsu tayi qasa dan haka Koda suka iso ANJOM GHAZ cikin Ayshaah ya tsufa yakai wata takwas.
A garin ANJOM babu mutane sosai sbd garin ya Riga ya mutu dan haka babu wata daula da tatttalin arziki kaman baya amma akwai kwanciyan hankali dan haka babu wahala ko tashin hankali aka karbesu tinda ansan waye shi hakama duk da shekaru sunja kamanninsa basu sauyaba.
Babu kowa a fadar mahaifinsa dan haka Sauran dukiyar daya taho da ita ya bayar aka dan yi gyaran dazai yiyu suka shiga batareda tsoro ba suka zauna tareda kokarin daga ANJOM.
Kokarin dayazo dashi da qwazo ya saka jamaar garin samun kuzari da qwazonsu suma ya dawo take garin ya fara komawa ANJOM dinsa na baya a bisa mulkin ABAAS GHAZ din.
#MAMUH
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 11:19 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee
68
ANJOM GHAZ ta dawo ANJOM dinta duk bazata taba komawa ANJOM din baya ba amma Abaas yayi iya kokarinsa ya sake kafata da dukiyarsa da karfinsa da lafiyarsa datake qasa sosai amma ya tsayu ya kasa barin ciwon kirji da zuciyar dake damunsa yakai sa qasa,
Ayshaah ma ta samu rayuwar kwanciyan hankali da nutsuwar da Abaas ke fatan ya bata sedai yanayinta itama sai ahankali lafiyarta tayi qasa sosai musamman da cikinta harya wuce watannin haihuwa bata haihuba dan haka aka ringa kawo mata addua da maganin al’adarsu tana sha,
Kauna da soyayya me girma tareda wata irin tsafta da nutsuwa take tsakanin Ayshahh da Abaas Wanda kusan duk ANJOM ansan irin son dayake mata da irin yanda ita kuma ya kere mata komai da duniyarta harma da rayuwarta dan haka yanayin jikinta ya saka duk Wanda yake garin mutuwar jikin halinda Abaas yake ciki Akan rashin lafiyarta.
Cikinta na cika wata goma sha daya cif ta Wanda yayi daidai da wata su uku cikin na hudu da dawowa ANJOM da samun rayuwa me nutsuwa Bayan shekarun gararin duniya da gwagwarmaya a qasashe cikin rashin gata hakama shekaru biyar cif da rasuwarta mahaifinta ta haifi ‘yarta,yar Abaas,jinin ghaz,hasken idaniyar mahaifinta a duniya wadda tana haihuwarta a idanuwanta kadai ta kalleta ko a hannunta Allah bai bata ikon daukanta ba tabar duniyar ta tafiyarta tabi mahaifinta Wanda bata taba Dena kewa da radadin rashinsa ba a rayuwarta tabar masoyinta da ‘yarta a duniyar da basuda kowa sai junansu a yanzu.
ABAAS GHAZ wannan shine farkon bude dukkanin kofofin karfin ciwon dayake cin tasa zuciyar wadda ta kasa dauka da jure rashin matarsa wadda itace take riqe da zuciyarsa dake a zube tin acan baya ta rashin yan uwansa a rayuwarsa dan haka mutuwar Ayshaah ta karya duk wani karfin hali da jarumtar dayake da ita ya fadi ciwon da bai taba samun waraka daga garesa ba,
A haka ya rungumi ‘yarsa da sabuwar kaddararsa a cikin qunci da ciwo,
Ya zama uwa kuma uba ga yarsa
Ya zamo aboki da dangin uwa da dangin uba ga yarsa wadda ta taso itama a rayuwarta batasan kowaba Bayan mahaifin nata sai tarin sunayen da kunnuwanta da zuciyarta sun riqesu,
Duhu ne a rayuwarsu da babu ranar shigowan haske a cikinsa,
Qunci ne a rayuwarsu da babu ranar saukar sa sbd duk wani daci da qunci da baqin ciki tareda duhun rayuwar mahaifinta ta dabaibaye tata rayuwar ta shigo ciki tayi zaman da bata taba sanin menene farin ciki ba bare dandanon yanda yake,
Bata taba sanin haske a rayuwa ba bare sanin yaya yake a ruhi,
Bata taba sanin walwala ba bare sanin ya murmushi yake ba a zuci da Fuska dan haka a haka ta taso tin mahaifinta nada karfi da kuzarin kulawa da ita har karfinsa ya qare shima ciwo ya kaisa qasa yana jiyo qamshin mutuwarsa datake gap da iskoshi dan haka tinda ya kwanta ciwo ya sadaukar da Sauran numfashinsa gurin rokon Allah a kowace daqiqa Akan Allah ya kawo masa Ayanah kafin ransa yabar jikinsa sbd yarsa Ayanaah,
Ya roki Allah a kowane Hali Ayanaah take Allah a kawota garesa kafi mutuwarsa sbd goben yarsa ta inganta,
Ya roki Allah ya tsaya Akan rayuwa da duk wani lamarin BAHAR,
BAHAR itace rayuwa da sanyin idaniyarsa da ayanzu yake rokon Allah ya zama gatanta ya tsaya a lamarinta ya bata kariya da tsari daga kowace irin sharri na rayuwa da zata fuskanta.
Tinanin rayuwarsa na sake zuwa gangara babu haske ko daya a rayuwar dazai bar BAHAR dinsa ya saka ya roki Allah dauki ransa tareda ‘yarsa subar duniyar tare sbd zuciyarsa ta kasa riqe tsananin daci da radadin dayake ji na tinanin barinta a duniyar da babu komai a cikinta Bayan zalinci da son zuciya ita kadai ba uwa ba uba ba dangi ko daya sai tarin duhu da qunci.’’
****Wani wahalallen Numfashi ya sauke ahankali daqyar numfashin yana sarqe wa ya dago jajayen idanuwansa Akan NUAB ya sauke yanason bude baki yayi magana amma karfinsa yayi qasa sosai baya iya jan Numfashi da kyau hannuwansa na dan rawa yanason dagawa ya sake Kama hannun NUAB din amma karfin ya qare,
Da sauri Aleey ya da idanuwansa ke zubda ruwa ya qaraso ya mayar masa da oxygen sbd NUAB ganinsa ya dauke tsaf sbd yanayin mummunan Jan tashin hankali da jijjigar zuciya daya shiga hannuwansa rawa sukeyi yana riqe da hannun Abaas din daya gam,
BAHAR da tinda mahaifinta ya fara bada labarin suka iso amma bata shigoba itada sakinah suna tsaye kofar sakinah na Wani irin kuka mara sauti jikinta da kafafunta na rawa,
Ita kuwa jikin bangon gurin ta jingina tana rintse idanuwanta dake Wani irin silili da yajin azabar radadin dayake cikin zuciya da jininta da suka zama rayuwarta datake tamkar fanko,
Shigowa tayi kafafunta na wata irin rawa hawaye masu tsananin zafi da radadin dayake Neman fasa zuciyarta ta iso gurinsa tana zubewa qasa kan kafafunta ta Kama hannunsa daya da hannuwanta biyu dake wata irin rawa ta Dora kanta Akan tafin hannunsa ta fasa wani irin kukan da bata taba fasawa ba a rayuwarta me tsananin tsima zuciya da tafa tsigar jiki tana kasa cewa komai Bayan sake hannunta da nasa datai kanta na kai batasan me takeji ba a yanzu Bayan gajiya da rayuwa,
Bata taba shaawa ko so daya taci gaba da rayuwa ba idan mahaifinta yabar duniya sbd babu abinda zata tsaya ta samu a duniyar,
Mahaifinta shine kadai hasken dayake rayuwarta idan ya tafi rayuwar batada Sauran amfani sbd duhun dake cikinta kasheta zaiyi dan haka bata taba sauya adduarta daga Allah ya dauki ran mahaifinta tareda ita ba.
Ahankali ya bude idanuwansa dake rufewa ya Ambaci sunanta daga Wani irin sautin daya saka kukanta tsananta tana dukan kirjinta dake tsananin ciwon da tinda ta tashi itama dashi ta tashi sbd baqin ciki da qunci kawai.
Aleey ne daya fita ya dawo ciki da sauri tareda isa gefen NUAB cikin nutsuwa da qasa qasa ya sanar dashi komai na tafiya da Abaas din ya zama ready.
Gyada kai NUAB din yayi a hankali yana kallan Abaas da idanuwansa dake cikeda tsananin kaunarsa yana sake riqe hannunsa daya a cikin nasa yace a kira doctors.
Babu bata lokaci doctors suka taho tare akai masa wata allura a cikin drip tareda Sauran abubuwan da suka kamata aka bada umarnin kowa a fice.
BAHAR da NUAB ne kadai basu fice ba hakama babu Wanda ya iya sakin hannunsa a cikinsu saima Wani irin kukanta sanyayyan sauti dake tashi tana sake cusa fuskarta cikin tafin hannunsa daya sake baya motsi ko kadan.
Fitowa akai dashi aka saka ambulance suka fada motoci suma kai tsaye aka wuce airport dashi inda komai yake a shirye.
Private jet suka shiga Bayan dan dogon shirye shiryen dabai dauki lokaci ba Wanda akaiwa kowa tinda suka iso da Abaas din dan haka kai tsaye jirginsu ya daga gabaki dayansu.
#MAMUH
09033181070
[09/12, 11:22 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee
69
Bayan doguwar tafiya Greece suka isa inda suna sauka jirgin sultan me BOYEM na isa qasar tareda Ayanah wadda jikin yake buqatar ganin likitocin nan da NUAB din ya tanadar mata tini amma basu taho ba dan haka doctors din su buqaci a kawota sbd ta farfado a kusa dasu dan su tabbatar sun bata treatment din dazai hanata rasa hankalinta.
Hakan ya saka NUAB shima kai tsaye tahowa da Abaas din nan dan ganin likitocin,
Manyan motocin ghaz dake qasar ne suka taho har airport suka daukesu shikuma Abaas ambulance ta asibitin ce ta taho dan haka kai tsaye asibiti suka dunguma gabaki dayansu.
Koda aka isa asibiti da Abaas ya farfado sedai zuwa lokacin gabaki dayansu jikinsu yafara mutuwa me tsananin gaske ta yanayinsa dan haka Koda suka iso abinda NUAB ya saka akai musu shine hade Abaas din da Ayanaah a daki daya.
Koda suka iso asibitin babu kowa sbd baa barin relatives shiga kai tsaye dan haka sultan Bayan an kammala komai na admitting Ayanah dashi da tenya tareda securities dinsa da fadawansa barin asibitin sukai zuwa masaukinsu sai kuma idan an nemesu dan haka Sam basuma San isowan su NUAB ba.
Duk wani taimakon gaggawa da doctors zasuyi wa Abaas dayake fidda jini a bakinsa a duk ya yunqura da tarin da bayama fitowa sbd rashin karfi ko kadan daya rage a jikinsa sunyi sunga ma sunbarwa Allah dan haka NUAB shigowa yayi dakin a sanyaye kafafunsa da Wani irin mugun nauyi ya tako ya iso inda yake.
Tsayawa yayi ahankali bakin gadonsa tareda miqa hannunsa a tsananin sanyaye ya Dora Akan na Abaas din Wanda ya fara bude nasa idanuwan da ganinsu ya fara ragewa ya saukesu Akan NUAB din.
Wani irin Numfashi me tattare da sanyin jiki NUAB ya sake tareda daga hannun Abaas din ahankali ya Dora Akan na Amminsa dake kwance har lokacin bata farfado ba ya hada hannuwansu guri daya ya matse musu su da nasa hannuwan biyu yana sunkuyar da Kansa qasa wasu hawaye masu tsananin Zafin gaske suna ciko idanuwansa ya kasa cewa komai….
Kokarin tsayawa Numfashi da bugawan zuciyar Abaas sukeyi sbd abinda ya dirar masa zuciya ya Lumshe idanuwansa ya bude ahankali da qurawa fuskar NUAB dake sunkuye ido batareda ya juyoba yaga fuskar hannun dayake hade da nasaba sbd bazai iyaba.
Aleey ne dayake Bayan NUAB din ya tako a sanyaye shima nasa idanuwan na cike da hawaye masu zafi ya Kama kan Abaas din cikin kulawa da ya juyo dashi setin fuskan Ayanaah dake gefensa Akan nata gadon daban idanuwanta a rufe fuskarta fayau asalin kamanninta babu abinda ya sauya sai manyanta datai….
Wasu hawaye ne masu tsananin dumi suka gangaro daga cikin idanuwan Abaas daya kasa kyaftawa daga kafe idanuwansa dayayi Akan fuskar Ayanah hawayensa na tsanananta gangarowa da Wani irin dumi,
Bude bakinsa yakeson yi ya Ambaci sunanta amma Allah bai basa damar hakan ba dan haka hannunsa ya dan iya motsawa ahankali ya Kama hannunta cikin nasa tareda sauke ajiyan zuciya me sanyi ya rufe idanuwansa ahankali wasu hawayen suka gangarowa ahankali idanuwan na rufe.
Shiru gurin ya sake dauka me tsananin gaske Wanda ya saka NUAB sauke ajiyan zuciyar daya sauka tareda wasu irin hawaye masu Zafin gaske daga idanuwansa da suka kasa riqe dukkanin jarumtarsa.
Aleey ma Juyawa yayi ahankali yana saka hannunsa daya ya rufe idanuwansa dake fidda hawaye sosai har hannuwansa rawa sukeyi kaman yanda na NUAB ke wata irin rawa sbd tabbatarda Ran ABAAS GHAZ ayau yabar jikinsa ya amsa kiran ubangiji.
Sakinah dake bakin kofa rawa jikinta itama ya dauka me tsananin gaske ta saka hannu da karfi ta rufe bakinta tana fasa wani irin kuka Mara sauti zuciyarta na tsananin ciwon me Zafi.
BAHAR da bata fahimci meya ke faruwa ba tana tsaye daga waje idanuwanta jajir ganin irin yanda sakinah ke Wani irin kuka jikinta na jijjiga ya sakata fara takowa ahankali ta sako kai cikin dakin kafafunta na rawa.
Gap da isowa ga mahaifinta data kafe da ido takeyi Aleey ya sake fasa wani irin kuka me sautin daya sakata fahimtar Abaa dinta ya bar duniya yabarta.
Duhu ne ya rufe zuciya da idanuwanta ahankali Wanda ya sakata kafafunta gazawa ta yanke jiki a gurin ta zube jikin NUAB Wanda ya tarota da hannu daya har lokacin Sauran hannunsa daya yana riqe da hannun Abaas da Ayanah.
Doctor shigowa sukai suka fara kashe naurorin dake manne da Abaas din bayan sun rubuta time of death nasa.
Daganan ficewa sukai sukabar fmly da jimamin rashin.
Kuka sosai sakinah takeyi kaman rayuwanta tazo karshe sbd wannan itace kaddarar karshe data qarasa yanke farin cikin dasuke sakaran yi a gaba,
Ayau Abaas ya tafi yabar duniya kaman yanda Nurat da Ayshaah suka tafi sun barsu da tabo da gurbin da bazai taba cikewaba har abada.
NUAB daukan Bahar yayi yakaita Dayan dakin da doctors zasu dubata kafin aleey ma da yasha kuka sosai ya fara shirin komawansu da gawar da bazaa rufeta a nan ba dole zasu koma dashi ghaz acan zaa rufesa.
Zaman qunci da damuwa tareda zullumi me tsanani sukai kafin cikin saa suka samu jirgin dawowa da gawar wadda Washe gari tinda safe suka Juya kuma har lokacin Bahar bata farfado ba haka suka dawo da ita.
Haka suka kuma doguwar tafiya kafin suka sauka kai tsaye suka sake daukan manyan motocin da suka kaisu har cikin ANJOM ghaz da gawar Abaas GHAZ Wanda a lokacinda Bahar ta farfado rungume gawar tayi ta kasa cewa komai hatta kukan ya kasa zuwar mata idanuwanta ne kadai sukai Wani irin ja.
A haka babu bata lokaci akai janaizarsa aka rufesa a cikin masarautar gefen kabarin mahaifinsa da mahaifiyarsa da Ayshaah da akai a cikin masarautar duka dan haka Ana gama janaizarsa suka tattaro suka juyowa tareda Bahar wadda gabaki daya baa San ma Wani halin rayuwarta take ciki ba sbd ko kyaftawa kaman batayi komai nata ya tsaya cak tana rungume a jikin sakinah wadda take jinta har cikin jinin jikinta.
Suna isa qasar inda zasubi jirgi anan NUAB ya bada umarnin Maa sakinah da Bahar a wuce BOYEM dasu shikuma zai koma ga Amminsa.
Zasu wuce Bayan kowa ya fice kallan Maa sakinah NUAB yayi da manyan idanuwansa da sukai tsananin Laushi ya tattaro dukkanin nutsuwansa ya bude baki yace
‘Maa ina Neman wata alfarma da nakeson kimun alkawarinta a yanzu,
Inason kimun alkawarin idan Ammi ta farfado bazaki taba fadawa mata Abaas yabar duniyaba sbd bazata iya dauka ba a yanzu da muke kokarin Neman lafiyanta,
Kimun Alkwarin bazata taba sani ba
Bazata zan komai ba har sai ranar dana fada mata hakan da kaina,
Zuwanmu ghaz da duka abinda ya faru Inason ya zama sirrin da bazai taba fita ba sbd lafiyarta da bazata iya dauka ba,
Ki riqe ‘yarsa Amanace ya bar miki amma kada Amminah tasan wace ce ita sbd sanin ita waye din zai saka dole tasan anga Abaas ankuma rasashi dan haka ita din batada kowa sai ke sbd auren da aka daura ba aure ne dazaa tinaba bare qararwa,
Maa Inason kiyimin wannan alkawarin’
Numfashi mai tsananin dumi sakinah ta sauke tareda dagowa ta kalli NUAB tukuna ta Gyada kanta alaman tayi wannan Alkwarin har karshen rayuwarta matiqar ba shine ya tado zancenba ta rufesa kenan har ranta ya fita.
Numfashi me nutsuwa ya sauke kafin yayi sallama da ita aka wuce dasu airport ba bata lokaci jirginsu ya daga zuwa BOYEM.
Suna wucewa da awa hudu suka nasu jirgin yayi daga zuwa ga Amminsa wadda bazai taba dawowa da ita ba matiqar lafiyarta bata daidaitaba.
#MAMUH
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laoualir
*_HAYATEEM_*
Mamuhgee
70
A jirgi kwance jikin Maa sakinah Bahar ke kwance idanuwanta da sukai ciki ciki jajir da galabaitar rayuwa da zuciya tareda sarewa da fidda rahama ga rayuwa gabaki daya,
Rungumeta cikeda wata irin kulawa da kauna me tsananin gaske da Jinta har jininta Maa sakinah tayi sbd BAHAR itace Abaas da suka rasa har abada sai kuma Aljannah idan Allah yayi sunada rabon haduwa,
BAHAR itace jini daya tak ta Abaas dinsu a duniya da idan basu jita har cikin jininsu ba me zasuyi?
BAHAR itace jinin Abaas da duniya Ayanah batada kamarsa,
Ayanah Allah baiyi tanada rabon sake Dora idanuwanta Akan ‘dan uwanta ba rabin jikinta ba sedai tanada rabon rayuwa da ‘yarsa a matsayin matar ‘danta da bazata saniba sbd ita kanta koda NUAB bai sakata alkawarin kada ta fada mata Abaas ya tafi yabar duniya ya barta ba itama kanta bazata taba iya fada mata mutuwar Abaas ba Wanda Ayanah bazata iya dauka ba dan haka wannan Alkawari ne ta daukanwa kanta itama bazata iya fada matan ba sedai shi NUAB din duk ranar dayaga ya kamatan,
BAHAR Amanarta ce a yanzu da zata riqe da rai da rayuwarta tareda bata kariya da dukkanin kauna da kulawan tareda tattalin data rasa tin tasowanta,
Insha Allah indai kulawa da nuna kauna da soyayya me tsanani sune suke kawo haske a rayuwar datake cikin duhun kadaici to tabbas zata cikewa Bahar duhun rayuwarta da haske koda kuwa zasu qare a cikin wannan sirrin su mutu matiqar hakan na nufin kariya da samun tsaronta.
Numfashi ta sauke ahankali me sanyi da mutuwar jiki tana tina rayuwarsu ta baya da yanda suka Baro ANJOM GHAZ da kuruciyarsu