Showing 72001 words to 75000 words out of 121560 words

Chapter 25 - HAYATEEM Hausa Novels By Mamuhgee.txt

10 Dec 2025

3758

sai sunan gari daya,
Zuhrah itace wadda ta raunana kanta taso daukan rayuwarta Akan zama imebēti,
Zuhrah itace wadda aka yankewa hukuncin qarasa rayuwa a gidan yari har abada,
Wannan zuhrahn itace wadda kunnuwanta ke Jin cewa uwa daya uba daya take da wishmah,
Jini daya ne yake gudana a jininsu?
Jinin mahaifiyar LEUL ne yake yawo a jikinta itama,
Kanwar mahaifiyar LEUL kenan??

Wani irin mummunan zufa mai Zafin gaske ne ya gangaro mata ta qaraso tsakiyar dakin kafafunta a sanyaye batada karfin jiki ko kadan idanuwanta na sauyawa jajir dan shikenan ta shiga masifar da batasan Yaushe suka qulla abar su ba,

Dagowa tayi ta kalli Sakinah da duka jikinta ke tsananin rawa da fizga idonta jajir hawaye ma sun qafe mata sbd tashin hankali tana kallan tenya din da tinani Kala Kala a ranta na yanda tenya zata dauka lamarin nan me girma,

Dawo da idanuwanta tayi Akan Ayanah da bata damu da rasa rayuwarta da zatai ba kuka takeyi sosai mara sauti sbd zata rasa ranta ne batareda ta ceto yar uwarta ba zata tafi ta barta a qangin bautar da kila zatai har qarshen rayuwarta.

Kukan Ayanah dake saka har jikinta jijjiga ahankali ya saka tenya kasa cewa komai saima miqa mata NUAB a hankali jikinta a sanyaye yana dan rawar tashin hankali itama dan kuwa ita datake masarautar tafi su sanin girman tsantsar hadarin abinda suka aikatawa masarautar.

A hannuwan Ayanah din ta Dora NUAB daka motsa ahankali cikin showel dinsa ita kuwa Ayanah tsayawa kukanta yayi cak jinsa a cikin hannuwanta ta bude idanuwanta da sukai jajir akansa ta zuba masa ido tana kallan fuskarsa me kyau da daukan Idon da babu abinda ya Bari a cikin kamanninta se gurbin mahaifinsa daya dauko,

Kammanin duka yan uwanta dasuke Kama guda daya da ita da mahaifinsu ya dauko tinda komai nata irin na yan uwanta ne musamman Nurat da Abaas sunfi Kama sabanin Zuhrah da Ammansu tafi Kama da ita dan haka fuskokin yan uwanta da mahaifinta take gani suna yi mata yawo a fuskarsa zuciyarta na Wani irin shiga radadin rashinsu a tareda da ita Ayau data haifar musu ‘dan kanta,

Wasu hawaye masu radadi da sanyi ne suka gangaro mata ahankali suka sauka Akan gefen fuskarsa ta rufe ido tana sake fasa sabon kuka Mara sauti tana dagosa jikinta ta saka a kirjinta ta rungume tsananin radadin rashin Abaas na dawo mata sabo a zuci da ruhi sbd shine Wanda a duniya yafi kowa fata da son ganin wannan rayuwar a rayuwarsa wato ranar da zata haifar masa ‘dan zai dauka ya rungume a matsayin nata sbd irin tsananin son dayake mata,

A koyaushe ya aurar da ita ta Haifa zuriar da zata hadu da tasa shine adduarsa da fata da burinsa tin yanada qananun shekaru gashi Ayau Allah ya raba rayuwarsu da basusan ko iyaka cin rayuwar da zasuyi kenanba,

Tsima zuciyarta kukanta keyi ta sake qanqame NUAB kirjinta tana adduar ‘Ya Allah kada ya dauki ranta sai ta hadu da ‘dan uwanta rabin jikinta hasken idaniyarta Abaas,
Ya Allah kada ya dauki ran Abaas batareda burinsa ya cika ba na ganin zuriarta data haifa a duniya.’

Sakinah dataji adduar da Ayanah ke yi a bayyane zubewa tayi qasa kan gwiwoyinta tana fidda hawaye masu tsananin Sosa zuciya itama tana sunkuyar da kanta qasa tana Jin radadin rashin Abaas din itama yana dawo mata sabo tareda wargajewan ahalin GHAZ din da basuda burin daya wuce ganin wannan rana ta ganin jinin da Ayanah zata haifa dan Bayan Abaas Nurat ce me tsananin son ganin jinin Ayanah na farko sbd tace itace zata zama uwarsa duniya da lahira Ashe itama bazata gani ba tabar duniyar gabaki daya a cikin Hali mafi muni da har su mutu bazasu dena tinawa ba.,

Irin kukan da Ayanah ke yi tana sake qanqame ‘danta da yanda ke buga kanta a qasa itama tana yi da sauti me kashe jiki da tsima zuciya ya saka tenya jikinta mutuwa tsoronta da fargabanta na komawa tausayi da fatar rage radadin dayake zukatansu da babu komai a cikin rayuwarsu tin farko da kunci da damuwan da bata taba ganin ta gushe daga idanuwa da zukatansu ba.

Tsawon lokaci suka dauka suna kukan qunci da ciwon rayuwarsu daya dawo musu sabo kafin sakinah ta rarrafo ahankali batareda ta dago ba kanta a qasa ta miqa hannuwanta biyu ta Dora a kafafun tenya dake tsaye a kansu ta rintse idonta dake jajir hawaye masu dumi suka gangaro mata tareda sauka Akan babban yatsar kafar tenya din ta bude Baki cikin mafi karyewan sauti tace

‘Kinji sirrin da muka dauki lokaci muna karewa da rayuwarmu Wanda kuma muke da niyar cigaba da karewa har karshen rayuwar tamu dan kawai mu tsira mu rayu ko baa tare ba,

Har abada Ayanah bazata taba rayuwar farin ciki ba duk duniyar da zata samu kuwa sbd ta rasa duka abinda yake bawa rayuwa farin ciki ta hanyoyi mafi ciwo da kasa fincikewa….’

Dago kanta tayi da idanunwata da sukai jajir ta kalli tenya tace,

Ni baiwa ce matsayina be kaiba Banda yanci da ikon rokon kowace irin alfarma ce koda ta numfashin da zan shaqa ne kuwa amma ina rokonki alfarmar da zata hana LEUL tashi maraya babu uwa dan kuwa bayyanar gaskiar alaqar dake tsakanin Zuhrah da wishmah zai iya yin iyakacin ranta dan kuwa ko baa rabata da ranta ba ita ta tsira aka kashe Zuhrah to tabbas zaa iya rasata itama har abada dan haka dan nake bada rayuwata ki rufa mana wannan asirin alfarmar wannan jaririn dayake hannunta ki badan a matsayin wadda take yar uwa ga Zuhrah ni a dauki rayuwata na sadaukar da ita dan bada kariya ga duka su biyun.,

Wani kallan sabon zallan mamaki da shiga matsanancin tsoron dake tada gashin jikinta tenya ke kallan sakinah sbd alamu dai sun sunma tabbatarda ita kanta sakinah duka sunada alaqa kenan Wanda Masifafen hadarin hakan yafi rikitar da tinaninta dan kuwa tana isar da wannan sakon babu Wanda zai kara ko awa daya a duniya cikinsu,

Babban tashin hankalin dake sake jijjigata zufanta na sake jiqata tsoronta na bayyana shine itama hukuncin bazai wuce kanta ba sbd tsawon fiyeda shekara tana tareda su suna qarqashin kulawa da saka idonta amma ace ta kasa gane akwai alaqa a tsakaninsu Wanda hakan shine ya gama tabbatar da hukunci daya akansu da ita dan hakan take Jin hankalinta na tsananta tashi,

Fadar laifin hukuncin barin duniya,boye laifin tareda su kuma duk ranar daya fita kaf zuriarta ne zasu amsa hukuncin kisar tareda su masu laifin dan hak taji kafafunta na silalewa qasa tana zame wa qasa Zaune,

Dago idanuwanta da sukai ja tayi itama ta zubawa Ayanah ido wadda kwata kwata bata cikin firgici ko tashin hankali na bayyanar zancen alamar kowane lokaci bata tsoron fuskantar mutuwa kamanma duniyar ta isheta mutuwar kawai take nema ta dauketa ta huta sbd qunci ne a dabaibaye a rayuwarta duk Wanda ya kalleta zai iya ganin hakan,
Dawo da idanunwata tayi Akan sakinah ta bude Baki muryanta na rawa tace

‘Kunsan me hakan ke nufi kuma kuka aikata?
Kina maganar a sauya ki a maimakon wishmah shin Kinsan ba iya ke kadaice zaki rasa ranki ba hadda Zuhrah din a tare zaku rasa ranku gabaki daya dan a tare kuka aikata laifin da………

Bata qarasa ba Ayanah ta ajiye babyn hannunta ya sauko gadon babu kuzari a jikinta ko kadan koina na jikinta rawa yakeyi ta zube gaban tenya taba dago idanunwata da suka saka gaban tenya faduwa ta bude Baki cikin ficewa hayyaci tafara rokonta kada ta Bari Zuhrah dinta ta rasu tana mata Wani irin roko hayyacinta baa jikinta ba wata rawan daya saka tenya sake shiga tashin hankali jikinta keyi.

Yanda Ayanah ke yi kaman hankalinta ya gushe jikinta gabaki daya yana rawa tana yiwa tenya Wani irin rokon ta cetan mata zuhrah ya saka tenya riqeta da hannuwanta biyu tana kokarin mata magana Ayanah din ta fasa wani irin kuka mai qarfi da taba zuciyan daya saka sakinah ma fara kukan mai sanyi tana dagowa ta kalli tenya batareda tsoro ko shakkar abinda zai iya biyowa baya ba ta fara bata asalin labarin komai na abinda ya faru a rayuwarsu tin kafin watsewan ANJOM GHAZ dan kuwa a daidai wannan gaban data tabbatarda qarshen rayuwarsu Yazo gwara asan waye su da kaddarorin da suka fuskanta sbd Bayan barinsu duniya Ayanaah bazata taba dawowa hayyacinta ba da zata iya tina ko waye ita bare tina labarinta.
#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee

42
*_MAMAN YUSUF LIKITAR MATA_*
07069711327
GYARA SHINE MACE
*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327

*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻

-Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata
-Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi,
-Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji,
-Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki,
-Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ba,
-Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki,
-Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso,

KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻

Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi

Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi

Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu

Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra

Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa

Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a
Akwai hadin farinjini na matar aure
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka

*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers
07069711327
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata.

************
Tenya da idanuwanta sukai jajir hannuwanta na rawa ahankali dago jajayen Idon tayi ta saukesu Akan fuskar Ayanah dake rintse da ido kanta cikin kafafunta tana Wani irin kuka mai tada tsikar jiki sbd rasuwan Nurat data dawo mata sabuwa da rashin Abaas harma da rabuwa da Zuhrah da irin rayuwar da sukai ta qangin bauta a hannun wainda bazata taba mantawa ba kusrawa.

Ita kanta sakinah data bada labarin kuka takeyi sosai komai ya dawo musu ‘danye da harma suke Jin sun yadda mutuwar suke so su huta kawai,

Tenya duk yanda taso riqe kanta saida zuciyarta ta kasa tayiwa Nurat kukan daya sakata Miqewa tana juya musu baya tana yinsa sosai sbd yanda komai da akai mata ya ringa ratsa kunnuwansu tin farko har gamawa da yanda Abaas ya koma macen da duk wannan tsawon lokacin bai taba bude Baki ba ya bayyanarda azaba ko baqin cikinsa ba yan uwansa su kaji muryansa ba har suka rabu rabuwarda shikenan har abada.

Tsit dakin yayi dukkaninsu sunyi kukan da har karfinsu ya qare musamman Ayanah da daman karfinta ya tafi gurin naquda da haihu.

Sakinah ma karfinta ya qare babu me kuzari a cikinsu hukuncin tenya kawai sakinah ke jira Banda Ayanah da kamar ma bata hayyacinta dan kuwa zuru tayi bata iya ko dagowa da babynta a jikinta da kila rabuwa zatai dashi take ji kaman yanda ta rabu da kowa nata.

Tenya Ayanah ta zubawa ido zuciyarta gabaki daya ta karye akanta,
Acan baya tana tsaye a kanta da duk lamarinta ne sbd cikar burinta na wargaza duk abinda HAILE zata so a rayuwa amma ayanzu Jin tsananin kauna da tausayi tareda sonta takeyi yana ratsa jini da zuciyarta a tsaftace babu sirki babu wani Buri,

Shi NUAB tinda ya fado duniya a hannunta ya fado take kaunarsa mara sirkin komai ta shigeta da zata iya komai akansa amma ayanzu dataji waye mahaifiyarsa sabuwar kaunarsu ce mai karfi da zata iya bada ranta akansu ta shigeta dan haka take daukanwa kanta alaqawarin tsayawa a kansu da lafiya da rayuwarta har inda tata rayuwar zata qare,

Cuta da hadari kowane iri ne indai zata gansa ko jisa zata basu kariya kota halin yaya dan haka a yanzu da gaske qiyyyar HAILE take ji a jininta da batajin zata iya barin kowace burinta Akan Ayanah ya cika dan shi LEUL jinin BOYEM ne kuma magajin kujeran BOYEM duk Wanda yayi gangancin tabasa tamkar miqa rayuwarka ne kayi ga zakunan da zasu ci namanka da ranka a gangan,tinda Yazo a jinin sultan YASAR ai yagama samun kariya duk duniyar da zaa bawa kowane irin me rai dayake BOYEM bazai iya cutatar dashi ba dan haka mahaifiyarsa ce a hadari da buqatan me tsaya mata a kowane irin yanayin da zata samu kanta.

Cikin yanayin daya saka su dukansu biyun dagowa suka kalleta ta kafe idanuwanta Akan Ayanah da sauti me cire tsoron hadarin da zasu iya shiga su dukan tace

‘Kinada alfarmar fiddo Zuhrah daga kurkuku amma bakida damar ‘yanta ta sbd hakan zai iya zamowa hadari fiddota da yantata,
Kinada matsayin wishmah dazai Baki cikakkiyar daman da zaa cika miki Buri uku na rayuwarki,
A ranar da zaayi bikin sunan NUAB a ranar zaa yi taron Baki cikakken matsayinki na wishmah a kuma ranar ne zaa Baki damar fadar Buri uku da kike dasu Wanda Kina fadar su Sai an cika miki su,

Bazan fada miki abinda zaki fada ba sbd bansan burin da kike dashi ba a rai amma dai zan fada miki Abu daya idan har kinason zuhrah ta rayu rayuwa me kyau wadda ko bakwa tare zata samu rayuwar nutsuwa da kwanciyan hankali Wanda hakan shine burinki to kada ko fiddata daga kurkuku kuma ki yantata a lokaci daya dan kuwa kika yin hakan Zaki iya rasata gabaki daya dan sedai ki tashi Washe gari ki ga gawarta kwance a gabanki,

Na miki alkawarin Zuhrah zata samu rayuwa me kyau da gata tareda kwanciyan hankali amma idan zaku iya sadaukar rabuwa da rayuwa batareda juna ba har abada…..

Wasu hawaye ne masu dumin gaske suka gangaro daga idanuwan Ayanah tana kasa dauke kallanta daga tenya cikeda Wani irin yanayin dayake sassara rayuwarta zuwa matakin qarshe na qunci da radadin zuciyar datake mutuwa daga Sauran walwalan rayuwa.

Itama sakinah rintse idanuwanta tayi ahankali jikinta na sakewa wani dumi na zagaye jikinta da sarawar Kai.

Tenya tasan ba abune me sauki ba ko kadan hakan kuma qunci ne sabo da zai dasu a zuciyar Ayanah na har abada amma hakan shi kadai ne mafita dan kuwa matiqar zasu yadda ita tayi alkawarin da dubararta zata kawo sauyi da aminci a rayuwar Zuhrah duk da har abada su biyun zasu rasa rayuwarsu kenan ta walwala ko farin ciki dan kuwa zasu tabbata ne a quncin rashin juna suna ji suna gani.

Girgiza Kai Ayanah ta fara yi ahankali da karfi tana fizga kafin sakinah ta riqeta jikinta da karfi tana rungumeta tana Gyada Kai tana hawaye tana cewa

‘Indai Zuhrah zata fito zatayi rayuwa me aminci zaki iya Ayanah,Zaki iya Ayanah….’

‘Bazan iya ba,bazan iyaba shine abinda take fada da karfi tana qwacewa amma dole sakinah ta saka karfi ta riqeta harta gaji dan kanta tayi Laushi.’

Ganin tayi Laushi ya saka sakinah da tenya da kanta suka kamata zuwa toilet inda hadaddun ruwan Zafin wanka ke jiranta suna fidda hayaqi da dan qamshin wani maganin al’ada na wankan haihuwa.

Su biyun ne sukai mata gashin wanka me nutsuwa dukansu jikinsu a sanyaye kaman yanda ita kuma ta koma tamkar batada sauran hankali ko kuzari a jikinta.

Sun dauki lokaci sosai kafin suka fito sakinah ce ta tsaya tayata shiryawa tamkar yanda aka Saba gashinta ta goge mata ta busar dashi ta Kamasa sako sako sbd karya dameta ta dauko mata Kaya tana miqa mata tana sakawa kamar wadda bata gani.

Abinci da lafiyayyar dafaffiyar madarar datasha hadin Kayan qamshin da zafi sosai aka kawo mata tenya da sakinah ne suka tirsasata taci aka kwantar da ita take bacci me nauyi ya dauketa sbd akwai maganin bacci a cikin madarar.

NUAB ma sabon wanka da shiri tenya tayi masa da kanta sbd bata yadda da kowaba Akan Ayanaah da shi yanzu,

Wuni Ayanah tayi tana bacci sai yamma lis ya farka aka sake hada mata ruwan Zafin da aka kuma gasata da kyau ta shirya ta zauna a daki ita kadai sakinah ta saka mata NUAB a hannunta San shayar dashi,

A lokacin data masa shayarwar farko Jin tayi wani abu ya ratsata Wanda ya sakata kafesa da idanunwata da suka qanqance sbd kukan baqin cikin rayuwarta da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login