Showing 39001 words to 42000 words out of 121560 words
kashe dayansu abar daya sbd kawar da zargi hakama duk ranar da dayansu ya kalli daya shima hukuncin daya ne.
Miqa musu Id cards nasu akai tareda jansu zuwa ciki Wanda kowannensu babu abinda yake aiki a gangar jikinsu Bayan kafafunsu dake jansu kaman marasa lakka a jiki.
Hawaye ne masu tsananin zafi suka gangarowa Ayanah tanajin kusan komai nata na Dena aiki tanason dagowa tayiwa Zuhrah kallan karshe amma damar ta qare hakama itama Zuhrah Ayanah takeson kallan ba damar ta qare sedai hawaye suka sauko mata ta rufe idanuwanta tana bin inda ake tafiya dasu hanya daban da wadda aka tura Ayanah da sakina.
Duk Taku daya da Ayanah ke yi jin takeyi tana rabuwa da ruhinta sbd a yanzu kam takai matakin karshe na rasa komai nata batada Sauran hasken da idanuwanta zasu gani ko miskala zarratan,
Rawa kafafunta keyi zuciyarta na kasa wa sbd bazata iya rabuwa da Zuhrah ba koda hakan zai rabata da rayuwanta ta yadda dan haka ta dakata ahankali daga tafiyan datake,
Dagowa tayi ahankali zata juya ta kalli Zuhrah koda hakan zaiyi sanadin rayuwanta,
Da sauri sakinah dake bayanta ta riqeta cikin nutsuwan da bazata bari a gane su ba ta hanata Juyawa sbd bazata iya barinta Juyawa ta rasa rayuwanta kokari da sadaukarwar Zuhrah ya tashi a banza,
Wasu hawayen ne masu tsananin zafi suka cigaba da gangarowa Zuhrah wadda itama bata juyoba tana Jin ciwo da radadin halinda Ayanaah take a jikinta,
Sakinah ce ta iya waiwayowa a hankali ta zubawa Bayan Zuhrah dake tafiya jikinta na bayyanarda gap take da samun bugawan zuciya,
Tausayinta ne ya rufe zuciyar sakinar sbd ita zata rayu bateda duk Wanda rayuwarta ta taba sani ba dan gwara Ayanaah din ita tana tareda ita,
Koma menene tasan wannan ma wata sabuwar jarabawar ce Allah zaici gaba da jarabtarsu da ita,
Ahankali ahankali aka gama rabasu zuwa bangarori da dama Wanda sai da aka kuma daukansu cikin wasu motocin aka isa dasu can ciki inda duniyar boyem take,
Tsari da yanayin gini da aljannar duniyar dake cikin Masarautar boyem ya wuce tinanin duk wani labarin daular duniya da ake bada labari da tarihin Masarautu,
Tamkar suna tafiya baa cikin duniyar ba haka suke jin kansu sbd koina da ake giftawa dasu madubai ne suke ganin kansu a ciki suna daukan idanuwansu dan haka tsoro duka ya cika su suka sake saukar da kawunansu a qasa suna kama jikinsu dake rawa sbd tsoro suna tattaro nutsuwarsu sbd itace gaba a komai na aikinsu.
Kai tsaye sabon bangaren bayin dake cikin masarautar aka kaisu aka basu daki shima kamar wancan da suka Baro daular bayi sedai wannan Mutum uku uku ne a daki.
Duniyar da aka jefata daban data Zuhrah sbd tsakanin bangare da bangare akwai yar tazara da kuma tsaro sosai dan haka ita kai tsaye ita bangaren imebētiś aka kaita Wanda yake duniya ce guda mai zaman kanta wadda take dauke da part part sun kai hamsin duka na imebētiś ne maana mistresses na sarki,
Duk macen da sarki ya kwana da ita indai ta samu ciki anan zaa bata flat dinta mai shegen kyau da wata irin daula a cikinsa tareda bayi sama da goma wainda sun zama nata zatai rainon cikinta anan ta haihu anan ta reni jini boyem cikin jin dadi da daular da hankali ma bazai daukaba kuma anan zataci gaba da rayuwanta da bayinta cikin jin dadi da yanci har sai jinin BOYEM data haifa ya girma ya kai shekaru goma sha biyar shikenan zaa ware masa nasa muhallin daya zarce tinani acan cikin asalin ginin da sultan yake a zuba masa bayin ya koma can sedai Yazo gaida mahaifiyarsa kokuma ita taje gurinsa.
Duk macen da sarki ya kwana da ita kuma bata samu ciki ba bangarensu daban bautar suke komawa sedai Ana sauya musu guri a cire su cikin asalin bayi,
To Ayanah a cikin bayin dake kulawa da sabuwar imebētin sultan aka kaita itada sakina ita kuma Zuhrah a can asalin bangaren uwargidan sultan aka kaita dan haka sukaiwa juna Nisan da babu ranar cike gurbin.
Tinda suka iso dakinsu Neman somewa Ayanaah keyi sbd halinda tashiga na rabuwa da Zuhrah daqyar sakina ke kokarin bata taimakon daya hanata somewan sedai har tsakar dare tana fama da ita kafin Allah ya kawo mata dangana ta sakawa kanta karfin halin hakura.
Washe gari tinda asubar fari suka shirya cikin uniform dinsu tsaf suka fito zuwa aikinsu,
Kai tsaye bangaren sabuwar imebetin suka isa su shida ne dan haka suna isa suka bude suka shiga kai tsaye kowannensu ya fara hidimarta tin kafin ma ta tashi.
Ayanah aikin gyara toilet tayi tareda wanke Kayan wankin da ime din tayi amfani dasu ta wanke su sosai da hannuwanta batareda ta saka washing machine ba duk da an koya musu komai da yanda zasuyi amfani da koman a gurin karatunsu,
Tana gamawa sake gyara toilet tayi ta hada mata ruwan wanka masu dumi sosai da Kayan qamshi masu dadi na wanka Wanda duka shima an koya musu dan kusan babu abinda baa koyar musu ba komai kankantarsa,
Tana gamawa ta koma bakin toilet din ta tsaya kanta a qasa tana jiran farkawanta,
Tsayuwan mintina talatin tayi kafin ta fito daga cikin makeken lafiyayyan gadonta mai rumfar dataji ado da dukiya.
Tana qarasowa ko amsa gaisuwan da Ayanah din tai mata bataiba ta zare rigar baccinta ta Sama ta Bari a gurin tareda shigewa toilet din daya gama tsaruwa,
Sunkuyawa qasa Ayanaah tayi a natse ta dauke rigar data zare din tana barin gurin ta kai rigar inda Kayan wanki suke ta dawo ta isa inda towels suke sama da guda ashirin ta dauko guda uku harda na goge kai suna wani qamshi me sanyi ta dawo bakin kofar ta tsaya da towels din.
Tsayi me tsanani tayi a gurin batareda ta motsa ba duk kuwa azabar datake ji ta tsayin hakan take a tsaye kanta a qasa har tsawon lokacin da batasan Yaushe ne ba tukuna ime din ta bude kofar toilet din Wanda Ayanaah tayi saurin miqa mata towel din farko ta amsa ta daura a jikinta kafin ta sake bata wani t rufo jikinta kafin na ukun ta Dora akai dan goge kanta.
Tana wucewa gaban mirror Ayanah ta fada toilet din ta sake gyaresa tsaf ta qamar da ruwan toilet din tsaf duk kaman ba yanzu aka fito wanka cikinsa ba.
Tana gamawa ta fito tana gyara dakin da gadon dakin sakina da wata baiwar daya suka shigo suna busar mata da gashinta tareda gyarasa tana zaune tana kallan kanta a madubi.
Tsawon lokaci suka dauka suna hidimarta kafin suk kammala ta fito cin abincin da Sauran su suka dafa mata sama da Kala daya ta zauna suka zagayeta kowannesu da abinda yake mata.
Har dare suna tsaye kan kafafunsu basu zauna ba Bayan sallah babu abinda sukeyi sai hidimarta wadda bata qarewa.
Sai tsakar dare sosai suka koma daki Bayan tayi bacci,
A tsananin gajiye suke dan haka komai babu Wanda suka iya yi bacci suka buge dashi mai karfin gaske,
Asubar fari aka buga qararrawa tashi yake suka fito sukai ayyukan bangarensu na bayi har lokacin sallahn asuba yayi sukai sallah sukai wanka tareda shirya wa suka fice ayyukansu na iyayen gidansu.
Kaman yanda sukai jiya yauma haka suka wuni suna aikin wahala da bauta babu sukuni abincin da sukeci ma a tsaye suke cinsa ba yancin zama.
****farkon wannan wahalar da suka samu kansu a cikinta na bautar da babu Hutu ko kadan dan Baka isa kayi bacci ba sai Wanda kake bauta wa yayi nisa sosai a nasa baccin,
Farko farko kafin su Saba sosai suke jin jiki amma ahankali ahankali suka saba da wahalar wadda ta zama jiki har basa jin komai,
Kaman computers haka suke da aiki ba mantawa ba kuskure a natse,
Watanni hudu kenan yanzu a zamansu cikakkun bayin boyem da suka Riga suka saba da tsantsan na masarautar da dokokinta ba kuskure ko daya,
Idan aka hada da watannin da sukai a daular bayi kusan wata bakwai kenan a BOYEM Wanda yayi daidai da shekara guda harda wata daya rabon su iyayensu,
Tsawon watannin nan babu ranar da Ayanaah bata baqin ciki da quncin rashin Zuhrah,
A kowane motsi da numfashinta babu abinda ya rage na rayuwar baqin ciki da quncin datai tareda rashin yan uwanta a tareda da ita,
Sakinah ce kadai zata iya shedar da qunci ne zallansa a daddabe da zuciyar Ayanah amma a bayyane ta rungumi kaddarar datake cikinta.
Ime dinsu da suke bautawa kwatsam Allah ya azurtata da samun cikin daya saka aka yayeta daga zuwa shimfidar sarki sai kuma idan ta haihu idan tanada rabon ya sake kwanciya da ita kenan.
Yayeta da akai ya saka dukkanin bayi shiga fargaba da tsoron sabbin imebētin da zaa zabar wa sarki Wanda a yanzu baya qasar kafin dawowansa zaa kuma zabar sabbin imebētin da zai huta dasu dakyau idan ya dawo.
#MAMUH
#ROYALTY
#AYANAH GHAZ
#NUAB BOYEM
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: _*HAYATEEM*_
Mamuhgee
24
Duk damuwa da fargaba da duka kyawawan bayin dake BOYEM ke dan shiga da tsoron sabbin imebētin da zaa zaba Ayanah bata taba ma San da hakan ba sbd bama huriminsu ne na shiga ba dan kuwa tasan a cikin sama da mata bayi sama da dubu dake bauta a masarautar bama sa cikin wainda zaa iya gani bare sani tinda suna bangaren imebētis din sarki suna bauta basa can bangaren matansa biyu da bayansu bai taba qarawa ba.
Dan haka bautarta kawai takeyi babu tinani kowane iri a zuciya da rayuwarta Bayan na ‘yar uwarta datake azabtuwa da rashinta a kowane daqiqa,
Tinda ta rabu da Zuhrah bata taba jin sassauci na rashinta ba ko kadan a zuciyarta Wanda bama ita kadaiba kowace daqiqa tana wuce mata ne da tsananin ciwo da quncin rashin Nurat da Abaas da Zuhrah din,
Suna tsananin so da kaunar iyayensu amma yanda suke tsananin son junansu da irin gwagwarmayan da suka shiga ya saka suke jin mummunan ciwon rashin junansu fiyeda Zafin rashin iyayensu,
A nata zuciyarma gabaki dayansu a cikin jininta yake jinsu tamkar itace ta haifesu din da gaske sbd uwar data zama garesu musamman Nurat datake ambatarta da AMMAH kafin rasuwarta,
Ciwon rashin ‘yan uwanta da sune rayuwanta bazai taba barin zuciya da ruhinta ba har abada,da wannan ciwon zata mutu idan ma ba ciwon rashinsu bane zai zama ajalinta sbd a yanda takeji babu wahala ko azabar da bazata iya dauka ba amma ciwon rashinsu abu ne da zuciya da gangar jikinta bazai taba dauka ba musamman irin rasuwar da Nurat tayi.
Rayuwanta a Masarautar BOYEM bata taba sakewa ko sabawa da kowa ba Bayan sakinah wadda take tsananin kulawa da ita idan suna daki sbd tsoron bugawan zuciyarta datake riqe da abubuwa da dama ta kasa saki ta kuma kasa fada Bare nunawa,
Cin zuciyarta damuwa da quncin sukeyi Wanda suke bawa zuciyarta illa ahankali batareda saninta ba dan haka sakinah batada damuwa itama a nata rayuwar yanzu Bayan ta Ayanah din,
Itama sakinah ko a mafarki ma bata taba saka kanta a lissafin da wasu bayin keyi na shakka ko tsoro sbd ko zasuyi shekaru dari a BOYEM babu ranar ma da ko bawa irin su zai iya cewa yana shaawansu bare me qasar da kansa duk da bai taba zaben macen dazai kwanta da ita ba da kansa duka wannan aikin shugabar jakadan qasar BOYEM ce gabaki dayanta wadda take Zaune cikin masarautar itama da nata bayin sbd babu me matsayi dake Masarautar BOYEM fa baya cikin nasa jin dadin da daula me girma tareda tarin dukiya.
Meleketen’ya wadda ake kira da Ten’ya wato jakadiya da yarensu itama matsayi ne da ake gadonsa sbd tin kakanni da shekarun da suka gabata jini daya ne suma suke riqe wannan matsayin dan haka shima matsayi ne me girma da iko dan kuwa duka bayin dake cikin asalin masarautar BOYEM a karkashin iko da umarninta suke yawo da aiki,
Hakama tenya din itace me kulawa da dukkanin abinda ya shafi sirri da babbar buqatun matan sultan da ‘yayansa wainda suke jininsa,
SULTAN YASAR ALMAZ BOYEM shine Sarkin Boyem da ikonsa yake zagaye da kusan fiyeda Rabin daulolin dake duniyarsu,
SULTAN YASAR sarki ne da mulkinsa yakeda tsananin zafi da karfi tareda tsananin doka da ikon daya saka ko dabbar masarautar shakkar laifi takeyi sbd hukuncin dayane fa Mutum ga dabba wato cire kai kawai dan haka a cikin tarihi yana cikin sarakuna masu Zafin gaske da akai a BOYEM,
Sultan YASAR yana daya daga cikin sarakunan jinin BOYEM da su keda abubuwa da dama da suka Zarrah na kowa a tarihi dan hakanne shima yayi Wani irin sunan da sunan BOYEM yake sake gauraye duniya,
Sultan YASAR yana tarin dukiyar data qara Habbaka dukiyar Masarauta duk da asalin BOYEM sunada da wasu irin arziki wadda basa talauci Allah ya gama bude musu kofofin arzikinsa tin asalinsu babu talaka ko daya hakama su kansu basa sanin tarin arzikinsu sbd yawansa da yaduwarsa,
Sultan YASAR yana daya daga cikin sarakunan BOYEM da sukai karatun ilimin boko sosai da Larabci sbd asalinsu balarabiya ce Matar farko ta BOYEM dan haka suke tamkar ruwa biyu amma sunfi maida hankali akan karatu da samun ilimi da yarensu na Amharic da arziv dan haka qalilan ne a cikinsu suke karatun ilimin boko da larabci sosai dan haka sultan YASAR yana daya daga cikin masu bokon hakama yana cikin masu zafi,
Bayan duka wainnan sultan YASAR ya sakance cikin wainda Allah bai azurta da samun namiji ko daya ba a tarihin wainda suka mulki kujeran BOYEM,
‘Yayansa duka mata ne suma kusan duka imebētinsa ne suke haifar masa su,
Matansa biyu rak suma aure ne da kaman Alkawari da ake wa kowane Sarkin daya hau mulkin dan kuwa su biyun jinin BOYEM ne suma auren gida ne duk da bama qasa daya suke Zaune ba sai da akai auren aka kawo masa su a rana daya a lokaci daya,
Uwargidan itace HAILE wadda duniya take fadar kyauta da kaf BOYEM ba kamarta,
Jinin BOYEM ne yake yawo a jikinta itama,
A qasar Morocco take rayuwa itada iyayenta a cikin wata irin daula da ikon da mulkin da suke zubawa kafin auren daya kafa tarihi ya dawo da ita cikin BOYEM qasar da kowa ke kwadayi da maitar son zuwa yayi rayuwa a ciki dan haka ita a duniyar babu me saa irin tata samun kanta a matsayin Matar sultan YASAR ALMAZ BOYEM kuma uwargida dan hakanne duniya ke kiranta da HAILE(me power) kenan hakama kaf duniya Bayan bayinta babu Wanda yake da saa ko matsayi ko ikon ganin asalin fuskanta da ake cewa tafi kowace mace kyau sai shi sultan din da kansa Wanda take tsananin so fiyeda komai na duniya da ita kanta,
Kishinsa take kaman zata kashe kanta sbd son da take masa yayi yawan daya fita hankali dan hakanne ta ringa haihuwa bata jira sbd son ta haifar masa namiji amma Allah bai bata ba tana Ji tana gani aka ringa wanke masa imebēti masu kyau da daukan hankali Ana kai masa yana kwana dasu,
Da farko duk imebētin daya kwana da ita bada umarnin a kawar dasu takeyi sbd zuciyarta bata iya dauka Wanda hakan ya saka bayi da yawa shiga mummunan Hali daga lokacinda aka Zabesu zuwa shimfidar sultan sun San kwanansu ya qare ne a duniya,
Abinda ya kawo sauki da sassaucin kishinta akan hakan shine fara samun ciki da sukai suna haihuwan yaya mata kuma babban me mata duba ya sanar da ita itace zata haifawa sultan YASAR ALMAZ BOYEM namiji.
Wannan bayanin ya saka ta sassautowa ta kyalesu ta duqufa rokon Allah samun ‘da namiji koma yaya yake ko wane iri ne tanaso hakama tana hada wa da aikin bokayen malamanta masu tsananin karfin gaske.
‘yayanta uku mata wainda sune manyan yayan sultan YASAR wato ASLAM,NEESAT da MERYAM,
Sun girma sun zama yan matan da sukafi kowace mace daraja a qasar BOYEM sbd sune arzikin sultan da BOYEM a yanzu tinda sune jinin sultan YASAR ALMAZ na farko a duniya,
MARAKI itace Matar sultan YASAR ALMAZ BOYEM ta biyu wadda itama kyauta kusan daya dana HAILE sedai anfi zuzuta na HAILE cin sbd itace uwargida kuma wadda kaman sultan din yafi Ji da ita duk da bawai ya fada ko nunawa bane kawai macen da sarki yafi kwanciya da itace wadda yafi so kenan a cikin matansa ko imebētis dinsa dan hakan na nufin samun cikakkiyar gamsuwa yake da ita,
MARAKI batai shekarun HAILE ba duk ba wani shekaru ta bata ba hakama ita MARAKI bata taba samun haihuwa ba kwata kwata Shiyasa batada wani power kaman HAILE amma itama kam duniya ce gida take Juyawa a bangarenta wanda yake dauke da bayin hidima sama da ashirin sbd girmansa da daular datake ciki,
A cikin matan sultan da duk wata mace wadda take jinin BOYEM babu wani adon dayake jikinta Wanda ba asalin zinari bane yake motsi a jikinta,
Sarkan wuyansu,
‘yan kunnen dake kunnuwansu Wanda a qalla zaa samu huji sama da uku a kowanne kunnen,
da zoben hujin dogayen hancinsu na gadon asalin BOYEM,
Zobunan hannuwansu da chains na hannu da bangles,
Chains na kafafunsu da zobunan yatsar kafarsu da sarkar adon dogayen gashin kansu gabaki dayansu na zinari ne kawai suke amfani dashi sbd basusan kowane irin abin ado ba Bayan na zinari Wanda kaf idan ba a jini da masarautar BOYEM ba babu irin wannan dukiyar,hatta abinda suke rufe fuskan su me kyau adonsa akwai zinari a cikinsa dan hakanne ake zuba asalin mulki da sarauta a BOYEM.
A cikin imebētin da suka haifawa sultan YASAR yaya basu fi goma ba dan kusan su kansu imebētin Wanda tenya taji bai mata ba a gurin haifawa sultan yaya tsarin hanasu daukan ciki takeyi,
Rashin samun ‘da namiji a masarautar yanzu shine babban qalubale da tashin hankalin da ake ciki Wanda shi kansa sultan rashin samun LEUL BOYEM ne kadai abinda ya taba taba zuciyarsa dake tsaye babu sanyi ko kadan a cikinta,
LEUL BOYEM shine kowane sultan daya mulki BOYEM baya da nutsuwa sai ya Haifa sbd shine ze qarasa kafa tarihin mulkinka,
Rashin haihuwan LEUL BOYEM na nufin sarautar BOYEM Bayan kai zata koma wani dakin Wanda kai Baka cike tarihinka ba kenan,
Babu qasar da bata tsoron yaqi ko tinkarar masarautar BOYEM,
Babu sarki ko sultan din da baya shakkar sultan YASAR BOYEM,
Babu bawa ko wani Mutum da baisan ransa baa bakin komai yake ba a masarautar BOYEM idan