Showing 111001 words to 114000 words out of 121560 words

Chapter 38 - HAYATEEM Hausa Novels By Mamuhgee.txt

10 Dec 2025

3822

zai masa shi da Bahar wadda batasan kowaba a dangin uwa da ubanta ba.

Tasowa yayi ya iso gaban Bahar din zai furta sunanta ta ja da baya cikin wani irin mutuwar jiki da mafi girman tashin hankalin rayuwarta tana girgiza Kai ta sake furta sunan Abaa dinta idanuwanta na yin wani irin ja hawaye masu tsananin zafi na taruwa a cikinsu sbd kadaici ze kasheta idan Abaa yabarta shine kadai ran dayake cikin empty rayuwarta da babu kowa a ciki sai zallan sunayen da babusu maana yan uwan mahaifin nata da iya sunansu ne basu ba a rayuwarta.

NUAB da idanuwansa suke rintse tin lokacinda aka shafa fatihar auren dago kansa yayi ahankali yana bude idanuwansa da sukai jajir ya saukesu Akan fararen kafafun dasuke gabansa masu haske sosai na daukan hankali sarkar Farin azurfan dayake kafar duk motsinta daya na ja da Bayan datake Wani sauti me yar qarar dake shiga kunnuwansa yake fitarwa Wanda ya sakasa dauke jajayen idanuwansa zuciyarsa na Wani irin Zafin lokacin daya bata na cetan Abaas a gurin daurin auren da bai dauru ba a zuciya da rayuwarsa dan kuwa aure ne kadai na biyan buqatar wannan lokacin da suke so na tafiya da Abaas dan haka miqewa yayi batareda ya juyo ya kallo kowaba ya nufi kofa a takunsa na natsuwa da jinin mulkin daya dame sarautar GHAZ ya fice batareda ya cewa kowa komaiba.

Yana ficewa Aleey ya miqe shima yabi bayansa Bayan ya dan kalli Maa sakinah dake Bayan BAHAR da Sarkin fada yace suna jiransu a waje.

NUAB na fito bike din dake nan Sauran daya daya raye shi ya hau Kai tsaye ya wuce aka bar GHAZ din dashi.

Su aleey sai Sauran bikes din sun dawo da sukaji kai Abaas dan haka Aleey fidda wayar sa yayi yafara zagaya masarautar yana daukan videos din dayasan buqatan hakan zata iya tasowa daga baya dan haka ya bawa Maa sakinah da Sarkin fada guri da zasuyi magana da Bahar wadda babu abinda take son ji da gani kawai idan ba mahaifinta ba dan mantawa ma kwakwalwanta tayi da abinda taji na maganar auren da kunnuwanta sukaji an daura da sunanta kawai mahaifinta takeso da ganin idan ba tafiya yayi ya barta ba dan haka ta rikice musu gabaki daya Wani irin rawa jikinta keyi tana ambatar sunansa da karfin gasken daya saka a rikice aka fiddota aka tafi da ita zuwa garesa Bayan Sauran bikes din sun dawo.

Sbd yanda Bahar din ta fice hayyacinta tana kasa yadda da kowa harma da Maa sakinah ya saka dole da Sarkin fada aka tafi dan rakiya garesu.

Koda suka nufo wajen gari idanuwanta tsananta jajir sukeyi cikin wani irin nauyin kirji na zuciya take jinta duniyar na sake mata duhun da tasan itama kila a cikinsa zata rayu ta mutu kaman yanda mahaifinta ya rayu ya tsufa a cikinsa.

Koda suka iso an bawa Abaas taimakon gaggawan dayake buqata amma suna buqatan gaggawar isa dashi asibiti Wanda Dr ya bada shawarar bazai iya kaiwa qasar BOYEM a hakan ba dole suna buqatan fita can cikin babban birnin wannan qasar da suke ciki su fara tsayawa anan dashi asibiti saiya samu dan saukin da zai iya qarasawa dashi qasar BOYEM indai anason ya rayu.

NUAB baida raayin tsayawa kowace qasa dashi Bayan BOYEM amma kuma ga yanayin jikin nasa dayake gani dole maganar Dr din zasu bi ta tsayawa asibitin qasar kafin daga baya su wuce idan ya dan zama stable sbd mummunan nisa yayi Wanda yake girgiza zuciyar NUAB din yanajin kaman bazai taba iya fuskantar Amminsa ba idan Abaas yabar duniya sbd baisan tayaya har abada zai iya fada mata Abaas dinta ya tafi yabartaba dan hakan shine blow na karshe da rayuwarta zata iya samu dan haka zaiyi iya kokarinsa yaga ya isar mata BOYEM dashi koda ganin karshe ne su yiwa juna.

Kai tsaye barin ruwan dajin ANJOM GHAZ sukai Wanda kila shikenan sun barsa a rayuwarsu,
Sakinah tsirawa dajin ido tayi bata kyaftawa zuciyarta na narkewa fiyeda a baya ANJOM shine garin da har su mutu bazasu Dena marmarin dawowa su qarasa rayuwa a cikinsa ba.

Bahar ma dake Zaune gaban mahaifinta hannunta ta saka ahankali cikin nasa ta Kama tareda hade tafin hannuwansu tana Lumshe idanuwanta da sukai jajir wasu hawaye masu dumin cikinsu suka gangaro mata Sarkin fada ma kusa da ita su kadai a dakin dayake Sarkin fada na fada mata ‘dan Ayanar mahaifinta ne Yazo ga mahaifin nata dan basa lafiya.

Babu kowane irin farin ciki ko Jin dadi ko daya daya sauka ga zuciyarta na abinda Sarkin fadan ya fada sbd babu Sauran kowace kauna ko soyayyar datake Jin zuciyarta nada damar yiwa kowa sbd bata tashi da kowa ba a rayuwarta daga ita sai mahaifinta tayi rayuwa,
Rayuwa da zuciyarta a kulle take ga rayuwa da kowa a cikinta sbd kadaici da quncin data taso a cikinsa na rayuwa babu uwar data haifeta wadda ta rasu a ranar data kawota duniya hakama tasowa ta rayu a cikin duhun gidan da babu kowa a cikinsa sai ita da mahaifinta Wanda shima tinda ta bude ido duniya take kallansa cikin qunci da tarin baqin cikin daya hanasa lafiya har yau da rayuwarsa take cikin tsakiyar rayuwa ko mutuwa dan haka zuciyarta da rayuwarta a mace suke ta yanda basuda komai ciki da zata iya farin ciki dan haka rufe idanuwanta tayi ahankali wasu Zafafan hawayen na sake gangaro mata tana fadar idan lokacin mahaifinta ne yayi Allah ya dauki ransu a tare subar duniyar a tare.

Tafiya me tsayi sukai kafin suka isa bakin bodar qasar babu bata lokaci aka fito dashi zuwa ambulance da already ankira tana jiransu dan haka take ambulance din ta daukesa tareda Bahar din a cikinta da Sarkin fada su kuma Sauran motocin suka shiga a guje akai asibiti dashi.

Suna isa aka karbesa da gaggawa akai ciki dashi suka bisu jikin kowa a mace musamman BAHAR wadda zuwa lokacin ko kuka bata iyayi sbd babu alamar sauki ko kadan a lamarin nasa.

A inda ake jira suka zazzauna Banda NUAB da aleey wainda aka kaisu guri kebantacce dan jiran dan hakan har lokacin babu Wanda yayi noticing juna a tsakaninsu.

Maa sakinah ce Zaune a gefen Bahar din wadda kanta yake qasa ta dunqule hannayenta guri daya idanuwanta jajir.

Hannu Maa sakinah ta Dora a hankali kan na Bahar din tareda kallanta cikeda kulawa da kauna me karfin gaske tareda tausayi itama idanuwanta jajir batareda tace komaiba,
Itama Bahar din bata dagoba sedai rintse idanuwanta datai hannuwanta na tsananta rawa Maa Sakinta ta riqe su cikin nata gam alaman bata sassauci.
#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee

65
Zaman da kowace daqiqa take tafiya da tsananin bugun zuciyarsu da zullumi tareda tsoro me tsanani da fargaba sukai na kusan wuni guri kafin aka samu numfashinsa ya dan dawo daidai da oxygen hakama jini aka daura masa Wanda yake na NUAB dinne da kansa aka diba Bayan ya hana Yaransa bada nasu nashin yakeson a sakawa Abaas sbd a shirye yake ga bada jininsa gabak daya idan zaa buqata hakan dan Abaas ya rayu sbd kila Amminsa zata iya juriya da karfin zuciyar rashin sa amma bazata iya daurewa rashin Abaas ba.

Idanuwan Bahar sunyi munin da suka sauya kamanninta koina nata yayi jajir sbd kuka da damuwan datake gap da buga zuciyarta da babu kowa a ciki sai BAA din,

Sakinah dik da tana cikin mummunan tashin hankalin itama amma ta daure ta fidda karfin halinta a matsayi na uwa dake gurin ta bawa BAHAR dukkanin kulawa da kaunar datake buqata a daidai wannan lokacin Wanda hakan ne ya dan rage zarewan da yarinyar ke kokarin yi a Zaune gurin.

Shi kansa NUAB babu Wanda ya gansa a cikinsu dan hakane ma basusan jininsa ne aka sakawa Abaas dinba,
Aleey kadai suka gani shima abinci lafiyayye kusan Kala biyar ya saka aka kawo musu Wanda babu Wanda suka saka a Bakinsu
Duk yanda Maa sakinah tayi Bahar taci Sam ko sakewa babu a tsakaninsu da zata iya ma cusa kanta dole taci ba dan haka bata ci komaiba fatarta mahaifinta ya tashi ya samu lafiyar da zasu koma inda suka fito suci gaba da rayuwarsu su qarasata a tare su biyu kadai.

Dare na yi haka aka daukesu aka kaisu masaukin da yanda Bahar taga rana haka taga Daren batareda ta rintsa ba a Zaune take har asuba idanuwanta sunyi mummunan kumburan da kanta ke tsananin ciwon da ko gani sosai batayi amma Sam ba sassaucin datake ji a zuciyarta.

Karfe 8 na safe Aleey ya aiko mota aka maidasu asibiti inda ta tarar da mahaifinta yanda ta barsa tamkar babu rai a jikinsa yayi fayau yayi Wani irin haske ya qarasa bushewa sosai babu Sauran kowace albarkar jiki a tattare dashi.

A sanyaye babu kuzari ko kadan a jikinta ta zame gefensa ta zauna idanuwanta na cikowa da hawayen da basu gangaroba ta saka hannunta cikin nasa ta sake hadewa ta qanqamesa cikin wani irin sanyi dayake tabbatarda kaunar datake masa a shirye take da mutuwa tareda shi.

Haka ta wuni a dakin batareda kowa Yazo ba aka bata damarta sbd jikin nasa a yanda suke gani ba Sauran hope dan haka aka barta ta kasance dashi a lokutan da suka rage.

Kwana biyu da zuwansu asibitin bai farfado ba se a ranar na ukun tsakiyar dare kusan karfe biyu da mintina ya farfado dan haka cikin gaggawa asibitin suka kira waya suka sanar da NUAB Wanda a cikin Daren ya sako babbar jacket din fendi Akan Kayan jikinsa ya fito da hular sanyi Akan gashinsa suka nufo asibitin.

Suna isowa Kai tsaye dakin suka isa wanda doctors biyu ne da nurses hudu a dakin yana shigowa dukkaninsu suka jiyo suka kallesa cikeda tausayawa.

Takowa yakeyi a hankali zuciyarsa na tsinkewa a Karan farko dayake Jin tsananin tsoro na saka kafafunsa rawa da nauyin daya sakasa kafe Abaas din da idanuwansa da sukai ja yana Jin wata irin kauna me karfin gaske da tsananin so da fatar ya tashi daga ciwon sbd ya basa rayuwa me kyau da nutsuwa da kwanciyan hankali da kaunar da batada sirki.

Abaas dayake kwancen kamanninsa sun gama sauyawa daga dukkanin lafiyar da babu ko daya a jiki da jininsa bude idanuwansa Yayi ahankali cikin yanayin daya saka kafafun NUAB sake sarewa yaji kirjinsa yayi nauyin daya sakasa qarasowa da kyar,

Akan NUAB Abaas ya kafe idanuwansa masu tsananin Laushi yana Jin dukkanin baqin cikinsa da damuwarsa na yayewa a lokutan sa na karshen rayuwa dan haka Lumshe idanuwansa yayi tareda motsawa a tsananin sanyi ya bude tafin hannunsa na dama da NUAB din yake tsaye,

Zaunawa NUAB yayi a natse tareda Dora hannunsa ahankali Akan nasa din tareda kamawa ya riqe cikin nasa cikeda kulawa da kauna mara sirki.

Numfashi mara karfi Abaas ya sauke cikin rashin karfi ko kadan ya saka hannunsa daya ya zare oxygen dinsa Wanda NUAB yayi saurin riqe hannunsa shi da aleey a lokaci daya amma Abaas din ya girgiza musu Kai tareda bude baki cikin karfin Hali yace

‘Inason Ayanah tasan labarina a bakina kafin barina duniya idan Allah yasa na tashi zan fada mata da bakina idan ban tashi ba Ka gabatar mata da rayuwar da Abaas dinta yayi sbd kada tarihinmu ya zama ba qarasashe ba a tarihin duniya.’

Aleey baya yaja ahankali tareda fidda iPad dinsa da babu inda yake taba zuwa bada ita ba koman emergency kuwa,

Recording na video ya saka tareda tahowa ya ajiyeta a setin gadon Abaas din Wanda hannunsa yake cikin na NUAB yana jinsa har ransa sbd Jin yakeyi kaman hannun Ayanarsa ce a cikin hannunsa hade dan haka baida Sauran regret na rayuwa.

Juyawa aleey yayi waje inda securities suke yace suje su dauko BAHAR sbd ganawa da mahaifinta.

Yana dawowa wayar sa ya fice da ita dan fara hada tafiyar da zasuyi da asubar komai tsanani suna buqatan dagawa da Abaas din tinda ya farfado sbd likitocin su na gaggawa da suka hada suna can suna jiran isowansu.

Kafin Abaas ya fara cewa komai sake qanqame hannun NUAB yayi da dan karfin daya rage masa mara kuzari ko kadan dan ya bude baki ahankali ya furta ‘AYANAH BAHAR’

dago jajayen idanuwa NUAB yayi ya kalli Abaas din Wanda tin daga qasan zuciyarsa sunan ‘yar tasa ya fito harya manta da ita sbd aleey ne yake tsaye Akan kulawa dasu.

Ajiyan zuciya me sanyi Abaas din ya sauke kafin ya Lumshe idanuwansa a hankali sbd rayuwar komai ta farko data fara dawo masa radadi da baqin cikin na budewa yana famawa Wanda gashinan dashi zai mutu yabar duniya.

Asalin tarihinsu da rayuwar da sukai a qarqashin kulawa da kaunar iyayensu ya fara jerowa ahankali cikin nutsuwa da Wani irin ratsa zuciya da yanda kusrawa suka tarwatsa rayuwarsu suka sauya tarihinsu da kaddararsu zuwa mara dadi da kyau,

Yanda rayuwarsu ta sauya ne daga ranar da suka bar garinsu zuwa tafiya qangin bauta yafara zayyana wa Dayan bayan daya daki daki batareda ya boye ko kalma daya zuciyarsa na Kina da radadi me tsananin ciwo da baqin ciki,

Yana zuwa daidai inda aka lalata rayuwar Nurat wadda akai komai a cikin kunnuwansu qanqame hannun NUAB yayi cikin wani irin mafi zazzafan baqin cikin da har yanzu sautin kukanta bai fita kunnuwansa da zuciyarsa ba shiru ya dan yi jikinsa na rawa idanuwansa na rufewa cikin azaba…

Rawa jikin NUAB yakeyi sosai yana wata irin jijjiga a hankali ya qanqame hannun Abaas din da karfin daya saka Abaas bude idanuwansa yana sauke su Akan NUAB din Wanda yake hango Wani irin radadi da baqin ciki me tsananin karfi a cikin idanuwansa,

Rintse ido shima ya sake yi yana cigaba da bada labarin mutuwarta da abinda yaci gaba da biyowa Bayan nan har zuwa inda aka rabasa da yan uwansa,

Cigaba yayi da cewa,

‘Bayan an rabasa da yan uwansa anan kasuwar kwana yayi a daure a Wani ice tamkar dabba haka ya kuma wuni a rana babu ruwa babu Inuwa har saida karfinsa ya qare ya dunqule guri daya yana fita hayyacinsa sbd azabar rana da kishirwan dayake fatar ta dauki ransa dan kuwa bazai iya rayuwa babu su Ayanah a tareda shi ba dan haka duk duka da azabar da aka ringa gana masa Qin cin komai ko ruwan da aka basa yayi sbd yunwa yake sonta kashe sa ya huta.

Ganin taurin kansa ya saka sukuma suka siyarwa wasu marasa imani shi da niyar zasu je dashi su huta a tinaninsu mace ce gashi yaqi cewa komai dan Alkawari ne bazaiyi magana ba da yayiwa Ayanah harsai rayuwarsa ta kubuta dan haka bazai taba karya wannan Alkwarin ba.

Akan kudi ba masu yawa ba aka siyar dashi take wainda suka siyesa suka tafi dashi zuwa gurin hutawarsu,

Koda suka tafi dashi mummunan abinda suka fara aikata masa shine dukansa suka ringa yi har saida ya Dena motsi yayi mummunan illatar da baida Sauran amfani a duniya tukuna suka yaga Kayan jikinsa gabaki daya Akan zasu masa fyade sai suka tarar dashi namiji ne dan haka baqin cikinsu ya tsananta take suka qarasa kashesa da dukan tsiya suka tattara shi suka Kai bakin ruwan suka yar suka
Tafiyarsu.

A wannan Daren gap da asuba wasu suka tsincesa suma maimakon su taimaka masa sai suka duba suka ga yanada Sauran rai dan haka suka wankesa tas suka sake saka masa Kayan mata sbd ganinsa da yan kunne a kunne harma da abin hanci,

Gari na fara wayewa kafin rana ta fito suka kallaba suka siyarwa Wani matafiyi shi a matsayin baiwa mace sbd anfison bayi mata a Kasuwan yanzu Shiyasa suka fi tsada.

Matafiyin raya siya bawan asalin balaraben shemali ne Wanda yayiwa ‘yarsa kwalli daya alkawarin siya mata baiwa mace da zata zama tamkar kawarta sbd debe mata kewan rashin uwa da kawayen datake fama dashi dan haka har zai tafi ya samu baiwar duk da taji jiki tana cikin wani mummunan Hali sosai amma hakanan bai damu ba ya siye sbd jirgin ruwa zaibi zuwa komawa qasar sa bazai jira gari ya waye a fara cin kasuwan bayi ba.

Hakanan ya karbi Abaas ya wuce dashi Bayan ya biya kudin jirginsa na ruwa ya biya kudin kayansa da bawansa Wanda zaa saka guri daya da Kayan sbd haka akeyi bayi da kaya guri daya ake sakasa kaman wasu dabbobi dan haka babu komawa jirginsu yabar qasar.

Tafiyar wuni da kwana daya sukai suka isa qasar wadda take cikeda nata kalar arzikin,

Boukar shine sunansa hakama shi din mai arziki ne sosai a gurin yan uwansa dama garin nasu Wanda yake na qasar larabawan shemali ne,

‘Yarsa tak daya a duniya wadda mahaifiyarta bata jima da rasuwa ba tabarta da kadai cin daya saka ya siyo mata baiwa sbd ta fita daga kewan datake cikinta,

Baya tareda yan uwansa sosai sbd akwai Hassada da qyashi sosai a tsakaninsu dashi,
Duniyarsa ta tsone musu ido sosai,
Tsananin hanyar da zasu rabasa da dukiyar suke nema dan haka basa rabarsa ko kadan sbd rayuwarsa suke dako dan hakanne ma yake tsananin kiyayewa Akan yarsa da ita kadai garesa bai hadata da komai,

AYSHAHH ne sunan yar tasa wadda take balarabiya gabanta da bayanta sbd uwa da ubanta duka yan asalin shemali dinne dan haka da kyau da gata da nutsuwa ta taso tareda gatan da kusan a garin babu Wanda ya keda irinsa.
#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee

66
Koda boukar ya kawowa yarsa ayshahh baiwa tayi farin ciki sosai sbd tana tsananin buqatar Abokiyar debe kewa dan haka tayi kaunaci kyautar baiwar musamman ganin kusan kansu daya kila ma ba Wani sosai baiwar ta girmeta ba dan haka taimaka mata sukai sosai da magani da ruwa da Sauran abubuwan da abinci ta samu a cikin kwana biyu ta dawo daidai hayyacinta ya dawo Wanda a hakan bata tana magana ba dan haka ran boukar ya baci ganin Ashe Murna aka siyar masa dan haka yayi alkawarin sake siyo mata wata idan yayi tafiyar kasuwancinsa.

Sosai Abaas yayi jinya tukuna ya dawo tsaye a kafafunsa ya fara aikin bautar da aka siyosa yayi batareda har lokacin ya fara magana ba,

Bauta yakeyi a gidan da rayuwar masu gidan dan kuwa kaf hidima da wahalar aikin gidan shine yakeyi Bayan hutawa babu abinda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login