Showing 339001 words to 342000 words out of 411050 words

Chapter 114 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt

10 Sep 2025

8081

raka ta ?

'Yar Dariya Amnee tayi kafin tace " da wai ni cewa nayi ko Zainab ma tunda ita take kusa anan sai ta kawo yaran idan Mijinta ya yarda sai su tafi tare tunda ga Hajja da daman tare suke , idan ta haihu mu sai mu je .
Cike da Amincewa Prof yace
"wannan shawara ce mai kyau bari zan ƙira shi Maigidan Zainab sai na nemi iznin sa da kaina , Allah ya kai mu .

" Amin Amin , Amnee ta amsa cike da jin daɗi

Bayan fitowar su daga sashin Prof a harabar gidan suka ci karo da Yakaka sai kai-kawo take a mamakance Khaalty Rahima tace " ke kuma me kike yi anan ?

Da sauri ta matso tana riƙo hannun Amnee ta ɗan rangwaɗa kai sannan tace " Amnee Dan Allah zan raka Falmata Niger ɗin ? Bana son ta tafi ita kaɗai nasan duk takura zata yi a tsakanin su tunda basu wani saba ba .

Kallon kin cika sakarci Khaalty Rahima ta mata kafin tace " Da iznin wa za ki tafi ? Kin san dai da Auren ki idan kuma gaban kan ki za kiyi to ,
Mayar da ganin ta tayi kan Amnee ta cigaba da cewa
" Ukhtee mai sunan ki dai sai kina yi kina taro ta sam bata da wayo .

Daga haka ta shige ciki ta bar su a tsaye , Amnee ta dubi Yakaka fuskar ta cike da murmushi tace ," takwara kema ai Amarya ce duk yaushe aka yi bikin ki ,? Ki bari idan ta haihu sai mu tafi tare .

" Amnee kawai raka ta zan yi fa Wallahi tausayin ta nake ji ace ta sake tafiya ita ɗaya , sai Hajja .

" Zainab ma zata raka ta .

Ta katse ta .

Zata sake yin wata maganar Amnee tace " ki tambayi iznin Mijin ki idan ya bar ki sai ku tafi tare .

"Ɗan tsallen Murna Yakaka tayi ta ƙanƙame hannun Amnee da yake cikin nata tana cewa "Nagode , nagode Amnee naa .

A hankali Amnee ta zare hannun ta ta wuce ciki tana dariyar rashin wayon Yakaka , ita yanzu idan an bar ta sai ta sake kwasar ƙafa ta bi Falmata ita bata tunanin gina nata gidan auren da har yanzu bata da takamaimai matsugunni a cikin sa ? Ita kenan kome na rayuwar ta zai biyo bayan uzurin Falmata ne .

Jinjina kai tayi cikin ran ta ta kasa ƙiyasto iya adadin girman ƙaunar da Yakaka take yiwa Falmata , can sashi guda na ranta dariya take dan tasan ko kusa Hamza ba zai Amince da tafiyar Yakaka Niger ba bare kuma Prof .

Bayan wucewar Amnee Yakaka tsumu tayi a tsaye , ita sai yanzu da aka ce ta ƙira Doctor Hamza ne ma ta tuna ko number sa bata da ita a wayar ta , gaskiya tana son raka Falmata Niger ɗin nan saboda ko a hanya wannan ƙatuwar matar zata nemi ɓata mata rai ta tare mata .

Zama tayi akan dan dandamalin da aka yi shukar furanni ta cikin sa tana tunanin ina zata samu layin Doctor hamza , ita dai ba zata iya tambayar Amnee ba kunya take ji , ba kuma ta son ta tambayi Rahima ko da a waya ne tasan sai ta sille ta ta mata tsiya .

Wayar Mamar su ta faɗo mata a rai tasan babu tantama akwai number sa a kai , to ko zata ɗauka ta ƙira shi kawai ma ta wayar ta ta ƙila yafi ɗagawa da wuri fiye da idan ta layin ta ta ƙira da bai san layin ba .

Da sauri ta miƙe ta shiga ciki , ta hau sama ɗakin Khaalty Rahima da sa'ar ta babu kowa a ɗakin , daga gefen gado ta hango wayar , da sauri ta ɗauka ta shiga neman sunan sa cikin jerin sunayen dake kan wayar bata sha wahala ba ta samu sunan tare da number sa .

Shiru tayi ta gagara danna ƙiran , tana son tattaro kalmomin da zata yi amfani da su wajen yi masa magana ,

Idon ta ta kai kan agogon wayar ta ga sha biyu saura tasan dai duk tsiya yanzu ya tashi a bacci duk kuwa da cewa yau lahadi ce ba aiki .

Fargaba bai rabu da ita ba ta danna ƙiran layin bayan ta kai wayar kunne ta runtse ido gam tana jin wani yanayi mai ƙarfi na shigar ta , daga can ƙasan ran ta addu'ar samun nutsuwa ta fara yi .

Wural ta buɗe idanun ta lokacin da ta ji sautin muryar computer na bata tabbacin babu kuɗin da zai isa ƙira a wayar .

Dariya tayi da ƙaramin sauti , kafin tace " kai Maman mu sai a bar ta ko meyasa take barin waya ba kuɗi ? Ita kamar ma bata wani damu da wayar ba .

Numbers ɗin ta kwafa a wayar ta , sai da ta zauna a bakin gado sannan ta danna ƙiran .

ABUJA

Daga can Sofiya ce a ɗakin Doctor Hamza tana gyara gadon da basu wani jima da tashi a kai ba Doctor Hamza ya shiga wanka .

Tana gyara bargon su lokacin da wayar sa dake gefen gado ta ɗau kiɗa alamun shigowar ƙira .

Ba tare da ta dau wayar ba ta leƙa fuskar ta ga lambobi ne reras ba suna , ɗan yamutsa fuska tayi ta gatsina guntun hancin ta kafin tace "yau Sunday ma ba za ku bar mutum ya huta ba shi kenan cikin jigila tsakanin asibiti da gida yau kam rana ta ce sai na more lokutana da aka cinye na sauran kwanaki tsawon sati .

Har wayar ta gama ƙara bata ɗaga ba .

Daga can Yakaka tayi jim da waya a hannun ta , cike da tsoron kar ta dame shi ta daure ta sake danna ƙiran a karo na biyu ,

Wannan karon har Sofiya zata fice a ɗakin sai ta dawo baya , ta ɗau wayar kai tsaye ta ɗaga ƙiran tana kara wayar a kunne tace " Hello who's on the line ?

" Mukut
Yakaka ta haɗiye yawun firgici , jim tayi kafin tace " amm ni ce Yakaka ina kwana ? bata tsaya ba ta zarce da cigaba da cewa "ki kaiwa Yaya doctor wayar .

Ba domin Sofiya tana shakkar kar Doctor Hamza da tasan kunnen sa yana iya jiyo ta ba da ba abunda zai hana ta ɗuɗɗurawa Yakaka zagi .

Baki ɗaya fuskarta tayi jaa a take tana huci tayi ƙasa da murya kafin tace " To akuya sarkin naci ana ƙorar ki kina daɗa naniƙewa , shugabar 'yan rashin zuciya Miji bai damu da ke ba sai ke ce ke neman sa jarababba , to ƙwalelen ki ke da Doctor sai gani sai hange daga nesa-nesa dan kuwa zaman ki kenan a inda kike 'yar .....

Ƙit !

Ta ji Yakaka ta katse ƙiran ,

Daɓas ta zauna a bakin gadon baki ɗaya ranta ya cunkushe har wani raɗaɗi take ji a hancin ta kamar ta shaƙi barkono ," wannan jarababbiyar yarinyar watau har ƙiran Mijinta take yi ?

" Sofi waye ya ƙira ni naji kamar kin ɗaga wayar ?

Da sauri ta waiga kafin ta miƙe tsaye ta ƙarasa zuwa gaban shi inda yake tsaye yana goge kansa da towel ,

Tana zuwa ta karɓi towel ɗin ta shiga goge masa jiki , bata yarda sun haɗa ido ba fuskar ta babu walwala tace , " Akuya ce ta ƙira ka ? 🙄

"Akuya fa ?

Ya tambaye ta yana duban ta da mamaki ,

Cike da bagararwa ta kai hannun ta ƙirjin sa tana ɗan tsikarin sa tace " eh dan kukan akuya nake ta ji tunda na ɗaga wayar ina Hello , Hello , Hello . Ba'a cewa kome sai Kukan Akuya .

Jawota yayi ya haɗe tsakanin su , yana kallon cikin tsakar idon ta yace " Sofi baki fa da kirki a wasu lokutan nasan daga Office ne aka ƙirani , Ni yanzu muje ki bani abinci na ci yunwa nake Ji ina son na fita akwai wani waje muhimmi da nake son zuwa yau .

Kicin-kicin tayi da fuska jin cewar zai fita yasa ta sake jin tasowar ɓacin rai da ya ɗan fara lafa mata sanadin haɗuwar fatar jikin su .

Bai kula ɓacin ran ta ba yayi shirin sa cikin wani yadi mai ɗan nawi ruwan zuma ya fesa turare tare da ɗaura agogon sa sai lokacin ya juyo ya dube ta da take zaune a bakin gado ta kumbura suntum .

Fushinta bai wani taɓa masa rai ba yace " mu je ki bani abincin ba daɗewa zan yi ba zan dawo nima so nake na huta yau ɗaya .

Bayan ya ɗan cac-cakali Omelet da kidney Sauce ya ɗan kurɓi ruwan tea ya miƙe a gurguje ya mata sallama yana barin gidan .

Da fitar sa ta yi jaɓar ' akan kujera tunanin ƙiran wayar sa da Yakaka tayi ya bata tsoro , ita da ta saki baki ta zauna malumman ta sun ce mata an yiwa Yakaka da Hamza farraƙu to tayaya Yakaka ta iya samun damar ƙiran sa ? Kada dai ace asirin nan bai ci ta ba ?

Wani irin huci take yi lokaci guda ta tashi da gudu ta hau sama ɗakin ta ta shige laluben wayar ta , ya zama dole ta sabunta aikin ta .😂

***

Doctor Hamza kuwa yana fitowa hankali kwance ya dai-daita motar sa akan titi unguwar su Malama Maryam ya tasamma da bata kasance ɓaƙuwar unguwa a wajen sa ba , ya sha kai sofiya gidan ƙawar ta Samira .

Tsawon sati biyu da yayi yana bin duk wasu Matakai daki-daki domin tabbatar da zancen da Suleiman ya sanar da shi game da Yakaka gaskiya ne ko ba gaskiya ba ? Duk da cewa yana da tabbacin Suleiman ɗin ba zai masa ƙarya ba amma yana da buƙatar samun ƙwararan hujjoji ko dan ya wanke zargin ta daga ransa da hakan shine kaɗai zai ba shi damar samun nutsuwa tare da ita da zai iya rungumar ta hannu bibbiyu , tun usul ƙaunar ta bata tunbuƙe ba daga ransa girgiɗi kawai tayi da a yanzu kuma ta dawo ta tsaya chak da ƙafafun ta ta kuma shiga kaiwa duk wasu gaɓɓan jikin sa mamaya .

ASSALAMU ALAIƘUM MASU KARATU .

Da fatan duku kuna lafiya ? Sakamakon saƙonnin da nayi ta amsa daga masoya masu karatu kan taƙaice ƙarshen MHR da wasu ke ƙorafi wasu kuma suka nemi Alfarmar na ɗan sake jaan zaren labarin nayi dalla-dalla ko da kuwa ban yi filla-filla ba , hakan yasa na karɓi ƙorafi na kuma ɗan jaa kaɗan ba mai yawa ba da nan gaba kaɗan mu kan iya rufe bangon littafin mu adana shi Insha Allah

A ƙarshe ina godiya sosai da sosai ga dukkanin makaranta MHR na fili da na ɓoye daɗa nasan na ɓoyen sun ninka na filin yawa "ghosts readers barkar mu dai ina gaisuwa fa 😜❤nasan kuna tare da ni domin ina ganin inuwar ku , ko da kuwa baku bani tukuici ba .

Nagode.Mafari
( Hargitsin Rayuwa )






Umm'muaz






50







Lokacin da Doctor Hamza ya isa unguwar su Malama Maryam dai-dai layi da gidan da Doctor Suleiman ya kwatanta masa sai ya ga ashe ma ya taɓa sanin gidan duk kuwa da cewa da dare ya taɓa zuwa amma bai manta da yarinyar da ya taɓa taimakawa ba a wani dare ana ruwan sama babu shakka a ƙofar wannan gidan ya sauƙe ta .

Kasancewar ana haramar sallar Azahar a lokacin dan haka a masallacin da yake kusa da gidan nan yayi Sallah .

Bayan ya idar sai ya matsa ya miƙawa Liman hannu suka yi musabaha , nuni ya yi masa kafin ya ɗora masa bayanin gidan da ya zo , to amma kasancewar an sanar da shi matar tana da aure ya zama dole sai da iznin Mijinta zai gana da ita , tunda ba sanin juna suka taɓa yi ba dan haka yake son sanin Mijin ta da farko , a zahiri wata buƙata ce ta son samun wasu bayanai daga bakin Matar da ake ƙira Malama Maryam yasa shi tasowa musamman domin ganawa da ita .

Dan jim liman yayi yana sake nazarin Doctor Hamza , kafin yace " bawan Allah lafiya dai ko ? Ba dai wani al'amari bane marar daɗi ya auku da har yasa kake neman Malama Maryam ?

Da sauri Doctor Hamza ya girgiza kai kafin yace ' ah ah ba wani abu bane marar kyau , kawai tambayoyi nake so nayi mata akan wata ɗalibar ta da ta koyar wacce aka ce daga baya ta zama kamar 'yar ta saboda kusanci da ta samu da ita , sunan yarinyar Amina .

Shiru Liman ya sake yi kafin yace 'Kana nufin Amina Mustapha Dilmari yarinya 'yar Maiduguri ?

" ita fa Malam .

"Allah sarki yarinyar kirki ce ai Amina , ta koma can garin su a halin yanzu har an aurar da ita sati biyu da suka wuce , Malama Maryam da kake nema ai Mata ta ce , kuma ita ce Malamar Amina tsawon shekaru Shida da suka yi tare , bari na shiga gida sai nayi mata bayani na haɗa ku , amma kafin nan zan so jin ko kai wane ne ? Kuma daga ina kake ?

Cike da jin daɗin ganin sauƙaƙuwar lamura Doctor Hamza yace " Malam ai ni ne Mijin Amina bayan haka kuma ni wan ta ne da muke 'ya'yan mata biyu .

" Masha Allah ka ce babban baƙo ne da mu , to Bismillah mana mu shiga daga cikin Falona kafin na yi mata magana .

Ganawar Doctor Hamza tare da Malama Maryam ya zo masa da wani irin sauyi mai girma da yake sauraren bayanan da take yi  masa game da baki ɗayan rayuwar da Yakaka tayi tare da ita har ma da wanda tayi gidan uwarɗakin ta samy baby da a farko su kayi zaton yayar ta ce , kafin daga baya lokacin da ta faɗa musu haƙiƙanin gaskiyar kome game da ita ,su gane cewa basu da wata alaƙa ta 'yan uwantaka .

" alaƙar ta da Samy Baby da duk irin Yaudarar da tayi mata . har yadda daga baya Samy baby take son tilasta ta shiga harkar banza amma ta ƙi yarda da hakan shine ya kawo sanadin komawar ta Maiduguri .

Nisawa Malama Maryam tayi tana murmushi ta cigaba da cewa " Abu mafi daɗi da yasa nake yin Alfahari da Amina shine jajircewar ta wajen neman ilmin addini fiye da na boko , Amina ta fara karatun addini bata kai ga sanin ayoyi bakwai na Suratul-Fatiha ba amma sai ga shi cikin shekaru shidda da Yarjewar Allah ta samu cikakkiyar kyakkyawar Haddar izif talatin .

" bata san yadda ake yin cikakkiyar Alwala ba a shekaru shidda baya a yanzu Amina daga kan farillai , sunnoni da mustahabbai har makruhi na alwala ta sani , haka kuma sharuɗɗan Sallar ta sun inganta ta kuma san yadda zata yi gyara ga Sallar ta idan ta ɓaci.

" Amina ta san baƙi , ta iya karatu da rubutun Arabic ta kuma samu tarin ilmi daga littatafan addini da hadisai masu inganci dan haka ta san dukkanin haƙoƙin Ubangiji dake kan ta .

" Alhamdulillah shine kawai abunda zance da Allah ya rataya min nawin tallafa mata ta hanyar samu ilmin addini , ya kuma bani ikon koyarda ita tare da ni da sauran Malaman da ta ɗau ilmi a wajen su , nagodewa Allah da kafin barin ta wajena ta fita daga duhun jahilci .

"Halaye da ɗabi'un Amina mafi rinjayen su masu kyau ne ababen koyi , tundaga lokacin da tasan irin tarin zunubin da yake cikin kuskuren da tayi na baya bata sake kwatanta aikata makamancin sa ba , tayi kyakkyawan tuba da irin sa ake son duk wani mumuni ya yi .

" babu shakka kayi sa'ar Mata , Allah ya ɗorar da zaman lafiya a tsakanin ku, a ƙarshe shawarata shine kayi ƙoƙarin ganin ta samu cigaban karatun ta na addini kamar yadda ta ke fata a koyaushe watarana ta haddace Alkur'ani Mai girma Dan Allah ka bata dama ka taya ta wajen samun cikar burin ta irin Amina sune Al'umma suke amfana da su .

" Ya Rabb lakal-Hamdu ,  Alhamdulillah , Masha Allah .

Doctor Hamza yake furta haka fuskar sa ɗauke da wani irin annuri na farin-ciki , har wani irin zillo yake ji zuciyar sa na yi masa .

fuskar sa ɗauke da faffaɗan murmushi ya miƙawa Malam Idris ( Mijin Malama Maryam ) Hannu suka yi musabaha , lokacin da yake miƙewa da shirin tafiya , bakin sa ɗauke da duk wasu kalmomin da ake iya amfani da su wajen godiya ga mutumin da ya kai maƙura wajen yi maka Alkhairi .

Da farin-ciki su ma suke amsa masa suna masa rakiya , fitowar su tsakar gida ya zira hannuwansa duk biyu a Aljihu , kuɗaɗen ciki da bai ƙirga su ba su ya tattaro baki ɗaya ya danƙawa Sadiq da yake tsaye a gefe cike da ladabi ya sanya hannu biyu ya amsa yana godiya .

Sun rabu cikin mutunta juna ya jaa motar sa yana barin unguwar , daga cikin zuciyar sa yake jin ɗaguwar wani abu mai kama da nannauyan dutse da ya danne masa zuciya ya taƙaita masa walwalar sa shekara da shekaru ,

ji yake kamar an tsamo sa daga cikin wani zuzzurfan ramin da ya faɗa a ciki , yanayin da yake ji bai taɓa tsintar kansa a ciki ba soyayya mahaɗi ce ta rayuwar kowanne ɗan Adam wanda da zarar an samu tangarɗa ta bangaren ta sai rayuwa ta zama kamar lami babu armashi a cikin ta .

Tuƙin da yake yi yaji yana neman gagarar sa zuciyar sa na neman abokin taya ta murnar da 'yancin da ta samu , dan haka ya gangara gefen titi ya tsaya , jingina kansa yayi da jikin kujerar motar bai ankara ba ya tsinci kansa da yin murmushi lokacin da ya ji wani ruwa-ruwa na taruwa a gurbin idanun sa ( ƙwallar farin-ciki ) shi kaɗai kawai yake ta murmusawa wanda bai san shi ba wanan lokacin zai zaci

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login