Showing 279001 words to 282000 words out of 411050 words

Chapter 94 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt

10 Sep 2025

8086

bisa ga kowa da kome nashi , duk a domin ya rayu tare da ita .,

Sai ga shi domin Ubangiji ya yi masa babbar jarabawa sai ya sanya mutuwa ta raba tsakanin su , a kuma lokacin da kome ya rinchaɓe masa a dalilinta , lalle wannan jarabawa ce maigirma ,

Mayafin da aka rufe mata fuska da shi ya buɗe lokacin da yake ɗaga ta , Maimartaba ya dubi fuskarta da tsantsar tausayi cike a ransa ,

"Ubangiji yasa ki zamto dagga ƴa'ƴan da zasu zam silar samun afouwar Allah ga iyayen su daga tarin zunuba su ,

"Amin Amin Amin,

Hajja ta amsa tana sharar ƙwalla ,

duba guda Maimartaba yayi musu ita da su Yakaka yayi wucewar sa , Tafeeda ya bi bayansa da gawar Mama , Youssouf ma ya sauƙa ya nufi ƙofar ficewa , ya zo ficewa ya waiga garesu da har lokacin suke ƙasa dirshen a zube , muryarsa a ciki yace

"ku tasso mu tai ku wanke ta ,

Shiru suka yi babu wacce ta amsa masa ,

Ganin ya fita yasa Hajja cewa ,

"ku tashi mu tafi Falmata , Yakaka kuyi haƙuri kun ji , haka Allah yake ikonsa uwa ta haifo ɗan da ta fi nisan kwana, kuyi haƙuri kuyi ta addu'a mutuwar Mama hutu ce a gareta , kuyi haƙuri .

Zuciyoyin su a lokacin basa aikin da ya wuce na kuka da jin raɗaɗin mutuwar ƴar da suka shirya sadauƙarwa a domin ta sai gashi mutuwa ta ɗauketa a lokacin da kowaccen su take jin rayuwarta kachokam zata sadauƙar domin ta tsaya tare da ita ,

Suka miƙe ƙafafun su babu ƙarfi suka rufa masa baya , a motar da suka zo a ciki suka koma sai dai wannan karon wani ne ke jaan motar da basu kai ga sanin sa ba ,

Gidan suka tarar da yalwar mutane da suka wuce yadda suka barsu a farko yawa ,

Mutane maza da suke sanye da kaya mai launi guda , da kuma mata a falon nasu , Yakaka da Falmata ratsawa suka yi basu dubi kowa ba suka wuce ɗakin da yake na Falmata , suna shiga su duka biyun kuka suka sake sawa , a tsakanin su an rasa mai rarrashin wani ,

Shigowar Tafeeda ɗauke da gawar Mama shi ya dakatar da ƴan guna-gunin da ya fara tashi bayan wucewar su

Kai tsaye ya miƙata ga Hajja wacce take raƙube daga gefe tunda ta shigo babu wanda ya dubeta bare su amsa gaisuwar ta'aziyyar da take yi musu da basu kai ga sanin wa ya rasu ba , ganin sun yi biris da ita ya sa tayi shiru tana sharar ƙwallar ta ,

"Ki miƙata ga uwayenta sui mata wanka , su shirya ta yanzou za'a kawo likkafani ,

Sai ta ƙarbeta ta ratsa ta tsakanin su ta wuce ɗakin Falmata , zuwa lokacin hankalunsu baki ɗaya ya koma ga Tafeeda ,

Bai jira sun tambayeshi ba , ya ce 

"Diyar Biyamuradi Youssoufa ce da Allah ya amshi ranta a yanzou ,
Daga haka bai ɗora kome ba ya juya ya fita ,

Shiru wajen ya ɗauka , kafin lokacin da Hamshaƙiyar matar da ita ce ƙwal ɗaya a bisa kujera ta motsa , fuskar ta da wani yanayi da kai tsaye ba'a iya fassara shi ba ta soma da cewa ,

"Allahu Akbar innalillahi wa inna ilaihi raji'oon , kaico yarinya wahalar ki ta ƙare kin kuma huttashe da wasu dagga samuwar baƙin-ciki sanadin duban ki , to Allah shi jiƙan ki , ta tabbata dai Youssoufa yana da ɗiya mai shekarun ya wannan da kuma Amre ko ba Amre ?

Bata tsaya ba ta cigaba da cewa , "Mutumin da ya ƙi faɗar gaskiya yana haddasa wahala, wautace babba a ɓatar da lokaci akan aikin banza , mutumin da ya ƙamnaci zunubi ya irin haka , ai ya shiryawa hukunci ne , zunubi da kunyata kuwa tare suke rungumar mai su, shiyasa asharari bashi da wata ƙima  ,

Ta murza zoben hannunta , tana wani ɗan guntun murmushin cikar buri , ta  ɗora

" gaskiya ita dawwamammiya ce ƙarya kuwa ai ƙurarriya ce , ɗan da ya jawo wa Mahaifinsa ɓacin rai ya haka ,? Ai abun baƙin-ciki yake ga Mahaifiyarsa , to wanne farin-ciki za'a yi da samuwar baragurbi cikin 'ya'ya ?

A hankali Adda Ammi ta ɗaga kai ta kai ganin ta gareta bayan gama jawabinta lokacin da ƙaramar jakadiya tace ,

" Babu shakka ko kokonto cikin kalamanki ranki ya daɗe , kowa ya aikata abunda ransa ke so zai ga abunda bai so a lokacin da bai so ba ,

Kallon-kallo aka yi tsakani Ammi da Ubbo da kawo yanzu suka rasa halin da zuciyoyin su ke ciki kan mutuwar ƴar ɗan uwansu da ake duk wani ƙiƙi-ƙaƙa akanta ,

Sai dai kalaman Matar da take mazaunin uwa agare su , Matar Mahaifinsu , da kuma ta wakilci Mahaifiyar su wajen wanzuwarta anan , da kalaman nata ke nuni ƙarara da tazorci gami da kausasawa ga ƙaninsu , ko kusa bai musu daɗi ba , duba da cewa wajen gauraye yake da bayun su ,waɗanda Youssouf shugaba yake a wajen su duk da laifin sa ,

sai dai su basu da ikon tankawa ,"Hajiya Mama uwa take kuma shugaba a gurin su 

Ba'a ɗau lokaci ba Tafeeda ya dawo hannunsa riƙe da likkafani , ya miƙawa Ubbo ba tare da yace kome ba ,

Sai ta karɓa ta nufi ɗakin da ta ga sun shiga ta tarar da su su ukun suna kewaye da gawar Mama da take shimfiɗe a ƙasa ,

Yanayin da ta gansu ya taɓa ranta , bata ce ƙala ba ta miƙawa Hajja likkafanin ,

Ta juya , har ta kai ƙofa ta juyo , "kun iya wankan ? Ta tambayesu

Babu jinkiri Yakaka ta gyaɗa kanta , sai ta juya tayi ficewarta tana ɗauke ganinta daga kan hoton Mama da yake bangon ɗakin Falmata , tsananin kamannin da yake tsakanin Mama da nata ƴa'ƴan ya girgiza ranta .

Yakaka ita ta wanki gawar Mama da take rungume a jikin Falmata , ƙwarar idanun su bata huta ba wajen zubar hawaye ,

Tunawa Yakaka take tun daga ranar da suka ɗora ƙazamtatciyar alaƙa da Youssouf , har zuwa ɗaukar rainon cikin ta da ta samun ta ta haramtatciyar hanya , zuwa da ranar da ta haifeta , da ko fuskarta bata kai ga gani ba , ta tuno da ranar da ta zo irin kallon da tayi mata dake bayyana tsoro da rashin sanayya ,

' tsawon rayuwar da Mama tayi shekaru shida a duniya bazata ɗorar da kome na daga rayuwar yarinyar ba , ƴar da ta ƙi kallonta lokacin farko da ta fito duniya , ta kuma tafi ta barta bata ji tausayin ta tayi tunanin me zata ci ta rayu alhalin abincinta na jikinta ba , ina zata ji ɗumin jikin uwa irin wanda jariri ke buƙata a lokaci na hunturu ?

Babu shakka Samy Baby ta zalunceta da ta cisgeta daga cikin ƴar gajeriyar rayuwar ƴarta , ta yi mata yaudara mafi girma da ciwo , irin ciwon da ba zai rabu da ruhinta ba har ta koma ga Maliccinta ,

" Mama Allah ya jiƙan ki yasa kin samu hutu dawwamamme daga barin rayuwarki mai cike da jinyar gangar jiki , ki yafe min Mama , ki yafe min , addu'o'i ta cigaba da yi mata tana wanke ta .

Bayan sun shiryata suka fito da ita , Hajja ta fita ta ƙira Ubbo , zama tayi a ɗakin sannan ta ƙira Tafeeda ta sanar da shi an shiryata ,  babu jimawa suka shigo su biyu da wani , suka ɗau gawar Mama zuwa waje da za'a sallaceta ,

Falmata kasa riƙe kukan da yazo mata tayi ta fashe da kuka mai ƙarfin gaske , dake bayyana jin ciwon rabuwarta da ƴar da ta ƙwallafawa rai fiye da abunda ke cikin cikinta ,

Ƴar da ta so tare da sadauƙar da kome a domin ta , ƙaunar da ta mata ta fara daga ranar da ta rungumeta a jikinta bayan rashin mahaifiya da tayi , ta ɗau alwashin maye mata gurbin uwa da ta rasa , ta dunga tuno da yadda suka ƙaunaci juna ita da Mama , da bata san tana da wata uwa ba bayanta har ta koma ga mahaliccinta ita ce mahaifiyarta ɗaya tal, tabbas Mama ta bar mata gurbi a zucia sa babu ranar cikata shi .

***

Tamkar wutar daji haka labarin mutuwar ɗiyar Biyamuradi Youssouf/MaJor Youssouf da mutane basu san da wanzuwarta ba ya dunga kewaya ko'ina ɗauke da mummunan tambarin da Youssouf ya ƙi tabbatuwar sa ga rayuwar Mama sai ga shi bayan mutuwar ta labari ya bayyana an kuma ƙira ta da sunan da bai so ba .

Zaman makoki sosai ya kankama tun yammacin ranar da aka bizneta da kuma tun bayan jana'izar da Maimartaba sarkin Maraɗi da kansa yayi limanci , ya bar wajen tun kafin dawowar su daga maƙabarta ,

Ƙarƙashin rakiyar maƙarrabansa da suka zo tare suka koma , waɗanda mafi yawa manyan fada ne , masu faɗa a ji a harkar sarautar masarautarsu da amintattun manyan bayunsa , zaɓaɓɓu da aka aminta da Amanarsu

Da tafiyar tasu musamman ta samo asali ne kan zuwa su ganewa idanunsu inda Youssouf ɗin ya ɓoye yana rayuwar banza kamar yadda aka yi ta jita-jita a kwanaki zancen kuma ya dawo kunnuwansu Amma suka yi binciƙe basu samu shaida ba ko guda a wancen lokacin

Sai fa da yanzu shaida ta bayyana ta hannun Mouhammadou da yace shi ma fa bayani aka ba shi ,

Mafiya yawan masu zuwa ta'aziyyar abokan aikinsa ne da matan su sai kuma tsirarun mutanen gari da yake mutunci da su , daga masarautar su babu mutum guda da ya ƙiraye shi ko kuwa ya zo yi masa ta'aziyya tun bayan juyawar tawagar sarki da kuma ta su Hajiya mama ,

Tsakanin Hajiya Umma ko matansa babu wacce ta ƙira shi , haka ma 'ƴan uwansa idan aka cire Ubbo da Ammi da kawo yau da ake kwanaki biyu da mutuwar Kullum suna zuwa gidan nashi su yini a karɓi gaisuwa da su duk a ƙoƙarin su na son ganin sun rufa asirin ɗan uwansu daga mutanen da basu riga da sun san ta hanyar da ya samar da Mama ba ,

Sai dai a yau su ma sun kudurce cewa sun yi zuwan ƙarshe dan haka suka yanke shawarar yi masa magana ,

Har falon sa suka shiga suka tarar da shi , tare da Tafeeda da tunda aka yi mutuwar yana tare da shi , duk da cewa babu wata doguwar mu'amala ko da kuwa ta maganar baki ce da take shiga tsakanin su ,

A zaune suka tarar da su shiru tamkar kurame , shi Tafeeda yana aikin latse-latsen waya shi kuma Youssouf yayi tsumu irin yanayin da yake ciki tun bayan mutuwar Mama ,

Babu karsashi suka gaisa , bayanan suka yi shiru ,suna nazarinsa da ya sunkui da kansa , baki ɗaya yayi wani irin sanyi har ƴar rama yayi , ba kaɗan ba mutuwar ƴar sa ya taɓa rayuwar sa ,

Cikin taushin Harshe Ammi ta fara masa nasiha kan laifinsa na aikata zina da ta kai shi ga haihuwar Mama , har zuwa yin aure ba tare da sanin iyayensa ba , bayan haka ta tambaye shi tsakanin Yakaka da Falmata waye uwar Mama ?

Nan ya basu amsa da cewa Yakaka ce mahaifiyar ta ,

Ta tambayeshi kuma ta yaya yake auren Falmata alhai ƙanwace ga Yakaka kuma suna tare guri guda ?

   Nan ya basu labari a taƙaice kan yadda aka yi ya auri Falmata da zaton cewa Yakaka ta mutu ne , sai kuma kwanakin da suka dawo daga USA ya ganta a gidan bashi da wani masaniya kan labarin da ya shafe ta .

  Duk shiru suka yi , kafin ubbo tace
" to tunda Allah ya gwada karshen kome da ya zare wannan ɗiya a tsakani domin kawo maslaha a gare ka, sai kayi ƙoƙarin gyara duk wasu kuskuren ka ,

"tunda daman domin riƙon ita ɗiyar kake amren innar ta ai sai yanzou ka sau amren su yi tafiyar su , kai ma ka koma ga iyayenka ka biɗi afouwarsu , su yafe ma sabadda rayuwa tayi maka kyau Youssoufa , ka fuskanci aikin ka cigaban rayuwarka ka ji kou ?

Ba tare da ya ɗago kan sa ba yace

" to naji ,

Kallon rashin gamsuwa da amsar sa suka bi shi da shi , amma basu jaa zancen da tsawo ba suka rabu da shi , saboda sun san muddin ya tafi Maradi sai ya saki auren Falmata ba zai yiwu ya bijirewa iyayensa ba bayan tarin laifin da yayi masu muni .

Basu bi ta kan su Falmata ba bare su yi musu Sallama suka fita a gidan cikin motar Tafeeda , suka bar Youssouf shi ɗaya tal a ƙofar gidan ,

Matsawa gefe yayi ya samu waje ya tsugunna , kewar ɗiyar sa tare da ciwon rashin ta suna taso masa ,

kwanakin da suka biyo bayan mutuwar ta basu zo masa da sauƘi ba sanin da yayi bata raye a duniya yana murƙushe duk wani kuzarinsa ,

baya iya bacci daga ya rufe ido fuskarta ke yi masa gizo muryarta na amsa kuwwa a kunnuwansa ,

baya son doguwar magana da zata katange shi daga yin addu'o'i  , ko abinci sai yunwa ta kai masa maƙura yake iya tsakura ya ci .

Ƙaunar Mama dabance a wajen sa ko cikin abubuwan da yafi so a duniya tana a sahun farko , yasan a cikin 'ya'ya ba zai samu ya ita ba a samun zallar so da ƙauna daga wajen sa tayi zarra , sai ga shi tafiya bata miƙa ba , mutuwa ta shafe tsakanin su , ta ɗauke masa sanyin idaniyar sa .

'yar da silar ta ya haɗu da Fatima zahra har tayi sanadin ƙulluwar aure a tsakanin su ta wanzu tsawon lokaci tana ƙulla kusanci a tsakanin su  , har sai da ta sa bai farga ba ya faɗa tsundum cikin ƙaunar innar ta ,

Tunanin Falmata ya zo masa , a tun ranar mutuwar Mama rabon da ya sanyata a ido ko ya ji muryar ta , ya san tana cikin halin ɗimuwa kwatankwacin wanda yake ciki tana kuma buƙatar lallashinsa , 

Sai dai ba shi da wani sauran dauriyar sake fuskantar wani tashin hankalin da zai iya tasowa daga gareta bayan sanin da tayi cewa shi da Yakaka sun rufeta akan alaƙarsu da haihuwar Mama , bashi da tabbaci kan yadda ta ɗau lamarin , Dan haka ya zaɓi ya bata iska ,

Kafin zuciyar sa ta gama yanke shawara kan hukuncin da yake son zartaswa a gobe .

***

Yakaka da Falmata sun yi kwanaki biyun cike da kewa da jin ciwo na rashin Mama ,

Koyaushe su na ƙule a ɗaki , basa fitowa falo wajen da su Ubbo suke bare su ga juna , Hajja ita ke kai kawon kula da lamuran gidan, ko abinci kai musu take har ɗaki , duk kuwa da cewa basa yi masa wani cin kirki ,

Wani irin zaman shiru suke yi marar armashi da tunda suke su biyu irin shirun mai kama da na tsakanin baƙi juna bai taɓa gifta tsakanin su ba , kowacce tana jinyar ruhinta

Yau bayan sun idar da Sallar Azahar, suna bisa sallayun su , Falmata ta dubi sashin da Yakaka take , ta ƙira sunanta a hankali ,

" Yakaka ,

Yakaka ta ɗago kan ta ,daga karatun da take yi , ta amsa ƙiran da tayi mata tare da tasowa ta dawo kusa da ita ta zauna ta riƙo hannun ta da irin kulawar da ta saba bata tun tasowar su ,

Falmata ta ƙure kallonta ga Fuskar Yakaka da take iya hango haskenta , tace

"Yakaka , ki faɗa min , ki bani labarin tsakanin ku ,
   Tayi shiru kaɗan ,
"ki bani labarin na gaskiya tsakanin ku da Baban Mama , kuma ki bani labarin rayuwar da kika ki bayan haihuwar Mama Alhalin bakya tare da mu ? Ki bani labarin gaskiya Yakaka .

Shiru Yakaka tayi cike da zullumi sai dai ta san abune da tasan da faruwar sa ,tun gabannin ta tambaye ta dan haka ya zama dole ta sanar da ita dukkanin wata gaskiya da ta nemi da ta sani ,
Muryar ta babu kuzari ta fara bata labarin tun daga Rana ta farkon haɗuwar su da Youssouf , har zuwa ranar rabuwar su ta ƙarshe , ta ɗora da cigaba da sanar da ita irin gadar zaren da Samy Baby ta haɗa mata tun kafin zuwan ranar haihuwar Mama da a ƙarshe tayi nasara ƙarƙashin jagorancinta da mummunar huɗubar ta tayi tasirin rabata da rayuwarsu ita da Mama 'yan mintoci kaɗan bayan haihuwar ta ,

dakatawa tayi tana jin tashin hankalin yadda Falmata ta zare hannunwanta dake cikin nata , ta ɗago kai tana kai kallon ta ga fuskar ta ganin yadda hawaye suke zuba daga gurbin idanun Falmata ya ruɗa ta ,


Sai dai bata da wani zaɓi illa cigaba da sanar da ita gaskiyar kome kamar yadda ta alƙawarta , bata tsahirta ba ssi da ta gama tas da bata labarin rayuwarta a garin Abuja gidan samy baby , taimakon da Malama Maryam da ƴar ta Lubna suka yi a rayuwarta ,  har zuwa komawarta gida Maiduguri wajen Prof .

Ta ɗago kanta tana nazarin Fuskar Falmata wacce tayi ƙasa da idanunta ya zuwa yanzu ta daina hawaye ,  riƙe hannunta ta sake yi muryarta na rawa ta cigaba da cewa

" Falmata na san ni mai laifi ce a wajen ki , amma dan Allah kiyi haƙuri ki yafe min , nayi kome ne gurin ƙoƙarin na baku rayuwa mai kyau bansan cewa ace na kama hanya ne na rusa mana rayuwa ba , ki yafe min ki zo mu koma Nigeria wajen Baba prof shine kaɗai mutumin da ba zai kore mu ba , ki rabu da Rayuwa da Youssouf kamar yadda Mama ta bar mu , shi ɗin ba kowa bane da ya wuce Maƙaryaci

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login