Showing 351001 words to 354000 words out of 411050 words

Chapter 118 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt

10 Sep 2025

8144

tayi amfani da hagu da dama dan haka tayi hasashen sashin da yake hagu daga nan ta fito dan haka ta kama hanya .

Ko a tsarin harabar sashin bata ga sauyi daga wanda ta gani a ɗazu ba shiru sashin yake babu kowa duk hadiman sun kammala aiyukan su sun tafi ga makwantan su .

dan haka kan ta tsaye ta dunga ratsa falukan da ita take tura ƙofofin su da hannun ta har ta tarar da wanda ya mata iri ɗaya da nasu sai dai wannan ta lura kamar ba wancen ɗin bane saboda wannan babu kujeru sai wasu irin katifu da aka yiwa falon ƙawanya da su da ta tsaya da kyau ta lura sai ta ga kamar har labulayen falon ba irin waɗancan ɗin bane .

Tana ƙoƙarin juyawa ta nemi wanda zata tambaya ko nan ne sashin Umma kamar yadda ta ji ana ƙiran surukar ta da wannan sunan , dogon kunnen ta ya fara jiyo mata tashin muryar wata mace daga ɗakin da tayi zaton masauƙin ta ne dan haka ta ɗan taka gaba kaɗan zuwa kusa sa ɗakin tana saurarar kalaman matar da take yin su cikin tashin hankali da hargagi .

" Hafsatouwa ya zamo dole ki kouma wajen sa ki daɗa masa bayani da jaan kunne kada a samou watta matsala ga wannan karon wannan shegiyar ɗiya ta mutan agades da ta ɗora min jakar tsaba kaji sunka bini da tsattsaga ina buƙatar ya lalata min ƙwanyar ta , ta wanke ni ta wanke ɗiyana da bakin ta da ta min wannan sheri ta tona min asiri na da shike binne tsawon lokaci ina so ta lahe ɗoɗɗoyan aman da tayi da bakin ta .

" shi kouwa wannan taƙadarin yaro ɗan tamri Youssoufa da ake kome bisa kan sa ina so a sabunta min aikin sa yayi tsamri fiye da na baya a ƙara hargitse shi a gigitar shi ya fice hankalin sa , itta hegiyar ɗiyar da ya amro dagga Nigeria a sanya shi i mata shika ukku russ tunda na lura shina ƙamnar ta sosai hakan zai ci ran sa ya zaburar sa komawa ga ruwa ina so ya zama tamre wurin bibiyar mata a baya ya kwana da ya ya auri ƙamna gaba 'ya da uwa nake fatan ya haɗa kada kouma ya saurarawa barasa ya zuƙe ta tamkar nonon uwatai ya zama lalattace irin lalatar da zata sa iyayen sa su yahe shi dagga cikin 'ya'ya mutanen gari su masa korar kare dagga birnin Maradi .

"Daga nan na san baƙin-cikin haka shi zai kai Safiya ramin ta...tayi wata dariyar hango cikar buri .

Daga ƙasan ta inda tayi gurfano Hansatuwa da take sauraron ta tana taya ta dariya tace " Ranki shi daɗe maganin kukana ai wannan kullin magani da na kawo miki shi ita uwar ta su anka ce ana so ta ci domin barin ta haka nan tsakani yana lalata mussu aiki kin san ta da ibadar ganin ido .

" ar can kyale ta mu da muke ɗiyan liman ma munka saurarawa ibadar nan bare itta da haye tayi ɗaukar duman magaji da nishi dan kawai ace itta ta Allah , maganin ta nake yi wallashi sai na hana ta ga yin ibadar naga ƙaƙa ta ka yi ta lalata mouna aikin 'yar tselen uwa .

"Hafsatouwa muddin aiki shi tafi dai-dai da tsarin mu ki tabbata shekarar gaba ke ai babbar jakadiyar birnin Maradi doumin kouwa waccen kaucewa take ta baki guri da hannuna zan sallame ta da wani mummunan sharri ta yadda zuri'ar ta basu yin gadon matsayin ta sannan ban tsaya nan ba cikin jama'ar ki ɗai-ɗaya ne ba za su Makka ɗakin Allah ba sai fa wanda Allah bai ƙira ba .

Wata mitsi-tsiyar guɗa Ƙaramar jakadiya ta sake da hakan bai hana su jin motsin Falmata ba wacce a kokarin ta na yin baya ta ture 'yar randar da aka ajiye 'yar bishiyar fulawa daga sama kaɗan da inda take tsaye tana sauraron su tukunyar ta faɗo ta fashe .

A tare suka zaburo ƙirjin su na dakan tara-tara da jin tsoron ko dai an musu laɓe ?

"Idan kuwa hakane muddin ta kama mai mata laɓe sai ta sabauta shi kafin ta ɓadda shi ko wanene kouwa da dai ya fasa wannan sirri na ta mafi girma .Hajiya Mama ta aiyana hakan cikin ran ta lokacin da take nufar falon a ɗimauce .

ASSALAMU ALAIKUM MASU KARATU

DA FATAN KUNA LAFIYA TARE DA FATAN ALHERI .

KUYI HAƘURIN JINA SHIRU DA KUKA YI UZURIN DA YA GITTA MIN MAI GIRM ne .

A gaskiya bana jin daɗin ku masu karatu ta yadda bakwa musayan ra'ayoyin ku hakan ma na ɗaya daga cikin abunda ke duƙusar ni daga nayi yunƙurin yin typing sai nace "ah to yaya zan matsa kaina Alhalin ba'a nuna yabawa ?  Sai kawai na ajiye na fuskanci wani lamarin da ya zarta haka , da fatan kun fahimceni za kuma kuyi duba izuwa koke na ?

Nagode '

  
  
[4/15, 10:16 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: MAFARI
(Hargitsin Rayuwa )




Umm'muaz




51





Da baya-baya Falmata ta fara taku tana jin wani tsoro-tsoro daga ƙasan ran ta kafin ta juya da hanzarin son gujewa haɗuwar su da ita da mamallakan muryoyin da ta ji suna kitsa sharri da bata kai ga sanin su waye ba .

Sai dai taku biyu kawai tayi ta ji an fisgo rigar ta ta baya da matuƙar ƙarfi da ba domin rigar tana da faɗi ba da babu abunda zai hana ta yagewa bayan ta jefar da ita a ƙasa warwas .

A tsorace ta juyo da taimakon hasken lantarki suka yiwa juna kallon tsakar ido tsakanin ta da Hajiya Mama ,

Ba tare da Hajiya Mama ta saki rigar Falmata ba tana ƙanƙantar da idanun ta da suke cike da tashin hankali tace "wacece ke ? Me kuma kike nema anan ? Wa ya aiko ki ? Sannan me kika ji ana cewa ?

Falmata ta kif-kifta idanun ta da basu cika karfi ba kafin ta fara kici-kicin kwacewa cike da dakiya a muryar ta tace " Ni ce Falmata , matar unh ' Umh Yarima Youssouf Abdoul-aziz , kuma ki sake min riga ta na tafi .

Wani irin zillo Hajiya Mama tayi a take gumi ya karyo mata ta shiga juya kan ta daga ɓangaren hagu zuwa dama baki ɗayan jikin ta tsuma yake .

Idanun ta da suka fir-fito a halin yanzu su ta gwalalo cikin kufcewar nutsuwar ta ta shiga jijjiga Falmata da wata muryar da ta fi kama da raɗa take cewa "Annamimiya ke kuma salon ki kenan ? Da salon da kika zo kenan ?? Lalle kin yi kuskure mafi girma da da ɗai wallahi baki sake maimaita makamancin sa .

Juyawa tayi tana jaan ta ita kuma tana turjewa , cikin ɗakin da suka fito ta koma jaye da ita tana shiga ta ingiza ta ba tare da ta kula da cikin jikin ta ba da sauran ƙiris ta faɗa kan cikin ba dan ta riƙe gadon da ta samu damar ƙarasawa gaban sa ba.

Hafsatouwa da tuntuni bata samu damar cewa kome ba illa fargaba da ita ma ya cika mata ciki maƙil jin wacece Falmata , da matsayin ta a gidan da kuma alaƙa mai girma da take da shi da zancen da suke tsakiyar yin sa ita da uwargijiyar ta da babu shakka Falmata ta ji kome .

Tana shiga ɗakin ta rufe ƙofar ta murza ɗan makulli da hanzari ta juya jin sautin mari da ya karaɗe ɗakin .

Akan Falmata ta sauke ganin ta wacce ta durƙusa akan guiwar ta riƙe da ƙuncin ta da Hajiya Mama ta zage iya ƙarfi ta mare ta .

Sake chakumota tayi ta ɗaga ta tana sake chukui-kuiye ta tace "za ki faɗa min me kika zo yi nan wajen a dai-dai wannan lokacin kuma wa ya turo ki ? me kuma kika ji ina cewa ? ko kuma sai na shaƙe ki kin mutu ?

Falmata da zuwa lokacin hawaye ya gama wanke mata fuska zuciyar ta kuma ta cika da tsoro cikin rawar murya tace "wallahi ban zo yin kome ba kuma ba wanda ya aiko ni nan , mantuwa nayi na kasa gane hanyar komawa sashin da aka sauƙe mu saboda tunda muka zo ban taɓa fita ba kuma kin ga idona , idona wallahi bana gani mai kyau dan Allah kiyi haƙuri ku mayar dani sashin da Hajja take .

"Ƙarya kike yi munafuka , me ya fito da ke a daren nan idan da gaske dindimin kike yi ? Baki bani amsa ba me kika ji muna tattaunawa nace ? Kuma uban waye yace ki min laɓe ?

Mukut ! Falmata ta haɗiyi yawun tsoro cikin rashin sanin takamaimai amsar bayawar tayi shiru .

Cikin rashin sanin ta shirun da tayi shi ya basu tabbacin ta ji kome , abunda suke gudun kuma yana gaf da faruwa watau fallasuwar asirin su .

Falmata bata ankara ba taji sauƙar wani marin kafin tayi wani yunkuri ta ji sauƙar duka da dundu ta ko'ina kusan gabadaya Hajiya Mama bata hankalin ta dai duka kawai take kai mata .

Ihun da Falmata ta buɗe maƙogoro ta rafsa shi yasa Hajiya Mama dakatawa daga dukan ta , idanun ta jawur ta juya ga Hafsatouwa tace "Hafsatouwa tai ki ɗauko min wuƙa mai kaifi ki kawo min .

Da gudu Hafsatouwa ta miƙe daga durƙuson da tayi ta fita .

Cak Kukan Falmata ya tsaya ta shiga wara idanun ta da ganin su ya sake yin ƙasa saboda kukan da take yi , ta fara taku tana laluben hanya so take tayi wani yunkurin tseratar da kan ta .

Fizgota Hajiya Mama ta sake yi ta warɓar da ita a bakin gado da muryar da take cike da bushewar zuciya tace "ƙwarmato kike yi min ? Kina son tara min jama'a ? Yarinya baki sanni bane , amma za ki sanni dagga lokacin da na guntule miki halshe .

Cikin neman agaji Falmata ta zube guiwar ta a ƙasa dai-dai da dawowar Hafsatouwa da take riƙe da wata sharɓeɓiyar wuƙar yanka dabba a cikin kuɓen ta

hawaye na tsiyayo mata ta haɗa hannuwan ta biyu da sigar migiya tana cewa "Hajja dan Allah kiyi hakuri ki barni na tafi wallahi duk abunda naji ba zan faɗawa kowa ba , wallahi bazan faɗa ba , kiji tausayina ki ƙyale ni ko dan abunda ke cikina .

"Ki min shiru hegiya , ina ruwana da hegen cikin ki ? Kar na kuma ji kin ƙira ni ba suna na Hajja ba .

"faɗa min me kika ji ana cewa ? Maimaita min idan kuwa kika min ƙarya sai na yanka ki billahil azim.

Tiryan-tiryan Falmata ta maimaita musu hirar su kamar yadda ta haddace akan ta ba kalma guda da ta manta duk a ƙoƙarin ta na son suyi mata afuwa bata tsaya da bayani ba sai da ta dire sannan ta ɗora da cewa "wallahi shikenan abunda naji kuma nayi Alƙawarin bazan faɗawa kowa ba .

Sai dai tunanin ta ya tsaya chak lokacin da Hajiya Mama tayi wata gajerar dariyar da ke bayyana irin halin ɗimuwar da take ciki.

"Bayan duk kin ji wannan sirrin nawa da mutane uku ne suka san shi bayan ni a din duniya ? Sirrin da 'ya'yan cikina ma basu san shi ba , sirrin da yake ginshiƙi na rayuwata baki ɗaya , da na ta'alaka duk wasu nasarorina akai , shine kike tunanin zan bar ki ki tafi ? Na barki ki tafi kiyi rayuwa a cikin gidan nan ɗauke da sirrina a hannun ki ? Ko a hankali irin naki na dabbobi hakan abu ne da zai yiwu ?

Wata dariya ta sake yi kafin tace "yarinya wannan ba mai yiwuwa bane dole nayi abunda zai sa na kuɓutar da sirrina da yake hannun ki ...

"Wallahi Hajja bazan faɗawa kowa ba .

Falmata ta furta hakan tana sharar hawaye da rigar ta .

"Ni da kaina zan goge shi daga kan ki ko da kuwa ace hakan ba zai samu ba sai na raba kan ki da gangar jikin ki ne '

"Hafsatouwa ban wuƙar nan .

Da sauri ta miƙa mata ta sake komawa tana Sake jaan labulen windows din dakin.

A hankali Falmata ta ɗago kai zuwa lokacin ta karaya cikin ran ta ta saddaƙar mutuwar ta ta kusanto ,

Idanun ta ta sauƙe akan Hajiya Mama , tana jin yadda zuciya da ƙwaƙwalwar ta ke adana hoton kamannin fuskarta , a matsayin matar da zata raba ran ta da gangar jikin ta .

Fitsarin da take riƙewa ya kufce ya shiga bin ƙafafun ta lokacin da ta sauke ganin ta akan kakkaifar wuƙar da Hajiya Mama take jujjuyawa a hannun ta .

Wani murmushin mugunta Hajiya Mama ta mata kafin tace "ke kina jina ?

Cikin mutuwar jiki liƙis Falmata ta gyaɗa kan ta .

"Kina da zaɓi biyu ko dai na yanka ki a yanzu na kar ki na kar banza , na sa a ɗau gawar ki a yasar , ko kuwa kiyi duk abunda nace da ke ba tare da gardama ba , sannan ba kuma na son na sake jin tashin sautin muryar ki, ko numfashi mai ƙarfi kika jaa sai na yanke miki hanci bare ta kai ki ga magana babu makawa za ki tsinci halshen ki a ƙasa kina jina ko ?

Da sauri ta sake gyaɗa kai, wasu sabbin hawaye na sake tsiyayo mata .

"Hafsatouwa ki je ki kawo min rigar bayu da mayafi .

Kafin ta rufe baki Hafsatouwa ta yi waje ,

Nisawa Hajiya Mama tayi tana karkaɗa kafa cike da izza da mugunta tace "yarinya duk abun da kunnuwan ki suka jiye miki na kaddamar ina kuma kan gaɓar shirya wasu game da surukuwar ki da shi kan sa mijin ki haɗa da 'yal uwarki gasken gaske ne .

"Ki kuma tabbatar zan iya yin abunda yafi haka akan ki muddin kika yi kuskuren yi mini gaddama ko da sau ɗaya ne .

"Ɗauke idon ki daga kaina fitsararriya kin wani tsattsareni da ido uwa budurwar mujiya .

Ta ƙarasa zancen da tsawa da hargagin da yasa abun da ke cikin Falmata murɗawa.

Da sauri Falmata ta sunkuyar da kai tana jin tausayin kan ta na kawo mata , ita kuma irin tata kaddarar kenan mutuwa a hannun wannan azzalumar mata , da ita da abunda ke cikin ta , domin zuwa yanzu ta tabbatar babu wani mai tsaratar da ita sai fa Allah .

Dawowar Hafsatouwa riƙe da wasu tsummokara yasa Falmata sake tsorata "ka dai toshe mata hanci za suyi su hanata mumfashi har ta mutu ?

Saukar taunmokaran a jikin ta ya sa ta ɗago kan ta a firgice.

"Ki tashi ki saka kayan nan da gaugawa .

Babu yadda ta iya haka ta lafta waɗan nan kayan akan na jikin ta tana yi tana yunƙurin aman da yake taso mata sakamakon tsami da ɗoyin datti da kayan suke yi .

"Kiyi lulluɓi da kyau ki biyo ni a baya muddin kika yi wata alamar da tasa aka gane akwai wani abu wallahi kafin ki farga na soke ki.

Haka suka dunga ratsa sashi-sashi na gidan suna cin karo da bayu tsilla-tsillan da suke zubewa su gaishe da Hajiya Mama .

Har suka dangana da wani sashin da yafi kama da kango da yake can ƙuryar gidan da daga shi sai maƙabartan da take cikin gidan ta ɓaryar dama .

Da wani ɗan makulli Hajiya Mama tayi amfani ta buɗe ƙofar ainahin tangamemen falon da yake cikin sashin .

Ta ingiza Falmata wacce bata kai ga sanin cewa falon ya shiga ƙasa ba dan haka tana jefa ƙafar ta ta faɗa ciki ta gurɗe a ƙafa kiris ya rage ta faɗa a kan cikin ta Allah ya sa ta tokare ƙasa da hannuwan ta .

Lokacin da ta ɗago kai bata iya ganin fuskokin Hajiya Mama da Hafsatouwa saboda duhun da Falon yake ɗauke da shi , da raunanan idanun ta hasken da yake shigowa daga can harabar gidan yayi kaɗan su iya gani tare da shi .

Ɗallare mata ido da hasken wayar hannun ta da Hajiya Mama tayi yasa ta saurin runtse idanun ta kafin ta buɗe su da sauri jin abunda Hajiya Mamar take cewa .

" anan za ki cigaba da zama har zuwa lokacin da zan gama yanke hukunci kan matakin da zan ɗauka akan ki., idan kika yi yadda nake so ta hanyar zama salin-alin ba tare da kin yi wani motsin da zai sa asan kina nan ba , wataƙila na iya barin ki bayan na kafa miki sharɗaɗun cigaba da rayuwa a gidan nan .

"Muddin kuwa kika yi yunƙurin yin wani motsi da zai sa asan kina nan wallahi , wallahi , wallahi , ni ina iya kashe ki da hannu na kuma na sa a ɓatar da gawar ki .

Daga haka ta juya da sauri suka fita ita da Hafsatouwa daga inda Falmata take yashe tana iya jiyo saƙala ɗan makuba da aka yi aka kulle ta ta baya kafin ta fara jin sautin takun sawayen su akan busassun ganyayyakin bishiya su na barin wajen har dai zuwa lokacin da sautin su ya ɓace a kunnuwan ta .

Wani irin karkawa tsokar jiki zuwa gundarin zuciyar su ka shiga yi na tsananin tsoro da firgicin da ruhin ta ke ciki , kafin da wani irin sauti ta fashe da kuka , ta shiga rarrafawa da hannunwan ta da guiwar ta zuwa inda take tunanin nan ƙofar take ,

Lokacin da tayi karo da bango da hannuwanta duk biyu ta shiga bugun bangon cikin ɗimuwar rashin fahimtar ƙofa ce a wajen ko kuwa jikin bango ? .



Washegari da Asuba a Masallaci bayan sun idar da Sallah, Maimartaba tare da Youssoufa yana biye da shi a baya, kai tsaye sashin Maimartaba suka yiwa tsinke domin ganawa ta musamman .

Maimartaba yana sake tambayar Sa yanayin lafiyar jikin sa ?

Shi kuma yana amsa masa da cewa "yana cigaba da samun sauƙi sosai .

Bayan sun isa turakar Maimartaba Youssoufa zai zauna daga gefen shimfiɗar da yake kai , yace masa "dawo nan kussa gareni mu tattauna yana masa nuni da kan shimfiɗa kusa da shi .

Da jin daɗi mai yawa Youssouf ya matsa kusa da shi .

Gyaran

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login