Showing 288001 words to 291000 words out of 411050 words
Chapter 97 - MAFARI COMPLETE BOOK HAUSA NOVELS BY UMMU MUAZ.txt
kafin ya ajiyewa wani mutum doyar a teburin gaban sa , ya ƙaraso inda take
"Ke baiwar Allah ki tashi daga nan , idan bara za kiyi ki shiga cikin tasha ko kuwa ki nemi wani wajen amma ba nan ba wajen sana'ar mutane .
'kayi haƙuri dan Allah hutawa nake yi , ga kuɗina ka bani abunda kuke sayarwa na duka ,
Ta miƙa masa kuɗaɗen da bata san adadinsu ba da ta zaro daga cikin jakar hannunta ,
Kallon kuɗaɗen da bana Nigeria bane ya yi , kafin yace
"waɗannan takaddun fa ? Kuɗin ina ne ?
Kafin ya rufe baki ubangidansa ya ƙwalla masa ƙira
" Bashari wai kana ina ne ?wannan wanne irin tsagoron zunzurutun walaƙanci ne zaka tafi hirar banza ka barni da ayyuka , to wallahi idan har ƙazar nan ta ƙone a mai , na rantse sai ka biya ni dan ni da asara kullum saɓani muke .
Da sauri Bashari ya bar kan Falmata ba tare da ya karɓi kuɗin da take miƙa masa ba ,
Ya ƙarasa da gudu wajen ogan sa ,
"kayi haƙuri oga wata mata ce kamar mahaukaciya dai haka ta zo da wasu kuɗaɗe kamar na landan a hannunta wallahi oga wai ta miƙa min su na bata doya , kuma kuɗin dayawa oga
Da sauri Ɗanliti ya saki matsamin da yake hannunsa acikin mai ba tare da ya tsame doyar ba ,
"kai Bashari na fa sanka da sakin ƙwai , kuɗin landan fa kace ? Dala fa kenan ? Yau a masu sayen doyar tawa har da masu Dala ? Ina take ? Nuna min matar ?
Nuno masa Falmata yayi da har lokacin take takure a zaune ,
Cikin ƴar marairaicewa Ɗanliti ya kwararo mata sallama , da sauri ta ɗago kanta jin muryar wanda ta taɓa sani a baya ,
Suka yi arba da fuskokin juna, shirun ƴan wasu daƙiƙoƙi suka gifta kafin Falmata ta miƙe tsaye da sauri tunowa da tayi da ko wanene Ɗanliti.
' wa nake gani haka kamar un-un Ɗankachallari ? Wai kece ko kuwa kamanni ne ? Ah ai babu zancen kamanni ma ga ƙwala-ƙwalan idanun nan daga ina kike ƴarkachallari haka kamar 'yar bina ?
Muryar ta na ɗan rawa , tace
" Ba sunana ba kenan , sunana Falmata ,
' haka fa ashe sunan ki kenan , to dawo daga nan a kawo miki doya ki ci ki sha ruwa ko kya samu nutsuwa , na ga yunwa na tanɗar bakin ƙirshirwa a fuskar ki .
A ɗarare ta zauna a inda yake nuna mata kan wani benci , aka kawo mata zazzafar doya da ƙwai har da dafaffen ƙwai guda biyu da aka soya su da ƙwai ,
Tas ta cinye ta sha ruwan leda biyu , tayi hamdala
Ɗanliti da yake gurin suyar sa ya bari tare da sake dawowa yana sake tambayar ta daga ina take ?
A takaice ta faɗa masa daga inda take , daga haka tayi shiru
Ɗan jimm yayi yana kallon ta , kafin yace
" wai , tabɗi yanzu nan daga Niger kike ? shiyasa mana na ga kin koma busu-busu , ashe rairayin hamada ne ya turbuɗe ki , ai kin ma kaima barka da sahara bata haɗiye motar ta ku ba kamar yadda nake ji ana labari wai-wai , koda yake da kuma kun yi mutuwar shahadar nan da kowa ke nema ,
" nima kin ga ai yanzu duk na tuba na daina abunda yake jawo min tsinuwa , na kama ƴar sana'ata da nake rufawa kaina asiri da ita , aure ma nake shirin yi , O ni Ɗanliti mutuwar Saly Fara ta zamanto min alherin da na samu shiriya a domin ta ,
Ya ɗaga hannun biyu sama , yana ƙara cewa
"Allah na ƙara gode maka da ka kashe Saly Fara ni kuma ka shiryar da ni .
Shiru Falmata tayi tana sauraren bayanin da bata nemi jinsa ba , ji tayi ya cigaba da cewa ,
" ai ƴar danginku ma zan aura wallahi kuwa ,
Ɗago kanta tayi ta dube shi ,
"ƴar dangin mu ? Tambaye shi da mamaki ,
" eh Ƴar uwarku Yagana ba , ni kuwa ina Yakaka wallahi habibiya tana nemanta ruwa a jallo tace tayi ta zuwa gidan da kuke bata samun ku , can gidan wani mutum mai kuɗi wai a Danboa road ko ina ?
Da sauri Falmata tace ,
"Ina Yagana take ? ta san gidan Prof ? Ka kaini wajenta ta kaini gidan Prof ,
Kwantar da hankalin ki indai habibiya kike nema kin same ta tunda kika ganni , nan da mintoci talatin ma zaki ganta anan ta zo , ai tare muke sana'ar mu , ita take yi mana wanke-wanken farantan kayan sana'a , kinsa rayuwar nan cuɗanni na cuɗeka ne .
****
Yagana ita ta sada Falmata da gidan Prof da misalin ƙarfe biyu na rana , har falon prof ta so shiga da ita sai dai aka hana su saboda yana tare da baƙi , amma an musu iznin shiga ciki sashin matar gidan domin su jira shi .
"Falmata ai tunda na kawo ki ni zan iya tafiya ko ?
Yagana take neman iznin Falmata bayan sun kawo ƙofar sashin su Rahima ,
"Yagana , Nagode , Nagode zaki iya tafiya ,
"Babu kome Falmata ai mun zama ƴan uwa banda sharrin shaiɗan da ya rinjayeni a baya na aikata kuskure , Dan Allah idan Yakaka ta dawo zan zo na nemu gafararta ta yafe min .
Nan suka yi sallama ,ba tare da Falmata tasan wanne kuskure Yagana ta aikata ba da take neman yafiyar Yakaka ,
Jikinta babu ƙarfi ta nufi cikin gidan , a zuciyarta tana saƙa yadda zata yi ta tunkari Prof da zancen ya raba aurenta da Youssouf batare da ta bayyana mummunan laifin da suka aikata ba shi da Yakaka ,
Saboda bata so wasu su dubi Yakaka da wannan mummunan laifin , zata zama abun aibatawa a wajen Al'umma ,
A hankali ta tura ƙofar falon ta shiga sanyi da ƙamshi mai daɗi ya buso ta , daga ciki kaɗan ta tsaya tayi sallama da zazzaƙar muryarta ,
Cikin nutsuwa matar da take zaune a kan ɗaya daga cikin sabbin kujerun falon tana saƙa da zaren ul da kwarashi, ta ɗago kanta , idanun ta suka sauƙa akan Falmata da itama take iya hango alamun farar fatar ta daga inda take ,
Muryarta bata fita sosai ta amsa sallamar ,
Su dukkanin su shiru suka yi suna kallon juna ,
Cikin sanyin jiki falmata ta kalato murmushi ta ɗora bisa fuskar ta, zuciyar ta na bata cewa Rahima ce wannan take hangowa A hankali tace
"Rahima ni ce fa, ni ce Falmata ƙanwar Yakaka baki gane ni bane ?
Kwarashin hannun Khaalty Rahima ya faɗi ƙasa bata kula ba ta miƙe tsaye ta nufi inda Falmata take , zuciyarta na bata tabbacin cewa mafarki take , wataƙila kuma gizo take yi mata ,
Tana zuwa ta miƙa tafukanta biyu ta dafa kafaɗun Falmata idanunta suna jiran ɓacewar ta daga ganinsu ,
Ƴar dariya Falmata tayi , kafin tace ,
"Rahima kina mamakin gani na ko ? Yakaka ma ai tana zuwa wataƙila gobe zata iso ba tare muka zo ba Rahima....
Hannun Rahima da taji yana tattaɓa mata fuska , yasa ta haɗiye sauran kalmomin ta , ta riƙe hannuwan tana ƙoƙarin sauƙe su daga fuskarta , da wani irin sauti ƙasa-ƙasa , Khaalty Rahima tace
"Falmatana ke ce ? Ke ce wannan Falmata ? Ke ce ? Ina Yakakana ?
Rungumo ta tayi gaba ɗaya zuwa cikin jikinta tana fashewa da kuka mai sauti ...
Assalamu Alaikum masu karatu .
Da fatan duk kuna lafiya ??
Ina mai baku haƙurin ji na shiru da kuka yi wasu hidindumu ne suka sha kaina , da fatan kun min uzuri ? ❤
Nagode .
[12/16, 1:19 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
45
Da rashin yadda a fuskar Falmata , ta ɓanɓare jikinta daga na khaalty Rahima , Muryar ta na ɗan ƙyarma tace ,
"wacece ? Rahima kece ?
Zuwa lokacin Murmushi Khaalty Rahima take , murmushin da har ya bayyana haƙoranta , sake riƙe hannun Falmata tayi , da sautin muryar ta mai ɗan ƙarfi tace , "Falmatana ni ce Mamar ku , ni ce , ashe kuna raye Falmata , ina Yakaka ?
Da wani irin yanayi Falmata take sake wara idanunta tana ganin dusu-dusun fuskar matar da take gabanta , tana jin wani irin bugu da zuciyarta ta sauya a take da ziyarta ruɗani a tare da ita tace, "Mama na ? Ke ce Maman mu ?
Sai tayi baya da sauri kamar zata gudu , ta waiga dama da hagunta , da wani sauti tace , "Yakaka ina kike ? Kina ina ? Ki zo ki ganta wai wannan Maman mu ce ? Wai da gaske ita ce ?
Murmushin fuskar Khaalty Rahima bai ɗauke ba lokacin da hawayen fuskarta suke cigaba da sauƙa ta matsa tana sake kusantar ta , sai ta miƙa hannu ta jaa hancin Falmata da bai wani ciƙa tsayi ba , ta zarce da riƙe kumatunta duk biyu da hannuwanta , sannan ta haɗa goshin su guri guda , tana sake cewa ,"Ni ce Mamanku Faɗimah-Zahra ni ce Ina Amina ?
Wani irin yanayi ne na zallar Farin-ciki mai tafe da sanyi mai samar da nutsuwa , taji yana bin duk wata jijiyar jikinta , a sanyaye ta karkata kanta , muryarta da rangwamen sauti tace ," Maman mu ke ce ? Ke ce Mama da gaske ba mafarki ko gizo ba ? Mama daman kina Raye ? Mamana .
Bata jira ta amsa mata ba ta zarce da rungumeta ,tana sakin kuka da ƙaramin sauti , irin kukan da Ɗa yake irin sa a lokacin da ya tsinci kansa a gaban Mahaifiyar sa bayan tsawon lokacin da ya ɗauka yana haɗiyar baƙin-ciki cikin kewar ta .
Khaalty Rahima ta sa hannu biyu ta rumgumeta , tana jin wani irin tarin farin-ciki marar misaltuwa , ashe daman rayuwa zata sake iya yi mata sauyi mai tattare da farin-ciki irin wanda ta fidda rai da samun sa , ashe watarana zata zo da zata sake ganin ƴa'ƴan ta ? Allah abin godiya .
Sauƙowar Amnee daga Sama ita ta jaa hankalinta, da mamaki ta ƙaraso tana kallon su , da har zuwa lokaci , Falmata take kwakume da Mamanta bata bar kuka ba , da alamar tambaya a muryarta tace
"Ukhtee Rahima me ya faru ? wacece wannan ?
, jin sautin muryarta yasa Falmata ɗago kanta , kafin ta bi bayan Khaalty Rahima da take riƙe da hannunta , suka ƙarasa gaban Amnee , da murmushi Khaalty Rahima ta haɗa hannun Falmata da na Amnee , tana cewa
" wannan ita ce 'Ya ta Falmata da na baku labarin su ina zaton sun mutu ita da yayar ta mai sunanki Amina da ake mata laƙabi da Yakaka , ikon Allah da girma sai ga shi ya kawo min ita har gabana .
Sai ta waiga ga Falmata , tare da cigaba da cewa , "Fatima ya akayi kika san ina nan ?
Da bayyanuwar murna Amnee ta zarce da rungume Falmata , kafin ta ɗora da cewa , Alhamdulillah , Alhamdulillah , ashe ba haka nan ba na so yaran nan tun a rana ta farko da na fara ganin su , ace 'ya'ya nane , jini na , 'ya'yan 'yar'uwa ta , Ukhtee Rahima ai nasan Fatima da Yakaka tun shekarun baya suke rayuwa tare da 'yan uwansu a gidan nan ba tare da sun san dangantakar su da juna ba , kai Alhamdulillah .
Saman kujerun wajen suka zauna ,suna sanya Falmata a tsakiyar su , khaalty Rahima ta ce ,
"Ikon Allah Ukhtee ashe ma kun san su ? Ashe suna hannun ku ?
" ƙwarai na san su , ai yayan Zainab ( Doctor Hamza ) shine ya kawo su gidan nan a matsayin ƴan gudun Hijira , a gidan nan suke tsawon shekaru kusan biyar zuwa shidda , ikon Allah kenan ai kuwa ko zuwan Yakaka na kwanan nan taje har wajena ta gaishe ni , ai itace wacce kika ji na tambayi Rahima shekaranjiya kan ina take ta shaida min ta tafi Niger wajen Ƙanwar ta da 'yar ta , Allah ya saɓa haɗuwar ku ai da gidan nan zaki tarar da ita .
"Ikon Allah , to Alhamdulillah , Alhamdulillah , sune kalmomin da Khaalty Rahima take faɗi farin-ciki na sake gauraya ta , ji da tayi ashe ma 'ya'yan ta gida suka dawo , ashe ma tare suke da yayun su , ƙarƙashin kulawar mutumin da yake mazaunin Uba a wajenta , Babu shakka tare da dukkanin tsanani akwai sauƙi , kuma ba'a fidda rai daga Rahamar Ubangiji .
A kusan tare suka jefawa Falmata tambaya ,
"Fatima ina Amina da 'yar ta ?
Shiru Falmata tayi da famin raunin cikin ranta , a hankali ta ce da su ,
"Allah ya yiwa Mama rasuwa kwanaki huɗu da suka wuce ,
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon, Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon," suka haɗa baki wajen cewa , shiru kuma ya gifta tsakanin su cike da jimamin rashin jikar su da basu kai ga samun damar ko da ganin fuskarta ba a zahiri , babu shakka Allah baya barin wani domin wani ya ji daɗi .
" Ina Maisunan Ukhtee ita kuma ? Ba wajen ki ta tafi ba ?
Ƙhaalty Rahima ta sake tambayar Falmata ,
Shiru Falmata tayi tana sunkuyar da kanta ,
Wani busasshen yawu Khaalty Rahima ta haɗiye tana jin tashin hankalin da yake farmata , kada dai ace wani mummunan lamari ne ya afku ga ɗiyar ta mafi soyuwa gareta ?
Matsa hannun Falmata dake cikin nata tayi da ɗan ƙarfi , ta ɗan ɗaga sauti tana sake maimaita tambayar " Falmata ina kika baro Yakaka ??
***
A Niamey tunda Yakaka ta dawo daga tasha , bayan samun tabbacin Falmata ta riga ta tafi Nigeria ta wannan mummunar hanyar mai cike da hatsarin ƴan kungiyar Boko Haram ,
bayan kuka babu abunda take yi , gabadaya ta ɗora laifin gudun Falmata akanta , tayi danasanin zuwanta ƙasar baki ɗaya yafi a ƙirga , ganinta da ace bata zo ba da Falmata bata gudu ba , sai ta ji inama da ta zauna akan batun Youssouf da yace su rufa asirin tsakanin su kada Falmata ta sani a tun farko , ƙila da suna da damar da zasu haɗu ita da Youssouf su wanke kansu a wajen Falmata bayan sun ƙaryata ƴan uwansa a gabanta , da kuma lamarin bai kwaɓe ya haka ba ,
Ganin kuka ba zai mata magani ba yasa ta miƙe tsaye ɗauke da jakar kayanta , Hajja wacce take zaune zugum ta dube ta tare da cewa ,
"Babba uwar Mama ke kuma ina za ki ? Kadda kice min kema gudun fanfalaƙin za kiyi ? Kiyi wa Allah ƴar nan ki tsaya mu ji da damuwa ɗaya kadda ki ɓaro mana wata sabuwa , guje-gujen nan ba kana bane , 'ya'yan nan ai ƙwarya ta gari tana ragaya , kamar yadda darajar ɗiya mace ɗakin Mijinta kar ki tafi ko'ina Dan Allah ,
Ba tare da Yakaka ta dubi Hajja ba tana share hawayenta da gefen hijabinta tace ,
"Hajja gara na tafi saboda Falmata fa ko da taje Maiduguri lafiya , bata fa san hanyar gidan Baa prof ba, kuma bata san kowa ba a garin bayan shi , dole zanyi hanzarin tafiya nima ko Allah zai sa na haɗu da ita a tasha , na tarye ta Hajja ina ƙaunar Falmata ita ce kaɗai jinina a duniya ina tsoron rasa ta Hajja , zan tafi bazan iya zama ba nima .
Guntuwar ƙwallar da ta tarawa Hajja a ido ta sa hannu biyu ta shafe fuskarta ta muttsuƙe ,
" To Shikenan Yakaka tunda kin ce haka bari nima na haɗa ƴan kananun kayan buƙatu na mu tafi tare , ai nima zama bai ganni ba , to na zauna nayi me ƴar nan ? Ai tunda ganga ta fashe sai ƴan rawa su watse ,
Da hanzari Hajja ta shiga harhaɗa kayanta, tana cewa ,
"bari na tafi da waɗanda dole zan iya buƙatar su , sauran kuma idan Allah ya min dawowa na cigaba da Amfani da abuna idan kuwa ma tafiyar kenan , to a biyo ni da tsunmokara na , wannan lamari dai da ɗaure kai yake babu shakka da walakin wai goro a miya .
Yakaka da har lokacin a tsaye take akan ƙafafunta bata ce da ita ƙala ba ,
Cikin ƴan mintoci kaɗan ta haɗe kayanta a cikin wata babbar jakar matafiya da Youssouf ya taɓa saya mata , tana shirin yafa mayafinta suka tsinkayo sallamar Youssouf daga ƙofar falon , Hajja ta amsa tana nufar falon
A tsaye ta tarar da shi shirye tsaf cikin riga da wondo na kaftani da ya sha aiki irin na saraki , ba tare da ya yadda Hajja ta ga ƙwarar idanunsa ba fuskarsa babu walwala ko kaɗan sai tarin damuwa da tashin hankali da suka bayyana kansu ɓaro-ɓaro , cikin Amonsa da a yau ya sake kaurara da buɗuwa yace
"Hajja ni zan tai Maraɗi yanzou Hajiya Umma tai ƙirana , don Allah ku zauna a gida har na kai ga dawowa nan da kwanaki biyu , lamarin Fatima kouwa zan yi dukkanin ƙoƙarina da Yardar Allah babu abunda zai samu Matata da abinda ke cikin ta .
Ɗan karkata kai Hajja tayi da sigar tausayawa tace ,
" Babban soja Allah ya tsare hanya , sai dai kuma yanzu na gama fama da ita yayar Falmata kan cewa da tayi a yanzu itama za ɗau hanyar Nigeria saboda ko Allah zai sa su gamu da ƴar uwarta a tasha idan sun isa Maidugurin dan ita Maiɗakin naka ai kasan bata san ko'ina ba a