Showing 33001 words to 36000 words out of 155577 words

Chapter 12 - BUDURWAR MIJINA BOOK COMPLETE BY Sadnaf.doc

Sadnaf   

07 Nov 2025

2781

a tura shaidar biya ta 08033719070*

*BM*

*Page 13*


Mummy da mmn Iman ne Suka bini aguje suka rikeni ta baya.

Na saka ihu Ina "ku cikani na kashe shi dan Allah ku cikani"

Mummy ta sakeni ta dawo ta gabana ta kwasheni da mari tana hucci

"Dama haka kike Lubna Ashe bakida hankali kishi hauka ne"?

"Aikuwa ga kishi nan ya sakata hauka ta zama Yar dabba kila har shaye shaye tanayi dan idan ba shaye shaye tayi ba,ba yanda zata zo ta samu Yar mutane ta kulle ta ringa dirmar ta Kai dalla shashasha lusari zoka wuce ka d'auko Yar mutane mu kaita asibiti Kuma wlh a yanzu zaka saketa ka gama aurenta"

Ammi tacewa mahfuz daya tsaya a bakin k'ofa Yana zare Ido,shi kawai na zubawa Ido Ina kallonsa,kallonsa da nake ya Kara tunamin Abubuwan da yamin, kirjina Kamar an dora bullo sabida nauyin daya min da azabar tsanarsa rad'ad'in da hannuna yake yasa na d'auke kaina daga kallonsa na kalli tsakiyar hannuna dana Sha Jan kunshi da baki duk a san na burge namijin daya kawomin budurwarsa har gida ya daidaita ni da ita ko nace ya fifita ni akanta,tunda Abubuwan da ya mata ko rabinsa bai min ba, itama har kunshi ta masa ta Sha kitso,na tuna yanda ta fito da Yan dari bibiyu sak irin Wanda mahfuz yabani nata ma yafi nawa yawa tamin karyar a banki ta ciro take na sake tuna wasu Abubuwan da ya Kamata na nasan gaskiya lamarin,hakane yasa na m'ike Sam bajin ma Mai mummy da Ammi ke cewa ba

"Ina zakije"?

Naji muryar mahaifiyata a bayana duk sun dauka kila dakina zanyi naga alamar tsorona ma mmn Iman da mijinta suke ji,akwai mutane a tsakar gida,Ammi har lokacin bata fasa masifa ba tana "Bari na duba Yar mutane naga ko ta jawo Mana balai tunda wancan shashashan ya kasa zuwa"?

Ta shige bandakin ta rafka uban sallati kafin su ankara nima na shige dakin da gudu na fada bandakin a bakin k'ofa take hakane yasa na bangajeta dan da balain gudu na Shiga dan nasan mummy zata iya rikeni.

Flat tayi a kasa ta saki ihu na danna k'ofar na saka mukulli najiyo takunsu da ihu dan Ammi itama ihu ta saka tana "Shikenan ta hadamu waje daya zata kashemu Mahfuz"

Ta hau kwallawa mahfuz kira ko kallonta banyi ba na tsugunna a gaban Hadeeza dake kwance da alama ta fara fita a hayyacinta jini sai fita yake akanta

"tashi zaune"

"Bazan iya tashi ba Aunty kimin rai wlh jiri nakeji kaina kamar baa jikina ba Aunty kin karya min hannu Hajiya ki taimaka min ku kaini asibiti Zan mutu tace wa Ammi, Ammi kuwa mahfuz kawai take ihun Kira tana yazo ya cecesu a haukace nake.
Ban kalleta ba nacewa Hadeeza

"Kin dauka Wasa nake Miki ko"?

"Aaa Aunty"

Ta fara k'ok'arin mik'ewa zaune tana cije baki Ammi kuwa ihu kawai take tana Mahfuz yazo ya bude kofar zan kashe su sai k'ok'arin balla k'ofar suke, mahfuz na sallati mummy kuwa kuka ta fashe dashi,mmn Iman ma Ina Jin kukanta"

"Damka na kaiwa hannunta da yafi kumbura ta saka ihu"

Nace "Kudin kunshi da kitson nan mahfuz ne ya baki ko"?

"Ee Aunty shi yabani wlh shi yabani dubu Ashirin"

Na cije lebbena

A ranar daya baki kin bashi kanki kenan"?

"Eee Aunty shekaran jiya ne a ranar ya fara sanina"

Murmushin takaici nayi dan Ammi sakin baki tayi tana kallonta na watsa Mata harara
Na Kara kallon Hadeeza dake sallati tana juya Kai dan jinin sosai yake fita a jikinta nasan dole ma a kwantar da ita a asibiti

A gaban ta na ringa hada kayan da nake so nayi amfani dasu dan na farantawa mahfuz kila tama sha wasu bansani ba tunda tana shiga kitchen din Kai tsaye Kuma a Fridge yake take na tuna tsumin dana Sha Mai daci

"Ke Kika zuba min abu
Mai daci a tsumina ko"?

Na Kara matse hannun ta saka ihu tana "eee Aunty shanyewa nayi na musanya Miki da abu Mai daci,na Sha zumar ma dayawa dan Allah Aunty ki cika min hannu zan mutu"

Zanso ta mutun a lokacin data ce ita ta shanye min tsumin dana kashewa kudi,nida siya ita da amfani dashi dan ta jiyar da mahfuz dadi anya na tab'a ganin Mai karfin halin Hadeeza kuwa,sai a yanzu na tuno yanda take hararata a fakaice,har da shigowa dakina duk dan taga ya dakina yake.

Yanzu da ace ta zubamin guba a abinci naci fa dan duk Wanda zai iya abinda ta yi zata iya kisan Kai har da fasa min bokiti dan tagani da mahfuz.

Idan har shekaranjiya ya fara kwanciya da ita hakan na nufin jiya ma wankan tsarki yayi ya nemeta,yaji dadinta kenan ya koma mata na saki murmushi takaici hawaye masu zafi suka hau kwaranyo min

Banida nauyin bacci banida Jin bacci da wuri tunda tazo gidanan na fara bacci da wuri mai nauyin gaske har ta Kai idan mimi ta farka sai nayi dagaske nake iya bud'e idona

"Mai kuke min keda mahfuz nake bacci da wuri"?

Na matse hannunta da k'arfi

Wlh magani yake samiki dan kiyi bacci da wuri har yazo dakina ya tafi hannuna zai fita na Shiga uku

Maganarta ta dakeni,Ashe Mahfuz ne yake samin magani a exotic din da yake min tayinsa idan muna cin abinci Na runtse idona jikina da kirjina wani irin rawa yake

Na sakar Mata hannu a daidai lokacin da sukayi nassarar balla k'ofar, Mummy ta shigo da sauri tana shigowa ta rufeni da duka

Tana "Lubna ko dai dagaske shaye shaye kike kanki daya kuwa wanan wane irin azababben kishi ne daga mijinki ya kawo kanwar abokinsa gida sai ki nemi kasheta.

Ban bar zubar hawaye ba ina kallon mahaifiyata nace "Abinda yace miki kenan,Hadeeza ke kanwar abokin Mahfuz ce"?

Na jefawa Hadeeza tambaya da k'arfi ta bani amsa da sauri

"Aaa Aunty wlh ni budurwarsa ce"

Mahaifiyata wani irin dafe kirjinta tayi ta maimaita kalmar budurwa ban kalleta ba na fito daga bandakin mahfuz yayi sauri yayi baya,bana kaunar ganinsa a rayuwata na fito daga d'akin inajin mijin mmn Iman na "A gaskiya baka kyauta ba idan har hakane Mahfuz ya za'ayi ka kawo budurwar ka har gida kaci mutuncin matarka wlh baka kyauta ba har gidan Aurenka fa mahfuz"

"Kanwar abokina ce Hamisu ba budurwata bace tsorata ta tayi shiyasa ta Fadi haka,zarginmu take na rasa Mai ya hau Kan lubna daga na fita massallaci na dawo ta kulle k'ofar zata kasheta ya fada cikin rawar murya

Naso na juya inda akwai tabarya a hannuna ko muciya na jefa masa sanin ba komai a hannuna mahaifiyata na biye dani yasa ban juya ba,Koda na fita palon jiki a sanyaye mahaifiyata ta biyo bayana mmn Iman kuwa sai jijjiga Mimi take tana kallona.

"Ammi ta fito tana dafe kwankwaso tana na karyata,har lokacin mahfuz bayani yakewa mijin mmn Iman dake ta Masa fada ce Masa yake yazo ya taimaka Masa ya Kai Hadeeza asibiti kar ta karasa mutuwa,mijin mmn Iman yace haram baa motarsa ba ya dauka mahfuz mutum ne mai hankali da sanin darajar Aure Ashe haka yake ya fito daga d'akin a fusace yacewa mmn Iman tazo su wuce su tafi ya kalleni cikin tausayawa Yana "Kiyi hakuri Lubna wlh bai kyauta ba bai kyauta ba koma waye dole ya dauki mataki yaci mutuncin Aure ya fita a fusace.

Sai a lokacin kukan da nake dannewa ya kufcemin na rufe fuskata na fara kuka mahaifiyata ta tsugunna a gabana itama idonta cike da kwalla mmn Iman itama ta tsugunna a gefena ta fara k'ok'arin rike hannuna dake ta zubar jini naga tsumma a hannunta kila so take ta dauremin itama sai hawaye take tana rike hannuna na fusge a fusace cikin kuka ina "kinsan komai mmn Iman,kinsan budurwar sa ya kawo min cikin gida Baki taba fadamin ba Kika sa na Zama shashasha na ringa hidima da ita,Mmn Iman idan nice bazan miki haka ba"
Ban bari tayi magana ba na cigaba da rusa kuka itama kukan yaci karfinta dan har ga Allah taso ta fada mata a ranar da taga mahfuz ya tsaya nesa da gidan Hadeeza taje ta same shi ya dauketa suka tafi a ranar tsananin mamaki yasa ta kasa tabuka komai,anan ta Kara tabbatar da zargin da take akan Hadeeza ba dan Allah take zaune da lubna ba taso fada mata amma batasan ta hadata fada da mahfuz hakane yasa ta bata shawarar ta sakawa hadeezar ido ta daina sakar mata fuska.

Kasan makoshi mahaifiyata t???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ace "Lubna bansan abinda ya faru ba kenan"

Na dago cikin ihun kuka na hau dukan kirjina Ina "Mummy har cikin gida ya kawo min budurwar sa yace min kanwar abokinsa ce wani abu tazo yi mummy na yarda dashi,ya kawo min budurwarsa har cikin gida nake bauta mata har daki nake Kai Mata abinci mummy abinci ma sai ta zabi Wanda take so zan girka mata mummy da zuciya daya,bai tab'a yimin shopping ba amma sabida zuwan budurwar sa gidanan yayo siyayya Mai yawa Ina murna nice har da Masa addua,sau tari inasan abu haka nake hakura duk a tunanina bashida kudi,bana ma iya tambayar sa komai mummy,iya k'ok'arina haka nake yi dan na kyautata Masa,wani zubin na samu canji da kudina nake siyan Naman Miya duk dan Miya tayi zaki yaji Dadi,ko yanka daya bana ci har sai ya dawo yaci san ransa kafin naci sauran mummy amma tunda ya kawo budurwa sa ya tsiri siyo nama balangu duk a tunanina budi ya samu,ya bani dubu biyar kudin kunshi da kitso ya bawa budurwarsa Dubu ashirin,mummy ya kawo budurwar sa gidana tazo ta gane min sirrina su ka maidani shashasha tunda tazo gidanan ya daina kwanciya da wuri,sai yacemin kallon ball zaiyi ya ringa sakamin magani a lemo duk dan nayi bacci da wuri ya tafi d'akin ta yaje ya kwanta da ita,duk hotel din garin nan bai gani ba,ya kawota gidana yasa na ringa hidima dasu mai na Masa dana cancanci haka daga wajensa mummy Mai na Masa"

Na Kara fashewa da kuka.

Naji muryar Ammi daga d'akin dan komawa d'akin tayi mahfuz ya kasa fitowa "kaje ka dauki yarinya nan ka kaita asibiti karta mutu fa kanta na ta zubar da jini dan ubanka na biku naga likita dan yarinya nan ta karyamin kwankwaso.

Ammi bari na Nemo abin hawa Kamar ta suma

Duk Ina jinsu idona ma na kan k'ofar ya daga labule kad'an ya lek'o ya koma da sauri
Ammi ta hankado shi waje tana "dalla wuce muje ka Nemo abin hawa"
Bango ya fara bi Yana kallona cikin wani irin speed na daka tsalle na sha gabansa na cakumo kwalar jallabiyarsa cakuma bana wasa ba nace "Bani takardar sakina dan kutumar ubanka kafin ka Kai karuwarka asibiti tsinanne laanane Allah ya tsine maka albarka"

"Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Wai dama haka yarinya nan take dama Yar dabba ka aura wai"?

Ammi tace cikin masifa

Mummy tace "Yanzu abinda Zaki ce kenan Aseeya danki yayi wa yata irin wanan cin amanar bazaki Masa fada ba shine kike Kiran Lubna da Yar dabba"?

"Ina ganin ikon Allah fadan uban me zan Masa bayan urban dukan daya sha a hannunta har ni bata kyalle ba,ni ban yarda budurwarsa bace azaba ta sha shiyasa ta amsa laifin da ba nata ba dan Sam bata gane Hadeeza ba sabida kamaninta daya canja.

Hannuna a shake da wuyar mahfuz da hannu biyu Jin abinda Ammi tace yasa na kalleta cikin tsananin takaici Ina "Taya Zaki yarda budurwar sa ce bayan ta baki abin duniya kin Sha atamfa da mayafi da kudi,ta Ina Zaki yarda kin haifo asarare dan iska dan wuta,taya zaki taba yarda"

Lubna mahaifiyata kikewa magana haka"?

"Gutsun uwarka da ita nake ka sakeni"

"Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Mahfuz agaban idonka take zagina tana gayamin magana dama Kai dan iskane yanzu kyautar da yarinyar nan tazo tamin zuwa kayi ka fada Mata"

"Wlh aa Ammi bansan yanda akayi tasani ba"

"Allah ya Isa tsakanina da Kai mahfuz Allah ya tsine maka albarka

"Wlh ka gama da Yar iskar yarinya nan a yau zaka saketa na rantse da Allah"

Sake shi Lubna kinji"

Mummy tace na girgiza kaina na Kara rik'e rigarsa Ina "wlh tallahi sai ya bani takarda ta"

"Mahfuz bata takardarta yanzu Nan kafin na tsine maka"

"Ammi bazan iya sakinta ba wlh inasan ta sharrin shaidan ne bansan Mai ya hau kaina ba nayi Mata ba daidai ba ki tayani bata hakuri Ammi ta cikani Kar Hadeeza ta mutu"

A wanan gabar na hau Kai masa duka a kirjinsa da karfi Yana k'ok'arin rike hannuna Ina "wlh sai ka sakeni na gama Zama dakai mahfuz ko a lahira bana fatan na ga Mai iirn fuskarka"

Lubna dan Allah kiyi hakuri

Mummy ta janyeni dak'yar daga gabansa Ina rsntsuwa sai ya tsinemin

"Wlh indai ni na tsugunna na haifeka sai ka saketa a yau dinan ba iya duka abin nata ya tsaya ba har da cin mutuncina da zagi tace Ina da kwadayi ni da nake mahaifiyarka ka saketa kafin na maka Baki"

"Wlh bazan iya sakinta ba Ammi ni na Mata laifi wa kikeso ya kular min da mimi ko wata daya batayi ba taya Zan rabu da ita"?

Hakan dayace ne yasa nace "idan mu hadu a kotu ka bani takarda ta"

Nayi daki a fusace banida lokacin d'aukar komai iya hijabina kawai na sako mahfuz a gigice ya hau bani hakuri Ammi na dura Masa zagi mummy kuwa ta karbe Mimi daga hannun mmn Iman dake sharar kwalla hakan da nagani ne yasa nace "mummy bashi yarsa bazan shayar da ita ba ya kaiwa budurwsa ta shayar da ita Mimi jinin mahfuz ce banasan naga wani abu daya danganci mahfuz"

Gwallo ido Mummy tayi tana mimin Zan ajiye Masa yarki ce fa"

"Yarsa mummy kaddara tasa ta tsago jikina ta fito ki basa yarsa mu tafi"


"Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun lubna ki rufamin asiri karki min haka"

Mahfuz yace hankalinsa a balain tashe "Mama ki tayani bata hakuri mmn Iman ku tayani bata hakuri"

Tsaki nayi na fice duk da zuciyata kuka nake na rabuwa da yata da nake satar kallonta zuciyata a bushe take bana jin komai.

Ina jinsa Yana bina ban kallesa ba Ammi kuwa sai masifa take tana a bata mimi ai tana da nonon zata nemi mai bawa Mimi nono.......


Duk wacce tamin sharing Allah Yana kallonta
Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba>??

Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali
Ina masu pimples
Tabo(spot)
Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance
Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai>??? @&?duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba

Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki

Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu

Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself
100%tested nd trusted

Soap price:3k
Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free

Maiso kindly message 08062991549
Call 08064532391

Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai=?O?

Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta=?O?adade anayi sai gsky>?-?>??

Mg's skincare


*Bm*
*Na Sadnaf*

*Page 14*

Hijabina ya ruko Yana "Lubna ki rufamin asiri karki min haka ni na miki laifi ba abinda mimi ta Miki ke uwace yarinyar nan har yanzu bata Kai wata daya ba Kika barmin ita kin zalinceta"

Ban saurare shi ba na cigaba da tafiya ina Jin tafiyarsu a bayanmu Ammi sai kwalla mai Kira take tana ya dawo ya Kai Yar mutane asibiti ya karbi Mimi ya kawo ta goya ta.

Machine mai kafa uku da nagani yasa na mika hannu na fara tsayar dashi,har lokacin Mahfuz na rik'e da Hijabina

Ganin na tsaya yasa ya sha gabana

"Dan Allah lubna namiki ba daidai ba nasani ban kyauta miki ba wlh har da sharrin shaidan"

"Ai Kaine shaidan din Mahfuz wlh da kasan abinda nakeji a zuciyata game da Kai da ko kusa dani baka matso ba ka bani hanya na wuce idan mu hadu a kotu sai ka bani takarda ta domin ni lubna nagama zama da mazinaci dan iskan dan Haram, budurwarka har cikin gida mahfuz ka siyo maganin bacci kake zuba min a lemo sabida nayi bacci kaje d'akin budurwar Ina matarka ta sunna kake sakamin magani a lemo,Mahfuz Allah ya tsine maka albarka wlh bazaka gama da duniya lafiya ba,ka bani hanya na wuce"
LUBNA wani irin bangaje shi nayi na shige Ina Zama mummy ta karaso da Mimi a hannunta Mmn Iman sai hawaye take tayi tsuru tsuru tana kallona.

"Mummy ki bashi yarsa ya bawa budurwar sa ta shayar da ita mummy banasan na budi Ido naga wani abu daya shafi Mahfuz wanan yarinya jinin mahfuz ce dagaske nake mummy idan har Kika matsamin sai na shayar da ita mumy bazanje gida ba sai na hakura da zuwa gidan"

Nacewa mummy data fara k'ok'arin Shiga Napep din.

Da alama mamaki na bata dan Ido kawai ta zubamin tana kallona

Ko kad'an bata tab'a kawowa haka Lubna keda zuciya ba.

Tana k'ok'arin Magana na fashe da mugun kuka Ina Mummy ki bashi yarsa mu tafi bazan shayar da ita ba"

"Mama dan Allah dan annabi ku rufamin asiri nasan na muku laifi mummy ba Wanda yafi karfin shaidan ke uwace inasan Lubna wlh azal ne ya hau kaina idan bata shayar da Mimi ba wa zai shayar min da ita,dan Allah"

Ganinsa da Jin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login