Showing 51001 words to 54000 words out of 155577 words

Chapter 18 - BUDURWAR MIJINA BOOK COMPLETE BY Sadnaf.doc

Sadnaf   

07 Nov 2025

2779

ne taya zata kulle gidan Taki bud'ewa.

Gajiya yayi da kiranta a waya ya cigaba da bugawa sai gashi shine har Sha biyu na dare a waje, ransa ba karamin b'aci yayi ba shi da gidansa zata kuleshi a waje...


LUBNA


Gobe Ina da dan uzuri zaku iya jina late sosai idan ban samu ba ayimin hakurin jibi dan Allah ngd


Yanzu Kuma wayafi laifi Lubna ko mahfuz>??>?? nidai da take bani labari na dan bata rashin gaskiya
Mg's cakes nd more
For the lovers of cake,Ina masu biki ko suna ko wani shagali na musamman ko dan jin dadinku da morewar ku ko kuma akwati kuke Shirin ansa zaku bayar matsayi tukwaici,tofa nesa tazo kusa domin kuwa zamu tabbatar mun fidda ku kunya mun kuma gamsar daku da hadaddun abubuwa kamar su,cake nd cupcakes,meat pie,fish roll da kuma egg rolls,to me ya rage muku ai kawai ku tuntube mu ta number nmu kamar haka 07067210195,08062991549 cika alkawari shine taken mu,adade anayi sai gaskiya




*WANAN NOVEL DIN NA KUDINE BIYA 500 zuwa 2029764071 first bank nafisa Nuhu sai a tura shaidar biya zuwa ga lambar Nan 08033719070 ko katin mtn mutanen Niger Airtel Kika min SHARING bansanki ba Allah Yana kallonki na barki dashi*


*Page 20*

Lubna

Koda na Kira Mummy na fada mata fitar da mahfuz yayi da girkin da na masa yaki ci cikin kuka na Kara da "mummy wlh mahfuz a yanzu baya sona hankalinsa ba'a kaina yake ba, shiyasa nace miki bazan dawo ba wlh dan biyan bukatarsa ya dawo dani, yau kwana biyu da dawowa gidansa har ya fara fita wajen budurwarsa wlh abinda na dauka a baya bazan iya dauka ba yanzu, tun daga lokacin da na kamashi da budurwarsa ya fice min a rai mai kaunarka bazai tab'a maka haka ba dan haka wlh mummy bazan iya zama ba zan hakura da aurensa yafimin alheri"


"Shikenan Lubna mijinki bazai fita ba sai kice zance yaje?wai wanan wane irin abune kinfi so tun kina karamarki a ringa kirga miki aure? Kin isa ki canja abinda ya faru ne? Idan kina haka zai goge abinda ya riga da ya farune?,shikenan dan kin kama shi da laifin cin amanarki duk wani motsi ko fita da zaiyi cin amanarki yake"? Lubna bazaki ki kwantar da hankalinki ba ko?bakya Jin magana ko?kinaso ki nuna ban Isa dake ba ko?to ki kashe auren naki tunda bazaki iya zama ba "

Kit naji ta kashe wayar.

Nabi wayar da kallo hawaye na zubo min mummy ta kasa fahimta ta ta kasa gane halin da nake ciki,duk abinan da mahfuz yamin taya zan iya mantawa da wuri,har na iya sakin jikina dashi,ko zan saki jikina dashi sai na tabbatar da rabuwarsa da Yar iskar budurwar sa da ni nasan bazai iya rabuwa da ita ba idan har yasan bazai iya rabuwa da ita ba ya aurota ya sakeni,dan bazan tab'a zama da Hadeeza da Sunan kishiyata ba,ko fitar da yayi ban yarda abinci yaje nema ba nasan wajen Hadeeza ya tafi,idan har Yana Sona dan nayi fushi akan abinda yamin,bai Kamata yayi fushi ba har yak'i cin abincina.

Haka bakin ciki ya cikemin zuciya Ina kallon agogo har tara ta wuce ko uwar abinci yaje ci yaci ace ya gama ci ya dawo idan ba wulakanci ba da Rana ai da yayi zuciya da abincin zuwa yayi ya dafa bai fita nema ba.

Tara da rabi na wucewa na mik'e naje na kulle k'ofar ba inda yaje sama da wajen Hadeeza dan me ya matsamin na dawo bayan Yana tare da ita.

Na dauki Mimi muka Shige daki muka kwanta ni kadai nasan bakin cikin da nake ciki,mahfuz ya Raina min hankali.

Ina kallon agogon har goma ta wuce da minti goma anan na yanke sai dai ya koma wajen Hadeeza ya kwana amma ko ya dawo bazan bude masa kofa ba Kuma sai ya bani takardar sakina ko yanaso ko bayaso gwara ya sakeni yaje ya karata,idan ya ga dama ya auri Hadeeza idan yaga dama ya kawota gidan ta zauna na dindin din wanan matsalarsa ce amma matsawar Ina amsa sunan matarsa ina zaune a gidanan wlh sai dai ya zabi Hadeeza ko zama dani tuna duk abinda nayiwa mahfuz daga lokacin da muka hadu zuwa na aure shi nayi hawaye ya hau zubomin,na tuna akwatin Aurena da ba kayan arziki ya zuba min ba haka kawayena sukayi tayi dani,ko damuwa banyi ba dan Ina kaunarsa,duk wani abu Kuma da nayi da mukayi Aure rabin hidimar mummy ke bani kudin dan duk wata inta dauki albashi haka take binmu da kudi ba iya ni kadai ba dani da Zainab dan tana d'aukar albashin da yawa gashi dagani sai zainab da yayata da nake bi.


haduwata da mahfuz yasa ban cigaba da karatu ba dan yace kishine dashi,haka nake zaune sai mummy ce ma take cemin na bari idan na haihu zata bani jari na kama Sana'a,ban tab'a b'atawa mahfuz rai da gangan ba,duk wani abu da nasan Mahfuz naso Ina iya k'ok'arina na Masa koda ni banaso amma sakayyar da mahfuz zaimin shine ya kawomin budurwarsa har gida ya munafirceni,ya fifitani akanta ya Kuma Sakani hidima da ita,dan Nagano shi nayi fushi shine zaiyi fushi shima,Mai amfanin zama da mahfuz, mutumin da hankalinsa ya koma kan budurwarsa da taki aurensa sabida bashida abin duniya,banma san Yana da rufin asiri ba sai da budurwarsa tazo gidan har ya iya bata Dubu ashirin kudin kitso da kunshi,har a yanzu dubu ashirin a dunkulle bai tab'a bani ba.

Na kara kallon agogon naga goma da minti talatin da biyar adaidai lokacin da naji bugun kofa na maida idona na rufe dan dagaske so nake ya kwana a waje idan gari ya waye yayi zuciya ya bani takardar saki na.

Duk bugun da yake Ina jinsa har Kiran da yake min a wayata da nasaka a silent.

Idona biyu bai fasa buga kofar da Kiran?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? waya ba har daya na dare yayi.

Haushin karnuka kawai nake jiyowa a waje burina ma su cije shi buga kofar da naji ya daina na tsawon mintuna yasa na bud'e idona,wayata dake ta kawo haske na leka naga mummy ce take kirana,da sauri na mike zaune na daga wayar

"Lubna yanzu mijin naki Kika kulle a waje innalillahi wa Inna ilaihi rajiun dama haka kike a yanzu na tabbatar da kina da matsala a yanzu na yarda akwai mugayen Abubuwan da kikeyi dayasa yarinya nan ta d'auke masa hankali wlh idan baki so naci ubanki kije ki bud'e Masa kofar nan"

Kuka nasaka Ina k'ok'arin Magana ta kashe wayar.

Na duro daga kan gadon nayi waje a fusace na bud'e k'ofar na ja da baya Ina jiran ya shigo.

Sai daya dade kafin naji Yana kokawar shigowa da machine dinsa.

Ina tsaye har ya shigo fuskarsa a balain had'e,kamar yanda nima nawa yake a had'en.

Yana saukowa na fara shakar kamshin turaren Hadeeza daya saka kirjina wani irin bugawa na tabbata ko hauka nake ba'a hayyacina nake ba idan naji kamshin turaren Hadeeza nasani.
Dagaske mahfuz wajen Hadeeza yaje daga dawowa ta bai ma iya daga kafa na kwana biyu ba tunda na hanashi kaina gwara yaje wajenta ta bashi,nama bashi yaje wajenta ballantana yanzu da na hanashi.

Wani irin zafi naji kirjina namin daya kusanto wajen da nake tsaye a fusace ban bari ya karaso ba na daka tsalle na isa wajensa na cakumo wuyan rigarsa sosai yake kamshin turaren hadeeza

"Bani takardar sakina mahfuz na balain tsanarka cutar da kayimin Allah ya Isa ban yafe maka ba bani takarda sakina mahfuz"

Wani irin fincike hannuna yayi daga rukon da nayi masa cikin hucci yace "Ni kikayi wa laifi amma zaki zo ki cakumi wuyan riga na kice na sakeki"

"Mahfuz mai yasa ka dawo dani gidanan bayan kasan bazaka iya rayuwa ba Hadeeza ba? yau Zan kwana biyu da dawowa amma mahfuz har ka koma wajenta idan har kasan kana santa haka Mai yasa ka dage min na dawo"?

"Ke fa dama idan Kika tashi haukarki bakya lissafi da tunani ni nace miki wajen Hadeeza naje"?

"Ko baka fadamin ba mahfuz ga kamshin turaren ta nan a jikinka ga Jan baki nan a kwalar rigarka dan Allah bakaji kunya ba Mahfuz na tsaneka ka sakeni kaje ka aurota idan Kuma dawo da ita gidanan zakayi sai ka dawo da ita mahfuz amma ni lubna na gama zama dakai ka rubuta min takarda ta mahfuz wlh na gama aurenka"

Nace cikin ihun kuka tare da Kara cakumo rigarsa Mara gaskiya ko a ruwa yake gumi yakeyi Ina cewa Yana kamshin turaren Hadeeza ya hau zare Ido,gumi na tsatsafo masa ya jawo kwalar rigarsa ya hau dubawa bai kalleni ba ya runtsa idonsa na cigaba da jijjiga shi Ina ya sakeni

"Ki yarda dani ba wajen Hadeeza naje ba abokina ne ya fesa irin turarenta yarsa da na dauka yasa na goge janbakin bakinta"

"Kutumar uban abokinka da yarsa baka ma iya karya ba mahfuz,yaushe maza suka fara fesa turaren mata mahfuz bana kaunarka bana San ganinka idan baka so na tara.maka jamaa ka bani takardar sakina gobe da safe na bar.maka gidanan kaje kayi duk abinda kaga dama da Hadeeza"

"Lubna dan sakeni dan Allah dan annabi karki manta dare yayi mu Shiga ciki muyi magana"


"Bazan sake ka ba sai ka bani takarda ta mahfuz wlh dak'yar nake numfashi sabida ganinka da nakeyi mahfuz ka bani takardata"


"Lubna na rantse da Allah bazan iya sakinki ba Ina kaunarki dan Allah ki tsaya mu fahimci juna wlh indai Hadeeza ce zan rabu da ita wlh sabida na faranta miki rai na canja layin wayata yanzu ma na saka layin ne dan na kwafi lambobi dan Allah kiyi hakuri ki cikani"


"Mahfuz idan kaga na cikaka wlh ka furta kalmar saki a gareni mahfuz yau kwana daya da wuni duk abinda kayimin duk baka ga girmansa ba daga dawowa ta ka Kara koma Mata,Ina san da kake min yake mahfuz ka daina yaudarar kanka,Hadeeza kake so ba lubna ba dan haka Zan hutashe ka ka bani takarda ta ka aurota ko kuyi zaman daduron duk abinda ka yanke yayi daidai nidai ka sakeni"

"Toh ki cikani mu Shiga ciki na rubuta miki"

Da sauri na sake shi yayi hanyar palo da sauri nabi bayansa Ina Jin kamar na shako shi dagaske ba abinda nake burin gani sama da takardar sakina

Muna Shiga palon ya shige d'akina na bishi har d'akin da shigarsa ya daki ya duka a kasa duk wani abu da mahfuz zaiyi yanzu bakinsa nake gani,ba abinda zai fadamin da zai Shiga kunnena duk rokon nan da ya ringayi na dawo ashe na munafirci ne daga dawowa ta ya tafi wajen budurwa bazan zauna mahfuz ya saka min hawan jini ba,ban damu da durkusawan da yayi ba na hau dube duben inda Zan samu takarda da biro,drawers din dake gefen mudubi na nufa da sauri,na hau watso da tarkacen ciki jikina sai rawa yake tamkar yanda na kamashi da Hadeeza zuciyata ta ringa Kuna haka nakeji a yanzu dan Koda bangansu a taren ba kamshin turaren da yake da dan janbakin gefen wuyansa ya tabbatar min da wajenta yaje babu ma ja


"Lubna dan girman Allah ki nutsu muyi magana Lubna ko kasheni zakiyi bazan iya sakinki ba Ina kaunarki lubna wlh sanki bai tab'a raguwa a zuciyata ba daidai da second guda"


A zabure na jawo drawer na jefa masa cikin ihu Ina "Karya kake Yi mahfuz da kana sona bazaka ci amanata ba,da kana sona bazaka kawomin budurwarka har gida ka ringa kwanciya da ita,da kana sona bazaka fifita budurwarka a kaina ba Ina matarka ka wuceni ka barni a gida kaje wajenta dan kawai na hana ka kaina bayan duk abinda kamin mahfuz,kwana biyu da dawowa ka Kara koma mata Ina San yake anan ka fadamin mahfuz ka maidani shashasha ka wulakantani kaci mutuncina ka nunawa budurwar ka banida wani matsayi a wajenka har gidanku ka kaita mahfuz sabida tsananin san da kake mata duk abinan daka min ka dage na dawo daga dawowa ta ka Kara komawa wajenta,Mai na maka dana cancanci haka daga wajenka mahfuz,dame na rageka da ka fifita budurwarka a kaina laifi ne dan na soka na aureka har yanzu ba muyi shekara biyu ba mahfuz"

Kukan da yaci karfina yasa na kasa cigaba da magana sosai nake Jin ciwon abinda mahfuz yamin

Zafin da kirjina yakemin yasa na dafe kirjina da hannu biyu bansan lokacin daya iso ba sai ji nayi ya kamkameni cikin rawar murya Yana "Baki rageni da komai ba Lubna wlh duk abinda ya faru sharrin shaidan ne bansan Mai ya hau kaina ba Hadeeza shuuma yarinya ce bansan ya akayi ta ja raayina har na kawota ba wlh ba wai bana kaunarki bane Ina sanki wlh Allah kiyi hakuri ki yafemin ki bani dama na gyara kuskure na nayi alkawari duk abinda kikeso shi zanyi a gabanki zan karya layin Nan da Hadeeza ta sani dashi"


Rashin kwari yasa bama zan iya kwace kaina daga rukon da yamin ba kamshin turaren Hadeeza da nake Shak'a a jikinsa yasa nake Kara Jin zuciyata na zafi


"Wane irin kalamai ne baka min kafin na dawo ba wane irin ban hakuri ne baka bani ba kafin na dawo daga dawowata mahfuz ka koma gareta mahfuz ka daina wahalar dani kana wahalar da kanka ka sakeni kaje ka zauna da Hadeeza dan Allah ka daina azabtar dani ka rabu dani na bar Mata kai duniya da lahira"


"Bani naje wajenta ba lubna ita tazo ta sameni a wajen da naje cin abinci"

"Shine ta danneka ta maka fyade ko mahfuz"?

"Dan Allah kiyi hakuri Lubna ki tausaya min ki kwantar da hankalinki"


"Kwanciyar hankalina shine ka bani takardata dan bazan iya zama da fasiki ba"


"Toh naji ki kwanta gobe da safe sai na rubuta miki"

"Bazan iya kwanciya ba sai ka bani mahfuz babban burina ka bani takarda ta"


"Wlh Lubna Zan rabu da Hadeeza duk abinda kikeso wlh Allah zanyi na Miki na farko na Miki na karshe idan kin Kara kamani da ko waya Ina Yi da ita nayi Miki alkwarin Zan sakeki"

Haukace masa nayi akan lailai sai ya sakeni,ya dage da magiya kaina danajin Yana baranazar rabewa biyu yasa na samu waje a gefen gado na zauna,

Yana k'ok'arin nufoni na daka Masa tsawa akan ya fice min daga d'aki.

Ya fita da sauri na koma na kwanta

Banida burin da ya wuce garin Allah ya waye na hada kayana,mahfuz ya Saba da Hadeeza ko min daidaita bazai fasa nemanta ba banga amfanin zamana dashi ba.

Sam bacci bai ga idona ba sai wajen karfe hudu bacci yayi awon gaba dani.


Mahfuz

So yayi tana bude k'ofar ko bai dauketa da Mari ba zai jijjigata har shi zata kulle a waje , sam dabaran Kiran mahaifiyar lubna bai fado masa na sai dayaga dagaske Lunbna ta shiryawa ya kwana a wajen hakane yasa ya Kira Aunty nurse duk da bashida tabbacin zata dauki wayar ga mamakinsa a kira na biyu ta dauki wayar bayan ya gaisheta ya fada mata kulleshi da lubna tayi a waje a san ya kara Kare kansa yace Mata abinci ya tafi nema kafin ya dawo ta kulle tunda lubna ta dawo take masa rashin mutunci jiya ma koroso tayi daga d'akin,daga yanda take sallati yasan ta fusata hakuri ta bashi akan bari ta Kira lubna Yana zaune ba dadewa yaji an bud'e k'ofar.

Ransa a b'ace ya shiga gidan so yayi ya zubawa lubna rashin mutunci Yana parking ya doshi wajen da take tsaya ga mamakinsa kafin ya Isa wajenta ta iso wajensa tare da cakumar rigarsa tana ya bata takardar sakinta haka kawai yaji gabansa ya Fadi har ga Allah inta furta sakin nan sai yaji hankalinsa ya tashi

Dakewa yayi ya mata martanin ita ta Masa laifi amma itace zata ce ya saketa


Kamshin turaren Hadeeza data ce yanayi da Jan bakin da tace Yana kwalar rigarsa yasa gabansa faduwa ya Kai hancinsa jikinsa ya kuwa shako kamshin turaren Hadeeza ya kuma ga jan bakin da bai san garin yaya ta shafa Masa ba duk wani kwarin gwiwar daya shigo dashi ya sace wani irin kunya ya lullube shi bazai yi saurin shiru ba ko yayane gwara ya Kare kansa

Hakane yasa ya yanko mata karya

Amma baiga alamar karyarsa ta Shiga ba hakane yasa ya yanke bata hakuri duk hakurin da ya ringa bata haka ta ringa botsarewa akan dole ya fito daga d'akin ya shige nashi d'akin duk hankalinsa a tashe, idan har baiyi dagaske ba zai iya rasa lubna bai Kuma shirya rabuwa da ita ba lubna ta riga da ta Zama Rabin jikinsa baisan Mai yasa baya iya danne kansa akan Hadeeza ba,Sam baiyi niyyar komawa Hadeeza ba tunda bashida niyyar aurenta zafin da lubna ta hada masa yasa ya kirata a waya gashi turaren da ta fesa ya tona Masa asiri ya zama dole ya Kira mahaifiyar lubna ya fada mata abinda ke faruwa ya Kare kansa

Haka yayi ta sake sake sallah asuba akan idonsa,sai a lokacin ya Shiga bandaki yayi wanka ya daura alwala ya fito a hankali wai Kar ma Lubna taji motsinsa.

Ana iddar da Sallah ya fito daga massallaci ya samu waje ya zauna ya Kira Aunty nurse a waya Yana Kira ta d'auka bayan ya gaisheta cikin marairaicewa ya hau bata labarin abinda ke faruwa a tsakaninsa da lubna ya hada rantswar shi bai hadu da Hadeeza ba tazo ta taimaka Masa ta bawa lubna Baki ya rantse ya rabu da Hadeeza.

Aunty nurse kuwa ranta ya balain b'aci da abinda lubna tayi inda ta bawa mahfuz hakuri akan tana nan zuwa"

Sai a lokacin mahfuz ya samu kwanciyar hankali ya koma gida karfe bakwai daidai sai ga sallamar Aunty nurse.

Mahfuz har kasa ya duka ya gaisheta yayi kasa da murya yana "Dan Allah mama banaso ki mata fada sosai so nake ki kwantar mata da hankali ta daina furta kalmar saki mutuwa nakeso ta rabamu mama,wlh Ina kaunarta bansan Mai takeso nayi ba na riga da nayi kuskure na Bata hakuri amma ta dage sai na saketa wlh na rabu da yarinya nan mama bansan Mai lubna take so na mata ba


"Jeka kiramin ita"

"Wlh tsoron zuwa d'akin nake mama"

A fusace Aunty nurse ta mike tana a wane daki take

Mahfuz yayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login