Showing 111001 words to 114000 words out of 137542 words

Chapter 38 - YAN ARABIC Book Complete By Layuza Kabir.doc

gafe ciki ciki nace " gata ".

Tasowa yai a hankali ya k'araso gaba na tare dasa hannunshi ya karb'e ta,ganin da yai na juya ina shirin fita yasa ya rik'oni,da sauri na kalleshi shima idon sa tsaf cikin nawa, kauda kaina gefe nai ina fad'in" meya faru kuma".

"Ki tsaya ina son muyi magana ne".

" amma ai ca kai kawai in kawoma ita".

"Eh na sani, amma don Allah kiban d'an lokaci muyi magana".

Bazan iya bijirewa umarnin saba don haka na juyo na tsaya kaina a gefe, kamo hannu na yai zuwa bakin gadon muka zauna,ganin yanda ya matseni sosai yasa na d'an matsa ,mirmishi kawai yai idon sa akan Babyn yana wasa da hannunta, ita kuwa idonta tsaf kansa,ta gefan ido nake kallon sa,yanda yake mata wasa yana kissing d'in ta.

Kusan mintina uku,sannan ya d'ago kansa gareni yana zama serious yace " Khadeejah! Shin yanzu Khadeejah bazaki iya afuwa gareni ba,bazaki sassauta min ba Khadeejah, nayi nadama nayi nadamar furuci na, ban san haka haihuwa keda dad'i ba Khadeejah saida Babyn nan tazo duniya duk bayan second's k'aunar ta k'ara tsanan ta take a zuciyata, don Allah kimin afuwa kinji ".

K'asa nai da kaina kawai don ban son mai rashin kunya domin nasan hukuncin hakan wajan ubangiji na,zafin zuciya bazai sani in fad'awa halaka,haka kuma ban shirya saukowa ba don haka shiru shine mafi alkairi daga magana.

Rik'o hannuna yai sosai cikin nasa yana k'ara matsowa jikina yace " k'unshin nan yai kyau sosai,da ina nan akayi zan bawa me k'unshin kyauta ta musamman. . . shafawa hannuwan yai tayi yana yaba k'unshin.
" shike nan tunda baza kiyi magana ba, daman kan batun sunan da za'a sawa Baby ne,shin kinada sunan da kike so a samata ?".

Girgiza kai nai kawai,yace "babu?".

Nace " Eh ".

" To daman tunda aka haifeta araina naso saka mata sunan mama na wato Ruk'ayya,hakan yayi miki".

Gyad'a kai nai ina fad'in "Eh yayi,Allah ya raya min ita ".

Cikin mamakin furucina ya kalleni nad'an sakwanni sannan yace " Allah ya raya miki ko ya raya mana".

Ban kalleshi ba na mik'e tsaye da fad'in "Bari na sauka nabar jama'a".

Bina yai da ido harna fice abuna

Girgiza kansa ya shigayi yana mamakin wannan shiru shirun dana koya a gareshi, shi wlh yanzu bashida matsala face ita, haihuwar ce daman bai so kuma yanzu yaji yana k'auna k'arshen ransa to menene kuma matsalar tunda daman akan ta suka sami sab'ani yanzu ai komai sai ya daidaita su had'u suyi rainan y'ar su cikin so da k'auna. Ya dad'e yana sak'awa da kwancewa daga baya ya zame ya kwanta yana kwantar da Babyn a k'irjin sa,a haka bacci ya d'auke shi.



Tunda na sakko k'asa mukaci gaba da hira da jama'ata amma rabin hankali na duk yanaga y'ata,musamman danaga lokaci yayi tsayi har awa guda da saukowa ta, nan duk idona ya koma ga stair's d'in ina jiran sakkowar sa amma har awa biyu lokacin na kalli agogo sha d'aya dai dai tun k'arfe tara kuma nakai mai ita, tabbas kunya da kawaici au kad'ai ne sukai min Katanga da tashi zuwa d'auko abata, sabida ko dai dai da minti guda banso in wulga idona ban ganta ba kusa dani.duk da bazan nuna hakan a zahiri wani ya fahimta ba amma zuciyata zata kasa sukuni kuwa.

Sha biyu dai dai kowa ya tashi daga hira don kwanciya,amma nikam ko baccin ma banji,Goggo ce tace " To yau dai da alama jinjira wajan Baban ta zata kwana tunda gashi har yanzu bai sakko da ita ba".

Yaya jummai tace "hhhhhhhh komai dare zaki ga ya kawo ta wuyar ta ta buk'aci nono ai, k'ilama bacci ne ya d'auke su amma data farka zata nemi uwar ta ai".


Daga haka naga kowa na k'ok'arin kwanciya, tashi nima nai zuwa d'akin jegon mu zuciyata ba dad'i, toilet na wuce na gyara jikina nai brush na fito sannan nai shirin bacci cikin doguwar rigar bacci me laushi wadda ta sauka har k'asa ,batada hannu sai d'an siriri,gabanta duk botir ne ajere har zuwa wajan ciki, d'an turare na goga na haye gadon da addu'a kan bakina.



Tunda na kwanta ko sau d'aya bacci baizo idona ba,yayin danaga sauran jama'ar d'akin sun bud'e baki sunata bacci harda minshari abinsu.

Duk motsin agogo na kan idona har wajan k'arfe biyu saura ji nake kamar in tashi inje in d'auko abata.
Can nakejin kamar sautin kukan ta na k'ara kasa kunne sosai kafin in tabbatar naji an bud'e k'ofar fatima ta shigo idonta cike da bacci take fad'in" Aunty kinga kizo Baby ta tashi gata can hannun Abban ta,muna kwance a parlour kukan ta ya tadani yace in kiraki".

Tashi nai nabi bayan ta muka fita,ina fita parlourn naji yanda take tsanyara kuka har cikin raina,da d'an sauri na na k'arasa ya mik'o min ita yana fad'in "yanzu ta farka kuma da kuka,bacci ne ya d'aukemu tun bayan fitar ki".

Ban tsaya sauraran surutun da yake ba na juya zuwa d'aki don kukan da take har tsakiyar raina nakeji.


Da sauri na d'auko ruwan zamzam d'in ta nai bisimilla ina samata fidar a baki ta fara shan ruwan da sauri saurin ta, daga nan na b'alle botir d'in Rigar na fara bata nonon cafka tai ta fara sha na lumshe idona ina k'ara rungume ta a jikina,wani sanyi na ratsa zuciya ta,ji nake kamar tai shekara bata wajena,ta dad'e tana shan nonon na canja mata wani shima saida na Tabbar ta k'oshi sannan nasata a kafad'a ina shafa bayan ta can naji tai gyatsa ,sauko ta nai na cire mata rigar jikin ta har pampas d'in na canja mata wasu, zuwa lokacin harta koma baccin, bayan na kwanta na sata jikina inajin wata nutsuwa na ratsani daga nan bacci me nauyi ya d'auke ni.






*TAKU* *CE* *Y'AR* *MUTAN* *JA'OJI*A???
??1]??1]??1]??1]??1]??1]
??-\??-\??-\??-\??-\??-\
*'YAN* *ARABIC*
??-\??-\??-\??-\??-\??-\
??1]??1]??1]??1]??1]??1]

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_
_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd


???a???_%??]IqkpHq??Fq?p? ?]Iq??
*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*
??Qd
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _lentertain_ _our_ _Readers_




0(???5(???2(???





Tun sassafe gida ya fara kacamewa da hayaniya, hidima kowa keyi, nikam ina d'aki cikin adona me sauk'i na atamfa super riga da zani,sai babyn da akaiwa wanka itama cikin kayan sanyi don da sanyin safiya garin.
Sweety ce ta shigo da gud'a tana fad'in "Broth ya biyani,ya gama min komai wlh,yayiwa sweet mom d'ina takwara kuma nima yayi min,shiyasa tunda akai haihuwan nake tambayar sa me sunan Babyn yak'i fad'a min nace zan bada ai mata calander ne yace ya bada ayi komai duk don yana son surprise d'ina,tnx tnx my broth".

D'aukan Babyn tai ta rungume ta tsam" Allah ya raya mana ke namecy yayi miki Albarka".

Kowa dariya kawai ke mata, ta jiyu tana kallona da kashe ido cikin tsokana tace"Em Aunty na naga wannan gidan naku baku bani d'aki ba sabida ba'a buk'ata ta,amma yanzu kam dole zanya kaina d'aki don inyi rainon sweet daughter ".

Dariya nai ina fad'in" hakan shi zaifi min dad'i wlh,ki kwaso kayan ki kawai".

Y'ar dariya tai tace tom "Tom yanzu me zamu rink'a kiran ta".

Kafin nai magana Aunty Amrah tace " Ai zab'i na gareki maman Baby ".

Farrr tai da ido cikin tsananin farin ciki da nishad'i tace " em mu rink'a kiran ta little ko Aunty na ".

Mirmishi nai ina fad'in" banida zab'i fa sweety duk yanda kukai".

Sauran y'an d'akin suka amsa mata da yayi, don haka ta juya cike da farin ciki ta fice.



Taro yai taro zuwa azahar gidan nan namu babu wajan aje k'afa aji dad'i, jama'a damk'am ,kowa barka barka,anyi hidima anyi yanke yanke ,anci ansha an raban kayayyaki ,sosai ga calendar, stickers memo,key holder abubuwa sosai aka raba, Duk hidiman da ake Abba shima yana can parlourn sa da mutanan sa suna waleema,haka uban gayyar,abokan sa kamar mata haka aka rink'a taron nan dasu,masu hotuna da video tako ina d'auka suke,abun yayi,ni kuwa sabida d'inki na ban wani zirga zirga,ina zaune main parlour yanda kowa yazo zai ganni sai dai in zan canja kaya nake tashi, pic's ma da k'yar naje aka yiyyi dani, na sake da UK anata mana hotuna ina fara'a ta kamar ba komai tsakanin mu,Babyn sa kuwa yana manne da ita, har sai da wani abokin sa ya tsokaneshi "Oh abokina nan kaita kukan an had'a ka da y'ar Arabic an gama dakai,to sai gashi daga aure kai bilulun da ita harda ciki da haihuwa".

Dariya yai yana kallon sauran abokan nasa yace " Wato guys wlh ina baku shawara kuyi azama kuje ku nemo *y'an* *Arabic* d'in nan wlh sunfi ribar aure,duk wata ni'ima an tattarata garesu,nutsuwa da kwanciya hankali tana ga mijin daya auri ma'abociyar addini ga sanin sirrin so da iya sarrafa soyayya nan da nan ake kwancewa mutum k'ulli. . . . ???i

K'arashewa yai da dariya yana tafa hannu.

Suma duk dariyan suka sa wani cikin obakan yace "d'an iska yanzu ai saika daina yimusu gani gani tunda ka latsa kaji bauwar dake tare dasu,ni daman shiyasa nafi son auran mace maabociyar addini wlh,ba ruwana da wani kyanta ko wayewa,don haka don Allah ka fad'awa Khadeejah ta lalubomin cikin k'awayen ta nima inbi sahun mijin *'YAN ARABIC*???i".

????      

                  ! " # $ % & ' ( ) * + , - . / 0 1 2 3 4 5 6 7 8 9 : ; < = > ? @ A B C D E F G H I J K L M N O P Q R S T U V W X Y Z [ \ ] ^ _ ` a b c d e f g h i j k l m n o p q r s t u v w x y z { | } ~  ?
Duk Kansu dariya suke wasu na mama kin yanda duk d'abi'un UK ya canja tun bayan auransa .



Bamu muka sami kanmu ba sai bayan sallar magriba gidan ya sarara sai masu k'ara kwana Wanda suma sunfi jiya yawa.


Ruwa me zafi sosai na samu nai wanka na gasa jikina,sannan na had'a tea me kauri nasha,daga nan naji dama dama, Babyn ma wanka aka mata da ruwan zafin don sabida yawan d'auka jikin ta zai mata ciwo,amma da aka gasata da ruwan zafi zataji dad'i.


Da wuri bacci ya d'aukeni ban tsaya sauraran su da hira ba.


*********
Washe gari tashi ba sai wajan Tara,bayan nai wanka Goggo tasa aka shigomin da kayan abunci naci nai nak Alhamdulillah, sai a sannan aka shigomin da Little Ruky an shirya ta tun tuni cikin jan kaya masha Allah tai kyau tsaf da ita sai tsotson yatsa take,a hankali na janye yatsan a bakin ta nasa mata nono ,idona akanta ina k'ara jin son ta na shiga zuciyata, naji an turo k'ofan an shigo, d'ago kai nai don ganin waye,ganin sa tsaye ya harde Hannaye yasa na maida kaina k'asa, k'arasowa yai bakin gadon ya tsugunna tare da rik'o hannu na cikin nasa d'aya hannun kuma yana shafa kan Babyn,tsawon mintina muna a haka daga bisani ya nisa kana yace"my deejah barka da safiya". Tunda ni ban samu matsayin a gaidani ba.

Kunya kuma naji ta kamani amma saina basar ciki ciki nace "ina kwana".
Bai amsa ba illa kafeni da yayi da idanuwa,sannan yasa hannu ya d'auki little ya zauna bakin gadon yana mata wasa.

Minti biyar ya waiwayoni tare da tattara dukkan hankalin sa ya fara magana" Khadeejah tafiya ce ta taso min da asuba aka kirani, wai ana neman mu a Lagos kan company d'in mu,ina tunanin one week zamuyi mu dawo insha Allah, yanzu haka ana jirana k'arfe 11 jirgin mu zai tashi,ki kulamin da mama na da kanki, kiyi hak'uri dani ki yafemin laifukana".

Shiru yai na d'an lokaci sannan ya d'ora " akwai kud'i a d'aki na,duk abunda zakiyi kije ki d'auka, sannan idan bak'in mu zasu tafi ki sallame su.

Mik'ewa yai da Babyn a hannunsa yana yin hanyar waje,tunanin shi zan biyo shi yaga ba niyya,saiya tausasa murya yace "zo muje ki dawo da ita".

Ba musu na tashi nabi bayan sa,a parlour ya tsaya yaiwa jamaar da sukai saura basu tafiba sallama,suka bishi da addu'ar Allah ya kiyaye hanya.

Ni kuwa a kunyace na ratsasu na wuce.

Driver na hangomu ya tada mota, baya ya shiga ya zauna sannan ya rungume ta jikinsa tare da kissing d'in ta,miko min ita yai idonsa k'ir cikin nawa,yana jira yaga me zance. K'asa nai da kaina a hankali na furta " Allah ya kiyaye hanya ya bada abunda akaje nema".

Cike dajin dad'i ya amsa"ameen ameen dear,ki kulamin da kanki da mamana ".

Gyad'a kai kawai nai na juya shima driver ya tashi motar suka tafi.


Dana koma cikin y'an uwana hira muka bud'e yayin da masu aiki keta faman aikin naman hakika.


*******
Washe gari kowa ya koma inda ya fito ya rage gidan dagani sai goggona da Aslamiyya y'ar Auntyn mu da zatai hutu anan.duk sai naji gidan yamin wayam,donma Goggo me hira ce tana bamu labaran dariya dana mutanan da.



****
Bayan kwana biyar da suna UK ya kirani a waya sama sama muka gaisa ya tambayi y'ar sa nace mai tanan qlau daga haka na kashe wayan.


Munci gaba da wanka tsawon sati hud'u na murje nai kyau dani Little Ruky ma tai b'ulb'ul Masha Allah da ita,ga wayo tayi don yarinyar akwai wayo kullum idonta k'yar tana kallon kowa. Zuwa lokacin ya zama UK bashida wani aikin in yana gida sai na kula da ita,don yanzu inya dawo sai intai kuka kawai nake ganin ta ya kawomin ita inbata nono ya koma da ita,ganin irin kulawar da yake bata yasa zuciyata yin sanyi don dama akan ta ne gabar,amma dukda haka fa ban sakar mai kamar farko,sai dai yanzu zamuyi hira kad'an kad'an fuskata ba walwala sosai .shi kam hakan ma yamai dad'i yasan a sannu zamu dawo normal kamar da.

D'inki na ya warke ras jikina ya had'e yanda ake buk'ata,gashi daman banyi dogon jini ba duka sati biyu ya d'auke min don haka na dage na fara gyara kaina da kayayyakin da aka had'omin daga sakkwato, Goggo ma batai sanya ba wajan bani wasu sirrika daya kamata me jego ta kiyaye bayan d'aukewar jinin bik'i,Masha Allah ni akan kaina inaji na zam zam duk da daman bawai na bud'e bane tunda bada kaina na haihu ba.


Watan mu biyu cif Goggo ta fara shirin tafiya gida,don daman mun dagene ta zauna mana har zuwa yanzu,amma tun muna ar'bain taso tafiya. Siyayya sosai UK yai mata na tsaraba hakama Abban su ya bada kud'i akai Mata siyayyan tsaraba,duk na shiga damuwa sabida ba k'aramin shakuwa da sabo bane ya k'ara shiga tsakanin mu, gashi d'aki guda muke kwana a k'asa ko yaushe muna tare, naso nabita ma muyi yawon ar'bain yayyena maza da basu gantaba in kai musu ita amma danaiwa UK maganar yace gaskiya bazan tafimai da yarinya har sakkwato ba tana wata biyu in bari inta k'ara k'wari da kansa ma zai kaimu, banso ba haka na hak'ura.


Daran da Goggo zata tafi mun raba dare muna hira har bayan sha biyu muka kwanta .

Kiran sallar farko naji ana mana knocking door, da mamaki nace " waye?".

Cikin muryar bacci naji yace "Khadeejah bud'e nine".

Tashi nai ina mutstsika ido na bud'e don nai tunanin ca zai in mik'o mai little don haka na d'auke ta nasa a kafad'a na fita,tsaye na ganshi yanata safa da marwa tsayawa nai a bayansa ina fad'in" lfy?".

K'arasowa kusa dani yai yana fad'in "lfy qlau ina Goggo?".

Nace " bacci take".

Yace "ki tasheta ki had'a kayanki kema yaya yai min waya yanzu wai an mai waya daga gida umma batada lfy zakuje ku dubata gobe zaku dawo".

Zaro ido nai ina fad'in "innalillahi wa innailaihi ra'jiun,meya sameta kodai rasuwa tai kuka b'oyemin ?".

Rik'o hannu na yai ganin jikina nata rawa ya karb'i little tare da zaunar dani kan kujerar dake gefe na," ki kwantar da hankalin ki Nahna,umma tana nan da ranta wlh kawai ciwon ciki ne yaya yace min to har an kwantar da ita ma a asibitin tun jiya da yamma cikin dare aka mai waya,to suna son zuwa yau don haka yace zasu biyo su dau Goggo tunda daman yau d'in zata wuce,yace inba damuwa kema in barki Ku tafi tare,ki kwantar da hankalin ki yanzu kije ki shirya ana fitowa masallaci zasu biyo ku tafi".

Share hawayen daya gangaro min nai ina mik'ewa zuwa d'aki .

Tashin Goggo nake cikin kuka ta farka da salati take take tambaya ta meye ina matse ido nake sanar mata meke faruwa, salati ta d'auka da mik'ewa tana gyara d'aurin zani tace "Allah ubangiji ya jishshemu alkairi, wannan ciwon ciki kwana biyu ya matsawa Yaya,yi maza ki had'a kayanki bari inyo wanka da alwala".

K'aramin akwati na d'auko na had'a kayana set uku dana little a ciki duk abunda zamu buk'ata na had'a, idona yak'i yabar zibda hawaye don gabana ya tsananta fad'uwa kawai ji nake kamar b'oyemin ake kodai ummata ta rasu ne.


Goggo na fitowa aka kira asubahi da sauri nima naje nai wanka tare da d'auro alwala,a lokacin UK

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login