Showing 18001 words to 21000 words out of 137542 words

Chapter 7 - YAN ARABIC Book Complete By Layuza Kabir.doc

inda mata ke kare mahimmancin ilimin y'a mace su kuma maza suke kare rashin muhummancinsa duka cikin harshen Larabci,

Sannan aka fara sako k'asidun da suka yiwa Kansu na rabuwa da juna, da Wanda sukaiwa prover's da malamansu.

Abufa yayi abu inda akaita d'aukan pictures ana video,

Basu tashiba sai bayan la'asar inda kowa ya kama hanyar gida da mutanansa,
Sweety taiwa Nahna hotuna kamar me tare da video don duk motsin datai saita d'auketa har abin ya fara bawa Nahna dariya.

Yau kam cike take da tarin farin ciki wanda fuskarta take bayyana hakan.

Bayan sallar isha'i suna zaune a parlour su Ashraf Aunty Hafsah sunata bawa yaya labarin abubuwan da akai a skl d'in su Nahna shikam ya biye musu yanata fad'in Masha Allah, madallah,
Zuwa can ya kira Nahna cikin murya me cike da kulawa yace " Nahna daman ina son muyi wata magana dake me mahimmanci don haka da safe kafin na wuce office zan ganki kinji. . . . . . . "








Taku ce
Y'ar mutan ja'oji???j%??]?j
??1]??1]??1]??1]??1]??1]??1]
??-\??-\??-\??-\??-\??-\??-\
??-\ *YA'N* *ARABIC*??-\


*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*
%???

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_
_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd



??Gc *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

??Qd .
%?'[? ?Z?? ?W??? d??W??? t?k ????uc?t??, M?kti???t?? ?l?? ???lt??W?t?i?l ?kuW? W????????W??UB?? '[? ??

%?8[Kq?? %?'[? ?Zaku iya samun littafan mu a Facebook%?'[? ?? ???a???_
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION


??ad %?'[? ?Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu%?'[? ?? ???a???_
Zamaniwriterassociation.@gmail.com



Wannan page d'in naki ne (Fauzidadi) na bakishi kyauta kiyi yanda kikaso dashi, sabida kulawarki ga wannan novel, na jinjina miki yanda bakya gajiya da adanaminshi.
???a???_???a???_???a???_???a???_???a???_???a???_???a???_




0(???1(???2(???





Damm Nahna taji gabanta ya fad'i, dukda bata San me yaya zai fad'??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????a mata ba amma tasan me muhummanci ne,ga yanayin data gani a fuskar sa, a hankali tace To yaya Allah ya kaimu safiyar, mik'ewa tai cikin sanyi tai musu saida safe ta shige d'akinta .

Haka ta kwanta cike da tunanin cikin ranta har bacci me nauyi ya d'auketa.



Bayan sallar asuba tana zaune kan sallaya tana karanta azkar har k'arfe shida ta shafa addu'a ta mik'e tana k'ok'arin ninke prayer mat d'in taji muryan yaya a k'ofar d'akin yana mata magana, da sauri ta aje tai waje, zaune ta sameshi kan kafet ya mik'e k'afansa yana jan casbaha, a hankali ta k'arasa gareshi ta zauna tare da gaisheshi ya amsa fuskanshi d'auke da fara'a ,

" Nahna ya gajiyan taro kuma "

" Alhamdulilah yaya "

" To masha Allah"

Shiru ne ya biyo baya na D'an lokaci daga bisani ya nisa yace
" Nahna kiban duka hankalinki nan, magana ce me mahimmanci matuk'a zamuyi dake "

Dammmm taji gabanta ya k'ara fad'uwa,

" Nahna nasan kinsan Alh Usman kinsan alak'ar dake tsakaninmu dasu, Nahna kin Sani cewa ina tare da shi ne sabida kasuwanci dake tsakaninmu Wanda zuwa yanzu zumunci ne me k,arfi Tsakaninmu."


Numfashi yaja yana k'ara gyara zamansa,

Zuwa lokacin duk Nahna ta matsu taji me zai fad'i,

" Nahna wato wata magana ce Alh Usman yazomin da ita me girma , yana son ya had'a zuri'a damu, yazomin da zancan yana son in kin amince yahad'aki aure da d'ansa, Amma Nahna ba dole za'a miki ba amincewarki nake buk'ata, don Nahna ko k'arshen alak'ata da Alh usman kenan in biki aminceba,wlh bazan aurar dake ga d'ansa ba,kije kiyi shawara Nahna in kinga bakya ra'ayi ki sanar dani kinji, abinda yasa ma nai miki maganar don naga baki kula kowa ne ma'a babu soyayyar wani a zuciyarki ko?"

Ya k'arashe maganar da kallonta.

Cikin kid'ima ta gyad'a kai tare da fad'in "eh yaya zanyi shawara ".

" To jeki ina sauraranki daga yau zuwa kwana biyu,amma fa karkiyi abinda zaki cutu kinji Nahna".


Tashi tai tana tafe tana had'a hanya ko gani batayi sosai don tsananin tashin hankalin daya ziyarceta, tana shiga d'akin ta fad'a kan gado tare da fad'in

"innalillahi wa'inna ilaihi ra'jiun, shin wace Masifa ce ke tunkaro rayuwarta,wane sabon tashin hankali ne wannan ,wai shin dama har yanzu UK bai fita cikin rayuwar taba , don tsananin masifa yanzu baya k'asarma amma har saida yabi k'wak'wk'wafin rayuwarta ya had'a da mahaifinsa da sunan yana son auranta kawai don ya cuzguna rayuwarta,wayyo Allah yanzu ina zatasa ranta ,kai wlh Sam babu abinda zatayi da UK matsayin mijin aure, baya cikin tsarin mazan da zata iya aura harta kai tai rayuwar aure dashi,".

Maganganu kawai taketayi cikin ranta tama rasa me zatai kawai saita fashe da matsanancin kuka Mara sauti.


Tsawon lokaci tana kuka me cin rai har bacci yai gaba da ita ,bacci Mara dad'i me cike da tunane tunane.


Bayan awa guda ta farka idonta yai mata nauyi sosai a hankali ta maidasu ta rufe bayan minti biyu ta k'ara bud'esu tana tunano abinda ya faru da ita ,sai taji gabanta ya fad'i rasss nan da nan idonta ya k'ara Kawo ruwa ,ta mik'e a hankali ta shige toilet tai wanka ta fito sanye da towel tana tafe tana Jan k'afa,k'arasowa tai gaban mirror ta shafa mai tare da d'auko riga doguwa tasa ba tare data tsaya yin wani kwalliyaba, don zuciyarta ba d'adi Sam, maimakon ta fita parlour don karyawa saita koma ta kwanta kan gadon tana dafe kanta dakemata tsananin ciwo.

Tunani take kala kala cikin ranta ta rasa ma ina zata tsaya ne . . .
Muryan Aunty Hafsah ta jiyo tana dafata
" Yadai Nahna tunanin me kike haka inata kiranki biki jiba,ko baki da lfy ne?"

Da k'yar ta tashi zaune tana mutsika ido tace " kaina kemin ciwo wlh Aunty, ban jinki ba sam"

"Ayya sannu tashi muje kici abinci kisha magani"

Badon taso ba ta fita, ba kowa parlour don Yaya ya fita office su Asharaf kuma suna skl, ta Shiga kitchen ta d'ebo abincin kad'an tare da ruwan shayi ta fito, cin abincin kawai take ba tare don tana jin dad'insa ba , Aunty Hafsa na gefe tana kula da duk motsinta.

Bayan ta gama Aunty ta mik'a mata magani tasha tana runtse ido, tace

"Aunty ya naga duk kinyi komai harda wanke wanke biki bari na fito ba "

" ba komai naga kina bacci ne yasa kawai nayi nasan akwai gajiya tare dake sosai , ga bashin baccin karatun exams da kika tarawa idonki".

Lumshe idonta tai kawai bata ce komai ba.

Cikin rashin jin dad'in ganin halin da take ciki Aunty tace " Nahna yayanki yamiki maganar d'an gidan Alh usman ko?"

Gyad'a kai kawai tai, Aunty taci gaba. " Nahna ki tsaida hankalinki kiyi shawara bawai dole za'a miki ba in kinga biki amince ba ki fad'i kawai kinji"

"To Aunty "

Daga haka tai shiru don bata son magana ko kad'an,
Ganin tai shiru yasa Aunty tace kije ki kwanta ki huta Nahna"


Mik'ewa tai ta shige d'aki ta fad'a kan gado zuciyarta ba dad'i .



Tsawon kwana biyun da yaya ya bata tayi tana sauraran taji ya kirata ya tambayeta meta yanke taji shiru , har kwana hud'u bai kirata ba.


Yau da dare tana kwance kan gado tanata sak'e sak'e aranta wai idan yaya ya kirata me zata ce, kullum dai addu'a take tana neman mafita gun Allah, shin wai dagaske UK sonta yake ko kuwa iskanci ne , ita dai tasan farkon ganinta dashi ya nuna mata samartaka daga baya kuma data nuna mai bata ra'ayi ya shiga gasa mata azaba da wulak'antata gaban mutane kuma yanzu yazo da wani zance kodai wulak'ancin da yai matane bai isheshiba zai aureta yaci gaba dayi mata, koma dai mene ne ai tana fad'awa Allah wani tunani ne ya fad'o mata arai, saita saki wani d'an mirmishi tana jinjina kai.




Kuyi hak'uri da wannan don Allah???a???a.






Taku ce
Y'ar mutan ja'oji???j%??]?j
??1]??1]??1]??1]??1]??1]??1]
??-\??-\??-\??-\??-\??-\??-\
??-\ *YA'N* *ARABIC*??-\


*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*
%???

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_
_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd??Nd



??Gc *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

??Qd .
%?'[? ?Z?? ?W??? d??W??? t?k ????uc?t??, M?kti???t?? ?l?? ???lt??W?t?i?l ?kuW? W????????W??UB?? '[? ??

%?8[Kq?? %?'[? ?Zaku iya samun littafan mu a Facebook%?'[? ?? ???a???_
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION


??ad %?'[? ?Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu%?'[? ?? ???a???_
Zamaniwriterassociation.@gmail.com




0(???1(???3(???




Misalin k'arfe sha biyu na rana ina kitchen ina had'a abincin rana naji anata knocking k'ofa a hankali nace

" waye "

" Autar Baffa yayanki ne usman"

Tsalle na buga tare da bud'e k'ofan parlourn ina fad'in
" yaya Usman oyoyo"

Shigowa yai ciki yana dariya yace " wash na d'auko gajiya auta ina mutan gidan ko basa nan?"

" eh Aunty taje Unguwa yaya yana office Yara suna skl saini kad'ai, yaya ya Hanya ".

" Alhamdulillah Nahna kin ganni ba zato ko? Wlh Sakkoto na nufa mun sami Hutu, kuma sai muka biyo ta kano yiwa wani abokin aikinmu ta'aziya ,nace to bari in biyo mu gaisa".

" kai amma yaya naji dad'in zuwanka wlh, nima ina ganin cikin satin sama zanzo sakkoton".

"Um su Nahna graduate an girma sai aure kuma ko?"

Mirmishi kawai tai ta tashi ta shiga kitchen don kawo mai ruwa da lemo.


Bayan ta kawo mai ta zauna sunata hira yaya usman yace
" ki shirya kawai mu wuce tare "

Da sauri ta d'ago tare da fad'in "kai anya yaya zai bari kuwa?"

"Me zai hana ya barki tunda daman kina shirin zuwa"

"To ai kai yau zaka juya kuma ni sai nan da sati zan tafi kaga bai San da tafiyar tawa ba yau "

" OK bari in fad'a mai ma nazo"

Wayansa ya d'auka ya kira number d'in yaya Haroon bugu d'aya ya d'auka

"Hello Usman ya kake "?

" yaya lfy qlau ya gida ya iyali?"

"Duk kowa lafiya , ya wajan aikin naku?"

"Alhamdulilah, gani ma na shigo garin naku,nazo gidan sai Nahna kad'ai"

" ah da gaske usman?"

"Hhhmm Allah da gaske"

"OK ina Office amma zanzo gidan yanzu hafsa kuma tana Unguwa, amma ai ba yau zaka wuceba ko?"

"Eh to da dai naso wucewa yau d'in amma zan bari zuwa gobe."

"OK to ina hanyar dawowa."

"Tom sai kazo Allah ya kawoka lafiya."


Hira sukaci gaba dayi da Nahna yana bata labarin ya samu mata k'anwar friend d'insa a nan kano take don haka insha Allah da wuri za'ayi bai so a wuce 7 month.

Murna sosai Nahna tai tana tambayar sunanta yace " Amrah"

Nan yake k'ara bata labarin yana sa ran zai samu transfer zuwa Kano nan da 2 month don haka zai sai gida a Kano ya zauna kusa dasu.

Haba murna kamar me gun Nahna ta mik'a mai hannu suka kashe cik'e da k'aunar juna irinta D'an uwa da y'ar uwarsa.


Ana kiran sallar azahar yaya haroon ya dawo,nan suka rungume juna da yaya usman suka gaisa da cike da k'aunar juna sannan suka d'aura alwala suka wuce masallaci ,kafin su dawo Nahna ta shirya musu abinci tare da had'ad'd'an zobo.

D'aki itama ta shiga tai sallah tana zaune tana addu'a taji shigowarsu shafawa tai ta mik'e don ta had'a musu abincin.

A tare a flate d'aya ta had'a musu abincin duka sukeci suna hirar zumunci cike da nishad'i,nan yaya usman yake bawa yaya labarin ya samu mata zaiyi aure sannan zai samu transfer zuwa Kano don haka yace ya fara nema mai gida nan kusa zai siya, shima yaya murna yai ya godewa Allah sannan yace zai shaidawa wani abikinsa me saida filaye da gidaje ya samo mai.

Anan ma yaya usman yake cewa yaya ya bar Nahna su wuce tare yaji tana cewa zataje wani week d'in, yai Jim sannan yace to ta had'a kayanta su wuce amma sati biyu zatai ta dawo.


Bayan la'asar yara suka dawo daga skl nan sukaita murna dunga Auncle d'insu, basu jimaba Aunty Hafsa ta dawo itama da fara'arta suka gaisa da Yaya usman sunata barkwanci.


Da dare da wuri na kwanta bayan na gama parking kayana cikin trolley back,
Aunty ta lek'o taga ina bacci ta koma take shaidawa yaya nayi bacci, jawomin k'ofa datai yasa na farka jin tana cewa yaya nai bacci yasa na gane nemana yake, dammm naji gabana ya fad'i don nasan kan dai wannan maganar ne. . .

K'asa k'asa nakejin muryan yaya Haroon yana magana tsam nai da raina ina sauraran me yake fad'awa yaya usman.

" wato usman uban gidana Alh Usman ne yazomin da wata buk'ata kan Nahna wai yana son in bashi auranta ga D'ansa, to tun a ranar na fad'amai bazan tab'a yiwa Nahna doleba, amma zan shawarceta kan batun inji ra'ayinta, to nai mata maganar tsawon kwana biyar na bata lokaci tai tunani ta yanke shawara , amma sai bayan nai mata maganar kuma nake dana Sani don na lura tun lokacin kamar batada kuzari,ina tsoron kar in takurata, bisa ga alk'awarin dana d'aukarwa kaina da kuma mahaifinmu kan rik'e amanarta da kuma kaucewa duk abinda zaisata cikin had'ari."

Cikin mirmishi yaya usman yace " To yanzu Yaya Haroon shike nan Nahna bazatai aure ba don gudun damuwarta, ina tunanin zuwa yanzu ya dace ace ko Nahna ba'a mata aure ba ace dai tanada wani tsayayye amma fa ga yanda Aunty Hafsa ta shaidamin Nahna ko saurayi batayi duk nacin mutum akanta hak'ura yake ya barta, kaga ai dama wannan da zaka tsaida mata shi a mijin aure tunda ba tab'a yin saurayi taiba shi d'in bazai sha wahala wajan jawo hankalinta ba , sannan Abu na gama kaga dai irin tarin Alherin mutuminnan a gareka bai kyautuba karon farko daya zoma da buk'ata ka watsa mishi k'asa a ido, kuma me sonka aishi zaiyi sha'awar had'a zuri'a da kai."

"Wato usman duk alherin da Alh Usman yaimin bazan manta dashi ba domin kuwa d'an halak bai manta alheri,ammafa hakan bazai sa inyiwa Nahna dole akan auran d'ansa ba koda kuwa hakan zai Kawo k'arshen mua'malarmu dashi,sannan wani abu Nahna fa bata tab'a ganin yaronba inba a hoto ba, koni bai wuce in K'irga ganina dashiba,kuma a ganina na farko dashi na gane irin sangartattun y'ay'an masu kud'in nan ne, duka shine abinda ya fara kashemin jiki dashi."

"A'a yaya karka karaya ka kira Nahna dai kaji meta Yanke shawara kafin mu wuce gobe , sannan maganar sangartacce ne wannan D'abi'ace ta mafi yawon y'ay'an masu kud'i matuk'ar dai yaron baya shan giya baya Neman mata to ba matsala bace auransa."

Jin jina kai yaya yai sannan ya d'ora
" a gaskiya Umar baya daya cikin lefukan nan Don na tab'a tambayar sectare d'in Alh yace baya d'aya ciki sai dai kawai ji da kai da nuna Isa tare da sangarta, sannan zan k'ara bawa Nahna dama harta dawo Daga Sakkoto sannan inji ra'ayinta,don bansan takurata ko kad'an sannan kafin nan zanta k'ara nufar Allah da lamarin yai mata zab'in miji mafi alkairi".



Wani gumi naji yana tsatstsafomin tun daga kaina har k'afata don a hirarsu na gane Yaya yana son had'in nan sai dai yafi k'aunar farin cikina fiye da komai, don haka nasa araina daga yau nai d'amarar sadaukar da burina zan amincewa auran uk kodan mu sakawa Abbansa Alherin da yake mana duk da nasan babu komai cikin auran Uk sai hak'uri da karb'ar k'addara amma zan jurewa hakan,kuma zanci gaba da kaiwa Allah kukana nasan bazai bari in wulak'antaba.

Sai kuma naji wasu hawaye masu zafi suna bin gefan kuncina ,Tunowa danai burina ya karye nason auran miji ma'abocin addini,don nasan Uk bai San komaiba cikin addini zanyi jahadi zan sadaukar da soyayyta ga Wanda ya tsaneni yake musgunamin Wanda bai San darajar d'an Adam ko kad'an . . . a haka bacci ya d'aukeni bayan nasha kuka na gode Allah.




**************
Da safe kafin in tashi har Aunty ta gama had'a break fast ta shirya Yara sun tafi skl Wanda duk aikina ne, ganin ina bacci yasa duk tayi hakan.

Bayan na fito a wanka a gaggauce nasa Kaya don ina toilet inata kiran yaya Usman inyi sauri in shirya da wuri yake so mu wuce , don haka ko kwalliya ban tsaya yiba na fita parlour.

A zaune na samesu suna jirana mu karya bayan na gaishesu na zauna muka karya, bayan mun gama yaya Usman ya dubeni yana fad'in "To maza d'auko jakarki mu wuce banso muyi rana "

Mik'ewa nai zuwa d'aki na yafo mayafina na d'auki jakata ta hannu na jawo trolley d'ita na fito,
Aunty ce cikin wasa take fad'in " To su Nahna yau sai Sakkoto birnin Shehu in anje a gaida Mama da umma a gaida duka mutan gidan".

Cike da fara'a nace " Tom Aunty duk zasuji insha Allah ,in su Ashraf sun dawo kice musu mun tafi bamuyi sallama ba."

"Tom zan fad'i musu Allah ya kaiku lafiya".

Yaya Haroon ne ya kaimu tasha muka d'auki shatar mota k'arama don Yaya usman bai son matsuwa .

Tunda muka d'au hanya muke hira daga bisani yaya usman ya jefomin maganar da sukai da yaya jiya yana nusar dani kan In tsaida hankakina gu d'aya koda zan d'ora degree d'ina hakan bazaisa in k'iyin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login