Showing 54001 words to 57000 words out of 231198 words
Chapter 19 - TAKARI Book Complete by Zainab Makawa .txt
Kamar zasu cinyeni dan ya,,
Yaran na takure gefe guda sundan rgumay hannun su ,sun wani man,ne majunan su ,zaban tausayi
Jawo su nayi nai masu wanka cikin sauri nadauko abinda zan karya kumallona da shi nabasu,
Har dan abinda zasuci darana saida na hada masu,shi ,sanan nafita zuwa wurin
Nikaina nasan cewa yau,na makara sosai,
Ina fita taxi, Kai tsaye na fito na mika ma mai taxi kudin shi ,
Duk da naga Almustapha a,kofar shiga gidan namu, kauda kaina nayi gefe kamar ban ganshi ba,
Don shima yasan cewa bazan gaishe shi ba,
Fada yafara yi min baiko kai aya biyu bu nadaga mai hannu alamar ya isheni hakana,
Cikin mamaki yake kallo na yana kuma yaba karfin hali irin nawa ,
Har shine zan daga wa hannu,
To yau kowaye min tsaye sai nabar gidan nan ,haka yake fadi azuciyar shi,,,
Na ci gaba da magana ina cewa shike nan don muna aiki bamu da incin kanmu ko wani lokaci na kan mu,
Ai yakamata a,dinga muna uzuri aduk lokacin da aka ga mundanyi wani abu bawai adauki matakin da babu dalili ba
Da in tsaya kana mari na ko zagina duk lokacin da kaga,,,,
Ban samu karasawa ba naga Sheriff's atsaye gaban mu yana muna wani irin kalon mamaki,
Mari mari fa,, Almustapha ,Subahanalla subahanallah ka doki mace macen ma,,,,,
Sai ya kasa karasa wa, naga kawai ya dunkule, hannunshi ya dan daki gudan da shi yana fadin subahanallah,,,
Nikan nasa kai na wuce cikin gidan ina jin yana cewa yaushe kai wanan aikin bansani
Ko kana dukan mace ita wanan din may zaka daka acikin ta,,,
Wuce wa yayi ciki gidan ran,shi bace dagani kasan yayi mugun, hasale ,yabar almustapha a wurin bakin get din, cikin damuwa,,,,,
Don ko yaga fushi yau karara a,idon sheriff din,,nashi wanda rabon shi da yaga wanan fushin yadade,,,,
Ban tsaya yin komai ba gurin tsuntaye nafara zuwa sudake da rai na basu abincin su,,
Don kusan kowani tsuntsu da kalar abincin shi,
Ruwa kuma akwai wanda nake sama ,magani acikin nasu, ruwan shan da samun kuzari da lafiya,,,,,
Danaga komai ya kam,mala sai na bar gurin aikin zuwa cikin gida don inyi aikina,,,
Daidai gurin da dawakai da dabbobin gidan suke yake tsaye ya rike ciyawa a hannun shi yana ba wani dan farin doki karami,,
Ke yace min cikin tsawa saida naji tsoro wanan kiran,
Ya,akayi mustapha ya mare ki yaushe ya,mare kuma a ina,,
Wani tambaya zan ansa daga cikin ukun,,,
Duk da ina jin kunyan shi yau sam banji ba
Saboda dama tun da daren jiyan abinda akayi wa lawisa a,kasan ya tayar min da hankali sosai ,
saboda naga bamu da wani gata ko daraja a, wanan kasan.
Batare da na bashi ansa ba sai na fashe da kuka mai kuna zuciya
Yana ganin na fara kuka sai ya rintse idanun shi don bacin rai jiyakeyi kamar a watsa ma garwashin wuta ajikin shi,,,,
In akwai abinda ya tsana yaga mace cikin yanayin kuka ko ban tausayi,
Ganin idona rintse yasa shi ya sulale yagudu yabar wurin don bai iya daurewa yana jin wanan sautin wanan kukan a rashi ,,,,,,,
Ni ko,kukan da , samun yin ,shi ,shiya dan sa naji wani dan sanyi azuciya na
Koda nagama kukan na dan kai dibana inda nagan shi tsaye sai naga wayyau, ba kowa wurin,
Haka na wuce nabar wurin jiki ba wani kwari don jinakeyi kaman ban iya tafiya,,
Ashe da sheriffudeen din mu yabar inda nake tsaye komawa yayi sama yana tunane azuciyan shi,,
May yasa almustapha zai dauki hukunci mai tsanani akaina,haka har da mari mari fa,,,,,,,,
Wurin nabari zuwa ciki don inyi aikina,
Ina shiga cikin gidan sam na manta cewa akwai bakin, agidan mutanen Nigeria dasu kazo jiya,,, saboda tashin hankalin da nake ciki,
Wa,daga cikin bakin,suna falon gidan zaune su,nata har kokin su,
Sai narasa ta ina zan soma aiki na ma , tsayi nayi wuri guda,,,
Don ku san ko, ina akwai mutane a falon,,,,,
Ina nan a tsaye tsakiyan falon sai naga wata yar dattijiwan takari bakuwace daga cikin mu, ta zo inda nake tana min murmushi ,,,,,
Cikin girmamawa take magana da harshen
larabci takecewa tundazu take jiran shigowa na ,,
tai min sannu da zuwa,
Tace min itace mai kula da aikin goge goge yanzun agidan
Da duk wani aikin da ya kushi cikin gida,
Mamaki ne ya kamani don naga aiko jiya nice nayi wanan aikin,kafin muje gida,,,
Sai,gashi jiya zuwa yau da safe wai an canza wata mai yi,,,
Kenan an,dakatar dani daga aikn ake nufi ko,,,
Daidai zan fita inbar falon naji mama mai abinci nace min inzo indiba ko abincin da suka dafa yayi ,,, kalonta nayi itama cikin mamakin
Don suna son su ba mutane abin kari,,,
Nuna kaina nayi ina waigen gefe da gefe na ina, nufin ni takewa magana kuwa,,
, tace min eh,,, dani take
Ba mussu nabi bayanta zuwa inda naga tabi, kitchen ta nufa,
Abinci ne na alfarma aka hada masu kyau da dadin gani,sai kamshin dadi ke tashi,,
Tana kokarin bude min kulolin abinci nace mata la,la,la ta bari don Allah komai ya yi,
Mama mai abinci tace min in bari ,in,diba in gani, in, akwai wanda bai yi ba sai su sake,dafa,wani,,,,,,
Nace mata yayi haba mama, yau kika fara wanan aikin,
Ta danyi murshi kawai na nuna kula da girmamawa
Niko duk mamaki ya cika zuciyana ga dinbin tanbaya min fal a,rai,,,,
Bayan anjera komai wurin very neat, ,
Rugaiyya tace min inje in fada ma mutanen gidan cewa table is ready,,,
Bayan mun fita Rugaiyya ke min bayanin cewa yanzu aikina shine kula da duk wani al,amarina aikin cikin gidan, nan nice da alhakin kuwa, dashi,,,,
Don Almustapha ancanza mai wuri zuwa can company
Nace ma Rugaiyya yanzu duk yawan mu sai nida nake yar karamar ku za aba wanan aikin
Wanan aikin aida mama mai abinci yadace bani ba
🐎ZEEE MAKAWA🐎
🐎HUGUMA GROUP🐎🐎
[10/4, 14:26] +234 703 602 1388: ✈✈✈TAKARI✈✈✈
👣👣👣👣👣
👣👣👣👣👣
4⃣1⃣
BY
🐎 ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎
🐎HUGUMA GROUP🐎
A, kulun muna gode ma Allah Subbahanahu Wata,ala daya Halice mu a matsayin musulumai,
Ya Allah muna kara gode maka da ka bakayi mu kafirai ba,
Allah yakara ma musulunci daraja da daukaka 👏👏👏
Allah ya kara rufa ma duk al,uman musulumi na duniya asiri
Almost true life story
Maimakon in yi farin ciki da cigaban da nasamu ,
Nikan hankalina yana gurin irin wulakancin da akeyi wa yan takari,,
Ga lawisa ta wuce tabar yaran ta acikin duniya, batare da sanin makomar su ba,,
Shin wai may yasa ake zuwa wanan aikin mai wahalar tsiya ,
Wahalar da ba riba ko kadan sai in Allah yataimaki mutum,, yatar fa wa garin mutum nono to shine zai tsira da dan wani abu,,,
Duk abinda aka girka a,gidan ranan , saida na sdibar wa,su hajiyan mu da yaran nan, na lawisa,
Tun lokacin tashi baiyi ba nabar gidan aikin na mu,
Sauri nakeyi zuwa gida don inkai ma hajiya abinci suci,
Natafi da niyar gobe insha Allah zan daure in ma sheriff din mu magana ina son ataimaka mu,na indinga zuwa gida da wuri don indan kula da hajiyan mu da yaran lawisa,,, ,,,,,
Cikin sauri sauri na isa gidan tun ban shigaba nake jin dan she,shekar kukan yar macen yarinyar,
Wacce ban ko san sunan ta ba ma
Da, sauri na karasa shiga ciki don jin ko maya sami yaran
Hajiya na zaune gefe tai tagumi, sukuma yaran sun dan tsuguna daga bakin kofa shigowa cikin gida,,,
Banko kalli hajiya mu ba wacce ta nuna mamakin ganina nadawo yanzu
Tun lokacin dawowar mu baiyi ba,
Yaran nake tambaya hankali tashe komay yasamay su suke kuka
Ganin danayi basu da niyar yin magana,,,
yasa na wuce ciki kawai tubewa nayi ,nacire dogon rigar da nasa sama,
Nakoma dagani sai wata yar doguwar riga English wear kalar sky colour ,wace duk ta man ne min jikina rigar irin na yan Brazil's din nan ce
Sai kaina da na daure dawani ribon mai kama da gashin mussa, kalar fari kwal
wani dogon yan kune fari ne a,kune na, takalman kafana dama munfi sa cover shoes, don , muji dadin gudu idan an biyo mu,,
Plates najawo guda uku na fara zuba ma hajiyan mu abincin ta kala kala ,nakai mata
Nadibar ma wanan yaron nashi saida na cika mai plate , nabashi tare da abin sha,
Na hada muna nida wanan yar yarinyar a plate guda,
Cikin lalashi da hikima nasamu yaran suka ci abinci ,
Har suka dan sake jikin su dani, inda nake tambayar su sunan su,
Namijin yace min sunan shi umar macen kuma Aisha,,,,,
Saida naga hankalinsu ya kwanta sanan natashi na gyara wurin da mukaci abincin mu tsab ,,
Umar da Aisha,naja zuwa gidan su, don indan diba cikin kayan su koza a,samu wani abinda zai masu amfani ,
Muna fita naga yan kabilar larabawan dake gurin suna ta kallon mu,
Duk da sun tausaya ma yaran amma basu iya yin komai, gamay da uwar tasu,
Wani halarci da suke muna shine, indai kana zama a unguwar su baza su taba tona bakar fata ba in har yan bagaladi sunkawo samamay shiyan,,,,
Acikin gidan na lawisa naga wasu hotuna da takardun ta sai yan tsun makaran kayan ta dana yara,,,
Nadan tsinto masu masu dan kyau daga cikin kayan,,
Muka fito gidan,,,,,
Nasamu su Rugaiyya sun,dawo gida ko, takara zo muna da wani abinci wanda zamuci da dare,
Au ke fadima har yanzu yaran nan natare da ke,
Ashe shiyasa yau kika bar wurin aiki da wuri ,
don ki dawo wurin yaran na,ko, fadima baki da tsoro ko,,
Aiko kin dauko muna wani sabon magana wlh, bamu iya da kan muba shine kuma zaki jajibo muna wani sabon taulali,,,
Saida na bari ta gama maganar ta ,
Sanan nace yanzu idan mu bamu taimaki yaran nan ba wazai taimaka masu bayan mu, awanan uguwar
Kutuna cewa muda lawisa duk guda ne tun da itama takari ce,kamar mu
dakuma irin taimakon da tai muna lokacin da mukazo nan gurin,, bamusan kowa ba,,
Hajiya ce ta katse min zance na da cewa ai sai kisan yadda zakiyi dasu,
Don nidai ba ruwa na gaskiya,
mukan mu , ba musan yadda zamu kasan ce ba,, da tamu rayuwar ba balle
Allah zai dibe mu nidasu insha Allah na katse zancen kowa,,,
daga haka ban kara ce ma,kowa, komai ba
na,tashi nafara tanadar wa yaran da inda zasu rika kwaci,
Ina gamawa na wanke masu yan kayansu da zasu sa, gobe, don duk kayan nasu na da dauda,,,,
Washegari saida naga na tanadar masu da komai sanan na bar gidan zuwa aiki,,,, zuciya na nata min sake,saken yadda zan ma Sheriffudeen din,mu bayanin akan taimakom da nake so ai min, don in samu kula da yaran nan,,,,,,
Ina shiga gidan Kai tsaye gun tsuntsaye na,na nufa ,,,
Don ina ba,su abincin, su,
Saboda sune ban son makara zuwa wurin aikin, saboda sam ban son barinsu da yunwa,,
Gashi kuma mun saba da juna,,,
Amma ina zuwa wurin naga wani dan saurayin bakar fata bakon fuska, ne, agidan, yana watsa masu abincin su,,,
Tsaye nayi nisa da shi,kadan da inda yake ina kalonshi cikin mamaki,
Daidai lokacin naji karan bude kofar baya nadan waiga inga kowaye ke fitowa,,,
Sheriff din mune tare da wata bakar mata matar bata da wani tsayi gajera ce mara jiki,
Duk da ta lailaye jikinta da lafaya mai ruwan yellow sai dan adon duwatsu churculate colour dake jikin lafayan
Ina iya hango gabanta kamar ba komai, hannunta zanen kumshi ne irin namu na yan Nigeria,, yayi baki wulk
Takalmin ta ma charculet ne amma mai dan tsinin duduge, wanda nake ganin takalmin ya taimaka mata wurin karin tsayin ta
Sai wani kamshin turare kamar na turara garwashi da takeyi mai dan dadi wanda ban iya fassara kamshin shi,,, abindai siri ne kawai,,,
Gefe guda nadan ja na tsaya, don in basu hanya su wuce
tare da masu barka da safiya,
Batare da ya kalleni ba ya ansa min a dakile
Wani irin kallo yaimin mai alamar, may nake yi anan ,,, kaina aduke nayi cikin gidan takofar da suka fito,,,,,,,
Idon shi naga dan takarin nan mai ba tsuntsaye abinci,
Wanda baiko kula da inda nake ba, ma tunda na zo
Saida yaga shigewana yadawo da idon shi kan hanya,,,
Ita wanan din wace,ce ita habibi,
Matar ke tambaya ,batare da yabata ansa ba ya wuce yabar ta, tabishi da dan saurin ta,,,
Yau kida na shiga cikin gidan banga bakin mu ba
Sai gidan ya koma shiru ba kamar kwana biyu da akai yawa ba,
sai mu kadai ne ke ta zirga zirgan mu a cikin gidan,,,
Daidai lokacin da aka gama, hada komai na abin karin safen su bisa, dinning table din, ,,,
Lokacin su ma suka shigo cikin falon kai tsaye inda table din yake ke suka nufa,,,
Maigidan ne a gaba, matar na binshi
Yaja kujera guda ya zauna,,, don suci abinci
Inda yake zaune naje kusa kadan dashi,,,
Ina gyara wasu cups da suka danyi nisa kadan da shi,,,
gyara cups din na keyi ashe kamshin turaren zam,zam lau,, da,na dan murza a jikina yana tashi ban sani ba,,
Jin kamshin yayi har cikin zuciyar shi,,,, idon shi lunshe kadan,,, yabude su a,hankali
Jin yake Duk kamshin ya wani sukur,kuta shi wanda hakan ba halin shi bane,,,,,,, cikin dibara ya kauda kanshi gefe guda,
Yace min cikin larabci in barshi kawai zasu iya hada abincin, ai
Saidai indan ba ka saurara da kyau,ba bazaka ce anyi magana a,wurin ba,,, saboda tausa muryan dayayi
Ina kallo yadda matar ta cika plate fam da abinci,,, wai ita zataci,,,,
Cikin gidan nashiga don in di ba ko an,gyara masu, dakunan su duk na gidan ,,,,
Aiko kafin in,sauko kasa matar har ta cinye kusan rabin abincin plate din da ta zuba,,
Idona na fitar waje don mamakin ta
kallon abinda nake kallo sheriff din mu ke yi,, shima
Bin inda idona yai saiti yayi,,, aiko sai yaga plate din matar nake kallon ido waje don mamaki,
Kara diban abinda nake mamakin yayi,
Ai, shima da ya lura ta cinye wanan tulin abincin saida mamaki ya kamashi,,,,,,
Tana gani na tace min inzo in zuba mata juice a cup,
Hannu yadaga mata alamar a,a,
Yace mata she is not a Made,,
Cikin larabci yace min in bar wurin,
Tana son tambayan shi to amma ba fuskan hakan,,,
Duk Jina yau nakeyi , kawai ba wani kuzari ,ajikina,don, yau ban yi, wani motsa jiki ba ,
Saboda aikin komai banyi ba agidan , don akwai masuyin komai da nakeyi a,da,,,,
Almustapha ne mukayi kicibis da shi daidai fita wurin kofar shigowa falon , gefen shi nabi,
Zan wuce shi ba tare da na gaishe shiba ,
Yace min tun jiya yake bida na don yai min wani