Showing 78001 words to 81000 words out of 231198 words

Chapter 27 - TAKARI Book Complete by Zainab Makawa .txt

Jin da yayi ina kwatancen inda dakin da muke yasa shi barin kallo na,


ZEEE MAKAWA24/10/2017, 1:50:11 PM: Maman Safwan: ✈✈✈TAKARI✈✈✈
👣👣👣👣👣
👣👣👣👣👣
5⃣0⃣
BY
🐎ZAINAB IDRIS MAKAWA🐎
🐎HUGUMA GROUP🐎

Almost true life story,,,


Allah ya karama Annabi darajja da sahabban sa,,,
Jumma,atu mubarak yan uwa musulumai,,,

Almustaphane tare da bakon saurayin nan mai suna Salim suna dauke da kwandon abinci, da abinsha, a hannayen su,
Nina karbi basket din hannu almustapha, nakai inda zan aje na aje,,,
Ahankali nadawo inda nake tsaye, nadan tsaya muna kallon ledar ruwan da ake kara, wa Ummi,
Almustapha gefen da nake yazo ya tsaya gab dani, ,,,
Shima kallon ruwan da ake kara wa Ummin yake yi cikin tausayawa,
Dan juyowa yayi daidai saitina ya ce min Aisha na can yau tana fitina wai sai ankawo ta gurina,
Murmushi nayi nace mai tunda tazo aibantaba dadewa waje hakaba, batare dani ba
Yace yau kan Yumma tasha rigima sosai
Ina dan murmushi don tuna Aisha da irin rigimar ta,
Ina,dan juyo sai ko muka yi ido hudu da Sheriff din mu,
Dake tsaye daidai saitin inda muke,
Hannu shi cikin aljihu yadan jingina da gina kadan,
Ashe idon shi na inda muke muna magana da mustaphan
Wani irin harara Ya watsa min,
Tare da wani irin mugun kallo na zaki gane kuren ki,
,bansan lokacin da na sada kaina kasa ba,
Don kallon ya firgita ni sosai,
Tunda ni bansan abinda nayi mai ba, yai min wanan kallon na kishi ga hankalin ki, da ni,
Shiko Almustapha sai kara fada min yadda Aisha ke fitinar yakeyi,,,
Duk nadan daga kaina sai mun hada ido dashi daga inda yake tsaye suna magana da shehi,
Ganin da tayi mustaphan ba daina yimin kus,kus din da mukeyi zai yiba saboda bai lura da sheriff din ba da kallon da yake muna,
Don baya yaba ma sheriff din,,,,
Daurewa kawai nakeyi ina yar dariya kasa kasa,
Muryan , sherrif naji gab da mu yana ce min naje muci abinci da Amal a waje
Kafin in yi wani yunkurin tashi wurin saina ji muryan shehi yana cewa kamar ruwan baya tafiya ko,
Da sauri ya juya zuwa inda ummi take kwance don ganin robar kara ruwan
Sai kawai naji duk banjin dadi saina dan shiga halin damuwa,
Saboda ban iya fassara laifin da nayi ake min wanan kalon warning din,,
Abinda ya kawar minda damur dana dan shiga shine,
Farkawan da Ummi tayi daga barcin da takeyi sanadiyar dan taba mata hannu da akayi,
yasa nadan saki jikina da sauri na naje gurin ta ka,fin kowa ya isa ciki
Sauri ina mata sannu da jikinta, Ruwa tace zata sha saina dan daga kaina nakali inda yake ina fada ma sheriff din bukatar ta wanda dama idon shi naga mahaifiyar nashi,
Shima gurin gadon ya iso, yadan duka daidai saitin kan ta yace mata tayi hakkuri, Ruwa ake kara mata tabari indan ruwan ya kare sai abata, tasha ruwan shan,,,
Cikin sanyin gwiwa ya Mike ya na tafiya yana ce min cikin larabci koda ruwan yakare kada in bata ruwan tasha don akwai tests din da za,azo aimata dan anjima kadan,
Barcin ne yakara daukanta mai nauyi duk ina tsaye, akanta sai likitocine keta zuwa da dawo kanta, suna aune aune don su gane ko may ye matsalar ta
Amal tana gefe zaune ita da salim cikin damuwa ganin irin wahalar da mahaifiyar nasu keyi,,,
Muna nan zaune mukaji takon takalma tun daga nisa kwas kwas sai duk hankalin mu yakai ga kofar shigowar don gani ko waye,
A,she Nafisa ce tashigo asibitin da marance lip,,,, cikin shigar wando da riga irin na yan Pakistan, take,
Ta yafa mayafin kayan ta rufe kanta da shi,,,
Tana shigowa ko wani gaisuwar kirki bata yi wa koda shehi datagai dattijo ba cikin mu balle su Amal dake tsaye gefe
Direct wurin gadon da ummi take kwance ta nufa,
Tadan dibata tana tabe baki kamar mai jin wani, bashi ,bashi
Ta dan jin tsaye,muma ba wanda yako kulata,
Ko minti goma batayi ba da zuwa tace zata wuce,,,
Har takai kofa tajuyo tana min tabayar ina habibi cikin turan ci,,,
Da larabci nace mata yana can gurin ansan result din test din da akayi, wa ummi,
Yafuto ni tayi da hannu alamar in kai ta inda yake,
Ba musu na dan gyara na nufi hanyar zuwa lab, da ita,
Dan tafiya mukayi maidan nisa sanan muka isa gurin, da yake,
Zaune yake saman kujerun da aka tanadawa mutane,
Saidai kan shi yana duke, ba wai kalon jama,a yakeyi ba,
Dagani jira yakeyi yaji an kira shi, kawai,
Muryana da yaji cikin lokacin da bai yi tsamani ji, ba yasa shi dagawa da sauri,
Yana dagowa saida idon shi yabani tsoro
Saboda Idon shi yayi jajir kamar wanda yai kuka,
Nikan nasan cewa ma kukan yayi ,don ko dazu dana kai mai wani takarda da aka bamu na iske shi zaune cikin mota shidaya yana kuka,
Ganina dayayi yasa shi yadan wayance, don kada in san cewa kuka yakeyi,,
Tausayi yabani saboda mahaifiya ai ba wasa bace,
Don gani nima kusan kulun da tunane inna nake wace nake ganin kamar ban kara ganin ta a duniyar nan,
Gashi tunda naga makwabcin mu ban kara ganin wani dan garin mu ba,
Balle ma yanzu da ban bara ban talan gumama atiti kida alhazai sun zo balle inga idon sani,,,,


Yana dagowa kan shi yagan mu tare da nafisa aiko sai naga yakara tamke fuskan shi tam
Kamar wanda aka aiko mai da mugun labari,,,
Ita sam bata damu ba sai wani dan kokarin shige mai da take batun yi,,,
Nikan wucewa nayi don nakoma dakin da ummi ke kwance,
Don kada su bidi wani abu ban kusa,


Gida zamu koma don saboda asibiti majinyata basu kwana aciki,saidai mai jiya kawai da nurse's,
Saidai gaskiya shi shehi yace sam bazai koma ba zai tsaya asibitin, tare da ummi ne,,
Saida Sheriff yadan yi shige da fita aka bar shehin ya kwana, agurin nata,

Mu hudu ne a cikin motar a hanyar mu ta komawa gida
Sheriff ke jan motar duk da dare yayi sosai,amma baka gane wa saboda hasken da garin keda shi ko ina,
Zakaga duk hasken fitilo ne ya haske ko ina a garin jama,a kuma basu daukewa har galin Allah yawaye,
A hankali yake jan motar bakajin komai sai sanyin A C kawai dake ta aiki amotar , kirar Jeep baka, wulk,
Murya a raunane yadan juya gefen da salim yake ya na magana, dashi,,,
Yace, yanzu salim kun san cewa ummi batada lafiya kuka barta har ciwo yacita haka ba wanda ya kirani a waya, ya fada min,
Yanzu saboda Allah kunyi min adalci ke nan,
May ye amfanin samun da nayi a,duniya,
Har, da za,ace wai mahafiyata tana dauke da ciwon yunwa ulcer da hawan jini har yai mata mugun kamu, haka ban sani ba,
Amal ce ta katse mai maganar shi tace wlh yayan mu Kada kaga laifin mu
koda mun ce zamu fada ma sai ummi tace batayafe mu fada ma ba,
Wai kada mutayar ma da hankali, tunda kana iya kokarinka akan mu bai kamata mu dinga sama wasu wahala ba hakana,,
Wai zai zama kamar rokon ka muka yi ,
Salim ya karbe zancen da cewa ai ni koda yaushe nikan ce ma ummi sai na fada ma, tunda mutane zasu ga kamar cewa ka kasa kula da lalurar mu ne bawai daga ummin bane,,,
Ya ci gaba da fadin,,
Aiko wanan kiran da Shehi yai ma bada son ranta bane saida yaga ta rikice shine yadaga waya yakiraka,
Tsuki yayi yana mai kada kan shi cikin bacin rai,
,azuciyar shi kuma, yana tunane kawaici irin na mahaifiyar na,shi har yai yawa, watan ita dai haka Allah yai mata rayuwar ta cikin sanyin hali,
Hmmm Allah guda gari bambam ,,,,,Wai hausa ne sukeyi haka wanda sai da kyat nagane may suke cewa,
Get muka shiga ,muna paker motar mu mukafito,
batare da Amal ta tsaya ba tai niyar wucewa cikin gida abinta don duk a,gajiye take,
Niko lokacin na dauko basket din da aka kai muna abinci da rana ga flasks din ruwan tea da nake kokarin dauka wa cikin motar da hannu na guda,,,
Wani wawan tsawa ya,daka mata ta,tsaya wuri guda cak,
Tare da yi mata masifa, wanda ita dai duk iya saninta dashi baitaba yi mata hakan ba,,
Kayan dake hannu na yace mata ta tayani kwasa zuwa ciki,
Flasks din ta karba a hannu na ba shiri, jiki a sanyaye,
Shi kuma salim ya kwaso sauran kayan da muka kwaso daga asibitin,yashiga dasu,
Bin mu yayi da ido yana tausaya min irin wahalar da nasha yau,
Shin wai ita wanan yarinyar haka zuciyan ta yake ne,
Don dai gaskiya inbadon yasan ni tun ban karasa kai haka ba da sai yace kila don asani nakeyi wani abu,
Amma shi duk abinda zanyi sai yaga na tsakani da Allah ne babu kissa aciki,
Tsaki yaja lokacin da yake kokarin rufe motar,
Da ya tuna da Nafisa,
Wace ta nuna mai halin ko in kula, ga mahaifiyar shi,
Shi yarasa ita kowace irin mutunce mara tunane da lissafi,
Ace ankawo mahaifiyar shi asibiti daga Nigeria
Amma wai har ta biyo shi asibiti tana request din kudi a wurin shi,,,
Ita bata da aiki sai dai yawan tambayar shi kudi da bukata
Kuma sai yau yakara sanin halinta sosai don,ganin halin ko in kula da ta nuna mai akan ciwon mahaifiyar shi,,,
Da wanan tunanen ya shiga cikin gidan,,,,


Satin mu biyu muna cikin wanan sintirin zuwa asibiti da gida,
Inda ummi ke jiyan jikinta,
Saidai gaskiya ba laifi jikin nata yayi sauki sosai
Don yanzu har ummi na iya tashi mudan yawata cikin asibitin da ita,
Shakuwa sosai ya shiga tsakani na da Amal da Salim,
Saboda yawan zaman da mukeyi wuri guda, da su,
Sai ya kasan ce kamar mun san junan mu da ma ,har ina jin dadin su fiye da zaman da muka danyi da su jamila da mairo da suka zo kwanaki
Duk da nasan cewa Amal ta girmay ni sosai amma hakan bai hanamu zama guri guda ba da ita,
Muna mu,amula kamar kawaye,
Har tafiya Sheriff din mu yayi zuwa Riyadh yin wani aiki na musan man da yataso mai shi da mustapha suka tafi,
Nice yabarwa kula da duk wani lalura na asibitin
Har zuwa lokacin da suka dawo daga tafiyan
Tafiyan da kusan itace tafiyan da ta zama makowa nagidan alheri nan gaba,
Don ko Sheriff din mu yasamu cigaba sosai don yanzu ya samu sa hannu a kusan mafi yawan company tatar man fetur ta kasa,saudiya,
Saboda kasan cewar shi kwararen engineering da suka sani
Saboda suna ganin cewa zai iya barin kasan any time daga yanzu saboda hada hannu da suka ga yayi da company Abu Abdallah dake Dubai,
Cikin dare ya iso garin don haka direct asibiti suka nufa,
Suna iso wa lokacin su Amal na waje suna shan iska,
Nikuma ina tsaye kanta ina kokarin hada mata ruwan shayi,
Jin anyi yasa na waiga inga ko waye don nadauka ko Amal ce
Sheriff ne sai su almustapha dake binshi abaya,
Gurin mahaifiyar nashi ya nufa direct tana zaune saman gadon asibitin jikin ta yanuna alamar tasa mu lafiya sosai,
Mun mai sannu da zuwa inda yake ansa muna cikin muryan shi maikama da yanajin kasala ko yaushe,,,
Da kyat yake magana mai karfi don in kaji muryan sheriff to ta baci,rai ya gani tare da mutun ,,,
Waje nafita batare da sanin kowa ba don in dan basu wuri su dan zanta, shi da yan uwan shi don kusan nice kwai bare,,a cikin su,,,
A samane dakin da aka kwantar da ummi yake, don haka waje nafito, nadan tsaya,,,
Daga sama inda nake tsaye ina kallon ina iya hangen katon agogon nan dake mane a kofar shiga masallacin ka,aba,
Wanda duk inda kake cikin garin makkah za ka iya ganin shi
mutanen dake shige da fice cikin kofar asibitin, nake dan kallo jefi jefi,
A zuciya na kuma ina, Tausayin yadda naga sheriff ya,damu da mahaifiyar shi ne yakamani,
Don nasan cewa idan yai wanan irin tafiyan yadawo bai fita ko ina har wajen kwana biyu,
Yana gida yana hutawa saboda gajiya
Saidai in rana,kun ya dace da jumma,a a ne acikin ,, shi,,,, Amma yau sai gashi direct asibitin yanufa don gani mahaifiyar shi,,,,
Ya shiga yaga ni ,Yana,Ganin jikin ummin yayi sauki sosai yasa shi fitowa daniyar komawa gida, don yadan huta ma ranshi kadan,,
Turus yayi daga bakin kofar dakin lokacin da fito,
Don, yaga fadima tsaye wace hankalinta na ga kallon waje saidai kuma hawaye take gogewa a fuskanta
Wace ita kadai ce tsaye a wajen,,
A,hankali yatako zuwa kusa da inda take yadafa karfen dake gaban su, yace mata lafiya,
Kaduwa tayi duk jikinta sai yakama rawa saboda jin muryan da tayi na bazata, alokacin,
Kara tambayar ta yayi ko may take ma kuka hakana,
Cikin daburcewa tace mai ba,kuka takeyi ba abune ya fada mata a idon ta,
Bawai ya yarda da ansar data bashi bane kawai ya barta ne don yasan bazai samu ansa ba, a lokacin,


Nafisa ce zaune a falo tana waya ga Tufan da Anabi, aje agabanta sai madarar kwali wanda kwalin yasha rabar sanyin, friged ,da ke aje gefe guda tare da cup,
Waya take yi a,binta hankali kwance tana yi tana tsunkar Anabi din tana kadawa baki,
Sautin kidan yan kasar sudan ya tashi a cikin tv, dake man ne a falon, a hankali,
Kafarta guda saman dan stol din tangaran da ke falon
Har ya shigo falon yakare mata kallon Allah waddai,ya hau sama bata ankara da shi ba,
Sai gab da zai shiga dakin shi taga wulgawan shi,

Cikin sauri ta tashi ta rufa mai baya ,
Tana shiga ta iske yana na balle butur din rigarshi yana son shiga wanka,
Ta bayan shi tazo ta rugumay shi tana sun,sunar shi,
Batare da yace mata komai ba yadan juya ta kadan ya wuce zuwa bayi,
Ido tabishi dashi tare da mamakin wai shi wani irin mutum ne haka,
Sam mace bata agaban shi,
Kwanan shi kusan uku baya gari yanzu kuma da yadawo gashi ya nuna mata bata a gaban shi,
Zaunawa tayi tana jiran shi ya fito daga bayin,
Daure da rigar wanka yafito ajikin shi ga mamakin shi sai yaga Nafisa kwance rub da ciki, saman gadon shi tana dan daga kafar ta da ta mayar baya, a hankali sai hannuta da take, lalatsa wayanta, dagani abinda takeyi a wayan yadauke mata hankali sosai,
Wardrop ya nufa ya ciro wata jallabiya mai ruwan A,she,colour yasa
daidai yana zura rigar ta taso daniyar rugumar shi ,,
Dakatar da ita yayi cikin tsawa, yakama hanyar fita dakin,
Binshi tayi abaya tana fadin walahi ita tagaji da wanan halin ,
May wai yake nufi da ita ne ma, da zai dinga mata wanan wulakancin ita yau tana bukatar shi,,,,,
Daidai lokacin mukayi, Ido hudu dashi kuma a,daidai lokacin da take wanan furucin nata,
Ji yayi kamar ya nutse a kasa don kunya,
Saidai kuma ya basar da zancen nats kamar ma bada shi takeyi ba,,,
Ita ko bata daina ba sai kara ci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login