Showing 30001 words to 33000 words out of 184071 words
Chapter 11 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt
malami ne a jalingo, kuma sanadiyyarsu Hardejo ya musulunta har aka bashi aure, tace "maa ismuki ya ukhtee...
cike da jin dadi budurwar tace "ATIKA " *ATIKA SHEIK SAHEEB SAIFUDDEEN*
Juya sunan Baffa yayi tayi yace "kai ilimi akwai dadi, yanzu kinga sai musan labarinta ta dalilinki mai babban suna....
Mikewa Aisha tayi tace "bari in kawo mata abinci taci sai tayi sallah, kaga magariba ta kusa....
Bayan sallar isha'i kowa ya nutsu a gida,
kuka da karai kainin shanaye kadai ke tashi a cikin gidan,
matasa da yaran gidan duk suna zaure suna daukar karatun dare, yayin da wasu daga cikin malaman hardejo suka wanke gawar Habeeb da suka samu daukowa da kyar, hade da suturceta kamar yadda hardejo ya koya musu...
Zaune yake cike da damuwa ya zurawa abincin gabanshi ido, "mutanen kauyen nan har yanzu imani bai gama ratsasu ba,
duk irin fatawar nan da ake badawa bazai sa su hankalta su saduda ba,
Hannu yasa a sama yace " *YA ALLAH DUK WANDA ZUCIYARSHI TAKE A KESASHE BATA DA NIYYAR RUSSUNAWA KUMA BA MAI SHIRYUWA BACE YA ALLAH KAYI MANA MAGANINSU DA GAGGAWA* AMEEN
suka amsa dashi dukkansu,
Adduoi yayi sosai akan duk abinda zai zamto barazana akan alummar musulmi Allah ya kauda shi....
******
Cikin Harshen larabci take bawa Aisha da Hardejo labarinta...
Sheik Saheeb Saifuddeen shine sunan mahaifina,
dan asalin kasar cairo ne, babban malami ne kuma dan kasuwa wanda ake ji dashi a egypt..
Ummuna ta rasu shekara shida da suka wuce gurin haihuwar kanina,
ummuna mahaifinta dan cameroon ne,
mahaifiyarta ce yar cairo,
kasancewata babba gurin mahaifina yasa yake ji dani fiye da kowa,,
Tun bayan rasuwar mahaifiyata aka aura mishi kanwarta Ummul khair saboda ta kula da kanina,
tun daga lokacin rayuwa ta fara sauya mana zuwa yanayi na ban mamaki da tsoro,
abin ya faro ne saboda ganin da ummulkhair tayi Abbuna ya dauki dukkan kulawarshi ya bamu ni da kanina *ATEEK*
kiyayya iri iri babu wacce Ummul bata nuna ma Ateek,
kiyayyarta a garemu batayi karfi sosai ba har saida ta haihu,
a lokacin ne ta nuna wa Ateek karara ba ita ta haifeshi ba,
in na tafi makaranta na barshi kafin in dawo gida ya jigata da yunwa,
gaba daya Ummul ta shafe idonta ta manta da zumunci saboda kasa ta rufe idon ummuna wacce ta zamto yar uwarta ta jini,
burinta a kullum Abbuna ya kula da ita da yaranta guda uku " Haidar, Affan, da Farouk,"
saboda rashin zaman Abbunmu shiyasa bai taba sanin halin da muke ciki ba,
bai kuma kula ya duba ba, saboda a ganin shi kamar da ummunmu muke tare,
bai taba kawo ummul zata taba koda yi mana kallon banza ba, bare har ta kai ga cuzguna mana,
Kakarmu ita kadai ce gatanmu, gurinta hankalinmu ke kwanciya, wannan zuwan da mukayi ma ta'aziyar rasuwarta muka zo, daga can muka taho nan mambila inda kanwar kakanmu (wanda ya haifi ummunmu) take domin gaisheta..
gidan sam baya min dadi saboda duk yan uwa basa kulawa da lamarin mu saboda rashin idon uwa,
kuma suna ganin Ummul ce mai rike damu sannan ga kudi tana musu facaka dashi shiyasa duk suka dauke idonsu akan mu,
rashin jin dadin zaman gidan yasa da na ga Habeeb ya fito zai taho siyan madara na biyoshi dan in zaga inga gari hankalina ya kwanta,
ashe kaddararmu ce anan ni da shi,
tunanina daya *Ateek* da na tafi na barshi yana bacci,
yaya rayuwarshi zata kasance in har babu wanda ya biyo sahun duba ni,
yaya rayuwar Ateek zata kasance, ta karashe cikin kuka mai ratsa zuciya,,,,,
Share hawayen tausayi Hardejo yayi yace "zasu zo su sameki, nasan zasu zo dan na tura a nemo inda iyayen yaron suke,
ko basu zo ba ni zan je har mambilan in kaiki gobe,
cikin kuka tace jirgin su a daren yau zai tashi ya koma cairo,
kuma kasani ba'a samun jirgi akai akai,
Kwantar mata da hankali Hardejo yayi yace "Gobe tun da asuba zan tafi in kaiki, ki kwantar da hankalinki, "
"Abin da Hardejo bai sani ba shine labarin mutuwar Habeeb ya karade ko ina a tsaunin mambila, kuma an hade harda ita Atikar ance an kasheta,
saboda firgicin labarin kuma ance musu limamin garin yasa an dauke gawar an suturce yasa gaba daya yan uwanta suka shirya komawa Cameroon a daren,
harda ita kanwar kakar tasu wacce dama Habeeb din ne karfinta a garin....
Suna idar da sallar asuba sukayi janaizar gawar Habeebu,
bayan an binneshi kamar yadda Hardejo ya karanta sukayi mishi adduoi sosai sannan kowa ya wuce gidanshi,
ko abincin safe bai ci ba ya shirya ya tarar da Atika tana shan fura,
tana gamawa ta mike suka dauki hanyar tafiya tun kafin garin ya gama yin haske,
sai da sukayi tafiyar awa daya sannan suka samu motar awaki ta karasa dasu,
A garkame suka samu gidan da ya kasance daki biyu tall, cike da tashin hankali malam Hardejo yabi makotan gurin yana tambayarsu, sukace ai kuwa tun daren jiya suka tafi saboda firgicin mutuwar su Habeebu,
zamani na babu waya bare ace za'ayi kiransu su dawo,
Takalmin Ateek ta gani a kofar gidan kafa daya,
dauko takalmin tayi ta zauna dabas taci kuka ma ishi hade da rungumar takalmin tana sumbata,
"Allah yasa ina da rabon sake ganinka Ateek,
ya Allah ya hadamu da kai da alkhairi,,
Hardejo saboda tausayi baiyi yunkurin hanata ba,
saida tayi kukanta sosai sannan ta tashi suka koma can kauyen su Hardejo,,
kauyen da rayuwa tayi dadi hade da wuya ga Atika,
kauyen da ya maida yar gata baiwa,
kauyen da Atika tayi rayuwa mai cike da ban tausayi....
Ya Allah kai ka zama gatan mara gata,
Allah ka sanyani na zama uba kuma gatan Atika dan alfarmar annabi da hasken alkurani...
addu'ar da Hardejo yayi tayi kenan har suka isa gida......
Mrs Tijjani shattima....
[01/03 12:08 AM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU*•• 2⃣4⃣
By *Aysha Ya'u Kurah*
Satin Atika hudu ta fara sakin jiki da yaran gidan duk da bata gane yarensu,
karatun qurani da littattafai take yawan koyar da yan matan da yan yaran gidan, sai addu'oi na azkar wadanda ta koya daga gurin mahaifinta...
Shaho kuwa tunda ya fahimci tana gidan Malam Hardejo hankalinshi ya tashi,
duk iskancin shaho yana tsoron Malamin saboda kwarjinin da yawaitar ambaton Allah ya haifar masa,
kullum in yayi niyyar zuwa gidan sai yaga gidan ya zame mishi bakikkirin,,
gashi kullum bashi da nutsuwa saboda yawan mafarkin Habeeb da yakeyi,
bacci sam ya daina daukarshi dan daga ya rufe ido zaiga fatalwar Habeeb..
kwance yake yayi firgai firgai zuciyarshi cike da kunci da radadi wanda baisan daga inda suke ba,
hatta da abinci ya daina samun lokacin ci saboda yanayin rayuwar da ya tsinci kanshi,, rashin ilimin addini ya sa ya kasa gane jinin mu'muni da kuma adduar malami irin na zamanin da wanda baya iya yin komai na sabon Allah ne ke dawainiya dashi ba,
iyayenshi sun kasance masu kudin kauyen sosai, shiyasa yake yin abin da yaga dama,
ganin halin da ya shiga ba karamin daga hankalin mahaifiyarshi yayi ba,
duk irin sangartar da yakeyi ita sam bata ganin laifinshi,
ko da aka kawo mata labarin abinda yayi murna tayi tace "sai ku jerasu cikin sauran mutanen da ya kashe,
ai ba yau ya fara ba, ita a kullum alfahari takeyi da halayyarshi saboda jahilci....
Halin da taga danta a ciki ne ya sanya ta dangata halin da son bakuwar gidan Hardejo,
alkawari ta mishi na a cikin satin nan zata aura mishi ita koda kuwa duk abin da take dashi zasu kare.....
******-------********
Jin inuwar mutum a kansu ne ya sanya su dagowa daga duba littafin dake hannunsu,
Maryam yar Hardejo ta mike tsaye jiki na rawa tace "ina yini, bata amsata ba tace "kira min Mai babban suna,
da sauri ta shiga daki ta kira mahaifiyarta,
kafin su fito maman shaho ta karewa Atika kallo sosai,
a zuciyarta taji dadi da danta zai samu wannan zukekiyar yarinyar a matsayin mata..,
"Gambo kece tafe, Aisha ta fadi tana shimfida tabarmar kara,
ba zama nazo yi ba mai babban suna,
nazo ne in fada miki Shaho yana son bakuwar gidanku,
in Hardejo ya dawo kice mishi yazo ya sami Barde (mahaifin shaho) sai su shirya ayi musu aure yadda addinin Hardejo ya tsara,
"galala Aisha tayi a zuciyarta tace "yau isar har ta kawo kansu,
kafin tayi magana Baffa ya shigo gidan tare da ma'u,
duk abin da ta fadi akan kunnensu,
"ko bakiji abin da nace bane mai babban suna? Gambo ta tambaya tana huro hanci,
karap Ma'u tayi tace "yo ko taji amsar me zata baki,
yanzu ke d'anki har wani d'a ne da zakizo kina hurawa mutane hanci kina nuna iko akan yar mutane,
to walle duk wani iskancinku yazo kurewa,
dan ko sama da kasa zasu hade yarinyar nan bazata auri azzalumi irin shaho ba,
ba Aisha da matan gidan dake tsaye a tsorace ba, har Baffa da yake namiji saida ya kusa sakin fitsari,
dan yasan ahalin shaho gaba dayansu babu imani a tare dasu,
bai bari maman shaho tayi magana ba yace "kiyi Hakuri dan Allahn Hardejo,
kinsan Ma'u bata da hankali,
Da hankali na!! Nace da Hankali na, in sun isa su kas--- toshe mata baki Baffa yayi ya jata dakin Aisha,
hakuri Aisha ta bata hade da tabbatar mata da Hardejo zaizo har gida ya sami Barde,
Har kofar gida matan gidan suka rakata suna tausarta...
Cike da fargabar rashin son tashin hankali Hardejo yace
"Ya zama dole in yi wani abu akan yarinyar nan,
buri na in samu kudin da zan kaita gaban iyayenta har can egypt,
to a halin da muke ciki ko daya cikin kwatan kudin babu,
ga sarkar ta da nake tunanin saidawa an nemeta ko sama ko kasa an rasa,
dafe kanshi yayi yace "ya Allah ka nuna min hanyar da zanbi in ceci yarinyar nan daga sharrinsu Shaho...
Sallama dai...
dago kai Hardejo yayi cike da bacin rai yace "sau nawa zan maka magana akan cika sallama Muhammadu,
cike da girmamawa yace "Ayi hakuri, sai a hankali komai zai zauna min,
neman guri yayi ya raba ya zauna,
zuwa gidan yanzu duk dare ya zamewa Baffa jiki saboda zuwan Atika,
kallon Hardejo yayi yace "yanzu me ka yanke akan maganar Atika, shin zaka aurar da ita ga shaho ne tunda bamu da kudin kaita gida,
girgiza kai Hardejo yayi zaiyi magana ya kalli fuskar Muhammadu,
wani irin Hasken annuri yaga ya gifta a fuskarshi,
murmushi yayi yace "tabbas zan aurar da ita,
amma ga kai muhammadu,
kai zaka aureta saboda mu tseratar da rayuwarta daga azzaluman nan,
saida ya tsugune saboda tsoro,
ni kuma? A'a inaa,
sam bazan iya hada kaina da tashin hankali ba,
yo ta ina zan fara ma ma'u bayani,
sannan ni kake so ka bari da bala'in Shaho da iyayensa,
dariya Aisha tayi tace "matsoraci bashi zama gwani Baffan yara,
to dama ni nace miki ina son zama gwani ne? Ya fadi a harzuke,
dariya sosai sukayi,
Hardejo yace "yanzu dai fada min cikin biyu, wanne kake tsoro?
Ma'u,
wallahi bazan iya yi ma ma'u kishiya ba,
ka tuna fa rabo ta nayi daga can garin su na kawota nan ba uwa ba uba,
sannan yanzu inci amanarta, haba malam,
kaifa kace addinin ka ya hana cin Amana,
kwarai ya hana cin amana muhammadu, amma kuma shi addinin ya halasta auren mace hudu,
ko baka lura da matan dake gidana ba?
Kirne fusķa Baffa yayi yace "kai ai ka girma, ni fa?
duka yarana nawa,
biyu kadai sai ince zanyi aure,
ganin da hardejo yayi samm Baffa bazai fahimta ba yasa shi cewa "gobe zanje gurin Barde kawai a daura mata aure da shaho,
a kasalance Baffa yace "Haba malam!!
yanzu babu wata mafita sai wannan,
mafitar kenan, kuma kaki bamu hadin kai,
cike da Hikima irin ta mai ilimi Aisha tace "to me zai hana ya aureta har lokacin da zaka samu kudin da za'a kaita gida sai ya saketa, ta tafi,
yauwa mai babban suna kin kawo shawara Baffa ya fadi yana gyara zama,
yanzu kinga sai kije kima ma'u bayani gobe,
cike da mamakin irin tsoron da yakewa ma'u tace "babu matsala, in ka amince wannan duk mai sauki ne,
da wannan suka tsaida shawarar yadda zasuyi su taimaki marainiyar Allah daga sharrin ahalin shaho,
sam basu da masaniyar halin da zata shiga yafi wanda shaho zai sanyata,
wannan shine mafarin shigar baiwar Allah Atika cikin cakwakiyar rayuwar da zatayi sanadiyyar rayuwarta.....
A dimauce tayi wurgi da Boddo akan gado tace "samm bazai yiwu ba,
in har so yakeyi ya taimaketa ya saki wata a cikin matanshi ya aura,
in yaso sai ya maida ita bayan ya samu kudin kaita,
kuka ta saki da karfi tace "yanzu duk halaccin da nayi maka da wannan zaku saka min?
ashe ni dazu fadan da nayi da Gambo kaina na jawa,
ashe abin a kaina zai kare..
dakyar ya nutsar da ita hade da yi mata alkawarin bazai taba kusantar Atika ba, sannan yayi mata nuni da irin alherin da zasu samu da Atika,
"nasan kece kika dauki sarkarta! to in kinason sarkar ta zama taki har abada, kuma kinason ki samu mafiyansu in muka kaita gida ki bani hadin kai mu ceto rayuwarta,
alkawarin da nayi miki bazan taba canza shi ba...
ki yarda dani.....
(wannan kalmar nada matukar tasirin ruguza rayuwar macen da ke da saurin yadda).. Allah ka tsaftace mana zukatanmu, dan in mutum nada gurbatacciyar zuciyar da bata yadda da kaddara, to tabbas wannan kalmar ta sama zata sanya mutum cikin hadari in har aka samu akasin dagawar kalmar zuwa ga wani muhallin na daban...
Allah ka taushi zuciyar dukkan matan musulmi su yarda da kaddara in tazo garesu.....
Washe gari tun karfe goma na safe Hardejo ya daura Auren Atika da Muhammadu a sadaki nairah bakwai da sule biyar,
cikin kudin da ya fara tarin tafiyar ya cire ya biya dan yasan Baffa bazai biya ba,
bayan shaidu sun shaida daurin auren,
Hardejo yayi adduo'i sosai na neman tsari a garesu da samun zuri'a a tsakaninsu..
dan shi kam yana hango ma kaninshi alherin kasancewarshi da Atika,
zuwanta garin ma kaddara ce rubutacciya,,
(Abinka da adduar mutanen da, masu tsantseni da tsananin tsoron Allah,
malamai masu tsaftatacciyar zuciya wadanda basu san meye sabon Allah ba,
malaman da Allah ke amsa adduarsu cikin gaggawa saboda tsantseninsu.)......
Juyi yakeyi sosai yana rike da kirjinshi da yake jinshi kamar ya fitar dashi ya yar ya huta,
ba ciwo yakeji ba,
amma abin da yakeji yafi ciwo zafi,
Muryar mahaifiyarshi yaji tana shararo Ashar tana fadin yau lahira zatayi baki,
Da karfi shaho ya kwala kiran sunanta,
gurinshi ta nufa da sauri tana fadin kaji Hardejo ya aurar da matar da naci burin aura maka,
dan tsaki yayi yace "Gambo ke kike ta aure,
bakya ganin halin da nake ciki,
ko bacci bana iya yi,
daga na runtsa fuskar saurayin da na kashe nake gani yana matsowa kusa dani zai illata ni,
mafitar halin da nake ciki zaki nema, ba wai maganar aure ba,
cike da alajabi tace "yau ka fara kashe mutum?
a kiyasin da nayi ka kashe ya kai talatin banda dabbobi,
meyasa zaka sa wannan a ranka,
Katseta yayi yace "wannan na daban ne Gambo,
duk sauran kisan da nayi musu akwai kwakwkwarar hujjar yin hakan ya karashe ido yayi mishi jajur,
kasa daure damuwarta tayi tace "tashi muje gurin Hardejo,
tashi maza,
bazan juri rashinka ba Shaho,
mikewa yayi jiki babu kwari suka kama hanyar gidan Hardejo....
Allah gafurur rahim,
lallai "Bala Shaho" Allah yana sanka da rahama,
wannan abin da kakeji Allah ne ya fara nuna maka illolin abinda da kake aikatawa,
lallai jinin Habibu jini ne na mu'imini,
Adduoin da iyaye da yan uwanshi sukeyi akanka bazai taba barinka kayi sukuni ba,
A farkon zuwan musulunci kauyen nan, naso mu rugumeshi cikin tsaftatacciyar hanya,
amma sam kuka ki,
kuka amsheshi sama sama,
ku ka dinga aikata sabo saboda ance muku ko an aikata Allah na yafewa,
cike da kunan zuci shaho yace "maleee, (sunan da suke ce mishi kenan cikin isgili) yanzu ka fada min abinda zanyi in daina jin wadannan abubuwan da nake ji,
gyara zama malam yayi ya mishi bayanin addinin Allah da duk abinda Allah bayaso,
sannan ya daura mishi da cewa "ta yiwu Allah ya yafe maka saboda kayi abubuwan da kayi a baya cikin rashin sani,
kasan Allah baya kama mutum da laifin da baida masaniya akai,
sannan sharadin tuba,
sai ka tabbatar in ka daina ji da ganin abin da kake gani bazaka sake komawa cikin aikata sabo ba,
'""Bazan sake ba malee"" ya fadi da sauri,
ni kadai nasan irin wahalar da nasha,
to Alhamdulillah Hardejo ya fadi yana murmushi,
sannan ya fara koyar dashi kalmar shahada da kuma istigfari,
ya horeshi da yin istigfari kafa dubu a kullum saboda yana kankare zunubai,
sun dade tare yana koya mishi abubuwa zuciyarshi na samun nutsuwa,
ita dai Gambo zama tayi kamar gunki tana kallon sabon mutum a gurin danta,
da yake ita din mace ce mai son danta, da duk abin da yake so nan take itama tayi mubaya'a,
malam Hardejo ya cigaba da fadakar dasu akan abubuwan da Allah keso da wanda baya so.....
Rayuwar Atika a gidan Baffa, Rayuwace da ta fara yinta kadaran kadaham,
sam ma'u bata kishi da ita saboda sanin yanayin da sukayi auren,
da fari ta fara bijirowa da cewa tunda yanzu Shaho yayi nadama ya shiryu mai zai hana Baffa ya saketa ta koma ta auri shahon,
a lokacin taga ainihin Fillo Hardejo,
dan saida yayi mata wuzu wuzu sannan ta maida hankalinta,
da yaga ta nutsu ne yasa shi ya koma lallashi,
ya cemata ta sani ko tuban muzuru Shaho yayi,
irinsu ba'a gane tubansu har sai an musu gwaji mai karfin gaske,
cikin hikima ya kwantar mata da hankali,
samm baya ko kaunar hango rabuwar Atika da Muhammadu saboda yasan ko babu rayuwarshi Atika zata zame ma dan uwanshi alkhairi.....
****
Ashe dai ma'u baki da hankali ban sani ba kuma ban gama tabbatarwa ba sai yau,
yanzu har wannan tsaleliyar budurwar Baffa zaice