Showing 105001 words to 108000 words out of 184071 words
Chapter 36 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt
wuni?
"Kwana dai Nadeeyah ya fadi murya a dashe,
"umm haka ne,
ba kayi bacci ba?
dama bacci ne ya daukeni kuma bani da charge shiyasa na kiraka saboda tunin sakon..
"yasani sarai ta gani,
danne zuciyarshi yayi yace "mantawa nayi kanwata kuma surukata,
bari in fada miki da baki amaryar Small uncle,
yadda ya fadi murya na rawa ya sanyata kashe wayar da sauri,
dana sani ta dinga yi dan yanzu ya tabbatar mata a kunnenta,
Allah ya sani bata kin Musaddiq amma koda wasa bazata taba iya aurenshi ba,
komawa tayi ta kwanta tunane tunane marasa dadi suka dinga zuwan mata har wani baccin ya dauketa....
A parlor ta zauna da asuba tana jiran ganin Daddy ya dawo daga Salla,
ga mamakinta tare suka shigo da Musaddiq,
dama ita ke tashinshi Sallar asuba to yau taki zuwa,
tasan Daddy ne ya tasheshi,
Har kasa ta tsuguna ta gaida Daddy,
amsawa yayi hade da cewa baki koma bacci ba,
"gyada kai tayi tace
"eh Daddy dama ina son in tambayeka ne,
cikin palon ya shiga ya zauna yace
"zo zauna inji,
kusa dashi taje ta durkusa tace
"Daddy mun gama jarabawa,
dan Allah ina son inje Gombe,
tare zamu tafi da Husna,
fadada Murmushinshi yayi yace "jiya muka gama magana da mamanku,
ku shirya jibi Malam Ali zai kaiku,
godiya sosai tayi mishi ta mike ta shiga kitchen,
shima sama ya wuce dan bacci zai koma saboda lahadi ce babu aiki..
Saida yaji Daddy ya rufe kofar dakinshi sannan yayi saurin zuwa kitchen din,
tsaye ya sameta a kofar shiga kitchen din tana jiran su shiga daki itama ta fito ta shige daki,
Tana ganinshi tayi saurin juyawa zata koma ciki,
shan gabanta yayi da sauri tsayinshi yayi mata rumfa babu abin da take gani a gabanta sai shi,
jan hijab dinta tayi ta rufe bakinta tace
"zanyi aiki ne,
"nima shi zanyi ya fadi yana kwaikwayonta..
Gefenshi tabi zata wuce taga yasa hannu ya tare gurin,
marairaicewa tayi tace "dan Allah ka matsa,
ko baka san Daddy ya karya da wuri?
nade hannuwanshi yayi yana murmushi yace
"sai kin yarda muyi tare,
gyada mishi kai tayi alamar amincewa,
yauwa ya fadi hade da jan hannun jallabiyar shi,
dankali ta debo ta dauko abin ferewa guda 2 ta mika mishi daya,
karba yayi yana dariya yace
"Allah sa dai kar in yanke,
"in ka yanke zaka hakura ai ta fadi itama tana dariyar,
"har so kikeyi in yanke ko?
"Kai ka fada nidai bance ba!
"Kin ce mana,
ya fadi a shagwabe kamar karamin yaro,
dariya tayi hade da tattara dankalin ta juya mishi baya ta cigaba da aikinta,
"An fada miki sakona??
Wani irin faduwar Gaba taji da ya jefo mata tambayar,
bata samu bakin amsashi ba ta cigaba da aikinta hannunta na rawa,
Gabanta ya dawo yasa hannu ya dago fuskarta,
da sauri ta runtse idonta tace
"wani sako?
In abinci ne kasan yanzu zan gama,
"uhm ga acici ko?
To wannan sakon yafi cikina muhimmaci,
Hilal bai fada miki komai ba?
Ya karashe tambayar cike da kasalar da soyayyarta ta sakar mishi,
turo baki tayi hade da ture hannunshi tace
"ni bai fada min komai ba,
hannu yasa a aljihu ya dauko waya ya fara latsata,
da sauri ta daura hannunta kan wayar tace
"Dan Allah yaya Musaddiq ka bar wannan maganar,
yin soyayya ni da kai ba abu bane mai yiwuwa,
"dalili??
Ya tambaya fuskarshi ta nuna alamun damuwa,
rasa abun ce mishi tayi kawai tace
"saboda inada wanda nake so, zoben dake makale a hannunta ta nuna mishi tace wannan zoben alkawari ne,
kuma kasan babu kyau karya alkawari,
Hannunta ya rike a hankali yana shafa zoben zuciyarshi kamar zata soye saboda azabar radadin da take yi,
iya karfinshi yasa ya fincike zoben a hannunta,
tana kallonshi ya sa hakori ya karyashi yayi wurgi dashi ta window,
kallonta yayi da wani irin yanayin da bata taba gani a tare dashi ba yace
"koma waye saidai yayi hakuri dan ba samunki zaiyi ba,
ke tawa ce ni kadai,
kin gane ko?
Kasa tayi da kanta hawaye ya fara zubo mata tace
"kayi hakuri, ina sonshi sos----
*Nadeeeyah....*
ya fadi da karfi rai a bace kamar namijin gaske,
sautin kukanta da yaji ne ya sa jikinshi mutuwa,
hannu na rawa ya dago fuskarta ya fara share mata hawayen,
"kiyi hakuri ki daina kuka,
bazan iya jin bakinki ya furta san wani bayan ni ba,
bazan jure ba,
rage murya yayi yace
"dan Allah ki soni ni kadai,
kamar dada ingizo kukanta yayi saboda bata son ya matsa su shiga cikin matsala tare,
ganin yayi mata tsawo sosai ya sanyashi rage tsawonshi daidai fuskarta,
"Nadeeyah----
"dan Allah kayi hakuri ta katseshi cikin kuka,
"wai dame zan hakura ne?
ya za'ayi in hakura da abun da nake so,
kin san bazai yiwuwu ba,
ya karashe yana daura hannunshi a saman idonta,
"ki daina min kuka, bana so,
in ba so kikeyi inyi ba nima,
kiyi hakuri kinji?
ki manta dashi ga dan uwanki,
kinsan nafi sonki,
kuma kema kina sona,
zaki fi kula dani,
abinci na, komai na,
"Ni bana sanka ta fadi tana goge fuska da hannunta,
saboda shaukin so dake dibarshi baisan sanda ya hada jikinshi da nata ba ya kankameta hade cewa
"zaki soni sosai,
Fiye ma da kanki Ma...
Fiye da komai a duniya...
lumshe idanuwanshi yayi ya cigaba da fadin
*I love yhu Nadeeyah, more than life it self......*
Innalillahi wa inna ilaihir rajiun.....
maimata Kalmar Mummy tayi sau uku tana tafa hannun cike da mamaki da takaici.......
Mrs Tijjani Shattimah......
[05/04 10:42 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 5⃣4⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Na shiga uku ni Zainab!
yau me zan gani a cikin gidana,
Da sauri Musaddiq ya mike har takalminshi daya na fita a kafarshi yace
"me kika gani Mummy?
"Ubanka na gani ta fadi a harzuke,
abin da kukeyi kenan Musaddiq?
yau ni na shiga uku na lalace,
Oooh wato shiyasa kullum kike hanyar dakinshi da nufin tashinshi a bacci,
ashe zuwa kikeyi ki koya mishi yadda mace da namiji suke jiyewa kansu dadi,
yanzu Nadeeyah har kinyi girman da zaki koyawa namiji yadda zai dinga yi miki kiji dadi,
*DANKARI!*
lallai wannan abun babba ne,
"Wai Mummy me ya faru ne? babu abin da mukayi fa,
kawai ina taya----
zan ci maka mutunci in ka sake yi min magana,
wallahi kana cewa takk zan kwada maka mari,
sakarai wanda bai san inda yake mishi ciwo ba,
maza ka biyoni....
kallon Nadeeyah dake tsaye tana share hawaye tayi tace
"To munafuka maza ki wuce daki ki jirayi hukuncin da zan miki, yar iska mara mutunci,
Rai a bace Musaddiq yace
"ki daina zaginta Mummy,
me tayi miki da zafi har haka kike kiranta da munanan kalamai,
haba....
"Bance karka sake samin baki ba, zo ka fita ka wuce sama gani nan zuwa,
Saida ya bari Nadeeyah ta fita sannan shima ya fita ya haye sama yana kunkuni dan shi samm baiga abin da sukayi ba.....
"Ashe yarannan Iskancinsu sukeyi,
wallahi da wani ne yazo ya bani labarin cewa yaga Musaddiq da mace a yadda na gansu wallahi bazan yarda ba,
dan rashin kunya a cikin gida,
ita kuma dan ta gama zama yar iska harda kankame wuyanshi....
*Zainab....*
Daddy ya daka mata tsawa da karfi dan yaga tana neman wuce gona da iri,
shuru tayi tana hucin bacin ran kalaman da ta jiyo danta da ta gama shirin kece raini dashi yana fadawa Nadeeyah,
Nadeeyar Adamu mai gadi!
da sauri ta runtse idonta dan wallahi tuno abun ma mugun taba zuciyarta yakeyi,
kallon Musaddiq Daddy yayi fuska babu alamun wasa yace
"ka fada min gaskiya,
menene tsakaninka da Nadeeyah?
Nasan ko kai zaka iya rungumar mace Nadeeyah bazata taba kusantar namiji ba saboda i have full faith in Suwaiba's upbringing,
Shin me mahaifiyarka ta gani wanda ya sanyata yin wannan tunanin,
kamar jira yakeyi mahaifinshi ya kai aya yace
"Daddy dan Allah ka aura min Nadeeyah,
wallahi ina santa sosai,
"Bakin cikin kiran Sunan Suwaiba da Daddy yayi da kuma na kalaman Musaddiq su suka hadu suka dugunzuma zuciyar Mummy ta sakar mishi wata irin kazamtaciyar ashariya,
kallo daya Daddy yayi mata tayi saurin dauke kai idanuwanta sunyi jaa saboda bacin rai,
Maida hankalinshi gurin danshi yayi Zuciyarshi fess saboda dama abin da yake ma danshi addu'a kenan,
"ka nemi soyayyarta? Daddy ya tambayeshi cikin sakin fuska,
"Eh Daddy, ita ma tana sona,
"Karya kakeyi wallahi,
inaji tana cewa bata sanka,
Yadda Mummy tayi maganar ya sanya Daddy dauke kai dan dariya ta kusa kufce mishi,
jiya bata barshi ya runtsa ba saboda labarin Faida yar gidan *Hon Danjuma Diriss*,
ta matukar cin burin bikin,
shi kuwa a gurinshi sam bayasan danshi yayi auren
*MATAUL HAYAT*,
irin su Nadeeya ya dade yana fata,
sai gashi Allah ya kawo mishi cikin sauki,
waya ya daga ya kira number Husnah yace suzo tare da Nadeeyah,
Mummy najin haka ta dauko wayarta ta tura text din gargadi zuwa ga Nadeeyah,
A lokacin da ta tura text din a lokacin Nadeeyah da Husnah sun kusa taka step din karshe.....
Cikin hikima Daddy yayi musu Nasiha ya nuna musu muhimmancin aure at early age,
sannan ya kalli Nadeeyah yace
"Nadeeyah kina da wanda kike so? Aure zan muku ke da Husnah...
A kunyace taja hijab dinta ta kasa hada ido dashi,
ya za'ayi ta iya furta bata san danshi na cikinshi,
Daddy,
Hilal,
Anty Reemah,
Musaddiq,
Anty Raly,
uwa uba Husnah da bata banbanta kanta da ita,
duk a cikin zuriar mutumin dake gabanta yana tambayarta ko tana san danshi,
ta ina zata iya butulce mishi,
a cikin jerin da ta lissafo babu wanda bai taka rawar gani cikin rayuwarta ba,
kuma Daddy ne ya samar dasu,
dago kai tayi suka hada ido da Mummy ta harareta hade girgiza mata kai,
dauke kanta tayi da sauri ta kalli Daddy dake sake jefo mata tambayar,
gyada kanta tayi a hankali alamar eh,
wanene shi?
Dan Musaddiq yazo min da zancenki,
in wani kike so shikenan sai sawun giwa ya taka na rakumi,
wani irin girma ya kara a idonta ta kasa bashi amsa,
"Ko Musaddiq din kike so?
Hannun Husnah ta rike sosai ta kasa dago ido ta kalleshi bare ta bashi amsa,
sau uku yana tambayarta tana yin shuru,
dariya yayi yace su tashi tafi,
Nadeeyah har tana tuntube da kofa tayi saurin fita,
Maida kallonshi gurin Musaddiq yayi yace
"To Malam ka shirya ma aure?
nawa ka tara daga albashinka,
nidai kasan ba ruwana nima da kaina na auri matata ya karashe cikin zolayar dukkansu biyun,
Ganin ya saki fuska yasa Mummy zama a kasan kafarshi,
"Dan Allah Daddy ka rufa min asiri,
bai kalleta ba yace
"Allah ne mai rufawa Zainabu,
me ya faru?
Hawayen bakin ciki ta fara yi tace "Yanzu kai farin cikinka ne danka guda daya tiloo ya kare anan,
tsakani da Allah duk yadda manyan abokanka ke miko ya'yansu mata gurinka domin shi, sai kuma suga ya kare a gurin yar Mai gadi,
yadda ta fadi abun ya soki Daddy Matuka,
nan da nan fuskarshi ta sauya yace
"akan Nadeeyah zan iya bata miki rai wallahi,
idan kika sake kiranta da yar mai gadi a matsayinta na jininki wallahi hukuncin da zan miki ba mai dadi bane,
cikin bacin rai ta mike tace
"ba jinina bace,
uwarta ce kadai jinina,
kai kasan asalinsu ne,
wa yasani ma ko ubanta barawo ne ya shigo cikinmu aka bashi aure,
wallahi bazan yarda in hada jini da marasa asali in samu bara gurbi cikin zuri'ata da zanyi tunkaho da ita ba,
"wallahi bazata sabu ba,
ai nima ina da hakki akan shi,
saboda haka wallahi indai ni na haifeshi bai isa ya auri Nadeeyah ba,
Sam Daddy bashi da saurin hannu amma tabbas a lokacin yayi niyyar dauke fuskar Mummy da mari,
a hankali yace
"ke kika haifeshi,
ke kuma nike iko dake,
wallahi tallahi in har kikayi abun da auren nan yaki yiwuwa sai kin bar min gidana,
kinga sai kowa ya nuna ikonshi,
Asali kuma Nadeeyah bata da wanda ya fini,
a yanzu na zama asalin Nadeeyah,
ni ne ubanta,
ni ne danginta da komai nata,
sai ki je maiduguri ki binciki Asalin Alh Garba kyari mai fata,
kallon Musaddiq yayi yace ka tashi kaje ka fara shiri daga bangarenka,
ni a bangarena bani da matsala...
jiki a sanyaye Musaddiq ya mike ya fita daga dakin,
bai taba tunanin zai samu wannan matsalar ba,
gashi kuma har ga Allah yana son Nadeeyah bazai iya rabuwa da ita ba,
ga kuma Mummy zata yi mishi karan tsaye cikin rayuwarshi,
tunane tunane ya dinga yi ya rasa mafita ya dauki wayarshi dan kiran Hilal,
a kashe wayar take dan haka ya kwanta yanata sakar da bata da karshe....
Mummy kuwa tana fita dakinta ta wuce cike da bakin ciki ta daga waya ta kira Radiya da Raudha da ta dawo gida weekend tace su kira Raliya suzo su sameta a gidan Goggo,
jin yadda muryarta ke rawa suka san ba lafiya ba,
ko wacce hankali tashe ta shirya tafiya gidan Goggo...
"Radiya ina zaki da sassafe?,
ko abun karyawa bakiyi ma su Umma ba kuma kinsan ba ita kadai bace,
shekeke ta kalleshi tace
"ni ma uwata ke nema na,
ko bani da ikon amsa kiran,
su tashi su daura da kansu tunda dai suna da hannu,
shikenan ni bani da sukuni saboda umma tazo,
a'a wallahi bazai yiwu ba,
Raees babban danta ne ya shigo yace
"Mama wai inji Umma tace ki kawo mata ruwan zafi zata sha magani,
wani dogon tsaki taja tace
"maza jeka gurin Gyatum kace ta kai mata,
hijab ta dauko tasa tana kunkunin da tun zuwansu gidan takeyinshi,
Mikewa mijinta yayi ya kira kanwarshi Haleesah yace "tazo tayi ma Su umma abinci,
sam baya jin dadin abin da Radiya kema yan uwanshi dashi kanshi,
hakuri kawai yakeyi saboda darajar mahaifinta,
yana shiga kitchen ya tarar da wata yar budurwa wacce shekarunta bai wuce sha tara ba. tana tsaye tana taya gyatum aiki,
Da sauri gyatum ta gaisheshi ya amsa yana kallon yarinyar,
itama tsugunawa tayi har kasa ta gaisheshi,
kamanninta da gyatum shi ya tabbatar mishi yarta ce,
saidai wannan din bak'inta mai kyau ne,
da dara daran ido farare tass ga kyawun diri,
har zai fita yace
"Gyatum wannan yarki ce?
Murmushi tayi tace "eh Alhj,
auta ta ce,
a gurin kanwata take a jos,
a can take karatu,
yanzu ma tazo hutu ne tazo tayani aiki,
gyada kanshi yayi yace
"Dan Allah ku taimakeni ku hada ma su Umma abun karyawa,
in san samu ne ma su samu tuwon laushi,
da sauri gyatum ta mike tace
"har sai ka roka,
Bar wanke wanken nan Fatima ki fara hada kayan karyawa,
Cike da jin dadi ya fita dan ko abincin baiyi dadi ba yasan zai fita kunyar mahaifiyarshi da kannenta...
Cikin kwarewa Fatima tayi miyar kukar da taji daddawa da dagargajajjen naman kaza, sannan ta tafasa kifi kadan ta sa citta da karumfani da tafarnuwa ta dakesu tsaf ta juye a cikin miyar,
nan gida ya kaure da kamshi, tana gamawa suka shirya komai cikin cooler gyatum ta dama musu kunun gyada ta fito da garin kosai ta kwaba tasa kwai da albasa ta soyashi gunin dadi,
manyan Coolers gyatum ta zuba abincin aka kai musu sannan ta zuba a kananan coolers ta ajiye wa mai gidan a dining,
saboda farin cikin ganin tuwon malmala biyu Umma ta cinye,
cike da jin dadi Haleesa ta kalleta tace
"yau Umma taci abinda take so, san samu kullum da safe da dare a dunga miki tuwo,
to hakan bazai yiwu ba,
hidimar Maman Raees tafi karfinta,
harara Indo kanwar Umma ta jefawa Haleesa tace
"yau da tayi kasheta aikin yayi,
Dariya Haleesa tayi tace
"waya fada miki ita tayi,
ita bata gidan ma,
mai aikin gidan ce tayi,
a daidai lokacin fatima ta shigo kwashe kayan abincin,
albarka suka shiga sa mata har ta gama ta fita,
umma dai da ido ta bita,
a kullum tana ma danta adduar samun mace ta gari ba mai kyale kyale irin Radiya ba,
yanzu din ma bazata fasa ba,
ganin da tayi wa Fatima na farko taji ta shiga ranta,
saidai bazata tilasta shi ya nemeta ba,
za dai ta cigaba da addua,
dan tabbas danta bashi da mace a gidanshi......
*Wai ina Hajiya Goggo Ma'u ne*
Bangaren Goggo kuwa tunda Anni ta tare kullum cikin kunan zuci take,
tayi asirin,
tayi tsafin duk a banza saboda yin auren Baffa ma kadai karyewar alkadari ne,
ga yawan abinci sadaka da Anni keyi kusan kullum domin nema musu tsira ranar Gobe kiyama,
Tunda Goggo taga asirin nata yaki aiki saidai suyi ta cin kudinta sai ta hakura ta fara kunno wutar tashin hankali da masifa a gidan,
idan Allah yasa ranar a dakin Anni Baffa zai kwana tofa babu bacci,
dan ta dinga dukan kofar da muciya kenan,
abun ba karamin damun Baffa yakeyi ba,
Anni ke hanashi magana ta nusar dashi yanzu tsufa yazo,
ba lokacin sa'insa bane,
lokacin da zamu koma ga Allah ne,
haka zasu mike suyi ta Sallah har ta gaji ta koma daki tana zage zage kamar wata yarinya,
Yau ma kamar Kullum Anni na tsakar gida ita da mai aikinta suna girkin sadaka ,
Shinkafa ce da wake sai lettuce da su tumatur,
suna gamawa aka fara zubashi a farantai ana fita dasu waje almajirai na rige rigen karba,
makota masu karamin karfi suma suka shigo da robobinsu aka zuba musu,
sunyi nisa sosai gurin rabo Goggo ta fito da bokitin fenti karami, fitsari ne a ciki ya kai rabi,
nan ta doshi katuwar tukunyar ta antaya fitsarin a ciki,
Da kyar Anni ta iya danne bacin ranta dan ta harzuka matuka,
rufe tukunyar tayi tace
"Harira, ki kira almajirai su kwashe abincin nan su kai ma dabbobi yau ranar tasu ce,
tana kaiwa nan tayi hanyar dakinta,
gabanta Goggo tasha ta dinga dura mata zagi,
ita dai Anni dariya kawai takeyi tana fadin nagode,
"ni yanzu ai bana fada,
fada na yara ne da kuma wanda bai samu abinda yake so ba,
ni kuwa