Showing 171001 words to 174000 words out of 184071 words
Chapter 58 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt
ta koma...
Anty Reemah da Anni kuwa faďa suka rufeta dashi wanda ita kanta tasan na daďi ne....
Sun dade rungume da Anty Reema tana tambayar ina Zainab?
Cikin kuka Anty Reemah tace "Tayi Fushi,
kika manta da ita ma bare ita, tuni ta mance dake,
tana can gida suna jarabawa ne shiyasa ban taho da ita ba...
Dakyar Nadeeyah ta iya gane Mummy dasu Raudha,
har kasa ta tsuguna ta gaida Mummy wacce fuskarta tayi faca faca da hawayen farin ciki,
rungumae Nadeeyah tayi wani irin kamshin sanyi ya daki hancin dukkaninsu wanda tun zuwansu duniya har kawo yau basu taba jin irinshi ba...
Dafa kafaďunta taji anyi ta raba jikinta da Mummy ta waigo tana murmushi tana kallon matar cikin rashin fahimta,
"Nadeeyah,
dan Allah ki yafe min,
yadda ta haďe hannayenta biyu tana kuka sosai yasa Nadeeyah rike hannun tace
"Me kikayi min, baiwar Allah? Wallahi na yafe miki duk da ban sank----
Badariyyah zanyi fitsari,
Hannafi ya katse Nadeeyah yana matse cinya dan fitsarin ya fara zubar mishi,
Zaro ido Nadeeyah tayi,,
"Badar!!
Ke---ce... ta faďi cikin rawar murya,
nan take wani tsagoron tsoron Allah ya tsarga a zuciyar Nadeeyah,
tana kallon Badariyya ta ďaga yaron da yayi faca faca da fitsari tayi famfon waje dashi...
Jikin Papy Nadeeyah ta kwanta bayan ya gama mata faďa tana tambayarshi Ruwaidah...
"Tana can gurin su Jamal, a can take makaranta...
ya bata amsa yana mai jin dadin ganinta...
Husnah da ta tura mijinta daki saboda mijin Badar, ta fito kamo hannun Nour da Abi taga parlon a nutse sai manyan mutane masu rawuna dake zaune kowa na kasa a nutse,
Gefen da Papy yake ta kalla ta hango fuska kamar ta Nadeeyah,
tasan dai ta baro Maleekah a cikin daki tana sallah, to wacece wannan?
Karasawa tayi ta tsuguna ta gaida bak'in sannan ta kai dubanta kan Nadeeyah,
"Nadeeyah...
ta faďi da karfi har saida Hafeez ya jiyota..
Da sauri ya buďe kofar ya fito yana dube dube yana faďin
"Me ya sameta?,
duk tunaninshi Nadeeyar Hilal ce,
Ganinsu kankame da juna yasa shi saurin matsawa kusa dasu dan ya gasgasta idonshi...
"Yaya Hafeez..
ta faďi tana nufo inda yake,
Share hawayen dake idonshi yayi ya juya zai koma inda ya fito,
Da gudu ta bi bayanshi ta rungumeshi,
"Am sorry,
dan Allah kayi hakuri,
rufe idonshi yayi hawaye na mishi ambaliya..
gabanshi ta dawo tace
"Dan Allah yaya..
Share hawayen yayi yace
"In kowa yayi deserving haka ni banyi ba Nadeeyah,
in akwai wanda ya kamata yasan inda kike to nine,
meyasa zaki bar min tabo a raina?,
kullum ina ganin kamar gazawata ce tasa kika bace,
samm na kasa rike zumuncinmu..
Meyasa zaki min haka?
Sake kankameshi tayi tace
"Nasan ban kyauta,
haka kaddararmu take,
Dan Allah kayi hakuri Yaya....
sunfi minti biyar suna tattaunawa kafin ya sauko ya fara share mata hawaye....
Tun fitowar Hafeez Sarki Tidjani ya mike fadawan shi suka fara yan yameshi,
haka itama Shareefah da hirar Daddy da Anty Saude ta hanata jin komai ta mike cike da firgicin ganin Hafeez...
"ADAMOU YALLO...
sarki ya faďi cikin rawar murya,
Adamou,
innalillahi wa inna ilaihir rajiun, ashe kana nan da ranka Adamou?
Ajiye sandar hannunshi yayi ya isa gurin Hafeez,
sai a lokacin ya dawo hayyacinshi ya fahimci cewa shekarun da yawa Adamou bazai kasance haka ba,
fuskar Hafeez ya shafa yace
"Ina Adamou?
Mikewa Papy da Daddy sukayi suka isa gurin cikin girmamawa,
"Ranka ya dade,
ba Adamu bane,
wannan Hafeezu sunansa,
"Eh na gane yanzu,
ina Adamoun yake,
nasan tunda naga gudan jininshi dole shima ya kasance a kusa....
Garammm....
gaban mutanen parlon ya faďi,
Sai a lokacin yawancin su suka tuna cewa sunan buzu mai gadi marar asali da galihu
*Adamu*,
Daddy ne yayi saurin cewa "Kwarai Adamu shine mahaifin Hafeezu da Nadeeyah ne,
Allah dai yasa lafiya,
ya karashe cikin zullumi ko Adamun ya taba yi musu wani mummunan abu ne,
"Lafiya kalau sai alheri,
Shareefah ta faďi idonta cike da kwallar farin ciki,
"Ina Yayana Adamou??
Dan Allah ku nuna min shi,
ku nuna min shi ko zan samu salama a cikin zuciyata....
Kallon kallo aka fara yi a cikin parlon,
Papy ne yayi karfin halin cewa Sarki ya zauna sai ayi maganar a nutse,
Kamo hannun Hafeez yayi suka koma inda yake zaune,
share kwallar da ta ziraro mishi yayi yace
"Dan Allah ku kira min Adamou, ashe munada rabon sake ganin juna...
Anya ba kuskure kukayi ba?
Wannan buzu Adamu, mai gadi ne, bashi da wata alaka da sarauta,
inajin kamanni ne kawai,
kunsan babu yadda Allah bai iya yi cikin halittarshi...
Baffa ne ke maganar cikin taka tsan tsan dan kar ya bata ran Sarkin...
Murmushin takaici Shareefah tayi ta nuna Hafeez da hannu tace
"In dai wannan jinin Mai gadin ne, to tabbas jinina ne,
idan yayana yayi nisa dan Allah ko zan iya samun hotonshi saboda in tabbatar da zancenku in karyata kaina...
Cikin azama Daddy ya tashi zai nufi sama,
kafin ya karasa Hafeez ya dakatar dashi ya ciro wallet a aljihunshi,
kananan hotunan iyayenshi ne suka bayyana,
da sauri ya mika mata...
*Pappa.....*
Ta faďi cikin kuka dan fuskar mahaifinta ta gani a cikin ta dattijo Adamu,
shi kuwa Hafeez fuskar Yareemah Adamou Sarki Tidjani ke gani a idonshi,
Dan Allah ina yake,
Ku faďa mana inda yake??
Sarki ya tambaya cikin ďaga murya...
Da sauri fadawa suka shiga faďin Allah ya huci zuciyarka...
Baya tare damu,
dan uwanku ya rigamu gidan gaskiya,
ya tafi inda duk zamu tafi komi daren dadewa,
shin dama shi ďin dan gata ne kuka barshi cikin gararin rayuwa?
Ya ilahi me muka maida *ZUMUNCINMU A YAU*
ace yanzu sai in baka raye za'ayi Zumunci da kai,
To Adamu yayi tafiyar da ganinshi yake da matukar wuya,
Adamu yayi muku nisa,
saidai 'ya'yanshi....
yadda Daddy yake maganar ya sanya Parlon yin shuru, sai tashin sheshshekar kuka....
Cikin matsanancin kuka Shareefah ta zaune a kan carpet tace
"Yareemah shine Gata,
kalmar Gata in aka zo kanshi an disa aya,
Shine ďan Sarkin Agadez
*Diya Muradun Abdallah Yallo* na farko,
shine Yareeman Agadez....
Kaddararshi a nan take,
kaddarar samun magaji a nan Nigeria take,
hannayen Hafeez ta rike tana kuka sosai tace
"Rubutun Allah baya goguwa, Allah bai nufeshi da zama Sarki ba wanda hakan shine muradin mahaifinmu da duk daukacin mutanen Agadez,
lallai sarauta rigar ubangiji ce,
ya baiwa mijina wanda yake ďan uwa ga mahaifinka,
sannan ya hanamu haihuwa dan dama ya tanade ta ne domin ka..
Wallahi Allah dole ya zama abin tsoro da girmamawa cikin mu bayinsa,
domin ya wuce duk yadda muke tsammani,
ku duba kuga yadda ya maida dan sarki wanda ya kamata ya zama sarki bawa, mai gadi kaskantacce a gidan bayin da ya kamata su zasu bauta mishi,
cikin kankanin lokaci ubangiji ke sauya alkalaminsa,
ku dubi nisan Agadez da Nigeria, haka kudurar ubangiji ta ingizo shi nan da taimakon marasa imani da tsoron Allah,
duk dan saboda me?
saboda yasan akwai wanda ya tanadarwa aron rigar sarautarshi,
Lallai zaren kaddara baki ne,
ganinshi sai wanda ya halicci kaddarar kanta,
haďuwar Taheer da Nadeeyah,,
zuwan mu nan domin su biyun duk zaren ne ke janmu ba tare da mun ganshi ba,
Allahu Ahad,
Allahu Samad,
buwayi gagara misali,
mai dauke da rayukan da babu wanda yasan adadinsu sai shi kaďai...
Naji dadi matuka da Allah bai dauki raina ba sai da naga gudan jinina,
rungume Hafeez tayi ta yafito Nadeeyah ta haďesu tana kuka tace
"Ina sauran 'yayana?
Share hawayen farin ciki Papy yayi yace
"ďaya ce ta rage,
Zainab,
tana can Cyprus tana karatu,
ga wacce take rikonta can ya nuna Anty Reemah da hannu,
Kiranta gabanta tayi itama ta rungumeta tana mata godiya haďe yin hamdala gurin ubangiji....
Na faďa muku,
yanzu kun gasgata zancena? Yareemah Suhail ya faďi cike da kasaita,
maida dubansu inda yake zaune shi da 'ya'yanshi sukayi,
a harzuke Daddy ya mike yace
"Kai ku tashi ku fice min a gida,
mikewa Papy yayi ya dakatar dashi yace
"Yau ranar farin ciki ce,
ka bar shi alkhairin ne zai fitar dashi in shaa Allah.....
Labarin irin gatan da Yareemah Adamou ya samu da kuruciyarshi suka shiga basu har kawo sanadiyyar barinshi gida...
sannan Sarki ya faďa musu yadda suke da Adamoun ya kuma nuna Taheer yace
"Wannan shine dan kanina, shima dan uwan Adamoun ne....
Kallon juna sukayi shi da Nadeeyah yayi murmushi haďe da kashe mata ido,
da sauri ta kauda kanta cike da kunya,
dadin da takeji a yau kamar an mata albishir da gidan aljanna...
Ashe Taheer dan uwan Nadeeyah ne na jini, haba kaunar tayi yawa, Taheer baya taba likewa mace haka,
ashe connection din mai karfi ne, Anty Saude ta faďi tana dariyar farin ciki....
Dariya akayi a parlon duk da zuciyar Daddy ta ďan sosu da jin maganar kauna daga bakin Anty Saude.....
Baffa ne ya fara basu labarin irin wahalar da Adamun yasha da kuma haďuwarsu da Mamma Suwaiba har mutuwarsu...
Cike da jin daďi hira ta barke a tsakaninsu...
Har wannan lokacin su Daddy basu san da zaman junior ba dan basu ganshi ba.....
Su Mummy bayin Allah suna can dai a rabe har lokacin,
sunga karshen asali,
kowacce a cikinsu tana cike da dana sanin rayuwa..
Raliya da Reemah ne kadai ke kai kawo a kitchen suna hada hadar haďa lunch,
sai Husna, Maleekah da Nadeeyah dake tayasu,
Maleekah da Nadeeyah hira sosai sukeyi kamar sun dade da sanin juna,
gasu dukkansu wayayyu babu wacce ke jin kunyar yin magana...
Bayan sun dan taba abinci duk suka nufi waje dan yin Sallah..
su kuma matan suka nufi daki dan yin tasu a can...
Gyara parlon Husna da Nadeeyah sukeyi suna hirar yaushe gamo, labarin abubuwan da suka faru bayan bata nan take bata, ga mamakinta bata ji inda tace "Musaddiq yayi aure ba, sharewa tayi ta kauda tunaninshi a ranta domin yanzu tana son tayi moving forward...
rashin ganinshi a cikinsu ya tabbatar mata yana can yana rayuwarshi cikin jin dadi....
Duk wannan budurin da akeyi Musaddiq na cikin daki ya kure volume suna game shi a dole bayason jin wani abu da ya shafi su Badariyya....
Ganin little Nadeeyah tayi bacci ne ya sashi gyara mata kwanciya ya shiga ya watsa ruwa,
kananan kaya yasa wadanda suka fitar da kyawunshi sosai,
yanzu girma ya sanya Musaddiq ya zama moderate,
wannan kibar duk babu ita,
sai tsawo sosai da dan murjajjen jiki,
kwantacciyar kasumbarshi ya taje ta kwanta lup a fuskarshi, turaruka masu kamshi ya feshe jikinshi dasu sannan ya kashe wutar dakin,
Sallah kawai zanyi in nemi abinci,
abinda ya faďi kenan haďe da murďa kofar dakin ya fito....
Ta sama ya leko yaga ko an ragu a parlon,
ganin bakowa ya sashi fara tafiya cikin kasaita dan isa gurin steps din,
kamar ance ya sake kallon gefen console,
Tsaye ya hangota ta maida gashinta gefe tana kokarin cire dankunnenta a jikin rigarta,
Hannayenshi biyu ya daura akan karafen da ke kewaye da saman yana kokarin ganin fuskarta ta mudubin...
Haaaa...
ta faďi bayan ta cire dan kunnen, maida gashin baya tayi ta naďe shi ta goge fuskarta da hannunta sannan ta fara kokarin nade gyalen,
jin kamar wani abu yabi ta kunnenta yasata noke wuyan dayan dan kunnen ya sake makalewa, wannan karan ya shiga da karfi,
ajiye gyalen tayi ta fara dambe dashi tana tsaki....
Tunda fuskarta bayyana a gareshi ya shiga rudani,
da sauri ya mutstsika idonshi yaga ko gizon da ta saba yi mishi ne,
ganin dai mutum ce a tsaye ya sashi sake dubawa da kyau ko Maleekah ce,
yadda yaga tayi da baki kamar zatayi kuka yasa shi lumshe ido kirjinshi sai lugude yakeyi...
"Husnaa...
yaji ta faďi da muryar neman taimako,
A hankali kafarshi ta fara janshi,
shidai yaki gasgata idanuwanshi wadanda suka tara ruwa a lokacin..
Saura kaďan ya isa gareta yaji wani kamshi mai dadi acn gurin na bugo mishi,
zuciyarshi ce ta ingiza hannunshi ya dagoshi da niyyar taimaka mata...
Mamma...
we am back..
Juyowa tayi da sauri ďan kunnen ya fita a kunnenta gaba ďaya,
kyammm..
idanuwansu suka makale cikin na juna,
nan fa zuciyoyin da suka daďe suna kewar juna suka fara zubar da hawaye a junansu,
daga Nadeeyah har Musaddiq babu wanda jikinshi baya rawa, babu kamar Musaddiq da a lokacin yake jinshi kamar mutum mutumi,
Cikin karfin hali da dauriya Nadeeyah ke kokarin raba idonta da nashi amma sam zuciyar da ta daďe tana ďoki da marararin ganin mahaďinta taki bata haďin kai.....
A tare Hilal da Musaddiq suka shigo parlon suna ďan taba hira,
hirarsu makalewa tayi da sukayi arba da abinda ya sosa ran Taheer..
Hannun da Musaddiq ya ďaga yasa a gefen rigarta ya cire mata dan kunnen har lokacin bai dauke idonshi cikin nata ba...
Badariyyah data fito daga kitchen ta tsaya kallonsu zuciyarta sai rawa takeyi hawaye ya shiga yi mata ambaliya..
a yanzu tasan mai gadi ma rayuwarshi tayi mata nisa bare Musaddiq..
Mamma..
Junior ya faďi yana girgiza mata riga,
a firgice ta kalleshi cikin sanyin murya tace
"Ummm,
ina kaje?,
"Munje yawo ni da namesake,
yace shima sunan mu ďaya haka ne Mamma?
Gyaďa mishi kai tayi ta karbi ledar hannunshi ta ajiye ta wuce kitchen da ďan gudu gudu tana maida numfashi.....
Bayanta Junior ya fara kokarin bi Musaddiq ya rikoshi da sauri,
dafashi yayi ya tsuguna kirjinshi na dukan uku uku yace
"My Twinny,
Zaro ido Junior yayi yace
"Yayyy
*MMK* right?
Yess...
Musaddiq ya faďi jikinshi samm babu kuzari..
Kallon inda Taheer yake tsaye yayi ya taho da sauri yace
"Daddy, zo kaga strangern da na gani a Hallmark,
i told u he is just like me,
har gaban Musaddiq ya janyo Taheer yace
"Kaga idonshi irin nawa,
i will not lv here sai nayi grabbing face dinshi,
sketch din da nayi baiyi kyau ba....
*Daddy.....*
Musaddiq ya dinga maimatawa a cikin ranshi,
dakyar ya iya dago kanshi suka haďa ido da Taheer,
nan take halittar nan marar dadin faďi a baki ta shiga motsi a zukatansu...
Ganin haka Hilal ya karaso gurinsu da sauri yana murmushi,
"Hey Kyari,
ka ganeshi, Uncle din su Nadeeyah,
ashe all this while Nadeeyah is with him..
sun kula da ita sosai da gudan jininka,
Janyo Junior yayi kusa da Musaddiq ya haďe hannayensu guri ďaya yace
"He is ur blood Kyari,
ur flesh and blood..
"Tell him ur name,
Hilal ya sake cewa ma Junior cike da doki,
*MUKTHAR HILAL MUSADDIQ KYARI* a.k.a *MHK TAHEER* ya karashe haďe da damke hannun Taheer....
Runtse ido Musaddiq yayi yanajin dukkan nauo'in biyu a cikin zuciyarshi,
farin ciki da akasin haka,
a hankali ya buďe idonshi ya sake tsugunawa a gaban Junior, janyoshi yayi ya rungumeshi tsamm a jikinshi..
Wasu zafafan hawaye ne suka shige tsere tsakanin idanuwanshi zuwa kuncinshi,
da sauri junior ya raba jikinshi da nashi saboda jin ruwan hawaye da yayi a kafaďunshi,
"Hey twinny, ya faďi a dan tsorace yana ja da baya zai koma gurin Taheer,
rike hannunshi Musaddiq yayi yana girgiza kanshi wasu hawayen na fitowa kamar ana ingizo su,
"Daddy...
Junior ya fara faďi yana kokawar kwace hannunshi cikin na Musaddiq,
a tsorace yake matuka dan bai taba ganin zubar hawayen babba ba,
Cikin sanyin jiki Hilal ya tsuguna a gaban junior,
dayan hannunshi ya kamo yace "My dear he is ur Dad too,
ur biological father,
go to him,
he is *MUSADDIQ KYARI*
His name is connected with urs...
Juyawa Taheer yayi wani makoko ya tokare kahon zuciyarshi,
hawayen da yaketa matsesu suka zubo daga idonshi..
"Noo...
Junior ya faďi haďe da fisge hannunshi daga dukkansu,
da gudu ya koma gurin Taheer ya rungume kafafuwanshi ta baya,
"Dis is my Dad,
his name is also connected with mine,
"Daddy plss tell them u are my biological father ya karashe bayan ya dawo gaban Taheer ya tsaya..
Daga kai Taheer yayi sama ya share hawayen da ya sake taruwa yana neman zubo mishi, dan kar Junior ya gani,
ďagoshi yayi ya daurashi a kirjinshi yace
"He is ur father Sweetheart,
i'm ur father and ur name sake is ur father too,
we are all ur Dad..
"Only one is my biological,
who among the three?
ya tambaya idonshi kyamm akan Taheer,
Runtse ido Taheer yayi maganar da yake kokarin yi ya kakare mishi a makoshi...
Share hawaye Anty Saude tayi ta karaso ciki da sauri ta karbi Junior,
"Ina ka shiga My dear,
ko abinci baka ci ba, and all ur so called fathers basu damu da su baka ba,
duk kace bakayi dasu muje kaci abinci..
Kwantar dashi tayi akan kafadarta ta wuce cikin kitchen dashi,
tayi hakan ne dan ya samu nutsuwar sanin ainihin mahaifinshi,
duk nauyin Junior a wannan lokacin Anty Saude ji tayi yayi mata shafal,
zaunar dashi tayi akan kujera ta kwalawa Nadeeyah da ta hangota acan baya kira....
A gaggauce Mummy tabi bayan Anty Saude itama idonta cike da kwalla,
samm bata damu da ganin su Daddy tsaye curko curko bayan gama kallon abinda ya faru ba..
Tana shiga ta kankameshi tana kuka mai sauti haďe da sumbatar ko ina na jikinshi...
Cike da kyankyami kamar zaiyi kuka yace
"Momma,
plss lts lv dis house...
Mummy bata damu da kyankyaminta da yaji ba ta sabashi a jikinta ta durkushe gaban Nadeeyah tana kuka tana rokon gafararta,
cikin kuka Nadeeyah ta tsuguna tace
"Dan Allah Mummy ki bari,
we are all humans, we are bound to mk mistakes, walhy ban rikeki a raina ba..
"Kuskurena yakai girman da za'ayi min koma meye,
sakarcina ya hanani hango alkhairan dake tare dake Nadeeyah,
yanzu wannan jikan nawa da kuskurena ya sanya fitarshi bazan taba yafewa kaina ba,
dan Allah kuyi hakuri ta karashe cikin matsanancin kuka....
Su Anty Reemah da suka shigo gurin duk idonsu ya ciko da hawayen tausayi,
Raudha da Radiya ma cike da Kuka suka tsuguna a gabansu suka shiga ba Nadeeyah hakuri...
Hamdala Raliya tayi a cikin ranta sannan ta sake godewa Allah da yasa dukka yan uwanta da mahaifiyarta suka gane kuskurensu...
To kukan ya isa a miko min jikana in bashi abinci,
dariya Mummy tayi ta Saki Junior da yake a matse dama,
da sauri ya koma gurin Anty Saude ya ďane jikinta haďe da kwanciya ya runtse idonshi....
Sai a hankali zai saba,
kunsan yanzu ne ganinku dashi na farko,
sai kunyi hakuri da koma meye...
yadda Anty Saude ke maganar cikin fitar da tsammanin zamanta tare dashi ya sanya Nadeeyah barin kitchen din da sauri,
ta riga ta gama yanke hukuncin zama da Taheer,
babu wani dalili na tausayi ko wani abu da zai canza mata ra'ayinta,
Halaccin da zatayi wa bayin Allahn nan kenan, ta kare rayuwarta tare dasu.....
Gyaran murya Sarki Tidjani yayi yace
"Hukumullahu laa Ajabun, hukuncin Allah ba'a mamaki akanshi,
abin da ya kawo mu daban sai gashi